Join Our WhatsApp Group

Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

NAMIJIN DARE Complete Hausa Novel Document by NAMIJIN DARE


NAMIJIN DARE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 41123



NAMIJIN DARE

Reading Time: 3 Hours

Added On: 20, Jun 2024

Author: Ummy Mrs Khamis ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09137879957

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 243.2 kb

File Type: txt

Views: 431+

Download: 464+

Last download: 9 hours ago

Description/Story: 🥺🥺🥺🥺🥺🥺


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```


*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957


*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s . w . t .a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*


TAƘABBALALLAHU MINNA WAMIN KUM INA MUKU BARKA DA SALLAH ALLAH YA KARBI IBADUN MU ALLAH YASA MUNA DAGA CIKIN WA ANDA AKA ƳANTA CIKIN WATAN RAMADAN MAI ALBARKA🤲🤲🤲🥰

______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


*page 1*


*BATSARI* ƙaramar hukuma ce dake jahar Katsina, garine dake dauke da ƴan boko!, mafi yawancin yan garin suna da ilimi sosai na addini da na zamani.

so! suna gabatar da rayuwar su abin sha'awa, dan komai sukan yi shi cikin wayewa...

a ƙofar wani matsakaicin gida naga wata matashiyar budurwa, dake tsaye da wani dattijo, da ke ta faman washe haƙora, kamar gonar audiga, yana kallonta kamar ya haɗiye tah, sai kace tsohon maye......

yanayinta kaɗai ya isa, yasa a gane basan tsayuwar take ba.
dan da dukkan alamun ma tsoron shi take ji.
juyawa baya tayi da sauri , tana mai shigewa cikin gidan kamar zata kifa, dan saurin da take.

cikin yanayin kaɗuwa da ɗaga murya take cewa...


"innarmu!!! innarmu!!! innar....... "

"ke da Allah minene,? kin dameni da wani kira sai kace tsohuwar makauniya.."

cewar wata dattijuwa da tafito daga ɗaki, tana wa budurwar da ta shigo gidan, tana faman ƙwala mata kira. kamar wata ƙaramar yarinya...

dattijuwar ta cigaba da cewa

"haba Asma'u yaushe zakiyi hankali ne, kullum kina girma kuma kina ƙara sakarcewa.."


"uhmn.. wllhi innarmu wancen Alhaji Tankon da yazo..., nidai bana sonshi wllhi, in yayi dariya fa kamar wani gwaggwan biri..,
ke dan ma baki ganshi ba!!, amma ina zankai wannan tsohon banza.." Asma'u ta faɗa tana mere bakinta.."

inna da ta gama ƙuluwa da al'amarin Asma'u, tama rasa mai zata ce mata, can sai ta nisa tace

"Asma'u kenan,.. ina lafin wanda yace yana sonki, kuma mah ni wllh banga wani muni da Alhaji tanko yake dashi ba,. kawai de ke kice bakya sonshi ne, amma ba sai kince haka ba.."

inna saida tayi ajjiyar zuciya tukun ta cigaba da cewa

" kinyi kuskure da har kike jin a wannan shekarun naki, sai kin zaɓi irin mijin da kike so ki aura, shi miji ba yawo ake da shiba, bare adinga ce miki baida kyawu, duba kiga sa'aninki daga mai yara uku sai mai yara huɗu..
ƙannen ki biyu akama aure, amma ke hakan bai dame kiba, shikkenan tunda kin fiso ki zauna a gida muyi ta jera kafaɗa dake.."


inna ta ƙare maganar ta cike da tarin damuwa, Asma'u dake tsaye
hawaye na shirin zubo mata, ta tare su da hannu zuciyarta na mata zafi, shigewa ɗaki tayi da sauri, inna da tabita da ido tana ayyana abubuwa da dama aranta

* * *
shi kuwa Alhaji tanko, ganin Ma'u ta shige gida da gudu, hakan yasa shi cikin farin ciki marar misaltuwa, zuciyarsa ƙal yabar ƙofar gidan tare da zumuɗin samun zankaɗeɗiyar budurwa ta bugawa a jarida kuma ta yawo a ko ina dan nuna wa duniya.....✍️



*inga comments fa hakan zaisa ku riƙa ganin post akai akai , ba kama hannun yaro😁*


*_more comments_* 😃

*_more typing akai akai_* 🥰💃




```har kullum taku ce ummussalama s
y matar khamis🥰💃```




by



*~MRS KHAMIS🥰💃~*

[4/29, 5:00 AM] matar khamis🥰💃: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```


*by*
*_ummy mrs khamis_*


*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s .w .t .a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



*~GARGADI~* ~ban yarda a juya min littafi na ba, ta ko wacce siga, ko ayi amfani da shi ta wata hanya ba tare da an nemi izinina ba.~
*pls a kiyaye🧏‍♀️*




______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*





*page 2*



__________________________________________________________




Bayan magriba Asma'u ce zaune kan katifa ta zabga uban tagumi, kamar wacce akawa mutuwa, Domin kallo ɗaya zaka mata kagane tana da tarin damuwa a ranta..
sosai tayi nisa cikin tinanin data ke, inna ce ta shigo ɗakin, bakinta ɗauke da sallama, har ta zauna amma Asma'u batasan take shigo ba, sai da ta yi dafa ta, tukuna tayi firgigit ta dawo hayyacin ta...

cikin kulawa inna tace, "Ma'u menene yasa baki son maganar aure kwata kwata,.? tun samarin suna zuwa yanzu har sun gaji, daga kice Wannan ya miki yaro, sai kice wannan baiyi kala da irin namijin da kike so ki aura ba, to shi wannan namijin ah ina yake..?
inna ta ƙare maganar da jero mata tambayoyi...
ita de ma'u shiru tayi, ta sunkuyar da kanta,. tin inna na mata magana da lumana, har ta fara mata faɗa faɗa, dan ta inda take shiga ba ta nan take fita ba ...

cigaba inna tayi da cewa "duba kiga shi yanzu kawun ku in yaji kalar cin mutuncin da kika yiwa abokinsa zai ji daɗi.?
iyee,? magana fa nake miki!!. kin min shiru...!"
daƙyar Asma'u ta ɗago kai tace "innar mu dan Allah kiyi haƙuri,"
ah ƙufle inna tace "ke za'aba haƙuri tunda mu muka takura maki...."
hakade inna ta gama sababinta tukunnan ta fita tabar mata ɗakin....

asukwane ta zamai ta kwanta kan katifar da take kai,
wasu zafafan hawaye ne ke zubo mata, wanda takasa tseda su, sai da tayi mai isarta, sannan bacci yayi awon gaba da ita haka ta kwanta cike da tarin damuwa.....
cikin bacci taji ana shafa mata face nata, wanda hakan yasa tayi sauri buɗe ido.
wanda tayi tinanin ko shine , shine kuwa, tayi tozali da kyakkyawar fuskar sa..
tsadadden murmushinsa ya sakar mata haɗe da miƙa mata hannunsa yana mai mata nuni da ta taho gare shi.......




*more comments*😃

*more typing akai akai*🥰💃



```taku har kullum```


~ummussalama sy~✍️






*_matar khamis🥰💃_*
[5/6, 11:19 AM] matar khamis🥰💃: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```



*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957




*short story*




*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```




```bissimillahir rahamanur rahim```




*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s w a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


____________________________________________________________



*PAGE 3*



Da saurinta ta ƙaraso gare shi, janyota yayi zuwa qirjinsa, tare da sakin wata nan nauyar ajjiyar zuciya...
saida suka dau tsawon lokaci a haka , sannan Ma'u ta ɗago tana kallon kyakkyawar fuskarsa, cike da shagwaɓa tace

"shine ka tafi kabarni ko"

tana maganar tana turo baki.
tsayawa yayi kallon ɗan mitsilin bakin nata, da yake jin kamar ya cinye shi dan matuƙar birge shin da yake..

Ma'u ganin ya tsaya yana kallon ta, hakan yasa ta cigaba da ƙananun shagwaɓaɓɓunta..
ita kuwa bata san ƙara kunna shi take yi ba...
bata ankara ba sai da taji bakinsa cikin nata, lumshe idanuwan ta tayi haɗe da sauke ajjiyar zuciya..

shi kuwa wani zazzafan kissed yake sakan mata, wanda a dalilin haka ne wata nan nauyar kasala ta sakko musu....
saida ya gaji dan kansa tukun ya ƙyale ta , yana maida numfashi..

goshinta ya kaiwa sumba😘, sannan yace
"har abada babu batun in tafi, inbarki., duk runtsi, duk wuya, ina tare dake,. bazan taɓa rabuwa dake ba, namiki alƙawari...."

sosai Ma'u ta shagala da kallon kyakkyawar fuskar sa, dake ɗauke da wani ainahin sirrin murmushi.
azuciyarta tana jin wani irin nishaɗi marar misaltuwa.

hura mata iskar bakinsa yayi,.
hakan yasa ta dawo daga duniyar tinanin da ta tafi..
saida ya sake sakan mata murmushin sa , mai tsada, sannan yace
" *Nurul aini ,..* tinanin mai kike yine haka,? ko kina da buƙatar wani abun ne, ? faɗa minshi indai a kwai shi...


Read / Download NAMIJIN DARE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album