Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[10/27, 10:33 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: *A GIDANA*

In the name of Allah the most Beneficent the most merciful.
Praise be to Allah lord of the words.
The beneficent the Merciful.
Master of the Day of judgement.
Alone we worship;Alone we ask for help.
Show us the straight way
The way of those on whom Thou has bestowed the Grace, those whose portion
Is not wrath, and who do not go astray.


   Gaisuwa tare da jinjina da fatan alkairi gareku daukacin masoyana, ina mika sakon gaisuwa gareku, dafatan kowa yana lafiya, musulmai da suka rigamu gidan gaskiya Allah ya jikansu, mu da muke da rai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya, masu ciki Allah ya saukesu lafiya, wadanda ke neman haihuwa Allah ya basu, masu neman aikin yi Allah ya taimakesu yasa su samu Ameen suma Ameen.
_Oh ina fatan me karatu yayi saurin cewa Ameen..... lol duk da nasan ke ko kai ka fada.........._

Dafatan za'amin uzurin jina shiru da akai😄

_Sai dai dan Allah inaso mai karatu yamin uzuri akan wannan littafin bazan samu damar yin posting kullum ba saboda wasu dalilai._

Nagode🥰

🍀 *A GIDANA*🍀

*_Na Ayusher Muhd_*

*Shafi na Farko*

Da sauri ta gama shafa hoda sannan ta dau dankwalinta ta daura, agoggo ta kalla sannan ta jawo jakarta da sauri, ta bude wardrobe ta dauko mayafinta ta rike a hannu ta fito.

Kitchen ta nufa dan tasan yana ciki, tana shiga ya juyo ya kalleta yace "Honey an fito?"

Rugumeshi ta matso tai tace "Yau wani irin bacci ne ya kammani dakyar ma bude idona."

Murmushi ya mata sannan ya sumbaci kuncinta yace "your tea."

Dauka tai ta kalleshi sannan ta sumbaceshi itama tace "Thanks love."

"Kin manta ni zan kaiki?"
"Oh! Ashe fa na sallameshi."

Kai ya girgiza yace "Honey a rage fada, dan Allah drivers nawa kika kora?"

"Ka zauna zani da kaina." Ta fada tare da juyowa, da sauri ya riko hannunta yace "na manta sune basaji."

Harararsa tai tace "wato ni uwar fada ko?"

"Nooo inji wa? Yanzu na dau mataki?"

Murmushi tai tace "ni ka bari na tafi da kaina yafi sauki."

Key dinsa ya dauko wanda ke saman fridge yace "muje."

Falo suka fito hannunsu rike da juna, Goggo suka gani zaune tana kallo a falan.

Kusa da ita ta karasa tace "Goggo ina kwanan mu?"

Goggo ta kalleta tace "ni jiya mantawa kikai kince zaki bani kudin anko?"

"Oh na manta, amma ni Goggo wai wani anko ne ku manya daku?"

Fuska ta hade tace "ba sai kin fadamin magana ba, in bazaki bani ba kawai kice bazaki ban ba, fadar maganar na menene?"

Kallan agogo tai ganin lokaci na wucewa tace "zan bashi sai ya kawo miki."

Da sauri tai gaba "ke wlh Goggo, ina laifin ki bari sai ta dawo? Bayan na fiki bukatar kudi yanzu."

Harara ta maka mai tace "wannan damuwarka ce, kuma wlh ka kawon kudina yanda aka baka."

Binta yai da gudu, tana tsaye gaban motarshi yai saurin bude mata sannan ya zagaya ya shiga gun driver.

Yana zama ya tada motar yaja suka bar gidan.

Mai gadin daya bude ta kalla tace "zan turama kudi kaba mai gadi nashi naga wata yazo karshe, sai kaba Goggo na ankon, dan ko tambayarta ban ba nawa ne."

Yai saurin cewa to, kallansa tai tace "ka cinye kudinka ne?"

Kallanta yai sannan yadan sosa keya, ajiyr zuciya tai sannan tace "zan turoma dan dama anyi albashi, sai dai Honey plz adan rage kashe kudi."

Kallar tausayi yai yace " sry Honey."

Murmushi tai ta riko hannunsa da hannunta dayan hannun koma ta dan kurbi tea dinta sannan ta sakeshi ta zuge jakarta ta dauko wasu takardu tana dubawa.

