Join Our WhatsApp Group

Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

ALJANI YA TAKA WUTA Complete Hausa Novel Document by ALJANI YA TAKA WUTA


ALJANI YA TAKA WUTA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 27494



ALJANI YA TAKA WUTA

Reading Time: 2 Hours

Added On: 03, Apr 2024

Author: Nazir Adam Salih ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Horror novels

File Size: 156.24 kb

File Type: txt

Views: 531+

Download: 381+

Last download: 18 hours ago

Description/Story: LABARIN ALJANI YA TAKA WUTA Part 1.
Duk wannan kadan ne daga cikin cikin kaunar da
yarinyar take nuna masa yau kusan shekaru shida
kenan tun suna firamire, kullum aikin t kenan
taso shi ta kuma yi masa wahala, kuma duk
sanda zai koma makaranta ita ke zuwa da motar
gidansu ta mayar dashi, bayan yan kananan siye-
siye da take yi masa har kudi take bashi. Amma
kuma abinda bata saniba shine mafi yawa daga
cikin kudin da take bashi a shaye shaye da
yawace-yawacen banza suke tafiya,domin in har
kana neman shaidani a duk fadin makarantarsu,
idan ka sami Nuraddin ka kare."Badawiyya
kenan". Nuraddin yace gami da dan tattausan
murmushi."Nuri 'darling' kenan". Badawiyya
tace.Ga mamakinsa sai ya ga ta dauko tsohuwar
jakar da take cewa bazata dauka ba, ta rataya
kafada."Zo mu tafi dan Allah Nuri so kake muyi
rana?Nuraddin na gaba dauke da jakankunan
ledar biyu, ita kuma na biye dashi a baya dauke
da mushenzakaran jakar Nuraddin. Duk inda ta
wuce, sai tabar iskar gurin da madaukakin
kamshin turaren dake jikinta, tana tafiya iska na
kada siraran gashin kanta wadanda ke kokarin
fitowa ta ciki farin gyalenta mai raga-raga dake
lullube da kanta.Hajara ta fito daga daki a dai-
dai lokacin da yaran biyun suka ratso tsakar
gidan. Badawiyya tayi sauri ta durkusa."mama
ina kwana?""Lafiya lau Badawiyya", Mahaifiyar
Nuraddin ta amsa, sannan kuma ta dubi
Badawiyya. "oh 'yar nan bakya rabuwa da
wahala, ko yaushe dai sai kinyi masa wahala,
'Badawiyya ta sunkuyar da kai cikin
girmamawada alkunya tace a hankali."ba.... Babu
komai mama"."An gode to, Allah ya saka miki
Badawiyya." mahaifiyar Nuraddin tace da ita
sannan ta juyo ga Nuraddin."Ga wannan ka tafi
da ita, malam ne yace a baka, maganin tsautsayi
ce, yace duk inda zaka, ka rinka tafiya da ita," Ta
mika masa wata 'yar kankanuwar laya wacce aka
rufeta da jara fata.Nuraddin ya karba, ya dubi
Badawiyya suka yiwa juna murmushi, sannan sai
yara biyun suka juya suka tafi."Allah ya kiyaye
Nura." mahaifiyarsatace dasu."To mama saina
dawo.Koda yaran suka fice daga gidan saibabar
Nuraddin ta dubesu sannan ta Dubi Badawiyya ta
