Join Our WhatsApp Group

SANGARTA Complete Hausa Novel Document by SANGARTA


SANGARTA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 89651



SANGARTA

Reading Time: 7 Hours

Added On: 29, Sep 2023

Author: Zulaihat Rano ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 468.67 kb

File Type: txt

Views: 745+

Download: 472+

Last download: 24 hours ago

Description/Story: Compiled By Umar Dalha Funtua.

Copied By Zulyheart Rano

[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*

©
*ZULAYHEART RANO*

*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*

```Wannan page din sadaukarwa ne ga MARYAMERHABDUL (KWAISEH), fatan Alhairi na ke maki a dukkan rayuwar ki, Ubangiji ya kareki daga sharrin makiya da masu yi maki hassada, Wallahi Allah ina kaunarki har cikin raina, Allah ya kara maki basira da kafin k'wak'walwa.

Ina yinki sosai marubuciyar DUHUN DIMINA```😍😍


_*MY BESTY KHADIJAH S MUHAMMAD, HMMMM BA SAI NA FADA MAKI IRIN SON DA NAKE MAKI BA, DON KE DIN SHAIDA CE*_💞

*27*

Wani sansanyar ajiyar zuciya ya sauke, tare da lumshe ido ya buɗe su fes a inda yake, sosai ya ke jin dadi na kewaya duk ilahirin jikinsa a fili ya furta

"Alhamdulillah! Na sauka a kasar haihuwata Nigeria kasar mu ta gado."

Duba ya kai ga agogon da ke manne a hannunsa, in da ya nuna masa karfe biyar harda mintina, sanye yake cikin kananun kaya wanda suka amshi jikinsa, ya yi kyau a ɗan zaman da ya yi na kwanaki bakwai a can, ji ya ke kamar ya yi tsuntsu ya gansa gabanta, babu abin da yake buk'ata a wannan lokaci sai ganin kyakkyawar fuskarta da daddaɗar muryarta, murmushi ya sauke ma kyau a fili ya ce

*I LOVE YOU AMEESHA*

Muryar direban su ne ya sa shi dawowa da hankalinsa sa kan shi, murmushi ya saki tare da fadin

"Har ka iso?"

"Eh! Yallaɓai."

"Madallah! Mu je kawai."

Shigo ya yi cikin motar, sannan direban ya ja, mintina ƙalilan suka isa gidan, a parking space direba ya faka motar sannan ya fita, da sallama ya shiga falon

"Assalamu Alaikum!"

Mummy da ke kai komo tsakanin falo da kicin ta amsa masa

"Wa'alaikumus salam! Barka da isowa NAJEEB."

Murmushi ya saki yana ci gaba da takawa har inda Mummy take, ya ce

"Yawwa Mummy na, *I miss you* ."

" *I miss you too my son*" Mummy ta faɗa cikin jin daɗi.

Zama ya yi akan kujera ya soma gaidata, da kulawa ta amsa tana tambayarsa yadda ya baro garin

"Ka ga kar ka zauna surutu, ga dukkan alamu akwai yunwa a tattare da kai, don haka tashi ka yi wanka sai ka zauna cin abincin."

"Wallahi kamar kinsan na yi missing ɗin abincin ki mai daɗi, bari na fito wanka sai na zauna." Ya yi maganar yana soma tafiya.

"Najeeb! Mummy ta kira sunan sa.

Dawowa ya yi yana faɗin " gani mum."

"Ka bar wankan nan, bari na hada maka kawai ka je da shi gidan ka, tunda yau kwana biyu kenan da aka kai maka amarya kuma ba ka nan."

Kallon Mummy ya yi mamaki kwance a fuskarsa ya ce

"Mummy Ameesha ta tare ne?"

Girgizar kai ta yi ta ce ya zauna, zama ya yi duk jikinsa ya yi sanyi, nusiha Mummy ta fara yi mu mai tsuma jiki

"Kana ji ko Najeeb! Ina so ka yadda da komai na duniya sai da Allah ya tsara shi, ka yadda wani ba zai taɓa auran matar wani ba, haka duk inda ka kai ga son abu matukar ba Alhairi ba ne bazaka taba samunsa ba, ka yadda Ameesha ba matarka ba ce, Rufaida ce matarka ina son ka yi hakuri da canjin da ka samu." Mummy ta dakata tana kallon wani yanayi Najeeb ya shiga, sai ta ga ya saki murmushi ya ce