Kallanta yai yace "in kaka nustu kina aiki you look soo......"

Kallan data masa ne yasashi yin dariya ba tare da ya karasa ba, tace "Honey a nemo wani driver din."

Ajiyar zuciya yai yace "wannan karan bari muga wanda zamu samo wata nawa zaiyi."

Kallansa tai tace "zaka fara ko? Wannan sai ya shekara 2 zuwa 3"

Dariya yasa yace "muna fata, amma indai wannan Honey dince hmmm."

Takardun hannunta ta cigaba da dubawa hakan yasashi yin shiru.

Suna isa yai parking, kallansa tai tace "bari na turama yanzu yanda zaka cirar mata nata dana mai gadin."

Yace to.

Nan ta dau waya ta tura mai kudi sannan ta dau jakarta ta fito, harta kusa shiga taji ya kirata, juyowa tai ya taho da sauri rike da tea dinta ya mika mata, thanks ta fada tare da nuna cup din alama ta amsa ta gode.

Ciki ta shiga, tana shiga cikin bakin kofar ta hade fuska tamau, duk inda ta wuce gaisheta sukeyi tana amsawa tana wucewa.

Tana shiga office dinta ta ajiye jakarta da tea din sannan ta juyo ta fito, gun program din ta fara shiga, kallan masu aikin gun tai wadanda ke kokarin ganin komai ya tafi daidai tai tace " acanza wannan background din is too light."

Da sauri yace "okay."

Kallan jikin camera's din tai kafin tace "meye hakan? Sau nawa zance a rage contrasts din nan?"

Da sauri yace "am sorry, yanzu zan gyara."

Dan ajiyar zuciya tai sannan ta duduba hasken light din gun sai da ta tabbatar komai yayi ta kalli agoggo sannan tace "is live so you have to be extra careful."

Da sauri sukace okay.



*********

  Da sauri ya fito daga soronsa ya fita waje, dan yanda ake kwalla sallama sannan daga jin muryar ya fahimci wanene.

Dan dattijon na ganinsa ya murtuke fuska tamau ya kalleshi rai a bace yace "Khalid karka batamin rai kar kuma ka bata min lokaci bani kudina."

Khalid ne ya kalleshi yace "Malam Mamman dan Allah kayi hakuri, ga dubu daya dazun nan aka biyani kudin fenti, gobe insha Allah......."

Dubu dayar ya amsa yace "karfa ka maidani dan iska, nan nan ubanka yai hatsari kazo kamar zakai min kuka na ara maka dubu goma ka kaishi asibiti yau wata hudu kenan amma haryanzu dubu biyar ka bani da wannan ta yau kenan, nifa shi yasa banasan harka da matsiyata wlh, ubanka yaki barinka kai aikin noma wai shi a dole sai kayi boko, to dakagama bokon uban me ka tsinana? Uban me kake dashi? Dubu goma ta gagareka biya a wata hudu? To wlh ni bazan dauki iskanci ba."

Khalid yace "kayi hakuri insha Allah zuwa karshen watan nan zan hada maka."

Tsaki yaja sannan ya wuce yana tafe yana masifa.

Shiru khalid yai sannan ya wuce ciki.

Mahaifiyarsa na tsaye a tsakar gida yana shigowa ta matso tace "Malam Mamman ne ko?"

Murmushi yai yace "eh amma bakomai Umma, ina Asiya? Ta biya kudin makarantar dana bata jiya?"

Tace "ta biya, haryanzu ba labari?"

Yace "Karki damu Umma insha Allah zan samu aiki."
Idanunta ne suka ciciko tace "shekara 4 kenan da gama karatunka, sai dai haryau babu labari sai uban wahalar siyan form kake kana zuwa yin jarabawa."

Murmushi yai sannan ya danyi gaba yace "kiyi tamin addu'a, lokaci ne."

Kallan tausayi tamai, ciki ya shiga inda mahaifinsa ke kwance ba lafiya, saboda hatsarin motar dayai wanda yasa kafarsa daya ta samu matsala, ya dade yana sana'ar tokin mota sai dai lokaci daya tsautsayi ya hau kanshi komai ya zama labari.

  Kusa dashi yaje yace "Abba kanasan wani abu ne? Dan zan wuce gun sana'ar mu ne."

