Join Our WhatsApp Group

MANNUBIYA BOOK 1 Complete Hausa Novel Document by MANNUBIYA BOOK 1


MANNUBIYA BOOK 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 137560



MANNUBIYA BOOK 1

Reading Time: 11 Hours

Added On: 21, Nov 2023

Author: Humayrah Bulama ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ELEGANT ONLINE

Author Phone : 09034413252

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 690.92 kb

File Type: txt

Views: 533+

Download: 521+

Last download: 14 hours ago

Description/Story: MANNUBIYA
O 1
NA
Humayrah Bulama


Daga k’ungiyar ELEGANT ONLINE ✍🏽

__________________

A shekarar 1990, A garin Kano.

A hankali yake tu’kin motarsa k’irar Daewo Nubira.

Kamar ba Ya so ya k’arasa inda
Zai je saboda yanayin tuk’in na sa daya ke yi a gefen titi a hankali, a hankali.
Sannu sannu Bata hana zuwa… in ji malam bahaushe don
A hakan ya samu ya k’arasa gidan shi dake unguwar sharad’a. Ko da ya k’arasa bakin gate din bai yi horn ba sai da mai gadin da kan sa ya ji tsayuwar mota ya lek’o
Tukunna ya koma da sauri ya wangale gate d’in Madaidaicin flat house d’in. Jikinsa na rawa
Sakamakon ganin uban gidan nashi ne ke tsaye a waje.

Ko da ya shiga ya k’arasa yayi parking
Kashe motar kawai ya yi ya d’aura kanshi a jikin sitiyarin motar ba tare da ya fito daga motar ba.


Yafi minti talatin a haka yana tunani shi ka’dai Kafin tashi d’aya gaban sa ya yanke ya fa’di.
Ransa ya sake b’aci
Sakamokon Jin fitowar ta .
Ko ba a fadi mishi ba ya San Khadijah ce ,tunda basu da me aiki a gidan daga shi sai ita sai mai gadi Wanda yake musu har wankin kayansu da guga.


Shiruu kawai ya yi yana jin ta ta rufe k’ofar parlourn data bu’de ta fito ta tunkaro motar Da yake ciki a zaune.

As he expected, tana zuwa
Ta banka’da k’ofar motar da k’arfi.

Ko sannu da zuwa babu
Cikin fushi ta ce “Shine sai da ka kira Abba ko? Cin fuska da
rashin adalcin da ka kusan aikatawa bai isheka ba.

Shine an kashe magana an gyara komai zaka wani wuce ka kira Abba, Me kenan kake so
Yanzu? So kake ya goya maka baya ko me?”

Bata jira Jan numfashi ba a hassale ta d’aura da cewa
“Tou bari kaji ,Ko ya Goya maka baya abinda kake so ba zai tab’a faruwa ba Wallahi, Tunda in kana tunanin Abba yana bayan ka ni kuma daddy yana baya na. Ta k’arashe maganar Tata cikin tsananin bacin rai da takaici.

Tun lokacin data iso ta fara magana Shima ya Ha’de rai ,
Fuskar nan tamau kamar bai tab’a dariya ba.
Ba tare daya kalle ta ba
ya zare key d’in motar
Ya d’auki abubuwan buk’atar shi ya mik’e ya fito daga motar.
Ko kallon inda take bai yi ba
Ya fara k’ok’arin wuceta .

Da dan karfi Sannan da sauri
Ta rik’o hannunshi
Cikin tsananin bacin rai ta ce
“IMAM ,Wallahi na fi k’arfin ka wulak’anta ni ,
Ai so ba hauka bane,bar ganin wai Ina sonka
Wallahi idan baka janye maganar nan ba zan maka abinda sai ka yi daka sanin ha’duwa da ita kanta khadijar zan Baka mamaki zan sanyaka ……..”

“Sannu Uwarsa”

Suka ji Muryar Abba daga sama
Wanda ba su san lokacin daya shigo ba
ta daki dodon kunnuwansu .

Tabbas ,ta sha jinin jikinta amman sam
Kishi da Bak’in cikin da yake a kwance a kan kyakkyawar farar fuskarta be Kau ba Sannan zuciyarta banda turnik’i da tafarfasa ba abunda take yi.

Ganin yanda Abban ya kafeta da idanuwa yana me
K’arasowa inda suke ne
Yasa ta d’an sunkuyar da kanta k’asa da sauri kuma ta cikawa
Imam din hannu .

