Join Our WhatsApp Group

SAMAREEN BANAH Book 1 Complete Hausa Novel Document by SAMAREEN BANAH Book 1


SAMAREEN BANAH Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 132298



SAMAREEN BANAH Book 1

Reading Time: 11 Hours

Added On: 13, Sep 2023

Author: Rahma Muh'md Rufa'i Nalele ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07038260028

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 766.92 kb

File Type: txt

Views: 795+

Download: 636+

Last download: 1 hour ago

Description/Story: [10:45PM, 02/11/2016] Rahamat Nalele: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*




*Na Rahamat Muh'md Rufa'i Nalele*

Part 1.....

*Nutsu da kyau me karatu ka karan farkwan labarin nan da kyau kuma kar kayi gigin mantawa. Dan xai temakema wajan gane ya abin xai kasance nan gabah*




Sunana SAILUBAH KASIM.
Ina garin KANO da xama awata unguwa da akekira fage
Ina da shekara ashirin da biyar aduniya wato 25 years

Na kasance mace mace kyakkyawa san kowa in wanda ya rasa
Ni farace soll doguwa me kyan bafali
Ina da hq da breast na 'daukar hankali
Bancika qibaba sannan baxa'a kirani siririya ba
Komai nawa ya ha'du kamar yanda kowace mace takeso ta kasance

Idan na kalli kaina a mirror hmmmmmmm
Dole najah numfashi anan
Dan ni dake da kai bana buqatar kufitoh kuce
Ya SAILUBAH kin ha'du
Na sauke alqur anin me girma inada ilimin addini daidai gwargwado dan baxa'a kirani jahila ba
Ayanxu ina U:J ina fannin san kasancewa cikakkiyar doctoh
Sai dai bawani damuwa nayi da karatun bah dan inada burukan da suka shige min gaban karatun

Na kasance mace mesan ku'di
Mesan na mallaki gida da mota
Sannan ku'di su ratsani

Inasan namiji 'dan gaye 'dan kwalisa me ilimi wayayye me hankali
Sannan ya kasance miskili ya kasance ni ka'daice xan mallaki dariyarsa da komai na halittarsa

Ya kasance nika'daice tasa abin dubawarsa amma in aka cire iyayansa da qannansa
Ya kasan me hakuri sannan me kishi akaina
Ya kasance naxama nice madubin dubawarsa. Shikuma yaxama shakallo agareni

Ina da burin Auran Attajirin Alhaji me ku'di da nera
Irin Alhazawan garin abuja nan
Maso ku'di da albaxaranci

Bana burin Auran qaramin yaro kamar wanda ya girmeni da irin shekara uku haka

Na fisan na Auri wanda yabani akalla shekara goma sha biyu

haka na saka araina baxan ta6ata auran qaramin yaro bah. dan na raina qarfinsa da jarumtarsa

Acikin unguwarsu akwai wani gida me kyau da 'daukar hankali wanda ya kasance gidan xuwana ne ako da yaushe naga damar xuwa
Inada aboki RAMADAN wanda shine ya kasance wanda yakejin sirrina
nayi matuqar shaquwa da RAMADAN irin shaquwar nan da akekira da inbakai baxan iya rayuwa bah

Ina san RAMADAN dan ya kasance yaro memin ladabi da biyayya duk da shi 'din miskiline
Amma ya ha'du tako ta ina dan ina qaruwa dashi tako ta ina
Dan yafini ilimi yafini hankali sannan ya fini nutsuwa
Duk shawarar da nanema agun RAMADAN idan yace min iyi kasa bar kaza nabarshi har abada

Yaro ne qarami 'dan shekara ashirin cif ba qari ba rage ayau
Idan me karatu ya koma baya toko xai gane naba RAMADAN shekara biyar kenan
Saidai RAMADAN funannan yaro ne. Xaki gane waye shi idan tafiya tai tafiya

