Join Our WhatsApp Group

BARR BASSAM Complete Hausa Novel Document by BARR BASSAM


BARR BASSAM

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 89579



BARR BASSAM

Reading Time: 7 Hours

Added On: 26, Sep 2023

Author: Shawty ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 480.83 kb

File Type: txt

Views: 698+

Download: 512+

Last download: 5 days ago

Description/Story: [1/7, 5:09 PM] ‪+234 813 551 5123‬: *BARR. BASSAM*
(The Gallant) ❣


An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__

By Shawty 💕


All rights are reserved. Any alteration of this write-up in any way renders it invalid.



*DISCLAIMER*
*All characters, character names, location names, properties used, names assigned are all fictitious and imaginary. If there is any resemblance to any person, location, property etc. It is purely co-incidental and not intentional. - Shawty*💕

___________________________________

_*I would like to make some clarification here. Nasan wasu zasu ce na fara introduction da turanci while labarin ba na turanci bane. Toh turanci dai is a universal language of course, na tabbata duk wanda ya iya rubutu da karatu yaje makaranta ne, kuma duk wanda yaje makaranta I'm adamant sure in one way or the other dole zai hadu da turanci. Beside, yanayin labarin ne yazo da haka so, I'm sorry for the inconvenience.*_


_Bismillah Arrahman Arraheem_✍🏻


*2017*

0⃣1⃣

*Sokoto, Nigeria.*
Alhaji Bala hamshak'in mai arziki ne wanda ya amsa sunan sa ciki da wajen Nigeria. Kaf a garin Sokoto ba wanda ya kamo ƙafar sa a arziki, tarin arzikin sa yasa ya zama abun kwatance a cikin al'umma. Yana da mata d'aya mai suna Hajiya Zainab.


Alhaji Bala gawurtaccen d'an kasuwa ne wanda ya gagara. Kasuwancin sa ya samo asali ne daga sayar da kifi, tun yana sarowa kad'an-kad'an har ya fara sarowa da yawa haka a hankali abun yayi ta bunkasa. Ya mallaki motoci masu fridges da fish ponds da yawa a kuma garuruwa da dama a fad'in Nigeria inda ake kiwata su ake kuma sarrafa su ana sayarwa.


Sai dai me? Dukiyar Alhaji Bala lokaci d'aya ta ƙara harzuƙa domin kuwa ya tara dukiyar da tafi gaban sana'ar kifi, ya mallaki filaye, filling stations, industries, companies da sauran kadarori daban-daban ya zama fitaccen dan kasuwa a lokaci daya kuma yayi watsi da sana'ar kifi wadda mutane suka diga alamar tambaya akan sa suna zargin akwai wani ɓoyayyen al'amari game da dukiyar sa.


Ita kanta Hajiya Zainab matar sa sosai take zargin sa da dukiyar sa, sau tari tana kudurta a ranta zata tambaye sa wacce kalar sana'a ce yake yi da ya tara dukiya mai d'imbin yawa irin haka kuma yayi watsi da sana'ar da ya dad'e a ciki wato sana'ar kifi.


Sai dai me? Duk lokacin da zata tunkare sa da wannan zancen zata diririce ta gigice wani tsoro da fargaba su ziyarce ta ta rasa me take ciki a yayin da shi kuma Alhaji Bala zai k'ura mata ido ne kawai yak'i ce da ita uffan, haka zai cigaba da yi mata wani masifaffen kallo mai matuk'ar razanarwa da firgitarwa ita kuma zata tsinci kanta a cikin wani wahaltaccen yanayi zuciyar ta zata yi nauyi ba zata samu sukuni da nutsuwa ba har sai ya d'auke idanun sa daga kanta, shi kuma sai ya tabbatar da kallon ya nutsar da ita sa'annan ya tashi ya barta a wurin.


Har ya tara wannan dukiya bayada magaji ma'ana Allah bai azurta su ba ta fannin haihuwa. Sosai abun yake damun su sunyi yawo a asibitoci daban-daban a ƙasashe da dama sai dai duk inda suka je labarin daya ne za'a tabbatar musu lafiyar su ƙalau kuma a koda yaushe zasu iya samun haihuwa kawai lokacin ta ne bai zo ba. Wannan abun ba ƙaramin ci musu tuwo a ƙwarya yake ba musamman Hajiya Zainab.


Kwatsam wata rana aka wayi gari Hajiya Zainab ta tashi da zazzab'i da amai bayan sun je asibiti anyi gwaje-gwaje likita ya tabbatar tana da juna biyu, zo kaga murna gun Alhaji Bala da Hajiya Zainab wane anyi masu bushara da gidan aljanna ne, haka Alhaji Bala yayi ta fidda kadarorin sa da kud'ad'e yana bayarwa kyauta sakamakon farin cikin samun magaji da zai yi a cikin 'yan watanni ƙalilan masu zuwa amma kamar an soka allura ne a cikin ruwa domin kuwa dukiyar Alhaji Bala bata ma san me ake ciki ba sai dad'a bunkasa take yi wannan abu ba ƙaramin bawa Hajiya Zainab mamaki da tsoro yake ba.


