Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

MANNUBIYA
O 1
NA
Humayrah Bulama


Daga k’ungiyar ELEGANT ONLINE ✍🏽

__________________

A shekarar 1990, A garin Kano.

A hankali yake tu’kin motarsa k’irar Daewo Nubira.

Kamar ba Ya so ya k’arasa inda
Zai je saboda yanayin tuk’in na sa daya ke yi a gefen titi a hankali, a hankali.
Sannu sannu Bata hana zuwa… in ji malam bahaushe don
A hakan ya samu ya k’arasa gidan shi dake unguwar sharad’a. Ko da ya k’arasa bakin gate din bai yi horn ba sai da mai gadin da kan sa ya ji tsayuwar mota ya lek’o
Tukunna ya koma da sauri ya wangale gate d’in Madaidaicin flat house d’in. Jikinsa na rawa
Sakamakon ganin uban gidan nashi ne ke tsaye a waje.

Ko da ya shiga ya k’arasa yayi parking
Kashe motar kawai ya yi ya d’aura kanshi a jikin sitiyarin motar ba tare da ya fito daga motar ba.


Yafi minti talatin a haka yana tunani shi ka’dai Kafin tashi d’aya gaban sa ya yanke ya fa’di.
Ransa ya sake b’aci
Sakamokon Jin fitowar ta .
Ko ba a fadi mishi ba ya San Khadijah ce ,tunda basu da me aiki a gidan daga shi sai ita sai mai gadi Wanda yake musu har wankin kayansu da guga.


Shiruu kawai ya yi yana jin ta ta rufe k’ofar parlourn data bu’de ta fito ta tunkaro motar Da yake ciki a zaune.

As he expected, tana zuwa
Ta banka’da k’ofar motar da k’arfi.

Ko sannu da zuwa babu
Cikin fushi ta ce “Shine sai da ka kira Abba ko? Cin fuska da
rashin adalcin da ka kusan aikatawa bai isheka ba.

Shine an kashe magana an gyara komai zaka wani wuce ka kira Abba, Me kenan kake so
Yanzu? So kake ya goya maka baya ko me?”

Bata jira Jan numfashi ba a hassale ta d’aura da cewa
“Tou bari kaji ,Ko ya Goya maka baya abinda kake so ba zai tab’a faruwa ba Wallahi, Tunda in kana tunanin Abba yana bayan ka ni kuma daddy yana baya na. Ta k’arashe maganar Tata cikin tsananin bacin rai da takaici.

Tun lokacin data iso ta fara magana Shima ya Ha’de rai ,
Fuskar nan tamau kamar bai tab’a dariya ba.
Ba tare daya kalle ta ba
ya zare key d’in motar
Ya d’auki abubuwan buk’atar shi ya mik’e ya fito daga motar.
Ko kallon inda take bai yi ba
Ya fara k’ok’arin wuceta .

Da dan karfi Sannan da sauri
Ta rik’o hannunshi
Cikin tsananin bacin rai ta ce
“IMAM ,Wallahi na fi k’arfin ka wulak’anta ni ,
Ai so ba hauka bane,bar ganin wai Ina sonka
Wallahi idan baka janye maganar nan ba zan maka abinda sai ka yi daka sanin ha’duwa da ita kanta khadijar zan Baka mamaki zan sanyaka ……..”

“Sannu Uwarsa”

Suka ji Muryar Abba daga sama
Wanda ba su san lokacin daya shigo ba
ta daki dodon kunnuwansu .

Tabbas ,ta sha jinin jikinta amman sam
Kishi da Bak’in cikin da yake a kwance a kan kyakkyawar farar fuskarta be Kau ba Sannan zuciyarta banda turnik’i da tafarfasa ba abunda take yi.

Ganin yanda Abban ya kafeta da idanuwa yana me
K’arasowa inda suke ne
Yasa ta d’an sunkuyar da kanta k’asa da sauri kuma ta cikawa
Imam din hannu .