Hannunsa ya riko yace "Allah ya taimaka, in inasan wani abu zan sanar da mamanka."

To saina dawo.
Abinda ya fada kenan ya mike.

Abba yace "adawo lafiya Khalid."

Fitowa yai daga dakin ya kalli Umma yace "na wuce."

Wayarsa ce tai kara ya dauka da sauri, Salmanu! Ya?"

"Kana ina?"
  "Ina danbatta ya akai?"

Salmanu yace "zaka samu zuwa kano yanzu? Dan wlh wani aiki ne muka samu gidan akwai maiko, kai sauri kazo."

Da sauri Khalid yace "turomin address din gani nan zuwa."

Nan ya kashe wayar yao waje da sauri.

Jakarsa kawai ya dauka a soro ya fita, yana zuwa ya samu mota ya hau ya nufi kano.


**********

A bangaren Adamu kuwa yana ajiyeta yai wata yar kara tare da duba account dinsa, gani kudi yasashi yar taka karamar rawa daga zaune, da sauri ya juya kan mota ya nufi Atm, yana zuwa yaciri kudin Goggo da za’a bata dana mai gadi, sannan ya ciri dubo goma yasa a aljihu, kida ya saka a motar yana tafe yana kada kai, yau akwai jin dadi a majalisa.

Jin dadin yanayi yasashi kawai yai ta dan yawo a gari, nishadi kawai yakeyi ji yake duk duniya ba wanda ya kaishi jin dadi.

Tsayawa yai yana kallan wanda ke kokarin tsalaka titi.

Fuskar sa ya kara kallo sai dai ya tsallaka titi, da sauri yaja mota ya nufi gefen titi yana binshi.

Horn din motar dayajine ya sashi dakatawa, juyowa yai cikin mamaki dan dai ba tare hanya yai ba.

Juyawa yai zai cigaba da tafiyar sa yaji ance “Danbatta.”

Cikin mamaki ya juyo, bai gane mai maganar ba hakan yasa ya dan matso kadan.

Hannu ya daga mai tare da nunashi yace “Danbatta kaine wlh.”

Khalid ya kalleshi yanzu kam ya ganeshi cikin mamaki yace “Adam?”

Dariya Adam yai yace “Danbatta cinye duu daga ina haka?”

Yace “daga danbatta saukata kenan.”

Shigo na karasa dakai.

Kallansa yace “karka damu yanzu zan nemi taxi ko bus.”


Dariyar dake neman kofcemai ya kara dannewa yace “shigo dalla.”

Ganin suna bata lokaci yasashi zagayowa ya shiga.

Adam ya kalleshi yace “ikon Allah, kwaro ashe da raban zan ganka.”

Ran Khalid yadan soso sai dai bai nuna ba yace “inasu Zakar?”

“Suna nan lfy, sai dai duk yanzu kowa hidimar gabansa yakeyi, kasan yanzu Zakar yana aiki a kaduna, Mansir kuma yana aiki a Abuja.”

Khalid yai yake “masha Allah.”

Adamu ya kara kallan jikinsa yace “kwaro ya? Kaifa? An fara aiki? A wani asibitin ko babban company?”

Khalid ya kalleshi yace “me kake nufi?”

Adamu yai dariya yace “me nake nufi kuwa? Kawai dai naga ne kai jarabawarka bazata wahalar dakai ba, duk fa shekararmu kai kadai ne ka fita da A class kaga kuwa ai kai sai babban company.”

Adamu ransa ya baci, kallansa yai yace “ai ba wannan bane hujja komai lokaci ne.”

Kai ya jinjina yace “haka.”

Sannan ya ja mota, shiru sukai kafin Adamu yace “yanzu dai ba aiki kenan kake san cewa ko me?”

“Eh.”
“Oh Allah kenan yanda kaci karatu waya taba kawo haka?”
Kallansa yai yace “saukeni anan, anan zan sauka.”

Nan?

Khalid yace “eh.”

Adam yai parking sannan yace “to ya? Ko na samoma aiki? Dan ni bana aiki kasan ni banasan wahala sannan jarabawa ta ma dai to, sai a hankali, sai dai matata akwai kudi, tana neman driver ko kana sha’awa na samoma?”

Kallanshi Khalid yai cikin mamaki, Adam yace “ya? Baka yarda bane? Wlh bana aiki, sai dai ta ko ina a jiki nake.”