A gefe d'aya dangin ta sai tsegumin ta ake game da yawan dukiyar mijin ta don kuwa kullum ƙara zarta hankalin me tunani take, lokaci d'aya kuma suka yi watsi da ita a cewar su idan ba zata gaya musu menene gaskiyar dukiyar Alhaji Bala ba to kuwa ba ruwan su da ita suna zargin itama da hannun ta dumu-dumu a badaƙalar da Alhaji Bala ke aikatawa. Ba su kad'ai ba har ma dangin Alhaji Balan duk lokacin da zasu bijiro masa da irin wannan zancen zaya tabbatar musu da sana'ar kifin sa ce Allah ya sanya wa albarka wannan dalilin ne yasa kad'an daga cikin su suka ƙaurace masa domin sam maganar bata kama hankalin su ba yayin da sauran suke zaune tare da shi a hakan wanda baya rasa nasaba da yawan alhairan da yake yi musu.


Gidan Alhaji Bala katafaren gida ne, ya zarta gidajen mafi yawan 'yan siyasa da masu riƙe da muk'aman gwamnati. Gidan cike yake fal da kayakin more rayuwa a ciki sai dai ba farin ciki a ciki, sun rasa farin ciki ne tun daga lokacin da dukiyar Alhaji Bala tayi tashin gwauron zabo suka nemi farin ciki a ciki suka rasa.


Soyayya da tarairayar da yake nuna mata a baya duk suka zama tarihi sam bayada lokacin zama yayi hira da nishadi da ita kamar da, shima kansa bayada lokacin kansa balle na iyali. A rana bai fi ta gansa sau d'aya ba. Kuma a iyakar sanin ta da Alhaji Bala tsawa da zagi ba nasa bane, baya duka balle barazanar saki amma kwarjinin sa da haibar sa su suke hana ta tunkare sa akan matsalar da suke fuskanta a cikin gidan su wanda a lokutan baya sam ba haka bane wanda itama ta diga alamar tambaya kuma take zargin baya rasa nasaba da chanza salon da dukiyar sa tayi lokaci daya.


A rana sau d'aya take samu ta saka shi a ido a main parlor nasu da safe kafin ya fita, anan take samun sa idan tana da matsala na kud'i ko wani abun ta sanar dashi idan ma babu haka zai firfito da d'aurin kud'ad'e ya jibge a gaban ta a cewar sa koda wata matsalar buk'atar kud'i zata taso kuma baya a gida. Duk lokacin da zata yi yunƙurin nuna masa wannan ambaliyar kud'in da yake yi mata yayi yawa zai yi k'ok'arin kwantar mata da hankali ta hanyar nuna mata idan bai kyautata mata ba wa take so ya yi wa, wasu lokutan kuma ba zaice da ita uffan ba zai sa kai ya fice abinsa bara ta sake saka shi a ido ba sai wata safiyar.


Haka stores na gidan, koda yaushe cike suke fal da kayakin abinci wannan ba zai ƙare ba za'a kawo wani, haka take fiddawa tana rabarwa mutanen da ke zuwa mata da kukan su don gudun lalacewa amma duk da haka wasu sai sun lalace ba tare da ta sani ba.


Ita kanta ba zata iya cewa ga adadin dukiyar dake accounts nata ba, daga kan gold, diamond da kud'ad'e ga kuma wasu kud'in jibge a gida.





*Shawty*💕
[1/7, 5:26 PM] ‪+234 813 551 5123‬: *BARR. BASSAM*
(The Gallant) ❣





By *Shawty*💕


*2017*

0⃣2⃣

Cikin Hajiya Zainab yana a wata na biyar ne abubuwa suka ƙara tsananta mata, na farko ga laulayin ciki na biyu sai ta yini ta kwana bata ga Alhaji Bala ba. Abun da yake ƙara bata mamaki dashi shine wasu lokuta ta tabbata ya dawo yana a cikin gidan amma sai ta neme sa ta rasa, wannan abun ba ƙaramin tsorata ta da bata mamaki yake ba, sam ta daina samun kulawar sa a dole tasa aka nemo mata 'yar aiki wacce zata dinga taimakon ta da wasu ayyukan gida kuma tana rage mata kewa.


'Yar aikin mai suna Hajara ba tsohuwa bace duka ba zata kasa shekaru ashirin da biyar ba tare da 'yar ta mai suna Kausar 'yar shekara d'aya da haihuwa. Tana da aure tare da mijin ta mai suna Abubakar, talakawa ne sosai wanda idan aka samu abinci yau to ba lallai bane a samu gobe ba wanda ya samo asali ne daga kariyar arzikin da Allah ya jarabi mijin ta dashi a wurin kasuwancin sa. A haka dai suke rayuwa cike da tausayi da ƙunci.


Ana haka ne kwatsam wata makociyar su tazo mata da zancen idan zata iya aiki a gidan shahararren attajirin nan wato Alhaji Bala ana biyan ta albashi a kowane ƙarshen wata, ba ita kad'ai ba har mijin ta wato mahaifin Kausar sunyi murna sosai don tabbatar Allah ya kawo ƙarshen wahalar da suke ciki bata yi gardama ba ta amince don kuwa ko ba komai zasu dinga samun isashshen abinci idan kuma Kausar ta isa shiga makaranta zata iya saka ta koda ta gwamnati ce don kwa a kullum burin su shine Kausar ta samu ingantaccen ilimi.


Cikin kwanciyar hankali Hajara ta fara aiki a gidan Alhaji Bala, bata fuskanci wata matsala ba domin kuwa Hajiya Zainab mace ce me kirki. Cikin lokaci ƙanƙani suka shaƙu da ita. Idan tazo da safe zata yi mata share-share da goge-goge kusan ma shi kad'ai ne aikin da take yi sai idan Hajiya Zainab zata aike ta wani wurin. Wasu lokuta koda ta gama ayukan da take yi ta kan zauna ta taya Hajiya Zainab hira kasancewar ita kadai ce a makeken gidan wanda kuwa haka ba ƙaramin dadi yake yiwa Hajiya Zainab ba.


A gefen Hajiya Zainab ma zancen d'aya ne domin kuwa sosai take jin dad'in aikin Hajara, bata da kissa ko girman kai bata taɓa nuna gajiya ko kasawa ba akan yi mata hidima, koda yaushe tana iyakar bakin ƙoƙarin ta wurin ta tsare aikin ta sai dai kuwa rashin lafiya ko dalili mai ƙarfi zai hana ta zuwa. Cikin lokaci kad'an suka saba da Hajiya Zainab ta zama kamar wata jinin ta har ta daina kallon ta a matsayin 'yar aiki ta mayar da ita kamar 'yar uwarta wacce ko wani abu zata yi zata nemi shawarar ta wanda ya samo asali ne akan gaskiyar ta da riƙe amana domin kuwa bata taɓa kama ta da cin amanar ta ba.


Sosai Hajiya Zainab take kyautata wa Hajara har ta cire ta a matsayin 'yar aiki ta d'auki wata, koda Hajara zata zo Hajiya Zainab ba zata barta tayi wani aiki ba sai dai su zauna suyi ta hira har lokacin tafiyar ta yayi. Ba Hajara kadai ba har 'yar ta Kausar da mijin ta bata barsu ba, duk ƙarshen wata take kawo kudi me yawa ta bawa Hajara tace ta bawa mai gidan ta yayin da Kausar kuwa ta d'auke ta kamar 'yar ta duk sanda zata je sayayyar kayan haihuwar ta to kuwa da na Kausar a ciki sosai Kausar ta shaƙu da ita har Hajara tana barin ta fiye da sati d'aya a hannun ta.



Rayuwa ta chanza wa Hajara da mijin ta domin kuwa Allah ya kawo musu Hajiya Zainab a lokacin da suke tsananin buƙatar taimako. Gida sukutum d'an madaidaici ta saya musu tace su tashi daga kangon da suke ciki, ranar har kukan farin ciki sai da suka yi su kam basu da bakin da zasu godewa Hajiya Zainab. Wannan dalilin ne yasa Hajara ta ƙara jajircewa wurin kyautata wa Hajiya Zainab don kuwa a ganin ta batada abunda zata sakawa Hajiya Zainab dashi sai dai tayi mata addu'ar Allah ya sauke ta lafiya.


******


_6:00pm_
Hajiya Zainab ce a cikin katafaren parlorn gidan zaune akan luntsumemiyar Sofa cikin shiga ta alfarma. Cikin ta kuwa yana a wata na tara saboda haka haihuwa ko yaushe tsammanin ta ake, hannun ta riƙe da remote tana chanza channels, shigowar Hajara ce parlorn yasa ta juyo daga kallon da take had'i da yin murmushi
"Hajara sai yanzu?" murmushin itama Hajarar ta mayar mata ta ƙarisa shigowa cikin parlorn ta sami wuri akan tiles ta zauna, da sauri Hajiya Zainab ta fara fad'a "Haba Hajara! Kinfi so nay ta maimaita magana d'aya ne? Iyeh? Na sha gaya miki bana san wannan zama ƙasan da kike tashi ki zauna akan Sofa mana" murmushi Hajara tayi ta tashi ta...


Read / Download BARR BASSAM

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album