"Mummy na fahimci inda nusihar ki ta dosa, wallahi na yadda da kaddara kuma insha Allahu ba zan bijirewa ikon Allah ba."

"Yawwa ɗan albarka, Allah ya yi maka albashi ya baka zuri'a dayyaba."

"Amin." Ya amsa cikin ɗan dariya, duk da zuciyarsa tana kuna da rashin Ameesha, sai dai hakan ba zai hana shi kula da Rufaida ba domin kuwa ita ce farkon masoyiyar sa.

"Mummy haɗa min in tafi." Najeeb ya yi maganar yana mik'ewa tsaye.

Tashi Mummy ta yi tare da nufa kicin ɗin, sai da ta haɗa masa komai sannan ta kawo masa, tana faɗin ƙasa Rufaida ta ci abinci da yawa, domin na kulla bata son cin abinci." Da yake tunda aka kai Rufaida kullum sai Mummy ta aika mata da abincin.

"Insha Allahu Mummy zan sanyata."

"Yawwa to ka gaidata, idan ka huta ko zuwa jibi ne sai ka kawo min ita." Don lokaci ɗaya Mummy ta ji son Rufaida, domin dai Allah ya yita da nutsuwa ga kunya.


******

Dr yana fita gida ya nufa, lokacin da ya shiga falon babu kowa, don haka bedroom ɗinsa ya shiga, shirin wanka ya yi cikin sauri sauri, bai wani jima da shiga ba ya fito, shiryawa ya soma yi cikin wasu kananan kaya wanda suka karbi jikinsa, sosai kayan sun yi masa kyau jikinsa yana fitar da wani sansanyar kamshi mai sanya nutsuwa a jikin dan Adam.

Rigar kalar ja ce an yi mata rubutu da kalar golden *Special one* sunan dake manne a jikin rigar kenan, ya yin da wandon kuma baƙi ne, wayoyinsa ya kwasa tare da key ya yi waje, har ga Allah ya manta da wata Aneesa, don burinsa kawai ya yi arba da Ameesha farin cikinsa, motsin da ya ji shi yasa shi saurin waigawa

Gabansa ya yi mummunan faduwa ganin yadda fuskar Aneesa ya kumbura, cikin sassarfa ya k'arasa inda take yana faɗin

"Anee lafiya?" Ya yi maganar yana kai hannu jikinta.

Harara ta watsa masa tare da kaucewa don bata son hannunsa ya sauka jikinta, juyar da kai gefe ta yi ranta yana tafarfasa ji take kamar zuciyarta zata faso waje muryarsa ta kuma shiga kunnenta

"Tambayar ki fa nake yi, ni yanzu bani da yancin taɓa jikinki kenan?"

Da masifa ta kalleshi ta ja tsaki tare da tabe baki ta ce

"Ina ruwan ka da lafiyata, maganar taɓa jiki kuma ai ina ga ka yi sabuwa sai ka je ka ci gaba da taɓa nata na bar mata, yanzun ma wajenta ka nufa ko? Wai don Allah Hamma dama haka kake ko kuwa dai zumudin amarya yasa haka?" Cikin kunar rai ta k'arasa maganar.

Murmushi ya saki ya ce

"Bari na dawo zan baki amsa, amma Please ki daure ki bar kuka haka, ki dubi yadda kika koma fa?

"Ina ruwanka da yadda na koma? Duk yadda na zama ai ina ga ba matsalar ka ba ce ko?"

"To ki daure ki ci abinci, kar ulsa ta kamaki."

"Ba ulsa ce zata kamani ba typoid zaka ce, kaga Hamma bana son *kankamba cirani ba miji a tafi ba ciki a dawo da goyon* ba zan ci ɗinba." A fusace ta dire maganar.

Girgiza kai ya yi cikin takaici da halin Anee, karin maganar ta ta karshe ce ta bashi dariya, har ya kusa yin dariyar sai ya yi saurin kumshe dariyar don kar ya kuma kular da ita sai kawai ya fita, tana ganin ya nufi fita ta ruga ɗaki da gudu bedroom ɗinta tare da sakin wani kukan.

Shi kuma yana fita motarsa ya shiga tare da bata wuta cikin gwaninta da kwarewa yake juya kan motar, har ya isa unguwar su Ameesha, farin ciki ke kwarara zuciyarsa har ya ɗan gana da get din yana hon maigadi ya buɗe masa, shi kuma ya cusa hancin motar cikin gidan yana gaida maigadin.

