Join Our WhatsApp Group

Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

SILAR MUTUWA Complete Hausa Novel Document by SILAR MUTUWA


SILAR MUTUWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 14789



SILAR MUTUWA

Reading Time: 1 Hours

Added On: 12, Jan 2024

Author: Fatima Rabiu (Zarah Royal Star) ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08130479973

Book License : Free

Category: Horror novels

File Size: 80.37 kb

File Type: txt

Views: 712+

Download: 319+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: *💔🧟‍♀️☠️SILAR MUTUWA🧟‍♀️☠️*💔
(Horror Story)





ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️






*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*




*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*



PAGE 1️⃣➡️2️⃣


*Federal University dutsinma*



Wata y'ar madai-daiciyar mota ce ta tsaya cikin filin school d'in bud'e marfin motar akai cike da takon k'asaita take ta fito daga cikin motar bak'in gilas d'in dage manne da fuskarta ta cire tana bin school d'in da kallo kasancewar zuwanta ne na farko.


Can ta tsinkaye wata murya na faman kiranta cike da murna taji an rungumeta da sauri ta waigo tana yamutse fuska da sauri ganin yadda duk suka rirrik'eta ta k'ara b'ata fuska ta ce "wai Bilki dake da Nawwara wai yaushe zaku canza ne shi yasa fa ban so zuwa school d'aya daku ba shi yasa again na ce ku fara yo gaba nabi bayanku shine daga isowata duk kunbi zaku wani kada ni", ta idasa maganar tana k'ara bin school d'in da kallo yadda taga duk Arna sunyi yawa a cikinta da sauri Nawwara ta d'an saketa ta ce "kai Surayya kefa akwai yarfa mutum wallahi mufa murnar zuwanki ne yasa kingah bamu san kowa ba a cikin school d'in nan", Bilki ce ta amshe da cewa "kai gaskiya Surayya daba dan mu k'awaye bane tun na yarinta da tuni mun barki da halinki akwai ki da murd'and'an hali".



Ganin kamar sunyi fushi yasa Surayya cewa "kufa dad'i na daku akwai saurin fassara mutum nidai kun sani sai kuna hakuri dani school d'in ce kamar b'ata kwanta min a rai ba", ta idasa maganar tana tafiya kamar ba ita tayi maganar ba ganin tabi wata hanya yasa da sauri Nawwara ta ce "Surayya ki tsaya ba'a cika bi ta wannan hanyar bafa tana da matsala", d'an dakatawa tayi da tafiya tana waigowa ta ce "to sabon salo ai na ce dai ana bi dai ko kuma zata iya kaini a inda nake so ina ce hakane?", d'aga mata kai sukai cike da d'an tsoro Bilki ta ce "dan Allah Surayya kiyiwa Allah karki bi ta wannan hanyar akwai tantiran makaranta dake zama ta wajan nan duk school d'in an sansu kuma ana tsoron su ba wadda bai san tarihin su ba".


Surayya kuwa tsaki taja tana ci gaba da tafiya tana cewa "zan so jin tarihin mi suka aikata har ake jin tsoron su, to daga yau za'a sake kafa wani tarihin cewa ga wadda bata shakkar kuwa dan banga wadda ya isa ya hanani zaga ko ina ko shiga wani waje dake cikin school d'in nan ba indai zuciyata taso hakan", ta idasa maganar tana shan wata kwana da sauri su Bilki suka rufa mata baya suna mamakin rashin tsoro da kafiya irin na Surayya.



Koda tasha kwanar idonta ya gane mata dan-dazon maza sun kai su bakwai sai zuk'ar sugari suke zuciyarta ce ta buga dumm dammm dakewa tayi tana tafiya irin ko a jikinta tana niyar wuce su, da sauri wani cikin y'an iskan dake zaune wajan ya ce "Oga Goga ga wata mai rabon shan duka ta biyo da hanyarka miya kamata muyi mata danna tabbata an sanar da ita waye kai", ya idasa maganar yana kallon Goge dage kallon Surayya da wani salon iskance ya ce "barni da ita wannan daga gani kalar mu ce", ya idasa maganar yana yin wata shegiyar mik'a ya nufi wajanta.



Surayya kuwa batai aune ba taga mutum a gabanta ganin sa gaf da ita kamar zai shige jikinta yasa da sauri tad'an matsa tana tushe hancinta saboda warin giyar da yake.


Wani murmushin gefan baki yayi yana fiddo harshan sa yana lashe bakinsa kamar tsohon maye yana kallon gefe yana cewa "da alama baki san ana tsoron biyowa ta nan hanyar ba ko? kuma baki san waye Goga ba baki binciki tarihin sa ba dami-dami ya aikata harya kawo wannan matsayin ba kohhh?", ya idasa maganar ya ware mata jajayen idonsa.