girgiza kai sannan tace cikin zuciyarta "kai
wannan soyayya ta yaran nan da ban mamaki
take, yanzu ace yarinyakamar wannan ta
makalewa wannan yaro wanda shi ba komai ba,
to, meyiyuwa dai shima farin jinin malam zai
biyo." sai kuma abinda bata sani ba shine farin
jini ma yanzu ya fara, domin kuwa bada dadewa
ba farin jinin zai sake hada shi da wata sabuwar
budurwar mai ban mamaki.*** *** ***Nuraddin ya
mika, sannan yayi wanikwakwaran fito ya dirgo
daga kan gado, ya dubi sauran gadajen dake
dakin babu kowa akansu sai gado daya wanda
Auwalu surajo ke kwance a kai yana karatu. Karfe
tarada rabi na dare, duk sauran daliban dake
daikin sun tafi ajujuwan karatunsu domin bitar
abinda aka koya musu.Nuraddin ya durkusa karka
shin gadonsa ya janyo akwatinsa, sannan ya
bude ciki. A lafe a kasan akwatin, kudin kusan
Naira dubu biyar duk Badawiyya ce ta bashi
kudin. Nuraddin ya zaro dari daga cikin kudin ya
tura ciki aljihun gaban rigarsa. Sannan ne yaji
motsia bayansa, yayi firgigit cikin sauri yarufe
jakarsa don gudun kada wanda ke shigowa yaga
kudin da yake ciki. Duk yake dai Nuraddin yasan
babu wani shege a cewarsa, daya isa ya taba
kayansa koda wasa ballanta nada sunan sata,
amma yasan in an tambaye shi dole shima ya
bayar, tunda ana bashi, wannan shiyasa baya son
asan yanada kudi da yawa."Mene ne na boyewa
ai mu dama ganin falleliyar babynnan ta
kawokacikin arniyar motar nan munsan da
karfinka ka dira.Nuraddin ya juyo domin ganin
mai maganar, duk da dai kafin ya juya ma yasan
duk daniyar ba mai muryar nan sai wazirinsa
Nafi'u {BOSS}."shegen duniya daga ina haka,
dakin karatu ko makaranta?" Nuraddin yace
sannan ya mika masa hannu suka tafa tas!
Kamar an mari jaki da faranti."wace irin
makaranta kuma banda wannan da muke ciki?"
Nafi'u boss ya tambaya lokaci guda kuma ya
zauna bakin gadon Nuraddin."Ku dubu allonku
daya nake nufi".Oh shet! Men, ai abin da ya kawo
ni kenan, ance kuwa fim din yau wani arnen
Indiya ne, ana fadamin labarin sai ka fado min a
rai, to ni sam-sam ban dauka ka bayyana ba to
shine hamza siyasiya ya ce min ai dazu yaga
bayyanarka kuma wai wata ba kyau din beby ce
ta kawoka,nan da nan na garzayo, domin yau duk
aljihun ka zamu shiga sinimar nan dan bai yiyuwa
fim din nan ya wuce mu". Nafi'u boss yace ya
dan tsagaita yana mayar da numfashi."to uban
shegen surutu ka gama tsarani din?""Ah! Haba
Nuri namu, kai kasan ai mu da kai haka muke".
Ya hada tafikan hannunsa biyu guri guda."wai ina
su Basiru logarizim ne?" Nuraddin ya tamba.Duk
suna can bayan 'central hall' kai muke jira kawai
yau duk aljihunka zamu shiga sinima kai harsigari
ma yau ba mai siya da kudinsa......