Khalid yace “ba laifi.”

Har ya bude motar zai sauka Adam ya zaro kudi yace “ga wannan.”

Khalid ya kalleshi yace “no, karka damu.”

“Na manta ashe Mr Right ne, nasan bazaka amsa ba, amma ga numberta in kanasan aikin kamin magana.”

Numbersa ya rubuta a jikin paper ya bashi.

Khalid ya amsa kawai ya fita rai a bace.

Adam yana ganin ya fita ya tuntsire da wata muguwar dariya, da sauri ya kira Zakari.

Nan ya fesa mai, ya kira Mansir shima ya fesa mai.

Dariya kam yashata har cikinsa sai daya amsa, sai a lokacin ya tuna ashefa baici abincin safe ba......

Khalid kam yana sauka ya nemi taxi ya karasa inda zaije.


*Ayusher Muhd🏌🏻‍♀*
[10/27, 10:33 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: 🍀 *A GIDANA*🍀

Haske Writers Association💡

Shafi na biyu

Wattpad/@AyusherMohd.

******

  Khalid yana sauka ya wuce inda Salmanu yamai kwatance, ganin anata aiki agun yasa ya gane ya iso, da sauri yasa hannu ya dauko wayarsa ya kirashi.

Jiki a sanyaye Salmanu ya daga yace "Khalid!"

"Na iso, kana ina?"

Salmanu yace "bari nazo." Ya kashe wayar.
Bai jima ba sai ga shi nan ya fito, Khalid na ganinsa ya matsa gun da sauri yace "ya? Har an fara?"

Cikin rashin jin dadi Salmanu yace "Khalid kayi hakuri wai mutanen da sukeso sun isa, ma fada musu akwai sauran daya da zai karaso yanzu sunce wai a'a iya mutum biyar zasu dauka."

Murmushi yai tare da dan dafashi yace "bakomai, shiyasa duk kai wani iri?"

Kallansa yai yace "Allah duk abin ne yaban haushi, gashi ni kuma wlh kudin nakeso kasan ina tara lefe da wlh na barma kayi."

Khalid yai dariya yace "Just forget, kaidai yanzu ka shiga kayi aikinka, kafin kai laifi."

Salmanu ya dauko dari biyu yace "gashi dan Allah na asarar mota dana saka."

"Kai ka sani? Ko na sa kaina?"

Salmanu yace "ni na saka wlh."

Khalid ya zare hannunsa daga kafadarsa yace "Good luck ni nayi nan."

Yai gaba ya barshi rike da dari biyun, Salmanu ya bishi da kallo a ransa yana jin haushin wannan lamari na kasarmu, bazai manta yanda Khalid yai karatu a makaranta ba, duk wani abu da za'ai a faculty's dinsu, shine yake wakiltarsu, shine yi musu tutorials da sauransu amma dan bashida hanya gashi nan ko karamin teaching ya kasa samu.

Khalid kam yana tafe yana tunanin kalaman Adam, ba shakka ransa ya sosu da yanda ya mai magana, dan duk wanda ya kalleshi ya kalli yanayinsa yasan yanayine na dauriya da wahala, amma wai tambayarsa yakeyi wai wani company din yake aiki?
Murmushin takaici yai tare da sa hannu a aljihunsa, dauramai dari uku.

Ajiyar zuciya yai dan wata yunwa da yakeji gashi kuma kudin motar komawa ma yamai kadan.

Mezai danyi yadan samu kudin da zaici abinci ya kara kudin mota?

*********
"Duka duka anan muka kawo karshen shirin mu na Yammacin mu a Yau, sai mun hadu daku a shiri na gaba.

Ni Zainab Aliyu Tahir nake cewa mu huta lafiya."

Ana dauke camera daga kanta ta shiga bubuga kafadarta saboda dan gajiyar datai, kallanta staffs din gun sukai sukace "Hajiya akoda yaushe ke ta dabance, in kina shiri gaba daya komai tsayawa yakeyi, mu kanmu rasa wayar da zamu dauka da texts din da zamu karanta mukeyo."

Kallan mai maganar tai tace "kuma sannunku da kokari."

Ruwan dake gabanta ta dauka ta sha sannan ta mike tace "Ina Ramla?"

Bata nan, dazu kuma tana nan a tsaye.