Abban yana k’arasowa
Imam ya durk’usa har k’asa ya gaida shi ,bayan sun gaisa
Ya ‘dora da cewa
“Abba ai da ka bari mun k’araso
Don Yanxu nake shirin in yi wanka mu karaso wajen naka.”
“kada ka damu ai
Babu nisa Kuma Ina buk’atar yin tattaki din dama”
Haka kawai Abban yace Yana kallon khadija wadda take gaishe shi “ ina wuni”
Cikin d’an russunawa .
Bai amsata ba,ya juya ya bi bayan Imam
Wanda ya juya ya nufi k’ofar parlourn nasu da d’an sauri yana ce wa “Bismillah Abba. Da kansa Imam ‘din ya shiga ya kawo masa lemo mai sanyi da ruwa sai ‘d’an snacks a Gefe.”
Dan khadija Bata riga ta shiga parlourn ba .

Tabbas yanda taga abba tasan ba ze bi bayan ta ba
Sannan ba
‘daga mata kafa
Zai yi ba yau ,kuma tasan Abban nasu
Baya tolerating nonsense da tirjiya .

Zata iya cewa Bata tab’a ganin soyayyar ‘ya da uba irin ta Abban ta da sister din ta ba Amman tunda tayi mishi lefi ya fita harkarta
Ya yafe ta
Yanxu hatta ita kanta Bata San inda yayar ta ta take ba .

Ayanxu
Tsoron ta daya
Shine
kar ya goyawa Imam baya kuma ya turje Akan se ta bi ta yarda da abunda Imam din yake so
Dan inde haka ta faru
Tou wallahi ta shiga ukun ta .

Ko da ace ba Imam ta aura ba ,
Bata jin zata iya zama da kishiya ,
Ballantana kuma Imam din ne ,
Ayanda take masifar sonshi
Bata Jin xata iya jurar ganin wata ‘ya mace a matsayin matar shi bayan ita .Watan ma kuma Khadija ,
Yarinyar data san yana tsana nin so
Domin ko
Satin daya gabata
Haka ya fito kiri kiri
ya ce mata albarkacin sunan su yaxo daya ne yasanya
yake mata raha
yake dan kulata

…….
Tasan rashin shigarta Akan lokaci
Ka iya sake hasssala Abba,don haka ta yi ‘ko’kari ta tsayar da kukan nata da kyar
Ta goge hawayen ta
Ta nufi parlour itama .

Abba yana zaune a kan kujera
Imam a gefen shi
A zaune a kasa

A
Haka ta shiga ta samesu ,
Dan haka itama ta karasa ta zauna a kasa dayan gefen kafar Abban.


Ba tare daya kalleta ba yace
‘’Se yanzu kika ga daman shigowa kenan ‘’
Be Bata damar cewa komai ba
Ya sake cewa
‘’Inaso ki nutsu kiji abunda xan fada miki yanxu
Na farko shawarace
Na biyu ma kmr shawarar ce
Na uku kuma umarnine
Kuma dole kiji, Sannan kiyi .

Still be dau lokaci ba ya daura da cewa
‘’In mata uku Imam yace xe k’aro baki da hurumin shiga Kice A’a ‘’.
‘’Ki zauna a matsayin ki
Sannan ki yiwa mijinki biyayya ki bashi goyon baya ,
Ni ma a matsayina na mahaifinki
Kiyimin biyyayya ki yi abunda nace ‘’.

‘’Khadija,!
Imam ze Kara aure
Banason in ji wata matsala ta kuma kunno Kai daga gareki
Har ayi auren nan a gama
Ina ba haka ba Wallahi …..’’

Kukan data rushe dashi kmr Ana yanka ta ne yasa duk suka xuba mata ido kawai ,
Suna kallon ikon Allah .


Cikin kukan tace
Haba Abba
Ko
Wata na biyu ban gama rufawa a cikin gidan nan ba
ace za ayimin kishiya
Kuma Kuce inyi hakuri inyi shiru ?,
Shi meyasa ba zai hakura ba ,
Daddy fa yace be yadda ba bayason ya sake Jin maganar.

Cikin katse ta Abban yace
‘’That was when daddyn besan cewa ita wachchar khadijan ya fara so ba
Kuma itace budurwar sa tun asalin farko ba ,
Bari kiji tun Kafin shi Daddyn ya fara maganar ku ke da Imam
Already
Imam yayi min maganar khadija ,
Maganar aurenki ce ta sanya ya daga kafa
Dan haka yanxu Banga dalilin da zai sanya ya fasa aurenta saboda ke a karo na biyu ba Wallahi ‘’.