Aljani Ya Taka Wuta!..2
;
;
sunyi sanadiyar faduwar dalibai da dama
jarabawa, haka nan tun da suka shigo
makarantar basu da aiki sai shiririta, yau kusan
shekaransu shida kenan, wannan itace
shekaransu ta karshe a sakandiren. Da yawa
daga cikin su suna zuwa makarantar ne kawai
don ace sun gama, amma badan su sami sa
kamako mai kyauba. Ba kowanne mutum bane,
ba kuma ko wanne mai karfin zuciya bane zai
baƙin kungurumin dajin dake tsakanin makarantar
zuwa cikin gari ba, domin tafiyar kusan kilo mita
biyar ne zuwa cikin garin, an kuma ce zai hanyar
cike take da aljanu da kwumakwumai, amma
hakan bai tsorata su ba musamman Nuruddin,
domin shi ko babu mai zuwa zai gwab kama
hanya abinsa shi kaɗai, dole ne sai yaje. Anyi
musu nasiha sunkiji an horesu da bulala duk
banza kai har wa'azi na anyi musu. Malam
mahmud bashir malamin arabiyyane a
makarantarsu Nuruddin ya taɓa cewa dasu
watarana suna ɗaukar darasi " kuyi a hankali
yara, mun sami labarin akwai wasu takadarai
acikin ku waɗanda kullum kwanan duniya sai sun
shiga gari sunyi kallo a sinima, to ina
shawartarku ku da ku bari, ba don komai ba
kuma sai don lafiyar ku, kunsha da jin haɗarin
dake tattare da wannan dajin na irin kwankwamai
dake ciki, amma don taurin kai ku nace sai kun
fita cikin dare. To wallahi kuyi a hankali inba so
kuke watarana wani ya farka a cikinku da siririn
hannu shanyayye kamar lagwanin risho ba "
yaran suka fashe da dariya to amma nasihar
malam mahmud bashir tamkar zuga ce ga
takadaran yaran biyar. "kai rabu dashi ajawo,
muzai yiwa wa'azi da wani dogon gemunsa
kamar buroshin wanke kwalabe ". Nuruddin yace
da yaran su kuma suka bushe da dariya. Watanni
biyar kenan da faruwan hakan.
****
Cikin sinimar ya dauki hayaniya lokacin da
bangwaleliyar kalmar *{ THE END }* ta yiwa
kanta gurin zama a kan farin allon sinimar. Ba a
dade ba su Nuraddin suka fito, suka kamo hanyar
dawowa makarantar karfe daya da rabi na dare,
domin ranar fim biyu akayi a sinimar.Yaran biyar
suka keto cikin bakin daji, bakajin komai sai
hayaniyar yaran wadanda ke tafiya sunata
hayaniya gami da tada kura kamar shanu. Babu
alamar farin wata a cikin dajin, babu kuma wani
kwakkwaran sauti sai jefi-jefin kukan gyare dana
tsuntsaye nan da can."Kai ku tsayani na taka
kaya." basiru logarizim yace dasu."Gafara can
malam waye zai tsayaka, ka kwana ma a nan
mana waya damu da kai". Nuraddin yace
dashi."To kada ku tsaya din mana wata tsiyar
ce". Sauran yaran suka busheda dariya sannan
sukayi gaba suka barshi gurin tsugunne yana ko
ƙarincire kayar.Basu dade da barinsa ba, sai
basiru yaji motsi a bayansa yana juyawa sai
sukayi ido biyu da wata katuwar kyanwa baƙa ƙirin
da ita kamar kwanta. Idanunta jajaye suna sheki
kamar kwalba a cikin rana. Basiru ya dubi magen
itama ta dubeshi , iska taci gaba da karkada
ganyayyakin bishiyoyin dake zagaye sannan ya
rarumi wani bushashen itacen bishiya dake kusa
da shi ya nufo magen, amma sai taki
guduwa."Ah! Kaga marar kunya! Basiru ya fada
cikin karaji sannan sai ya ɗaga itacen yakai mata
duka. Tun kafin itacen yakai ga kan magen yaji
hannunsa ya yi sakh yayi lararraf dashi kamar
tsumma, babu nauyi, ga mamakinsa sai yaga
hannun yana motsewa a hankali a hankali har ya
koma kamar kaurin kyandir, sannan sai yaji
hannun nasa ya fado jikinsa tamkar dama ba a
jikinsa yake ba."wayyo Allah na shiga uku! Ah!
Ah! Ah! Nura! Dan Allah kuzo na shiga uku.....Na
lalace".Sannan sai wata kakkausar murya ta kece
da dariya, muryar babu dadin ji kamar muryar
jaki.Ihun da suka ji a bayansu, shiyasa su juyowa
lokaci guda tamkar sojoji yayin faretin ban girma
a gaban shugaban kasa."Kunji wannan shegen
kamar sunana yake kira, ihun menen...Sauran
maganar ta makale a fatar bakin nuraddin lokacin
da sukaji an sake ihun, a wannan karon har da
kuka. Yara hudun suka dubi juna sannan suka
dubi ciki duhun dajin inda suka baro Basiru. Kuzo
mu ko mu gano shi. Nuraddin yace da sauran ko
wannensu tsumayake, sun gama tsorata don haka
sai sukayi sororo kamar gumaka suna kallon
Nuraddin."ko bakwaji nane?
¤¤¤¤
A dai dai lokacin ne suka hangi basiru ya ratso
cikin duhun dajin yana tafiya yana hada hanya
kamar dan giya hannunsa na hagu a dafe
ahannunsa na dama yana kuka, sannan sai
kakkausar muryar mai kama data jaki ta sake
kecewa da dariya. Yaran suka fara waige
waigecikin firgici a tsorace sai dai kuma basu ga
mai dariyar ba, duk abin nan da akeyi, shi
Nuraddin ko ajikinsa, domin idan akwai wani
abuda ake kira tsoro a duniya shi baima sanshi
ba."yau ga shegantakar banza inba tsoro ba a fito
fili mana!" Nuraddin yace cikin karaji. Dajin ya
amsa kuwwar abin da yace.Cikin firgici, Nafi'u
Boss ya matso kusa daf da Nura ya dakeshi a
baya."Me...Menene kuma haka nura, so kake a
halaka mu a banza?" Yace bakinsa na
rawa.Nuraddin ya buge hannunsa gefe guda
sannan yayi sauri ya tari Basiru wanda ke...


Read / Download ALJANI YA TAKA WUTA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album