Da sauri Surayya ta d'an k'ara matsawa cike da k'arfin hali ta dake tana aika mai da wata shegiyar hararara kamar idonta zasu fad'u, ta ce "waye kai kuwa inbanda bawan Allah kuma an gaya min ina sane na biyo hanyar tunda naga ai ba wani ya gina hanyar ba kowa nada ikon wucewa in...... Kamin ta idasa maganar ya daka mata wata uwar tsawa da cewa "keeee y'ar gidan abun wacece ke koh y'ar gidan wacece bata isa ina fad'a tana fad'a ba ba'a yota ba, kuma baza a tab'a yinta ba", dai-dai lokacin su Bilki suka k'araso suna tsaye gefe, ba abinda jikinsu yake sai kyarma na tsananin tsoro.


Goga ya bud'e baki da bud'ad'd'iyar muryarsa ya ce "kai guy's ku d'akko min ita sana ku had'a da y'an matan can", wata irin zufa ce ta yanko ma su Nawwara, suna fashewa da kuka suna cewa "Surayya kinga abinda kika zamana ko?".



Suna gaf da isa inda su Bilki suke Surayya ta saki wata irin dariya mai amsa kuwwa wadda tasa gaba d'aya wajan amsawa, d'an gyalan dage jikinta ne ya cire daga kanta gashinta ya sauka har gadon bayanta ya rufe mata fuska, ta duk'ar da kanta k'asa, cike da mamaki su Nawwara ke dubanta.


Goga kuwa dariya shak'iyanci yayi ya ce "mu zaki firgita da aljanun k'arya kai ku dakata bari na d'akkota da kaina", da sauri wadda suka nufi inda Surayya take suka tsaya dan ba k'aramar girgiza su dariyar tayi ba, ko dai Goga baiji dariyar da kyau bane kamar fa bata mutane ba ce kai wannan dariyar tafi k'arfin mutum yayi ta.


Kamin ya kai gare ta Surayya da wata irin murya wadda kwata-kwata ba tata bace ta ce "da alama har yanzu Goga baka daddara ba baka daina abinda kake can baya ba dama irin wannan yarinyar nake so tazo wacce bata da tsoro da ita zanyi anfani na shiga jikinta naci ubanku hankali kwance bazan tab'a kashe ka ba dan yanzu ba Goga saina gana ma azabar da sai ka gwamce mutuwa da rayuwa tunda kayi SILAR MUTUWA ta nida wadda nake k'auna", wata irin zabura yayi jin muryar wadda har duniya ta nad'e bazai mance mai ita ba, hantar cikinsa ce ta kad'a wata irin zufa ce ke yanko mai kota ina sai zazzare ido yake, su kansu wadda suke bimai baya ganin kamar suna Shirin tsire wa yasa ta k'ara sakin wata irin dariya mai firgita ruhin d'an Adam ta nuna inda suke niyar guduwa da hannu dan da nan wasu irin halittu suka bayyana masu mummunar kama fuskar su ba kyan gani suna zaro zungureran harshan su ga wasu zafga-zafgan bulali a hannunsu kamar na k'arfe umarni ta basu kan su fara aiki ai ko ba shiri suka fara zafga masu bulali wata irin azaba suke ji ihu suke babu mai jin su baka Jin k'arar komai sai na ihun su da k'arar bulala.


Juyawa tayi tana shak'ama su Nawwara wani farin abu nan take wani nandauyan bacci ya sure su tana sa hannunta ta shafe su b'at suka b'ace daga wajan.



Goga kuwa da yayi suman zaune ganinta gabansa tana wata y'ar iskar dariya gashinta ne yayi baya mummunar fuskar ta bayya na da tasa Goga sakin fitsari ganin rabin fuskarta naman dake wajan duk ya zaizaye tsutsotsi na bin wajan idonta ya koma fari fari fat ko d'igon baki babu bakinta wasu irin hak'ora ne y'an guntaye masu masifar tsini wani irin jini kalar ruwan ganye ke zubowa tana lashe baki...........✍️






*ZAHRA ROYAL STAR CE*



Share fisabilillahi🙏🥰


*💔🧟‍♀️☠️SILAR MUTUWA🧟‍♀️☠️*💔
(Horror Story)





ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️







*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*



PAGE 3️⃣➡️4️⃣



Wani irin jini kalar ruwan ganye ke zubowa tana lashe baki, nuna sa tayi da hannunta wani farin haske ya fito ya shigi Goga wata irin zabura yayi yana makyarkyata kamar wanda wutar neper ta kama sai da taga ya wahalu sana ta saki wata irin dariya mai k'arar gaske sana ta b'ace b'at sai dariyar da tayi ce ta karad'e lungu da sako na wajan wata irin amsawa kuwwa dariyar ke yi kamar yanzu ne take dariyar.



Su Goga kuwa ganin sun tsira ba wadda ya tsaya d'aukar wanni abu suka arce da mugun gudu yadda kasan ita ce ta biyo su a baya.



Basu sauka a ko ina ba sai a wani rub'ab'b'an gida wadda suke kwana kai daka kalle su kasan sun jiga tu wani daga cikin su ya ce "kai Oga na kasa tuna miye ma ya faru a wajan shin muryar wacece muka ji ne?", Kowa shuru yayi dan kwata-kwata kamar anyi masu yasa a cikin kwanyarsu sun kasa tuna shin muryar wacece ma suka da...


Read / Download SILAR MUTUWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album