Abban yana k’arasowa
Imam ya durk’usa har k’asa ya gaida shi ,bayan sun gaisa
Ya ‘dora da cewa
“Abba ai da ka bari mun k’araso
Don Yanxu nake shirin in yi wanka mu karaso wajen naka.”
“kada ka damu ai
Babu nisa Kuma Ina buk’atar yin tattaki din dama”
Haka kawai Abban yace Yana kallon khadija wadda take gaishe shi “ ina wuni”
Cikin d’an russunawa .
Bai amsata ba,ya juya ya bi bayan Imam
Wanda ya juya ya nufi k’ofar parlourn nasu da d’an sauri yana ce wa “Bismillah Abba. Da kansa Imam ‘din ya shiga ya kawo masa lemo mai sanyi da ruwa sai ‘d’an snacks a Gefe.”
Dan khadija Bata riga ta shiga parlourn ba .

Tabbas yanda taga abba tasan ba ze bi bayan ta ba
Sannan ba
‘daga mata kafa
Zai yi ba yau ,kuma tasan Abban nasu
Baya tolerating nonsense da tirjiya .

Zata iya cewa Bata tab’a ganin soyayyar ‘ya da uba irin ta Abban ta da sister din ta ba Amman tunda tayi mishi lefi ya fita harkarta
Ya yafe ta
Yanxu hatta ita kanta Bata San inda yayar ta ta take ba .

Ayanxu
Tsoron ta daya
Shine
kar ya goyawa Imam baya kuma ya turje Akan se ta bi ta yarda da abunda Imam din yake so
Dan inde haka ta faru
Tou wallahi ta shiga ukun ta .

Ko da ace ba Imam ta aura ba ,
Bata jin zata iya zama da kishiya ,
Ballantana kuma Imam din ne ,
Ayanda take masifar sonshi
Bata Jin xata iya jurar ganin wata ‘ya mace a matsayin matar shi bayan ita .Watan ma kuma Khadija ,
Yarinyar data san yana tsana nin so
Domin ko
Satin daya gabata
Haka ya fito kiri kiri
ya ce mata albarkacin sunan su yaxo daya ne yasanya
yake mata raha
yake dan kulata

…….
Tasan rashin shigarta Akan lokaci
Ka iya sake hasssala Abba,don haka ta yi ‘ko’kari ta tsayar da kukan nata da kyar
Ta goge hawayen ta
Ta nufi parlour itama .

Abba yana zaune a kan kujera
Imam a gefen shi
A zaune a kasa

A
Haka ta shiga ta samesu ,
Dan haka itama ta karasa ta zauna a kasa dayan gefen kafar Abban.


Ba tare daya kalleta ba yace
‘’Se yanzu kika ga daman shigowa kenan ‘’
Be Bata damar cewa komai ba
Ya sake cewa
‘’Inaso ki nutsu kiji abunda xan fada miki yanxu
Na farko shawarace
Na biyu ma kmr shawarar ce
Na uku kuma umarnine
Kuma dole kiji, Sannan kiyi .

Still be dau lokaci ba ya daura da cewa
‘’In mata uku Imam yace xe k’aro baki da hurumin shiga Kice A’a ‘’.
‘’Ki zauna a matsayin ki
Sannan ki yiwa mijinki biyayya ki bashi goyon baya ,
Ni ma a matsayina na mahaifinki
Kiyimin biyyayya ki yi abunda nace ‘’.

‘’Khadija,!
Imam ze Kara aure
Banason in ji wata matsala ta kuma kunno Kai daga gareki
Har ayi auren nan a gama
Ina ba haka ba Wallahi …..’’

Kukan data rushe dashi kmr Ana yanka ta ne yasa duk suka xuba mata ido kawai ,
Suna kallon ikon Allah .


Cikin kukan tace
Haba Abba
Ko
Wata na biyu ban gama rufawa a cikin gidan nan ba
ace za ayimin kishiya
Kuma Kuce inyi hakuri inyi shiru ?,
Shi meyasa ba zai hakura ba ,
Daddy fa yace be yadda ba bayason ya sake Jin maganar.

Cikin katse ta Abban yace
‘’That was when daddyn besan cewa ita wachchar khadijan ya fara so ba
Kuma itace budurwar sa tun asalin farko ba ,
Bari kiji tun Kafin shi Daddyn ya fara maganar ku ke da Imam
Already
Imam yayi min maganar khadija ,
Maganar aurenki ce ta sanya ya daga kafa
Dan haka yanxu Banga dalilin da zai sanya ya fasa aurenta saboda ke a karo na biyu ba Wallahi ‘’.