Cikin kuka tace
‘’Abba har fa ciki ta zubar
Kuma tsabar cin fuska
Har gidan nan ya kawo min ita
Lokacin
ko sati biyu ban yiba
a chan boys quarters din akayi jinyar ta
Saboda Bata da kowa ,
Taya za a hadani kishi da wadda ta gama shigomin gida ta San sirrina
Wadda Bata da iyaye
Me yawo a titi suna tallan Nono
…..’’

‘’Ya Isa haka ,khadija ‘’!
Abban ya daka mata tsawa cikin tarar numfashinta

Kafin yace
‘’Tashi ki tafi ki bani guri ‘’

Zata yi magana ya kuma daka mata wata uwar tsawar dan haka taja ta mike ta wuce ta shige daki tana wani irin kuka .

Ko da ta shiga dakin ma
ta jima
tana kukan Kafin daga karshe ta
Yanke shawarar Neman
‘Larai ‘

Saboda ta Lura Hatta mahaifiyarta ita ma bayan Abban take bi .
Iyayen ta sunada matukar kawaici
ta San Imam baya son ta
Biyayya ce ta sanya ya aureta,
Shiyasa su kuma iyayenta baxasu taba goyon bayan ta ba
Saboda
Gudun Samun matsala da
‘family frnds ‘d’in nasu .

Shiyasa gwara ta nemawa kanta mafita
Tun Kafin kawaicin fulanin iyayenta ya cutar da ita .

A nata lissafin
kamata yayi a ce an barta da Imam ta juyo da hankalinshi gareta ,
Bawai a hadata kishi da wata chan daban wadda zata zo ta lalata komai ta kuma janye mata hankalin masiyo ba ….

Khadija Tana shigewa ciki
Abba ya dan gyara zama ya kalli Imam kafin yace
‘’Naji Khadija ta fadi wani Abu wanda ban san dashi Akan khadijan da kake son ka auro ba
Ina fatan zaka cemin ba Dede bane ba .’’

Lumshe idanu Imam yayi
Kafin ya shafa farar fuskarshi
da tafin hannunshi ,
wanda tayi jajir zuwa yanzu tsabar shiga tashin hankali .

Abba. Is his only hope yasan shi kadai ze iya convincing su daddy su barshi ya auri khadija.
Abunda yaketa tsoro dama shine
kar su san kaddarar data afka wa khadijan dan yasan Muddin suka sani da wuya Abban shima ya yarda

Seda yaji Abban ya sake cewa
‘’Imam ,kayi shiru ‘’

Tukunna Ahankali ya bude idanunshi
Cikin sanyin jiki yace

‘’am Abba
Kmr yanda na gaya maka
Khadija Bata da kowa
Ita da Y’ar uwarta na sani tun farko suna kawo mana Nono office
Se kuma wani Uncle din su data taba hadani dashi
Wanda suke a gidanshi ,
A halin yanzu
Shima ya rasu
Kuma dama
matar tashi azabtar dasu takeyi
Tun a lokacin dayake a raye ma .

Shiyasa
Yana rasuwa ta tartara ta barsu ta yi gaba .
Su sunce
min Uncle din nasu da Baban su kawai suka sani
Ba su taba xuwa garin suba bama su dan garin ba har Baban ya rasu yanxu gashi shima kawun nasu ya rasu .
Shiyasa tun a lokacin naso in auri khadijar saboda itama yayar ta miji ya fito mata ta auri wani me mata uku da yara ashirin a layin nasu Amman yace ba zai rike Khadijah ba

Nasan zaman ta ita kadai akwai hadari
Shi kuma Daddy ya dage Akan sede ayi auren mu da Khadija tunda an Riga an gama magana

Ko uzurina be tsaya yaji ba
Gani yake yi kamar turjiya nake shirin mishi
Shiyasa na hakura
A wannan lokacin
kmr yanda kace inyi hakurin .

Itama ba yadda Banyi da ita Akan ta biyo ni ba Amman tace Zata iya zama ita kadai

Ni kuma abubuwa sun sha min Kai
A wannan lokacin
Ga hidimar biki
Ga aiki
A wannan tsakan Kanin ne aka samu wani Mara Imani yaje yayi mata fyade
Sam ba laifinta bane
Saboda seda tayi kwana biyu a asibiti Batasan ma a ina kanta yake ba

Tun daga lokacin naki amincewa taci gaba da xama a gidan ita kadai
Laifina daya dana kawota nan
Nasan be kamata in kawota nan ba
Tunda gidan aure na ne
Amman banida choice
Tunda su daddy baxasu Bari in Kai musu ita Chan ba
Ba tare da sunsan wacece ita ba
Gashi cikin data samu ata dalilin kaddarar data afka mata
Yaxo da matsala
Ana yin sati biyu ta fara bleeding muna xuwa asibiti ya zube.
Ga rashin lafiya ga rashin safety da shelter,
Shiyasa na kawota nan ita da nurse
Kuma
tunda khadija tayi bincike ta gano asalin gaskiya ta fatattakesu
Se da nayi kwana uku tukunna na nemota da kyar ‘’.

Shiruu ya danyi Kafin ya daura da cewa
‘’Dan Allah Abba ka duba Lamarin nan
Mu taru ni da Kai mu ceto rayuwar baiwar Allah ‘’.

ya karashe maganar cikin hade hannuwanshi kamr xe fashe da kuka .


Numfashi Abban ya fesar
Bayan dogon Nazari

Kafin ya kalli Imam din yace
‘’Zan ha’daka da driver gobe
ku je ayi duk wasu gwaje gwaje da suka kamata
Allah ya sanya alkhairi
Allah yayi maka albarka ,
Zanyiwa daddyn naku magana
Karka damu ze fahimta .’’


Wani tsananin sanyi ne ya lullube Imam ,har seda wasu hawayen farin ciki suka wanke mishi fuska .

Murmushi kawai Abban yayi ,
Daga haka ya mike da shirin tafiya .
Tsakanin uba da ‘ya se Allah
Yasan abunda yayi
Yake kuma shirin yi
Tabbas shine Dede ,
Amma kuma a take tausayin ‘yar shi se ya lullubeshi ,
Dan Tabbas yasan tunda har Imam ya rufe ido ya sake mishi zancen wata
Bayan ya aura mishi ‘yar shi
Ko watanni biyu ba a rufe ba ,
Tou fa ba karamin so yakeyiwa
Wachchar bafulatanar me tallan Nono ba .

Har ga Allah
Da ya ji shiru bayan wata daya da auren su Imam din
ya dauka ya hakura ne ,
Ashe abun yananan .
Tabbas rayuwar ‘yar shi khadija
Tana cikin garari .
Saboda tun shekara daya da ta gabata
A lokacin da aka fara maganar aurensu har kawo yanxu
Be taba ganin digon son ‘yar tashi a cikin idanun Imam ba .

Daddy is his best frnd
Tun yarinta ,Ba da ban haka da yanda yaga Daddyn ya nace da son yaga ya kulla aure a tsakanin su ba
Da babu dalilin da zai sanya ya yarda da auren khadjan shi da
Imam,
Tunda ya San
ba sonta yakeyi ba .

Yana fatan su samu su da sasanta ya so ta wata rana
Tou
Yanxu kuma gashi xe auri wadda yakeso .
Fatanshi daya Allah yasa khadijan tayi hankali ta kwantar da hankalinta tayi biyayya ta zauna lafiya
Watakila ta samu matsugunni a xuciyar mijinta
In ba haka ba kuwa
Bayajin tanada rabo a xuciyar Imam ……..


An dan Kai ruwa rana Kafin
Daddy ya yarda aka daura auren khadija da Imam a cikin sati daya ,
Ba kalar haukar da Khadija batayiba
Har kalanzir ta Barba’da a gidan yana bacci
Lokacin ana ‘I gobe ‘daurin auren
Allah ya taimaka
ya ji warin kalanzir din ya farka da wuri .
Yana xuwa ya tarar da ita tana kokarin kyasta ashana
Da kyar ya samu ya karbe
Yana jefar wa ta rarumo wuka,
Ganin fa dagaske kishi ya haukatata in ya barta kashe shi zatayi
Ne
Yasa ya fincikota dakyar ya fitar ya saka ta a mota .

Iyayenta kamar iyayenshi ne
Dan ze iya cewa
Shi da ‘dan uwanshi especially ma shi in particular kusan a hannun maman ta ma ya girma
Amman ya kamata a takawa haukar ta burki
Tun Kafin tayi ‘barna .


Ba dan yaso ba
Haka ya Kai ta gidansu ya fadawa su Abba duk abunda takeyi mishi
Har kokarin kashe shi data fara yau dinnan .

Sallamar shi kawai Abba yayi
Bayan ya bashi hakuri
Daga haka ya wuce...


Read / Download MANNUBIYA BOOK 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album