Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

AURE DA HAIHUWA Complete Hausa Novel Document by AURE DA HAIHUWA


AURE DA HAIHUWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 40868



AURE DA HAIHUWA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 13, Nov 2024

Author: Zahra Muhammad Mahmud Surbajo ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 231.01 kb

File Type: txt

Views: 577+

Download: 589+

Last download: 3 days ago

Description/Story:
*AURE DA HAIHUWA*




*Zahra Surbajo*

*Ina mai Baku hakurin jina shuru da kukayi,da sauyi da kuka samu game da yadda nasaba gudanar da lamurana,hakan ta farune sakamakon kaddarori da suka fadawa rayuwata Wanda banyi tsammaninsu ba,Wanda Alhamdulillahi da taimakon Allah na cinye su,ina godiya ga masoyana wainda basu yada ni ba,Allah saka da alkhairi,*

*Littafina na Hakki ne danake rubutawa watanni hudu kenan da yaci kasuwa,inda nasaida labarin ga wani marubuci Dan kasuwa ze wallafashi akasuwa,ayi hakuri don Allah hatimin nasara kowa ke nema shiyasa daya bukata na sallama ban sanar dakubane nabari se nadawo rubutun se in sanar da fatan zakui min uzuri,sabida tsawon watanni hudun nayisune ahali na rashin lafiya*

_wannan littafi nawa sabo ne me dauke da darussa masu maana,banyishi Dan cin zarafin wani ko wata ba,nayi ne domin fad'akarwa da nishad'antarwa,ga soyayayya me tab'a zuciyar me karatu,kuma kyauta ne bana kud'iba_

_Ku bishi ze k'ayatar daku_


*page 1*



I'd card d'in dake gaban rigarta ta gyara sannan ta gyara farin glass d'in dake fuskarta,cikin murmushi takai dubanta gareshi,tace cikin harshen turanci.

"Ranka ya Dad'e,bawai baze yiwu bane,ina de so ka gane ne wannan shine kwayoyin haihuwarka,da gwajin mu ke nuna mana na k'arshe ne, dole se anbi komai cikin kulawa da takatsantsan,inba haka ba,za'a iya rasa komai"cewar doctor Amina Galadima kamar yadda aka rubuta agaban rigarta.

Gyara zama yayi sannan yakai dubansa gefen matarsa dake ta cika tana batsewa, yayi murmushin k'arfin hali sannan yace,

"Doctor badamuwa na mik'a lamuran ga Allah, ko adace ko akasin hakan,Dan haka kiyi me yiwuwa kawai,kinsan yarda da nai dake ne kesawa in baro k'asata in zo gareki "be gama fad'in abinda yakeson fad'i ba,matar tashi ta katseshi da cewa cikin fad'a da harshen larabci.

"Farhan wannan shine karo na biyar da za'ai dashen kwayoyin halittarnan,wallahi matuk'ar ba'a daceba,to ni kuma zamanmu yazo k'arshe,taya in banda toshewar basira,kana zaune a k'asar Dubai, zaka wani taho Nigeria Neman haihuwa,shekara biyar kenan muna zuwa kullum ba sauyi,to Nide na fad'a maka"ta k'arasa maganar tana huci.

Jingina yayi da kujerar da yake zaune ya lumshe kyawawan idanuwanshi,yana sauraronta,harta gama,sannan ya budesu a hankali,ya zubesu akan matar tashi wacce yake ji inba ita baze iya rayuwaba.
Dubansa ya kai gun doctor Amina sannan yace cikin sark'akk'iyar murya,"doctor please do something meaningful to save my marriage"

Cike da tausayawa doctor Amina tace "insha Allah"

Sallama sukai mata suka wuce masaukinsu,bayan an amshi seamen sample d'inshi,ko a hanya matar tashi me suna shehnaz in banda masifa ba abinda take masa shide kallonta kawai yakeyi,Dan besan yaze mata ta fahimceshi ba.


Bayan wasu kwanaki doctor Amina ta buk'aci daya kawo matarsa Dan adasa mata D'an tayin acikinta.

Koda suka iso asibitin doctor ta shiga tiyatar gaggawa Dan haka d'aki na musamman aka basu su zauna domin jiran fitowarta.

A d'akin suka tarad da wasu mata da miji zaune suma daga dukkan alamu ita suke jira.
Sosai ma'auratan suka tafi da hankalin Farhan,kasancewar manne suke da junansu cikin so da k'auna,ya tsinkayo hirar da sukeyi cikin harshen turanci,inda mijin ke cewa.

"Baby ina fata da addu'ar Allah yasa in anyi dashennan mu dace da samun haihuwa"
murmushi matar tayi sannan ta shafi gefen fuskarshi tace"insha Allahu dear za'a dace jikina yabani hakan"ta fad'i cike da murna a fuskarta.

Sosai suka burgeshi duba da ganin yadda suka damu da junansu kowa k'ok'arin kwantar da hankalin d'an uwansa yake,sab'anin shi da tashi matar wacce keji kamar ta shak'eshi ya mutu ta huta.


Suna nan zaune doctor Amina ta shigo d'akin ita da wasu ma'aikata guda hud'u,daga kallon shigowar tata kai ba se an fad'a maka ba tana cikin tashin hankali,

Duk a firgice take,hakan yasa dukan su maida hankali kanta,cikin sauri sauri tace cikin harshen turanci."don Allah Ku gafarceni,Mahaifina ne Allah yayiwa rasuwa yanzu sakamakon hatsarin mota, zani gida yanzu,amma nayi musu bayanin komai,kuma zasu gudanar dashi cikin nasara"ta k'arasa maganar tana nuna ma'aikatan data shigo tare dasu.

A hankali Farhan yace"badamuwa doctor, Allah yajik'an mahaifinki,yasa ya huta"

Suma wa'incan ma'auratan ta'aziyyar su kai mata,amma banda shehnaz,wacce gaba d'aya ta d'auki tsanar duniya ta d'orawa doctor Amina sakamakon yarda da ita da mijinta yayi.

Cikin hanzari ta juya ta fice daga d'akin,ma'aikatan data shigo dasune suka buk'aci dasu taso su bisu.

Cikin nasara,kowacce an dasa mata sperm d'in a mahaifarta,se fatan Allah yasa adace.

Haka suka baro asibitin kowa na fatan dacewa gurin Allah.


Muje zuwa.


Surbajo for life.
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
*AURE DA HAIHUWA*
πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


*Zahra Surbajo*


*page 2*




Tsawon sati biyu kenan da yin dashen,kuma tsawon kwanakin da doctor ta d'ibar musu kenan su dawo ay musu gwajin ciki Dan aga ko andace.

Misalin k'arfe takwas su Farhan suka shigo asibitin, zuciyarshi cike da zullumin abin da ze tarar.a waiting room suka zauna zaman jiran iso daga doctor Amina.

Ita ko doctor Amina nacan cikin office d'inta cikin matsanancin tashin hankalin da ta ma rasa ta yadda zata fuskanci matsalar.

Cikin tsananin bak'in ciki da tashin hankali ta kai duban ta gun ma'aikatan da ta sa su gudanar da dashen,tace,
"Me kuka yi kenan?,innalillahiwainnailaihirrajiun,da wanne bakin kuke son in yiwa mutanen nan bayani,?hankalin ku na ina lokacin Dana ware muku na kowa?,wannan wanne irin ganganci ne?,fisabilillahi ta ina Sunan Rayhan yazo d'aya da Farhan,ta Ina?"ta k'arasa maganar cikin zubowar wasu hawaye masu zafi data kasa tsaidasu.

Suko ma'aikatan motsin kirki cikinsu ba Wanda ya iya yi,Dan sunsan ba k'aramar b'arna suka aykata ba,Dan haka sun rasa ma kalma a bakunansu bare su furta,.

A raunane ta danna k'ararrawar kiran su,ba'a jima ba Farhan suka shigo shida shehnaz dake ta faman cika tana batsewa,doctor na had'a ido dasu wasu zafafan hawayen tausayinsu ya zubo mata ta runtse idon ta, Farhan na ganin hakan yasan ba'a dace ba,Dan haka addu'oi yay ta karantawa a zuciyarshi da zasu sanyaya zuciyarshi.

Bayan sun zauna doctor tayi k'ok'arin dedeta natsuwarta,sannan ta fara magana cikin rashin tabbas,tace"da farko de Farhan inaso ka yarda da k'addarar Allah, mekyau ko Mara kyau"
Murmushin k'arfin hali yayi sannan yace"karki damu Amina, nasan ba'a dace ba na bar komai a hannun Allah"

A raunane tace"Farhan wannan karon ba dacewa bane ba'a yiba,an dace sede an samu matsala daga ma'aikatanmu,akwai wani bawan Allah me suna Rayhan,shima ya zo nan da matarsa Safna, suma haihuwa suke nema,to rana d'aya muka amshi sample d'inku, ranar da za'ayi dashen ni kuma akamin rasuwa,nabar komai a hannun abokan aykina,sabida wajibine ayi dashen a wannan Rana, to matsalar da aka samu,se suka d'auki sample d'inka suka sama Safna,shikuma na Rayhan aka sawa shehnaz"ta k'arasa maganar cikin zubar da hawaye,

Runtse ido Farhan yayi yana karanto duk wata addu'a da tazo bakinsa,tashin hankalin daya shiga baze iya misaltuwa ba,sei da ya d'auki mintuna a haka sannan ya bud'e idanun nasa a hankali,yace,
"To yanzu ya akayi,shi Rayhan d'in ya san da wannan batun?"

Cikin dauriya doctor tace"be sani ba Farhan, sabida shekaran jiya ya kirani,yace yana son ya kawo Safna ay mata gwajin cikin Dan jiya da asuba zasu bar k'asar,tafiyar gaggawa ta taso masa,sun zo nan an mata gwajin kuma sakamakon ya tabbatar da tasamu cikin,ban duba b'arnar da suka yi ba se yau nay ta kiran number Rayhan d'in domin in sanar dashi bata zuwa"ta k'arasa maganar tana zubar da hawaye.

Kife kanshi yayi akan tebur d'in dake gabansu ya fara zubar da wasu hawaye masu zafi,duk yadda yaso ya jure amma ya kasa dole ya koka,wannan wacce irin mummunar kaddarace D'an wani a cikin matar wani,?ina zesa rayuwarsa,yana tsaka da wannan tunani ne ya tsinkayo muryar shehnaz na fad'in.

"Wannan ni ba matsalata bace kai ta shafa,Ni de fatana a gwadani yanzu Allah yasa bana d'auke da cikin wani gardi da ban sani ba"

Ba su da ta cewa dole doctor ta auna ta,abun mamaki,bata samu cikin ba,ita
ayko ana sanar da sakamakon ta mik'e,ta suri Jakarta,ta kai duban ta gun Farhan dake cikin tashin hankali tace a wulak'ance,"zuwa yanzu kasan aure ni da kai ya k'are,Dan bazan k'arar da rayuwata a gidan auren da ba albarkar aure ba,wato Haihuwa,Dan haka na tafi ka san inda zaka ayko min da takardata"tana kaiwa nan ta bud'e k'ofar ta fice a fusace.

Sake runtse ido Farhan yayi yana karanta duk addu'ar data zo bakinsa.

Iya tashin hankali doctor Amina ta shigeshi,Dan haka rarrashin Farhan d'in ta shiga yi da duk wata Kalmar rarrashi data zo bakinta,
A hankali ya d'ago ya kalli doctor sannan yace,"Amina inason abinda wannan mata zata Haifa,da dukkan rayuwata,fatana ki tabbatar da kin samo inda suke kin kuma shaida musu cewa d'ana ne a cikinta,hakan da zakiyi shine kawai yafiyata a gareki,Duk tsawon lokaci Amina ina Dubai Ina kallon hanyar da zaki kawomun gudan jinina,"yana kaiwa nan yamik'e ya fice daga office d'in,doctor Amina na binshi abaya,jiki asanyaye,har zuwa gun da ya ajiye lafiyayyiyar motarshi,ya bud'e ya shige,a hankali doctor ta dafa window motar tace murya na rawa.

"Farhan ka taimakeni lokuta da dama a rayuwata,Kaine silar matsayin da nake kai yanzu,kayimin alfarma so shurin masak'i,nayi maka alk'awarin
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download AURE DA HAIHUWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album