A parking space ya faka motar ya fito, jingina ya yi tare da harde hannunsa a kirjinsa yana tasbihi ga Allah, a hankali ya zame hannunsa ya zaro wayarsa ya yi dailling Number ɗin ta,

Lokacin wayar tana hannun Meena don ita ke amfani da shi, ganin Number din babu suna sai ta yi kamar kar ta ɗauka, har tana daf da katsewa sannan ta dauka

"Hello."

"Assalamu Alaikum! Dr ya faɗa yana gyara tsayuwa.

Amsawa Meena ta yi tana dan zaro ido jin muryar kamar ta Dr. Maganar sa ce ta dawo da ita daga tunanin da ta faɗa. "Meena Dr ne gani a cikin gida, ki yi min iso a wajen Ummi."

"To." Meena ta amsa tana nufa bangaren Ummi, a falo ta samu Ummi Ameesha ta yi filo da cinyar Ummi ɗin, zama ta yi kusa da Ummi sannan ta ce

"Ummi Dr ne fa yazo!

Murmushi ta saki tare da shafa kan Ameesha ta ce

"Barkan shi da zuwa, a kawo shi nan bari in koma bedroom ɗina." Ta Kai karshen maganar tana mik'ewa.

Meena ma hannun Meesha ta ja tana fadin

"Mu je ki shirya tarbar Dr ga shi can a harabar gida." Tana maganar ne suna tafiya, suna shiga bedroom din Ameesha, Meena ta fara gyara mata kwalliyar fuskarta, domin bata wani dade da yin wanka ba, ko kayan jikinta bata canza ba domin dai doguwar riga ce baka, wacce ta sha adon duwatsu, sosai rigar ta yi mata kyau dankwalin rigar kuma aka yi mata rolling ɗinsa akanta sosai ta yi kyau.

Turaruka masu sanyin kamshi Meena ta feshe mata jiki da shi, kai masha Allah gaskiya Ameesha ta haɗu iya haɗawa, takalmi ta dauko mata shima baƙi, Meesha sai murmushi take yi don ita kanta tasan ta haɗu balle kuma shi ogan ya ganta. Sosai Meena ke kula da lamarin Meesha, duk wani abu da tasan Meesha tana yi a lokacin da take cikin tunanin ta, shi take mata. (Allah ka hadamu da kawaye na kwarai ameen).

Rike mata hannu ta yi har suka shiga falon, tunda Dr ya daura idonsa kan Ameesha ya kasa saukewa, domin ba karamin kyau ta masa ba, sai yaga kamar yau ce ranar da ya soma ganinta.

Ita ma Ameesha ganin yadda ya kafeta da ido fuskarsa da murmushi i it din ma ta sakar masa, kallon su Meena ta tsaya yi domin sun bala'in burgeta, Meesha tana isa inda Dr yake sai ko ta faɗa jikin sa tana faɗin

*"SWEETY ASMAD?"* Domin ta rike yadda ya ce mata rannan, sai dai ita da sigar tambaya take maganar.


_Nafee Ankerh korafi_☹

_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*

©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username *ZulayheartRano89*


*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*

_*Wannan page din sadaukarwa ne ga NAFEESA ANKERH (mr korafi) na sadaukar maki da shi ki yi yadda zaki yi dashi idan ma kika ce kar kowa ya karanta wannan ikon ki ne, ni dai kawai a barnin in inke yin typing a time da na samu dama hhhhhhhhh!, Fatan Alhairi a gareki Zulayheart Rano tana yinki sosai*_ 😍😍

*28*

Daddaɗar muryarta ne ya ratsa kunnuwansa, musamman yadda ta faɗin sunan sai ya ji ta saukar masa da kasala, dadingushi kuma yadda ta lafe a jikinsa, sai wani feeling wanda tunda yake da Meesha duk fadawa jikinsa da ta keyi, bai taɓa jin irin saba, gyara mata zama ya yi a maimakon da da yake zameta daga jikinsa ya ce

"My Meesha ya ki ke?"

Bata ce komai ba sai lumshe ido da ta yi, fuskarta har yanzu da murmushi, Meena kam tsayawa ta yi tana kare masu kallo don yadda Dr ya yi ko wanda bai san SO bane ya gansu to zai iya shaida su ɗin masoyan junane, murmushin farin ciki ta yi a ranta tana faɗin

"Alhamdulillah! Ashe Dr ma yana son Meesha Amma wannan abu ya min daɗi."

Ganin hankalin Dr yana ga Ameesha bai masan da wata Meena ba sai ta ɗan gyaran murya ta ce

"Dr ina wuni! An daura aure lafiya?"

Wata kunya ce ta kamashi, don da farko yaga lokacin da suka shigo tare da Meena ɗin, amma tunda Meesha ta matsa inda yake sai ya manta da komai ya maida hankalinsa kan Ameesha.

"Lafiya lau Meena ya kuke?"

"Duk muna lafiya." Ta bashi amsa tana tafiya.

Meena tana wucewa ya maida hankali kan Meesha da ke ta daddana wayar Dr ɗin. Ya ce

"My Meesha zaki bini gidanmu?"

Da sauri ta daga kai alamar "eh!"

Murmushi ya yi ya ce "to bari Abba ya dawo, sai na kaiki wajen Nenne ku gaisa." Ya ida maganar dai dai da zuwan Meena, abin motsa baki ta shiryo masa.

"Thanks Meena sannu da k'ok'ari."

"Your are welcome!" Ta faɗa tana tafiya. Shi Dr tunda Ameesha ta wanzu kusa da shi sai ya nemi yunwa ya rasa, don kasancewarta kusa da shi ba karamin farin ciki ne a gare shi ba.

Kallon ta ya yi tana ci gaba da danna wayarsa, cikin zuciyarsa fadi yake

"Ina ma ace Ameesha tana cikin tunanin ta aka daura masu aure! Lallai yasan da ace tana tunanin ta, to yau da abin ya fi masa jin dadi, amma a haka ma yana farin ciki, yana godiya ga Allah."

Dr ya manta da komai ya dauki lokacin da kacokan ya dankawa Ameesha, sam ya manta a gidan surukai yake, soyayya kawai yake nuna mata irin mai tsayawa arai dinnan, ya yin da ita kuma ta wani lafe a jikinsa kamar wani ya ce zai raba su, bai tashi farga ba sai da ya ji kiran sallar magriba, ɗago da ita ya yi yana faɗin

"Meesha time for prayer, zan je masallaci."

Da kallo take binsa don bata fahimci inda maganar sa ta dosa ba, ganin zata bata masa lokaci har ya rasa jam'i yasa ya kira Meena yana sanar mata to zo ta tafi da Meesha, babu bata lokaci sai gata, da wayau Dr ya samu ya guje mata.

****

Aneesa kam tana shiga dakin wani sabon kuka ta fashe da shi, zuciyarta tana wani irin zafi tana jin kishin Dr fiye da komai, zata iya yin komai don ta hana Dr zama da amaryar sa, yadda take kukan Ni kaina sai da na tausaya mata, don *kishiya ko ta kashin dankali ne babu daɗi* balle wacce aka auro don ku zauna a karkashin inuwar mutum ɗaya.

Ganin kukan ba shi ne solution ba sai ta jawo wayarta tare da dannawa Rukky kira, bugu biyu kuwa Rukky ta amsa

"Hello k'awata!" Rukky ta faɗa tana gyara wayar a kunnenta.

Shiru Aneesa ta yi har sai da Rukky ta yi magana sau uku kana ta iya sauke nannauyan ajiyar zuciya ta ce

"K'awata babu lafiya fa!"

Zaro ido Rukky ta yi kamar Aneesa tana kallonta baki har yana rawa ta ce

"Mai ya faru? Da ga jin muryar ki nasan babu lafiya faɗa min mai ya sameki?"

"Dr ya yi aure." Ta yi maganar cikin rawan murya.

"Aure! Kan uban... Rukky ta mulmulo wani katon ashar, ke Aneesa anya kuwa kin san me kika faɗa min?"

"Ce maki na yi Dr ya yi aure." Wannan karon tare da hawaye maganar ta k'arasa fitowa.

"Amma kuwa an yi mara mutunci, yanzu don Allah duk son da kike masa shi ne zai saka maki da kishiya? Lallai na...


Read / Download SANGARTA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album