"A ce mata ta sameni a office."
Ta fada tare da wucewa.

Zama tai a office dinta tare da daukan wasu takardu tana dubawa.

Knocking din datajine yasa tace "shigo."
Ramla ta shigo cikin yanayin tsoro dan ta tabbatar laifi tai, ko kofar bata maida ta rufe ba ta watso mata takardun dake hannunta.
Gaban Ramla ya fadi ta kalleta a tsorace.

"Me kika dauki media?"
Murya na rawa tace "media? Aunty Zee?"

Fuska ta daure sosai, tace "ya akai kika samu aiki a nan?"

Bakinta na rawa tace "munyi interview......"

Bashi nake tambayarki ba, kallanta tai a tsorace tace "munzo munyi audition...."

"Kin min shiru ko sai ranki ya baci? Karatun aikin jarida kikai ko me?"
Da sauri tace "shinai."

"Then uban me kika rubutamin?"

Idanunta ne ya ciciko tace "binciken da kikace naje nai...."

Ki koma kije ki sake report din nan sannan don't expect me in sake kiranki na miki bayani, ma tabbatar kinsan halina kinji me nakeyi in har nama mutum magana."

Hawaye ne suka zubo mata tace "insha Allah."
Haka ta tsugunna ta shiga kwashe takardunta, tana gamawa ta fita tana hawaye.

Zainab ta dansa hannu akanta dake dan sara mata, agoggo ta kalla, ta kusa tashi, nan ta dau waya ta kira Adam.

********

Shikam Adam yana rabuwa da Khalid ya wuce majalisarsu ta yan zaman kashe wando, suka sha hira da gulma, akai ta fasamai kai akan yanda ba cas ba as sai jin dadin rayuwa da yakeyi.

Dariya yasa sosai yace "nifa dama can ba mutum bane mai san wahala dan dai Allah bai bani dama bane, shiyasa yanzu da Allah yaban dama nake morar jin dadi na."

Nazifi ya kalleshi yace "wai da gaske kake ma ka nemi aikin kuwa?"
Yace "tab ai ko form ban taba siya ba, itadai ta dauka samune banyi ba."

Nazifi yace "Shegen aikai Allah ya maka baiwar sanin yanda zaka so kanka."

Adamu yace "kasan Ita akwai san bin abu yanda ya kamata, danace tasa a nemomin aiki fa cewa wai corruption ne."

Nazifi yace "ai shiyasa nakejin haushin yar iskar Kubran nan, sai anyi magana tace batada kudi, ni wlh haushi take bani, da alama aure zan sake wlh, kuma Hajiya zan nema nima."

Wata muguwar dariya Adam ya saki yace "tab amma lalai kai dan mugun san banza ne, irinsu Zee dita an fada maka sunada yawa ne??"
Nazifi yace "mudai yau mijin Hajiya dan Allah ka dubemu mu dan tauna mai yaji yaji."

Nan ya zaro dubu biyo aka siyo musu balango suka ci suka kora da lemo, sannan ya mike ya nufi gida.

Goggo na zaune tanata kallo tana dariyar ta ya shigo.
Tana ganinshi ta mike tace " Ina ka tsaya ne?"

Kallanta yai sannan ya kalli Tv yace "wai Goggo dan Allah bakya gajiya ke da kallo ne? Kullum kina gaban kujera kina kallo."

Tace "wannan ba damuwarka bane, sannan in na zauna a dakin ma me zanyi? Ba gwara nai kallo na debe kewa ba, ni ba wannan ba, bani kudina."

"Wai nawane ankon? Ai baki fadi kudin ba."

Kallansa tai tace "ban san fa iya shege ce maka akai bansan me nake ba? Ni bani kudina bansan jan magana."

Dubu biyar ya zaro ya mika mata yace "gashinan, amma wlh nasan ankon nan baifi dubu 3 ba."

Amsa tai sannan tace "wai ni Adamu wannan kudinka ne?"
"Na matata ne."
Komawa tai ta zauna tace "daga baya kenan, kudi ba naka ba sai bin ba'asi, wannan da kaine ma kake aikin kila ba ci zanyi ba."

Wucewa ciki yai ya kwanta, kan kace me bacci yayi gaba dashi.

Baccinsa yasha sosai, dan wayar Zainab ce ta tasheshi.

Yana ganin sunanta ya kalli agoggo sannan ya mike zaune.

"Honey kana ina?"

Cikin maganar bacci yace "ina gida na sha bacci ne."
Tace "nakusa  tashi inka samu driver din ka turoshi yazo ya dauken."

Da sauri yace "yanzu zanzo, bansamu ba tukunna."

Kashe wayar tai sannan ta duba laptop din dake gabanta, tana gamawa ta fara hada kayanta.

Adam kam suna gama magana ya sauko daga kan gado, da sauri ya dau key zai fita yaji fitsari, nan ya koma toilet yai sannan ya fito ko Goggo baima magana ba wacce ke zaune tana kallo tana cin abinci.

Da sauri ya shiga mota ya ja ya fita, dole na nemo driver bazan iya yawon nan ba, tuno da Khalid dayai ne yasashi yin dogon tsaki, ya akai ban amshi number shi ba? Ai da masifa da sai na sashi yin aikin nan.

Yana isa ya kirata a waya.
Nan tai sallama dasu ta fito.

Tana shiga ya kalleta cikin kulawa yace "Ayya Honey da alama kin gaji."

Murmushi tai tace "kawai dai fadan da ake sanine yake sani gajiya."

Hannunta ya riko ya sa akan kuncinsa yace "nasan duk wanda yaga shirin ki na yau zai ce waccece wannan? Ni kuma da ina gun zanyi saurin cewa My Wife, da magana ne."

Yanzu kam dariya tadanyi sannan ta zare hannunta tace "Honey."

Yace "kinga gashi harna saki kin ware."

Murmushi tai sannan tace "as always."

Mota ya tada dannan ya juya suka hau kan titi, kallanta yai yace "Honey zaki iya tuna Kwaro? Cinye du?"

Kallansa tai tace "wanda kake yawan labarinsa? Wanda ya maidaku hoto?"

Da sauri yace "shi shi, ai na fada miki komai malamai sai dai suce shi ko?" Tace "eh, ya akai?"

Wata dariya ya sheka yace "kinsan yau na ganshi?"

Kallan mamaki tamai tace how?

Cikin zumudi yace "a hanya, kin ganshi?" Ha ha ha unbelievable wai bai samu aiki ba, sannan kina kallanshi kamar talakan kauyen."

Kallansa tai yanda yaketa dariya tace "lalai Honey to menene na dariya?"

Kallanta yai yace "can you imagine?"

Tace "a yanayin kasarmu sosai, saboda mutane nawa ne suka dace suka cancanta a basu aiki amma suna nan ba labari?"

Dariya yake sosai yana cewa "ban taba kawowa ba wlh."

Kallan mamaki take mai, dan haryanzu bataga abin dariya ba.

Da kyar ya gama dariyar sannan yace "ai naji haushi wlh ban amshi number shi ba."

Kallansa tai batace komai ba.
Yace "namai rayin aikin driver dinki ai, wayyo Allah ubangiji yasa ya amsa."

"Driver?" Ta fada tana kallansa, yace "eh."

Wani murmushi tai sannan tace "baka tunanin u hurt his pride?"

Yace "taimakon sa zanyi ai, dayaje yana neman abinyi ga aiki a gida?"

Kanta tasa jikin window dan ta kasa fahimtar me yake nufi.

Adam ya jawo hannunta yace "me? Bakyaso?"

Tace "no, kawai dai ina ganin kamar bai kamata ba, abokinka ne fa?"

Ganin yanda ta dau lamarin yasa yai saurin canza maganarsa yace "na san bai kamata ba, amma bansan yands zanyi na taimakeshi ba, kins gani nima fama nake da neman aikin nan."

Murmushi tai tace "na fahimta yanzu, amma dai still da baka mai zancen ba, ba lalai ya fahimci dalilinka ba."

Hakane kuma, gashi banda numbersa.

Tace "kawai dai Allah yasa yai calling dinka back sai ka nusar dashi."

Kai ya jinjina sannan yace "Thanks."

Dame?

"Komai ma."
Murmushi sukama juna.


***************

Khalid kam mariri ya shiga yaje gun masu ruwa ya amsa kura akan zai biyasu duk kaiwa daya, haka yai tayi ya hada dubu daya ya nemi abinci yaci yahau mota ya koma gida.

Yana shiga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment