Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

ABDULJALAL Book 2 Complete Hausa Novel Document by ABDULJALAL Book 2


ABDULJALAL Book 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 202614



ABDULJALAL Book 2

Reading Time: 16 Hours

Added On: 10, Feb 2025

Author: Aisha Humaira ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07063065680

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 1.13 mb

File Type: txt

Views: 313+

Download: 753+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: ๏ปฟ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 1๏ธโƒฃ/54_

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki, da suka bibiyeni a littafi na farko, Alhamdilillah yanzuma gani na dawo domin kawo muku kashi na biyu, nagode da kulawarku, ku biyoni domin jin yadda zata kaya a cikin wannan littafi naku me farin jini.
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Gmail @ [email protected] Facebook @ real humaira

_MY FIRST NOVEL _

Jeje bude baki yayi yana kallon Hannah, dan yarasa meze ce mata, Hannah takuma kallon Jeje, ta nunashi da key din motarta
"wannan itace magana ta karshe dazanyi da kai, nidaku dan halak ka fasa, kome zefaru sena mallaki Jalal, indai na amsa sunana Hannah" daga nan ta dauki Jakarta tai gaba abunta. Dukan tabur jeje yayi da karfi, yasa kafa yai ball da tebur din "Why, ya haka ya za a yi abubuwa su lalacemin haka, akwai matsala muddin Hannah tace zata aikata abunda ta fada. Mukullin tasa motar ya dauka shima ya bar gurin.
Jalal yana gama cin Abincin sa ya mike yana hutawa, anata kiransa ana masa bangajiya, wayarsa yadakko, IG yashiga yana shiga yaci karo da hotunan birthday dinsa, abunda ya bashi mamaki, hotunan shida Jalila yafi yawa, shi akafi yadawa, fitowa yayi yakoma what's app still status din mutane hotunan ne suke yawo, shiru yayi ya kurawa hotunan ido, wani hotonsu ya tsaya akai yana kallo, yanda ta dan zumbura baki tana kallonsa, shikuma yana dariya, tsaki yayi "kalleta dan Allah se tsabar iya rashin kunya, shi mamaki yake yadda akayi tai mugun rainashi sam bata shakkarsa, kaman ba yarinyar dasuka dinga wasa da ita a zanin goyo ba, yan uwan sa mazama tsoronsa sukeji amma banda wannaan yarinyar, zuwa wani dan lokaci ya kashe wayar, ze ajiye kiran Jeje ya shigo wayarsa, kaman kar ya daga, seda ta kusa katsewa sannan ya daga
"hey man kana inane?"
"me zakayi min kake nemana?"
"ina wajene ina jiranka" "wajen ina kenan?" "kofar gidanku mana" "ok ina zuwa" Jalal ya duba yaga Jawwad yana toilet dan haka kawai ya fito, yana fita yaga motar Jeje a kofar gidansu, karasawa yayi ya tsaya bece komai ba, jeje ya fito yana wata shu'umar dariya da wannan katuwar muryartasa yace "man of the day, our celebrity yane?"
"Normal, mukarasa cikin gida" Jalal ya fada a takaice, yaiwa Jeje jagora zuwa part dinsa, suna zuwa Jeje yanemi guri ya zauna, Jalal yaje fridge ya dakko wa Jeje ruwa da lemo, ya hada da giya ya aje masa, Jeje ya dan kalli Jalal yace "J man, ya gajiyar jiya"
"gajiya tabi lafiya" "good wai ya akayi ka bar gurin nan jiya, ban san ka tafi ba?" Jalal ya danyi shiru yana tunani sannan yace "gaskiya i can't recall, Hannah tabani wayne jiya, bansan meyakuma faruwa ba, ban san ya akayi na dawo gidaba, na tambayi Jawwad ma yace min ba shi yakawoni gida ba, i think ansamun wani abu a giyar nan. Dan zare ido Jeje yayi, dayaji statement din Jalal na karshe amma ya maze yace "anyway but J man, akwai wata cute baby da pictures dinku suke yawo social media, tagama haduwa babyn nan, nifa tayimin wallahi, inaso insata a harka"
"wace yarinya kenan?" Jalal ya tambayeshi a takaice, Jeje ya zaro wayarsa ya nunawa Jalal hoton Jalila, tareda fadin "wallahi Jalal komai yaji ajikin yarinyar nan, zanso tayi joining insata a layi, zata kawo harka, maganar tama kawai abar sha'awa ce komai nata na birgewa ne, gaskiya ta hadu"
Wani mugun hade rai Jalal yayi, ya kalli Jeje a fusace yace "Are you out of your sense, wai kai bunsurun inane da duk inda kaga mace jikinka har rawa yake, let me warn you, Wallahi3 na rantse maka, muddin wani abu yasameta sena daureka, kasan wacece? Kanwar Jawwad ce, yarinyar da yakeso, danme zaka dinga wannan kazamin maganar akanta, karka kuma fadin wani magana akanta kota arziki kota sharri akanta, wannan yarinyar ba irin jakan matan dazaka iya nasarar lalatawa bane, kaji na gaya maka take your leave now "ya nunawa Jeje hanyar fita, wani irin kallo Jeje yaiwa Jalal, amma seya daidaita nutsuwarsa yace" is ok j man bansan abunda ke tsakaninku bane, ashe kanwar kace, na dena bazan kuma ba kayi hakuri "
" Naji amma for now tashi kabani guri, raina yagama baci, tashi ka tafi" ba musu jeje ya mike ya fita.
Da Jawwad yafito yaga Jalal ya tafi, kawai se shima yafito, yaga Jalila cikin flours dinta tana gyarawa, ya fuskanci tanason furanni, a hankali ya karasa inda take ya zauna, ta waigo ta kalleshi, tai murmushi "Allah yatemaki yayana na kaina" Jawwad yai murmushi yace "Ameen yar baby, ya meyasa kikeson furanni ne?" "nima ban saniba, kawai dai ina sonsu ne, na gidanmu a kaduna nasan sunyi missing dina, in bana nan ummi ke kularmun dasu" sekuma tai shiru idonta yacika da kwalla, Jawwad ya nisa sannan yace "am sorry, nagane kidena damuwa kinji kicigaba da addu a muna kan nemanta har yanzu" gyada masa kai tayi tareda murmushi, yace "Yawwa babyn Yayanta" yasa hannu a aljihunsa ya dakko chocolate yabata, hannu tasa ta karba tana murmushi, tareda kokarin maida hawayenta, tai murmushi tace "Nagode Ustaz" "yaukuma nine ustaz" "Eh mana" sukayi dariya gaba daya, Jawwad yace "yawwa baby, nace wai me yafarune jiya? Ya akayi manu ya kawo Jalal gida, dazu yake tambayata ya akayi ya dawo gida" Jalila tai ajiyar zuciya tace "Hannah ce ta kaishi wani guri suka bashi wani abu, naga yafita hayyacinsa, tasaka wani yaimata gadinsa ta tafi tana waya, kawai naji ban yadda da itaba, shine na dauke hankalin wanda tasa gadinsa nasa Manu ya daukeshi ya kaishi gida" shiru Jawwad yai na dan lokaci sannan yace "thank you for your contribution my dear, hakika kintemake shi, maybe akwai abunda sukeson yi masa, narasa meyasa Jalal yakasa gane basa kaunarsa, anyway mungode sosai Baby Amma ya akayi kikasan Hannah"?
"A a, ban santa ba agurin naji ana fadar sunanta, Yaya Jawwad no need kaimin godiya fa, manta kawai, amma akwai wani abu da nagani yabani mamaki"
"Mekika gani?"
"Wannan mutumin na rannan, da ya dinga zagin Jalal, dan kun gaisa da dansa, shima fa yaje gurin nan, abunda yakara bani mamaki shida wannan Jejen naga suna magana, shiyasa nace maka shima yana kama da yan shaye2"
"Anya kuwa shi kika gani, maybe kamace kawai, bana zaton baban Faruk a irin wannan gurin, saboda yanada tsatstsauran ra'ayi, kece dai kike masa kallon ba mutumin kirki ba "
"Yaya kenan shikenan tunda baka yadda ba, magariba tayi bari inje inyi salla"
"to shikenan, dan Allah anjima ki dafo mana wannan tea din naki me dadi"
"Hmmm yayana kwadayayye kawai" "ke kika koyamin kwadayin ai" tai murmushi ta mike ta tafi cikin gida, Jawwad kuma ya fita masallaci.
Tunda Jeje yafita yake zancen zuci "lallai tunda Jalal yaketa masifa akan yarinyar nan to ba karamin matsayi take dashi a gurinsu ba, lallai dama tazomin akan wannan fitsararriyar yarinyar zan jefi tsuntsu biyu da dutse daya" Jeje ya kyalkyale da dariya, sekuma ya hade rai daya tuno da maganganun Hannah, dakuma abunda Jalila ta gaya masa ranar birthday din Jalal, "muje zuwa yan mata mu daku zanga wazeyi nasara"

Bayan sallar isha'i Jawwad yasa Jalal a gaba yayi salla suka zauna suna hira, Jalal yace "Jawwad ina jin bacci, bari in tafi gida" "No karka tafi yanzu ka tsaya baby zata kawo mana tea, ka tsaya kasha seka tafi" "ok bari in jira, ina son sha, kasan wani abu"
Jawwad yace "A a seka fada" "har yanzu ina mamakin me aka zubamin a giya wanda ya bugar dani haka tsawon lokaci"
Jawwad yai ajiyar zuciya "Jalal shiyasa nake gaya maka tun ba yauba, hulda da mutane irin wannan be kamata ba, kasan wani abu? Jalila ce tasa aka dawo da kai gida, tunda kafita daga gurin nan, ni bansan meyafaru ba, bayan ka bugu tasa manu ya daukeka yakawoka gida" kallon Jawwad ya danyi, ya dan tabe baki irin he don't care din nan, wayar Jawwad tafara ringing, ya kalli Jalal yace masa "excuse me please" ya daga wayar
"Hello My Jawwad ya kake?"
Muryar Hanan ce, Jalal ya kafe Jawwad da ido, Jawwad yace "ina lafiya Hanan, ya mutan gidan"
"Nifa fushi nake, ashe Jalal yayi birthday bako gayyata ko my Jawwad"
"A a Hanan ba haka bane, Jalila ce ta gayamiki ko?" "A a, wannan ce
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download ABDULJALAL Book 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album