Tunda natashi banta6a ganin idan mahaifiyata bah
Dan tada'de da rasuwa tun ina jaririya
Ayanxu dai ina hannun matar babana ko ince muku Kakata
Ba lefi suna kula dani sosai saidai matar babana tana da san ku'di ba nawasa bah
Amma duk da san ku'din nata nafita

Babana dacan yayi ku'di Sosai daga daga baya ne karayar arxiqi tasa meshi
Ayanxu bashi dashi Saidai bama rasa na sawa abakin salati
Abu 'dayane ya bari adukiyarsa. shine gidanmu.
Gidanmu babban gidane kuma ginin xamani
Dan a unguwarmu in kacire gidansu Ramadan akyau toh cika saka gidanmu

Inada qawaye masu bu'dad'dun ido da wayewa fiye da tunanin me karatu

Wannan shine labarina akataqaice

👯👯👯
Sunana RAMADAN Nasir yaro 'dan 20 years
Na kasance ina da buri 'daya arayuwata shine
natashi da maseefar san wata mace me kyan sura. Da komai
Tayi tako ta ina
Ina santa
Ina santa
Ina santa
Ina da abokana ye biyu Fawas da Khamis
Duk ra'ayinmu 'daya yake dasu
Amma mutane da dama suna cewa nafisu nutsuwa da hankali

Na kasance 'dan gaye me san tsafta da qamshi
Duk unguwarmu ni ka'daine nafita xakka a iya wanka
Dan nayi xaman jos anan nasamo Sirrin
Inada kalamai masu tsayawa arai
Sannan Auntyna Tace ni futunanne ne
Ya ta6e baki sannan yaci gaba da cewa
Idan hakane Ku da kanku xaku sheda hakan idan kuka cigaba dabin Aunty Rahamat Nalele



Suna na KHAMIS
Inada shekara ashirin daidai yau

Ban tsaida wani buri araina ba tukunna
Sai dai inada san mata saboda Suna sani nisha'di. mata abin farin cikine kowane 'Da namiji ne


👯👯👯👯
Suna na FAWAS
Inada shekara ashirin daidai yau

Ina da San mata Sosai kuma inada burin Auran mace wacce ta xarce shekaruna da kamar shekara biyar haka ko shidda
Kuma bana san Auran wacce ta Waye nafisan Auran 'Yar qauye me halin yarinta
Tab😳



👯👯👯👯👯
Suna na Zainab Amma ana kirana da XEE dan nafisan akirani da hakan
Inada shekara ishirin da biyar.

Ina da saurayi Surajo ina matuqar sanshi da kishinsa
Sannan ni ta hannun damar SAILUBAH CE dan duk acikin qawayanta nice babbar qawarta



👯👯👯👯
Suna na Hameeda Ya'u ina xaune a qauyan takai Babana ya rasu Mamana mah haka
Ina hannun qanwar babana Innah Hansai
Ba qaramin ganamin axaba take bah
Duk aikin gidan ni nakeyi duk wani aika ni nake xuwa mata haka duk wani Girki ni nake yi
Duk da ko tanada yara Amma Sam bata sakasu sai ni

Sosai nake hango tsanata acikin idanta
Bata sona bata qaunata
Ta hana duk wani saurayi tsayawa dani wai tafiso na xauna inta yimata bauta

Ayanxu shekatata ishirin da hu'du 24
Bani da wani buri araina sai na kallan cigaba da bautar da nakeyi


*Toh Madallah masu karatu kunji tushen kowa acikin wannan littafi nawa. dan haka sai kugyara xama kusha karatu*


SAILUBAH yarince maisan ku'di kamar yanda tafa'da
Amma duk ku'din da xata samu basa rufe mata ido
Dan ko yanxu SAILUBAH tasamu ku'di xata iya kyautarsu gabaki 'daya dan Allah yayota da San temakwan mutane
Tana da kyauta Sosai ba 'dan ka'dan ba da tausayi

SAILUBAH 'Yar gayece Sosai
Duk unguwarsu ba'ayi yarinya me wankanta bah

Zama na musamman samarin layin nasu suke dan kawai suga fitowarta
Duk unguwar ba wanda baisan SAILUBAH da halinta ba
Kyauta San Mutane San ku'di fa'dar Gaskiya..............
Koda ko kar sa'an babanta ne kayi abunda bai dace ba toko ba shakka saita wanke ka da soso da sabulu
Duk unguwar ba Wanda baisan sha'kuwarta da RAMADAN ba
Suna San junansu Sosai dan shi'din abokinta ne
Mutane da dama idan sukaga SAILUBAH da RAMADAN xasu skull dake skull 'dinsu 'daya ba qaramin sha'awa suke basu ba
Fa'di suke tsakanin SAILUBAH da RAMADAN wayafi kyau ne


RAMADAN Yarone me hankali da nutsuwa
Sam baya shiga sabgar daba tashi ba
Komai xaiyi anutse yake yinsa
Baya 'daukar raini
Yarone me farin jinin jama'a musamman mata
RAMADAN na kowa ne dan Allah yayoshi da kwarjini
Duk inda kika kai da abinki idan kikayi toxali da RAMADAN sai kinso Ki mallakeshi a matsayin mijin Auranki
Ya ha'du ne tako ta ina RAMADAN yayi

Yana da da'din murya haka kallo 'daya xaki mai kisan anyi balaraban yaro

RAMADAN cikakken 'dan rainin wayone
Sam baxa ki gane inda yasa gaba ba
Yana ji da Auntynsa SAILUBAH. Sam baya San 6acin ranta
Duk Wanda yake tare dashi yasan da xaman wannan
Sai dai fah ahakan baqamin takurama SAILUBAN yake ba akan samarinta

Shi ka'daine namiji agidansu
Kuma Wanda kamanninsa yafita daban dana kowa
Sam RAMADAN bai ibo Komai na iyayan nasa bah
Mutane na mamakin wannan yanayi yanda RAMADAN ya futa xakka agidan nasu
Kome yasa hakan
(Tabbas kwakwalwa tana buqatar caji agun🤔)


Su ukune agun mahaifan nasu
Akwai yayar RAMADAN Saudat wacce ta kasance qawar SAILUBAH
Sai shi RAMADAN 'din
Da qanwarsa Khairat

Mahaifinsu Alhaji Naziru me ku'dine Sosai
Ya shagwa6a Su da ku'di Sosai
Haka ba qaramin SOO sukema RAMADAN ba
Kome yasa haka🤔

RAMADAN Yana da San karatu Sosai gashi da ilimi tunda ya taso ya fara xuwa makaranta bai ta6a fa'duwa akan Komai bah
Yanxu haka saura bai fimai 1 year ya gama kammala karatunsa ba
Inda yake san xama cikakken likita wato doctor
Yaxama kenan ra'ayinsa 'daya da Auntyn Sa SAILUBAH

Idan Nace muku RAMADAN 'dan rainin hankali ne karku musa min



Haka KHAMIS iyayansa Suna da ku'di Sosai shima an shagwa6a shi Sosai da ku'di
Su biyu iyayansa suka Haifa
Ianada Yaya Rahamat tayi Aure tana garin Abujah da xama
Ganin hakan KHAMIS shi 'daya shiyasa shi abinda yakeso kuma iyayansa suka biye nasa

KHAMIS Yanada San karatu inda yakeso yaxama cikakken loya Wato ya karanci low


Shiko FAWAS iyayansa shi ka'dai suka Haifa
Ba qaramin ji dashi suke bah
Sun shagwa6a shi da ku'di Sosai


*To Madallah me karatu gyara xama*



Yau take talata kuma antashi da ruwan sama yaf yaf yaf gwanin sha'awa

SAILUBAH sauri sauri gudu gudu takeyin Komai dan sunada karatu qarfe tara
RAMADAN ya shigo falan hannunshi 'dauke da Wasu takaddu Yace Auntyna lokaci ya fara tafiya fah
Da sauri tajuyo xatayi magana sai kuma tatsaya kallansa kamar alokacin ta fara ganinsa
Ya 'daga mata gira tare da qarasowa kusa da ita ya kar6i 'dan kunnan hanunta Yace in saka miki ko
Tayi saurin 'dagamai kai Tace kayi kyau Sosai Qanina
Yayi Murmushi Yace Nagode Auntyna



Gyarawa Sosai tayi ya saka mata 'dan kunnan ta'dauki gyalanta da 'yar jakarta tamaqala
Idan RAMADAN na kanta yana qare mata kallo. Ta 'daga mai gira
Yayi murmushi Auntyna tsaya na photo
Wayanka saita cika da pix 'dina
Yace in bake acikinta Wlhi bata da amfani
Tace kayi breakfast kuwa
Ya 'dan Sosa qeya Yace nayi
Tabishi da kallo ka'dan hmm bakayi ba
Yace toh Kinga lokaci yayi........
Cire gyalanta tayi tashiga kitchen kawai. RAMADAN yaja numfashi tare da kallan agogo yana tsaki
Bai ankareba sai gata qatan faranti ahannunta. Wanda ke 'dauke da lafiyayyan tia da kuma soyayyan dankali da kwai
Ta dire a gabansa Tace nabaka minti uku kayi Maza
Yace Aunty banajin yunwa...
Ta katse shi da jefa mishi wata muguwar harara
Bashiri ya fara ci
Yayinda ita kuma ta xauna tana amsa waya
Hello Alhajina ina kan hanyar xuwa makaranta
Yace Amma naso inxo in ganki yanxu. Plx Ki bani ha'din kai yanxu naganki
Aini takace. Kabari ina dawowa xaka ganni.
Yace toh Allah ya dawomin dake lafiya
AmEEn Nagode. Tafa'di hakan da kashe wayan
RAMADAN najinta Yace Auntyna dawa kikayi waya
Ta gallamai harara cikin 'daure fuska Tace ban sani bah
Yayi Murmushi Yace pls gayamin Wlhi ba'abinda xai faru
Tace hmm yama faru Wlhi saina baka mamaki idan kayi sanadin da Alhaji Jamilu ya dena xuwa gareni
Ya kalleta ka'dan dayin murmushin rainin hankali Yace baxanyi Komai bah Auntyna Amma dan Allah gayamin yaushe kuka ha'du da har ya kasance ban sani bah
Tace jiya muka ha'du a jifatu yaje siyayya

Amma shine ko jamishi aji bakiyi ba kika amsheshi daga ganin farko
Ta gallamai harara Tace ban jah mishi ajinba
Yace me yasa
Cikin maseefa Tace saboda shi me ku'dine yayimin tun kallan farko dana masa
Yace Amma.........
Tayi saurin katse shi da cewa. Wlhi RAMADAN ba wani abu daxaka fa'damin inji inbar mutumin nan dan yana da ku'di Sosai
Kyautar farko daya min jiya dubu 'dari uku ya ban
Yace haba Auntyna......
Na rantse da Allah ka cikani da surutu xakasha mari
Shuru RAMADAN yayi yaci gaba dacin abincinsa
Can ya kammala Yace toh mutafi ko. Yafa'da da 'daukar Wasu takaddunta
Suka fitoh ya bu'de mata gaban motarshi tashiga shima ya shiga da jansu suka ficce daga gidan

Direct gidansu XEE sukayi Suna parking tana fitowa
Tayi kyau Sosai cikin shigar riga da siket 'yan kanti
Ta shiga motar ta xauna tana mita wai basuxo da wuri ba
RAMADAN Yace lefin Auntyna ne fah
Tace aina sani tasaka gaba kayi breakfast ko Yace ko shakka babu.
SAILUBAH Tace hmm kema kisan inba ni'din nasashi gaba ba baci xaiyi ba
Haka dai sukayi B;U:K university.

Sunayin parking wata kyakkyawar budurwa tayi saurin isowa garesu
Cikin rashin kulawa SAILUBAH da XEE suka fito dayin department 'dinsu
RAMADAN yafitoh da Murmushi akan fuskarshi Yace ha'a kaga kyakkyawar yarinya. Tauraruwa me dishashe hasken taurari. Gayamin me ya tsaidake a wannan lokacin da yadace ace kina can kina 'daukar darasi
Cikin jin da'di da dariya akan fuskar Amina Tace baxan iya fahimtar Komai ba inhar banganka ba
Tunda naxo idanuna suke min ra'da'di dan rashin ganinka da basuyi ba
Yace toh gani sun ganni sai hankalinsu ya kwanta
Tayi Murmushi. Xanso muje shan iska anjima

Ya kulle motar tashi yana fa'din xanfi kowa farin cikin hakan. Maxe jeki kar darisa Su wucceki da yawa
Ba musu Amina tabar gun cikin jin da'din Ganin masoyinnata

Gab da RAMADAN xai shiga department 'din nasu
wata ta tareshi da sauri
Ya dafe kai cikin Murmushi Yace yane Asma'u
Xuciyata bugawa take in bata ganka bah
Amma na lura Sam xuciyarka bata damu dani ba Sam

Haba nutsuwata abin kwanciyar hankalina. Wlhi dake natashi araina

Meyasa toh kakasa nemana
Kin sanni da karatu banasan nayi missing 'din Komai. plx nutsuwata Ki lamince min nashiga na miki alqawarin yau xan baki lokaci na musamman dan kimallaki kalmomina
Tace toh Allah yasa ina maka fatan alkairi
Ya shigeta yana cewa tare dake........



Karatu ne Wanda sukayin shi cikin nutsuwata ahaka suka tashi inda SAILUBAH ta kalli RAMADAN Tace Amma fah abubuwa da dama na kasa fahimtarsu
XEE tayi dariya Tace aike Kullun a haka kike
Tayi Murmushi dacewa ai banda matsala tunda gani ga Qanina.
RAMADAN Yace aikuwa ammafa Auntyna kidinga lura saboda wata ranah.

Taturo baki da cewa toh naji muje gida nafara jin yunwa ba sai mun jira KHAMIS ba .......
KHAMIS 'dinne ya katsesu da fa'din dawai tafiya xukuyi kubarni bayan yasan yau ban fitoh da mota ba.
XEE ta kafeshi da ido Tace ya fa'da mana
Ammma fah kayi kyau sosai Tafa'da da shigewa motar Ganin SAILUBAH da RAMADAN sun shige.
Yayi Murmushi Yace kai Aunty XEE ina wani kyau anan. Yafa'da shima yana mai shigewa cikin motar


Cikin nutsuwa RAMADAN yake tuqin motar
KHAMIS Yace Kasan wani abu
Sai ka fa'da
Wlhi fitowata 'daxo na ha'du da wata xanka'daxiya......
Ta ha'du Sosai dan tatara duk wani abinda kowane 'da namiji yake buqata awajen mace
Dana kai agoge min motata tsayawa nayi daniyar agama goge min natafi da ita
lokacin ko wanka banyi ba
Sai gata tayi parking motar tata akusa dani
Ta fitoh tana wani yauqi da rangwa'da. dan Allah Malam motata nakeso a wanke min nanda 10 minutes

Ba sai ta cillamin key nata bah
RAMADAN Yace kut😳
Wlhi ina gayama sai kawai naxuba mata ido kusan na 2 minutes
Ka katsaya kana kallona ko baka 'daya daga cikin masu wankin ne
Ta katsemin tunanina da fa'din hakan.....
Kan nayi magana wanda yake goge min motar tawa Yace tab Hajjiya shima kawo tasa yayi. Baki lura da hutun da yake tare dashi bane
Kasan dake 'Yar iskace saita juyo da kallanta. Ayya am sorry
Na watsa mata wani kallo Nace Karki...


Read / Download SAMAREEN BANAH Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album