Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

KADDARARMU CE Complete Hausa Novel Document by KADDARARMU CE


KADDARARMU CE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 10313



KADDARARMU CE

Reading Time: 0 Hours

Added On: 24, Feb 2025

Author: Sanah S Matazu ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 61.18 kb

File Type: txt

Views: 105+

Download: 37+

Last download: 23 hours ago

Description/Story: Ga ubangijin talikai daya bani ikon rubuta
wannan ta'kaitacan rubutu kan MATSALAR
JINNI. Ubangiji yadda kabani ikon farawa kabani
ikon kamalawa.Sa'kon godiya ga daukacin member na group d'ina MATA MASU AJI. Ubangiji ya 'kara had'a kawunanmu amin.



SADAUKARWA.
Gareku bazan manta karamcinku ba.
Teemah Cool
Safdeeq Cool
Maryam Idris Katsina.
Jamila Umar Katsina.
Aina'u Jega.
YABAWA.
Taurari cikin NAGARTA (NWA).
Ummu Fadila.
Miss Hafcy
Meesha Luv
Aunty YBK.
Aunty Chuchu.
Addah Jabo.
Beneziratu Ammar Saje.


JINJINA GA 'DAUKACIN MASOYANA.
Kaduna.
Katsina.
Narasawa.
Gashuwa
Kebbi
Kano
Da sauran jahohi ubangiji ya kara mana 'kaunar juna.Sadaukarwata gaba d'aya ga
TAURARUWATA ita ce MAHAIFIYATA ubangiji ya bani ikon kyautatta maki.


************
GAMUNAN DAI.
Hassana Muhammad Kano.
Hassana Zakariyya Shahada Kano
Hussaina Garba 'Danlami Kano.
Hussaina Zamfara.
Hussaina Kaduna Shantaly.
Hussaina Gashuwa Munayshat.
************