Cikin kuka tace
‘’Abba har fa ciki ta zubar
Kuma tsabar cin fuska
Har gidan nan ya kawo min ita
Lokacin
ko sati biyu ban yiba
a chan boys quarters din akayi jinyar ta
Saboda Bata da kowa ,
Taya za a hadani kishi da wadda ta gama shigomin gida ta San sirrina
Wadda Bata da iyaye
Me yawo a titi suna tallan Nono
…..’’

‘’Ya Isa haka ,khadija ‘’!
Abban ya daka mata tsawa cikin tarar numfashinta

Kafin yace
‘’Tashi ki tafi ki bani guri ‘’

Zata yi magana ya kuma daka mata wata uwar tsawar dan haka taja ta mike ta wuce ta shige daki tana wani irin kuka .

Ko da ta shiga dakin ma
ta jima
tana kukan Kafin daga karshe ta
Yanke shawarar Neman
‘Larai ‘

Saboda ta Lura Hatta mahaifiyarta ita ma bayan Abban take bi .
Iyayen ta sunada matukar kawaici
ta San Imam baya son ta
Biyayya ce ta sanya ya aureta,
Shiyasa su kuma iyayenta baxasu taba goyon bayan ta ba
Saboda
Gudun Samun matsala da
‘family frnds ‘d’in nasu .

Shiyasa gwara ta nemawa kanta mafita
Tun Kafin kawaicin fulanin iyayenta ya cutar da ita .

A nata lissafin
kamata yayi a ce an barta da Imam ta juyo da hankalinshi gareta ,
Bawai a hadata kishi da wata chan daban wadda zata zo ta lalata komai ta kuma janye mata hankalin masiyo ba ….

Khadija Tana shigewa ciki
Abba ya dan gyara zama ya kalli Imam kafin yace
‘’Naji Khadija ta fadi wani Abu wanda ban san dashi Akan khadijan da kake son ka auro ba
Ina fatan zaka cemin ba Dede bane ba .’’

Lumshe idanu Imam yayi
Kafin ya shafa farar fuskarshi
da tafin hannunshi ,
wanda tayi jajir zuwa yanzu tsabar shiga tashin hankali .

Abba. Is his only hope yasan shi kadai ze iya convincing su daddy su barshi ya auri khadija.
Abunda yaketa tsoro dama shine
kar su san kaddarar data afka wa khadijan dan yasan Muddin suka sani da wuya Abban shima ya yarda

Seda yaji Abban ya sake cewa
‘’Imam ,kayi shiru ‘’

Tukunna Ahankali ya bude idanunshi
Cikin sanyin jiki yace

‘’am Abba
Kmr yanda na gaya maka
Khadija Bata da kowa
Ita da Y’ar uwarta na sani tun farko suna kawo mana Nono office
Se kuma wani Uncle din su data taba hadani dashi
Wanda suke a gidanshi ,
A halin yanzu
Shima ya rasu
Kuma dama
matar tashi azabtar dasu takeyi
Tun a lokacin dayake a raye ma .

Shiyasa
Yana rasuwa ta tartara ta barsu ta yi gaba .
Su sunce
min Uncle din nasu da Baban su kawai suka sani
Ba su taba xuwa garin suba bama su dan garin ba har Baban ya rasu yanxu gashi shima kawun nasu ya rasu .
Shiyasa tun a lokacin naso in auri khadijar saboda itama yayar ta miji ya fito mata ta auri wani me mata uku da yara ashirin a layin nasu Amman yace ba zai rike Khadijah ba

Nasan zaman ta ita kadai akwai hadari
Shi kuma Daddy ya dage Akan sede ayi auren mu da Khadija tunda an Riga an gama magana

Ko uzurina be tsaya yaji ba
Gani yake yi kamar turjiya nake shirin mishi
Shiyasa na hakura
A wannan lokacin
kmr yanda kace inyi hakurin .

Itama ba yadda Banyi da ita Akan ta biyo ni ba Amman tace Zata iya zama ita kadai

Ni kuma abubuwa sun sha min Kai
A wannan lokacin
Ga hidimar biki
Ga aiki
A wannan tsakan Kanin ne aka samu wani Mara Imani yaje yayi mata fyade
Sam ba laifinta bane
Saboda seda tayi kwana biyu a asibiti Batasan ma a ina kanta yake ba

Tun daga lokacin naki amincewa taci gaba da xama a gidan ita kadai
Laifina daya dana kawota nan
Nasan be kamata in kawota nan ba
Tunda gidan aure na ne
Amman banida choice
Tunda su daddy baxasu Bari in Kai musu ita Chan ba
Ba tare da sunsan wacece ita ba
Gashi cikin data samu ata dalilin kaddarar data afka mata
Yaxo da matsala
Ana yin sati biyu ta fara bleeding muna xuwa asibiti ya zube.
Ga rashin lafiya ga rashin safety da shelter,
Shiyasa na kawota nan ita da nurse
Kuma
tunda khadija tayi bincike ta gano asalin gaskiya ta fatattakesu
Se da nayi kwana uku tukunna na nemota da kyar ‘’.

Shiruu ya danyi Kafin ya daura da cewa
‘’Dan Allah Abba ka duba Lamarin nan
Mu taru ni da Kai mu ceto rayuwar baiwar Allah ‘’.

ya karashe maganar cikin hade hannuwanshi kamr xe fashe da kuka .


Numfashi Abban ya fesar
Bayan dogon Nazari

Kafin ya kalli Imam din yace
‘’Zan ha’daka da driver gobe
ku je ayi duk wasu gwaje gwaje da suka kamata
Allah ya sanya alkhairi
Allah yayi maka albarka ,
Zanyiwa daddyn naku magana
Karka damu ze fahimta .’’


Wani tsananin sanyi ne ya lullube Imam ,har seda wasu hawayen farin ciki suka wanke mishi fuska .

Murmushi kawai Abban yayi ,
Daga haka ya mike da shirin tafiya .
Tsakanin uba da ‘ya se Allah
Yasan abunda yayi
Yake kuma shirin yi
Tabbas shine Dede ,
Amma kuma a take tausayin ‘yar shi se ya lullubeshi ,
Dan Tabbas yasan tunda har Imam ya rufe ido ya sake mishi zancen wata
Bayan ya aura mishi ‘yar shi
Ko watanni biyu ba a rufe ba ,
Tou fa ba karamin so yakeyiwa
Wachchar bafulatanar me tallan Nono ba .

Har ga Allah
Da ya ji shiru bayan wata daya da auren su Imam din
ya dauka ya hakura ne ,
Ashe abun yananan .
Tabbas rayuwar ‘yar shi khadija
Tana cikin garari .
Saboda tun shekara daya da ta gabata
A lokacin da aka fara maganar aurensu har kawo yanxu
Be taba ganin digon son ‘yar tashi a cikin idanun Imam ba .

Daddy is his best frnd
Tun yarinta ,Ba da ban haka da yanda yaga Daddyn ya nace da son yaga ya kulla aure a tsakanin su ba
Da babu dalilin da zai sanya ya yarda da auren khadjan shi da
Imam,
Tunda ya San
ba sonta yakeyi ba .

Yana fatan su samu su da sasanta ya so ta wata rana
Tou
Yanxu kuma gashi xe auri wadda yakeso .
Fatanshi daya Allah yasa khadijan tayi hankali ta kwantar da hankalinta tayi biyayya ta zauna lafiya
Watakila ta samu matsugunni a xuciyar mijinta
In ba haka ba kuwa
Bayajin tanada rabo a xuciyar Imam ……..


An dan Kai ruwa rana Kafin
Daddy ya yarda aka daura auren khadija da Imam a cikin sati daya ,
Ba kalar haukar da Khadija batayiba
Har kalanzir ta Barba’da a gidan yana bacci
Lokacin ana ‘I gobe ‘daurin auren
Allah ya taimaka
ya ji warin kalanzir din ya farka da wuri .
Yana xuwa ya tarar da ita tana kokarin kyasta ashana
Da kyar ya samu ya karbe
Yana jefar wa ta rarumo wuka,
Ganin fa dagaske kishi ya haukatata in ya barta kashe shi zatayi
Ne
Yasa ya fincikota dakyar ya fitar ya saka ta a mota .