1-3
Cikin matsanancin gudu take wuce tsaunika tare
da tarin bishiyu, taka 'kayoyi take amma hakan
baya d'aya daga cikin abinda ya dameta, burinta
kawai ta tseremasa daga mummunan nufinsa a
kanta, cikin rashin tsamani ta taka wata
'katuwar 'kaya mai tsanani kaifi. Take ta 'kwala
giggitaciyar 'kara hakan yai dai-dai da
farkawarta. Cikin hanzari tabi 'kafarta da kallo
abinda yai matu'jar tsorata ta. 'Kayar data taka
a mafarki gata a tafin 'kafarta ga jini na bin
'kafafunta cikin tashin hankali ta soma waige-
waige. Shiru garin babu motsin bil'adama sai
kukan karnuka da tsuntsaye. A hankali takai
kallonta kan 'kofar d'akinsu cikin sakan guda
cikinta ya bada wani sauti. 'Kuuuuuuuuuu.
Cikin tsoro ta dinga ja da baya tare da karanto
duk adu'ar data zo bakinta. Ta runtse idonta ta
jiran 'karasowar 'KADDARARTA saidai ga
mamakinta sai ta tsinkayi muryar Mahaifiyarta
tana fad'in "Najwa me kikeyi baki kwanta ba?
Cikin sauri ta bud'e idonta. Sai ta saki ajiyar
zuciya. Cikin azama takaiwa 'kafarta bahagon
kallo dansan nunawa mahaifiyarta. Abin mamaki
da tsoro babu ciwo babu alamunsa. Nan da nan
ta nemi nutsuwarta cikin kaucewa kwataragin
daya dumfarota tace "Innarmu farkawa nai".
Cikin d'aurewar fuska tace " ina d'ankwalinki?".
Nanfa ta kama kame-kame sabida bama dashi
ta kwanta ba. Cikin fad'a mara sauti tace " wato
Najwa bakya jin magana ko ke kullum baza
agaya maki kijiba, kwanciya kai a bud'e ke ba
gwanar adu'aba sai anyi magana kice antakura
miki ko?". Cikin gunguni tace "Mantawa fa nayi".
Cike da mamaki tabita da kallo tana jinjina
taurin rai irin nata.Cikin nutsuwa take tafiya tamkar mai tausayi 'kasa, saidai zuciyarta cike da rud'anin mafarkinta na jiya tana jin kodai tagayawa Husnah kotai shiru. Can wata zuciyar tace " Ke Najwa yanzufa zamani ya sauya mutum ba'abun yadda bane, wani zaimiki kwance- kwance yaji matsalarki kawai dan yaji dad'in falasawa. Wani kuwa dan yaji dad'in yimiki gorine. Ki ri'ke matsalarki a ',kar'kashin zuciyarki da sannu ubangiji zai miki maganinta. Saidai ki ri'ki adu'a. Cikin farin ciki tai na'am da abinda zuciyarta ta fad'a.Kamar daga sama akaimata salama" Assalamu alaiki Gimbiyar mata". Shaidar mai muryar ne yasa ta d'ago cike da murmushi tana kallinsa cike da so da kuma 'kauna. Sai taji kaf damuwarta ta wuce. Amma miskilar saita maze. Mustapha yai murmushi yana dubanta yace,
"Najwa ina zaki cikin ranar nan?, ta ya mutsa
fuska alamun gajiya tace "gidan yaya Maryam
zani mijinta baya nan zan tayata kwana zuwa
jibi". Cikin jin dad'i yace "kice kwana biyu muna
tare"?. Ta gintse fuska "ba lallai bane tunda
kasan ra'ayin Innarmu shine nata". Yai ajiyar
zuciya " shikenan Najwa sai munyi waya". Yana
fad'ar hakan ya juya idonsa jajjir cike da
sassarfa. Duk sai ya bata tausayi, to amma ya
yakeso tayi ? Yasani sarai mudun ta sami labari
rayukane zasu 'baci a haka ta 'karasa 'kofar
ruwa cike da kasala. Tun daga soro Walid yake
oyoyo. Tilas ta aro juriya ta tari fara'arsa suka
shiga gidan. Da fara'a yayarta ta amsheta suka hau wasa da dariya. Cikin zolaya tace 'ina kuwa MUS'AB?". Take fara'ar data aro ta gushe. Kai tsaye d'akin da take sauka ta wuce ta barta anan shanye da baki. Tanata bambamin fad'a. Tana shiga kiranwayarta na shigowa jaka kawai ta ajiye ta wuce kan kujera. Tana karar wayar a kunnanta suka saki ajiyar zuciya lokaci guda.
Cikin tausasawa yace "menene?" Kai tsaye ta
amsa masa "babu komai hubbynah hope (fat an)
ka'isa gida lafiya"?. "Ba wannan ke gabana ba
Najwa dalilin ajiyar zuciyarki nake san ji, tai gum
tana juya lamarinsa a ranta tasani kad'ai ko
muryarta yaji yana gane yanayin damuwarta,
bale kuma ga rabuwar da sukai. Jin shiru yayi
yawa ya kira sunanta. "Najwah!!!!!!" Yar cigar
jikinta ta tashi cikin kasala ta amsa. "Na'am
hubbynah". " please menene damuwarki?".
"Mustapha kaine damuwata, kaine abinda ke
sani damuwa, ina duba yanayin da muka rabu
inajin araina ban kyautaba. Kobaka cancanci
SADAUKARWA ........"Ya'isa Najwa kinci abinci".
Duk saitaji haushin kanta wato shi 'ko'karinsama
cikinta, gaskiya inta auri Mustapha zata ga
tarairaya. Shigowar Yaya Maryam yasa tai masa salama. Bai matsa da sanjin daliliba ya katse. Zuciyarsa cike da tausayin rayuwarsu cikin azanci yace,
"KADDARARMU CE a hakan.
Haka ta 'karasa kwanakinta gidan cike da takura
sabida rashin samun jin muryar abin 'kaunarta.
Ranar da Abdul zai dawo tafi kowa murna da
zumud'i tun safe taimata aiki ta had'a kayanta.
'Karfe hud'u ya dawo gida, 'karfe biyar Najwa
taiwa unguwarsu tsinke. Tana shiga layinsu ta
saki sassanyar ajiyar zuciya sabida hango
'kawarta da tayi cikin sauri ta tarbeta suka shiga
gida tana fad'ar ",bestyna miss u more" ( ma'ana nayi kewarki da yawa). Cikin murmushi wanda ya zama al'adarta suka shiga gida.Inna na ganinta ta ta'be baki "wuuuu! Najwa 'yar nema wato har kin gudo ko"?. Ta turo baki " dole in gudo Innarmu aita saka aiki ba godi bare na gode, kuma kanayi ana hantararka". Duk sukai dariya Husnah ta jata d'akinta suna shiga tace "Mus'ab yazo sau biyu bakya nan, ya nemi numbarki Inna ta aiko na bashi, hope ya kiraki?.
Next Mustapha ya bani sa'ko anjima in munje
makarantar dare zan baki". Tunda ta soma
magana sai yanzu Najwa tai murmushi jin an
ambaci Mustapha . Cikin zolaya Husna ta d'aka
mata duka tai waje, aikuwa a guje ta biyota
kafin ta kamata ta kyalle. Cikin dariya Inna tace
"sababbu kun dawo zaku adabeni".
Cike da haushi ta cire d'ankwalinta ta suri buta
zuwa kewaye (band'aki), Inna kawai ta tsaya
taga gudun ruwanta, saidai bata da alamun
tsayawa ta daura. Cikin hargagi ta daka mata
tsawa." Keee! Najwa ina kalabinki? ('Dan kwali)
cikin basarwa tace "zan d'aura bari in fito". Bata
jira cewartaba ta shiga abinta. Mamaki ya kashe
Inna kwata-kwata Najwa bata jin tsoran fad'anta
mudin akan saka kalabine ko batun Mustapha
tun bata damuwa da lamarin harta soma
damuwa. Tana fitowa ta tareta da balbalin fad'a "wato ke Najwa bakyajin magana ko? Nahanaki zama babu kalabi kin'ki ji ko' uwa uba shiga bayi
babushi, waikin manta band'akine matattarar jinu amma kike 'kuga (saka) kanki ciki babu hijabi, wanda na tabbatar ko adu'arma da 'kyar idan kinayi". Inkin taka biron hanuna ya tanka haka Inna taita bambaminta Najwa tai biris.

Najwah Usmar Salis wadda abokanta suka fi kira
da Nus, d'iya ce ga Malam Usman marigayi tare
da Inna Hafsatu. Su shida iyayansu suka haifa
duk mata. Suna zaune a unguwar dandinshe
cikin 'karamar hukumar dala. Babbar yayarsu
Zainab na auran wani prof a gadon 'kaya
yaranta hud'u. Auwal da Sani da kuma Mahfuz
da Mahfuzaht. Sai mai bimata Saudat. Tana
zaune a unguwar tudun yola yaranta biyu,
Muhseen da Muhseenaht. Sai ta tsakiyar itama
yaranta biyu mai suma Fiddausi. Sai Ayshat ita
kuma tana 'kurfi tana aure bata ta'ba haihuwa
ba. Sai Maryam mai yaro guda tana 'kofar ruwa
sai autarsu Najwa. Mahaifinsu ya jima da rasuwa, tun suna yara. Rainansu da kulawarsu duk 'kar'kashin kulawar Inna Hafsatu. Innarsu macece mafad'aciya sossai. Bata san wargi (raini). Haifafiyar Kano ce unguwar 'kwali wajan gidan sarki hakan mahaifinsu haifafan 'kofar nasarawa ne. Tun bayan rasuwarsa danginsa basa basu wata cikakkiyar kulawa kasancewar shine bare cikinsu. Mahaifiyarsa ta rasu, tun tana kai yaran harta daina. Haka nan duk auran yaranta ita tai fadi tashinta babu taimakonsu. Macece mai zuciyar nema babu sanar da bataiba don rufawa kanta da yaranta asiri. Tana tsaya musu sui karatu kafin aure iyakarsu secondary inyaso inkinje mijinki na muradi kya cigaba. Itace yin surfe, wanki da sauransu. Harta gama auransu yaranta sai autarta Najwa.
Asalin iyayan Inna Hafsatu 'yan 'kasar Niger ne,
kyawawan fararren buzaye masu gashi da kyan
fasai. Doguwar mace sam'bal zubin Karas ba
d'ata ba. Cikin bayin da ake kawowa gidan sarki
aka had'o da mahaifiyarta anan ta had'u da
mahaifinta shima mutumin can ne kasan
cewarsu 'KABILA d'aya ba jinkiri sukai aure.
Inna Hafsat kad'ai suka haifa kyakkyawar mace,
shekarunta sha biyu akai wata annobar kwalara
suka rasa rayukansu. Hakan ya sa Usman yake
tausayinta har ya juye zuwa so ansha fama
kafin auransu saidai ikon Allah. MATAR
MUTUM....hausawa sukace wai 'kabarinsa. Duk
cikin yaranta Najwace ta d'auko komai nata.
Dan haka ina keji da d'iyarta.
Tunda ta gama aurar da yayyanta sai hankalinta
ya kwanta, Najwahce kad'ai gabanta. A da
yaranta makarantar gwamnati suke, amma ganin wadata da bud'i daga ubangiji tare da taimakon surukanta. Najwah na gama primaryn makara huta ta sama mata gurbin karatu a gora
academic. Najwa ta tashi cikin so da kulawar
yayye uwa da mazajan yayyanta. Kullum cikin
samun gata da kulawa take. Saidai duk cikin
yayyunta tafi shiri da Maryam dan haka tafi
zuwa gidanta. Sui tsiya sui dad'i sabida Maryam
akwai tsokana. Duk cikin yaran Innarsu Maryam ita ta kwashe halin Inna, akwaita da fad'a ammafa kan gaskiya batasan raini. Najwa bata da 'kawa ko daya sai ma'kwafciyarsu mai suna Husnah, 'kiriniyarsu iri d'ayace saidai akwai kwanyar nacin karatu. Ga masifaffiyar tsokana akwai wata al'adah guda d'aya da Najwa
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download KADDARARMU CE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album