Iyayenta kamar iyayenshi ne
Dan ze iya cewa
Shi da ‘dan uwanshi especially ma shi in particular kusan a hannun maman ta ma ya girma
Amman ya kamata a takawa haukar ta burki
Tun Kafin tayi ‘barna .


Ba dan yaso ba
Haka ya Kai ta gidansu ya fadawa su Abba duk abunda takeyi mishi
Har kokarin kashe shi data fara yau dinnan .

Sallamar shi kawai Abba yayi
Bayan ya bashi hakuri
Daga haka ya wuce ya barta a wajen su Abban don yace a bar mishi ita .

A tunanin ta fada kawai
Xa ayi mata
Daganan a maida ita
A ranar
Amman se taji Abba ya Hana
ya Hana ma a Barta fita ko kofar gida .
Tana ji Tana gani haka aka daura auren Imam da amarya Khadija .
Ba abunda yafi daga mata hankali irin yadda Abba yace
‘’baxata koma Kwata Kwata ba ‘’
Gashi auren datayi hauka akai ya Riga ya Kara
Dan haka
A take ta fara data sani
Hankalin ta ya sake tashi
Dan gani tayi
kmr ma ta bawa Imam damar cin
amarcin shi hankali
Kwance .
Ko sati ‘daya Ba ayi ba ta fita a haiyyacinta
kamar mahaukaciya haka ta koma

Ba da ban larai datake Bata Baki da mahaifiyarta ba
Da tuni ta xauce
….


Seda ta sha wahala ta fita a haiyyacinta tukunna
Dakyar su mama mommy daddy suka takurawa
Abba ya Kira Imam yace ya xo ya dauketa .
A Lokacin khadija amaryarshi Watan ta daya
Har da ‘dan cikinta
…..


Tare da Larai suka koma gidan nata
saboda itama a lokacin an dan samu matsala da ita a kauyensu
Taki ta koma

Ba karamin mamakin yanda khadija ta chanxa lokaci guda Imam yayi ba

ba kishi ba hauka Sannan taja abokiyar zaman ta a jiki kmr zata cinye ta dan so ,
Cikin jikinta kuwa ko ita uwar iyaka yadda zata kula dashi kenan
Komai
Nan nan. Ko abu me nauyi Bata ta’ba Bari ta dauka ,
Bata girki su sukeyi ita da larai
Ko ruwa taje tafasawa haka khadijan zata amshe
Ita ko larai wata ta tafasa
Ta Kai mata har daki


Wani
Abu da Imam yayi noticing
Shine
kullum fuskar khadija uwar gida
da idanunta a kumbure suke
Yayi tambayar duniya tace mishi kawai ciwon ido ne yake damunta .
A yadda suka hade kansu gidanshi kullum cikin xaman lafiya da lumana
Shiyasa ya kauda duk wasu negative thinking
Ya rungumi matanshi .

Shima a bangarenshi
yana ‘ko’kari Sosai wajen Kwatan ta adalci
Shi kan sa yasan yana namijin ‘ko’kari wajen ganin yayi adalci a tsakanin matan na sa
Duba da yadda yakeji game da ko wacce a cikin zuciyar sa

A yadda uwar gidan sa take kula da amaryar
Ya kamata ko Albarkacin haka ne
Ace taci
ta samu guri a zuciyar sa
Amman har gobe ya kasa bata
Ko da kaso daya a cikin Dari na zuciyar sa .
Saboda
Amaryar ta riga ta hade ta mamaye gaba daya kaso Dari din
Itace zuciyar tashi ma gaba daya .

Amman kuma dukda haka
sam baya Bari a gane
Yana iyakar bakin ‘ko’karin sa sa wajen boye hakan.
Abu daya yake yi wasu lokutan yake tonawa kam sa asiri ,

Kasancewar sa mutum me masifaffen kishi yasa yadda yake kishin amaryar su kansu su larai sun fahimci baya yi wa uwargidan ta sa .

Tsananin kishin sa ya San ya ko abokan shi ba ya Bari su gaisa da amaryar sa ,
In xa a fita ya dinga gyara mata xaman hijabinta yana rufe koina
Ko
Gaisuwar me gadi in ta amsa se ta hadu da fushin sa na en kwanaki .
Sa’banin
yanda yakeyiwa uwar gidan sa .

Shiyasa ko ba a fa’da ba ko ya boye su sun Riga sun sani
Ba tare da shi kanshi yasan sun gama gane wa ba ……


Cikin khadija amarya yana wata biyar Imam ya tattara gaba daya dukiyarshi ya damkawa babyn
Mace ko namiji be damu ba kawai de shi yasan ya gama yanke shawarar in aka Haifa mishi baby na farko a rayuwarshi to ya bada komai nashi .
Khadija har kuka ta dinga yi Akan ya janye wannan ‘kudiri nashi
Dan xe janyo mata bakin jini ,
Amman furr yaki

Daga karshe de ya tilasta ta ba yadda ta iya tayi shiru
Sannan
suka tsaya akan cewa
Maganar zata tsaya iyaka su biyu ,
In ta haihu shi zai ci gaba da kula da dukiyar har se yaron ko yarinyar ya Kai minxalin aure tukunna xa a damka mishi komai

A cewarshi a yanda ya fada mata
Saboda farin cikin Samun haihuwa ne Shiyasa ya shirya hakan a ‘dan shi na farko
Kuma ko da ace uwar gidan shi ce ta Haifa tou hakan zai yi .
Amman a cikin xuciyarshi
Har ga Allah yayi hakan ne saboda tsananin so da kaunar da yakeyiwa amaryar tashi ,
Saboda yanda yake sonta ya kwallafa rai a kanta haka yake ji da cikin jikinta kmr ranshi .


Wani sabon abu
daya fara lokacin da cikin yakai wata bakwai shine
Rashin godewa abunda su larai sukeyi ,
Duk irin ‘ko’karin da sukeyi da khadija se ya Dena gani ,
Ko maganinta ne Bata sha a kan lokaciba
Ranar se anga abun mamaki
Ya dinga masifa har washegari .

Kuma inde khadija tayi missing magana tou it’s either wachchar khadijan girki take mata ko wani Abu makamancin haka

Ganin rigima Tana shirin fara kunno Kai yasa ita da kanta amaryar ta kar’bi magungunan nata daga hannun abokiyar zaman nata Akan zata dinga sha dakanta

Dan ita kanta abubuwan da Imam din yakeyi Bata Jin da dinsu ,
Duba da yanda su khadijan suke namijin ‘ko’kari wajen Bata kulawa Amman Sam baya gani.

Abunda Imam yake yi Akan cikin nan zaka dauka akanshi aka fara haihuwa a duniya ,
Abu daya da uwar gidanshi tayi shine
Kauda Kai
Ta dauke kanta
Ta rufe idonta
Sam ta’ki yarda ta biye mishi,
Kuma
Sarai tasan da maganar yanda ya bawa ‘dan cikin khadija dukiyarshi kakaf Amman shima Bata ce ‘kala ba ,
Ita yanxu babbar damuwarta
Shine yanda har yanzu ta gagara daukar ciki,
Dan haka ta du’kufa addua
Ta bar Imam yanata kinibibin shi
‘Kar’kari in yace batayi wa khadija Abu ba
Ta bashi hakuri
A wuce wajen
Ko yana mita bata biyeshi .

A kwana a tashi ….
edd din khadija ya cika har ya wuce
Amman Sam
Bata jin ko alamun labour
Dan haka
Suka nufi asibiti .

suna xuwa a gwajin farko
aka fahimci
Babyn babu rai yama dade da mutuwa dan har kmr ya fara dagargajewa .

Sumewa Imam yayi a wajen da Jin wannan mummunan batu,
Dan xe iya cewa be taba shiga tashin hankali kwatankwacin wannan ba .
Har aka yi aikin aka gama aka cire babyn aka mata wankin ciki be farfado ba .

A tare sukayi jinya a asibiti
Dan ba kadan ba jinin shi ya hau

A bangaren khadija ma abun ba sauki
Dan bayan kwana biyu dayi mata wankin ciki
Yayarta ma ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment