Join Our WhatsApp Group

A ZATO NA Complete Hausa Novel Document by A ZATO NA


A ZATO NA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 74066



A ZATO NA

Reading Time: 6 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Jeedderh Lawals ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 389.75 kb

File Type: txt

Views: 827+

Download: 476+

Last download: 1 hour ago

Description/Story:  *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆*


*⋆©Jeedderh Lawals⋆*




*☆⋆01⋆☆*





Assalamu Alaikum wa Rahmatullah. Muna kara godiya da taruwarku a wannan zaure mai albarka, ina fata Allah Yasa mu gama lafiya kamar yadda zamu fara lafiya.

Littafin 'A Zato Na' mallakin wadda ta rubuta ne, ba'a yarda wani/wata su canza kowace irin suffa ta wannan littafi ba.

Muna fata zaku rike mana alkawari, ku kuma rike mana amana. Allah Yasa mu dace.
_Da sunan Allah Mai Rahma Mai jin Kai'_





'Kirr! Kirrr!!'...

Karan daya ziyarci kunnena kenan lokacin da na danna lambar wayar kawata Janan. Bata dauka nan take ba, sai da yayi kara kamar sau biyar.
Kafin ta dauka hakurina ya gama karewa, saboda haka tana dagawa, ban bari ko sallama tayi ba na tare ta da; "wai dallah can malama me kika tsaya yi ne kin tsaida mutane?".

Tace "jeez girl, bi a hankali mana. Ina jiran Anty Raheemah ne ta dawo kafin in fita".

Na ja dan siririn tsaki, "kawai ki fito ki bar mata gidan a haka mana. Ba maigadi yana nan ba?". Janan tayi ajiyar zuciya, "kin fa san abinda ya faru last time da nayi haka. Tace an shiga an mata satar kudi da jewelries, kuma dole sai da Yaya Bilal ya biyata sannan aka zauna lafiya, bana son abu makamancin haka ya sake faruwa". Nace "sai kiyi ta zama ai ta mayar da ke maigadinta. Ni dai wallahi idan baki zo nan da mintuna goma ba ko? Sai dai mu hadu da ke acan kawai!". Ban jira ta kara cewa komi ba na kashe wayar na ajiye ta a gefena.

Browsing naci gaba da yi da system dina, sai da nayi kamar minti goma sha biyar kafin na kashe na ajiyeta a mazauninta. Janan na sake dannawa kira, tana dauka tace "gani nan don Allah, sarkin gajen hakuri kawai!". Na tabe baki ba tare da na damu da abinda tace ba, nace "better. Idan kin iso ki kira ni kawai mu hadu a main entrance" tace "toh".

Gadona na dan gyara kafin ta iso. Zuwa lokacin da Janan ta kirani, na gama kimtsawa. Na dauki gyale na nada shi a kaina yadda ya zagaye rabin kirjina da bayana, na dauki wayar hannu, purse da flat din takalmi ruwan goro kalar veil dina da zanen flower da yake jikin doguwar rigar gown ta atamfa da na sa, na zura shi a kafata. Aylah, roommate dina na yiwa sallama na fita.

A bakin hostel din Queen Amina dake cikin campus din ABU Zaria, na tsaya ina karewa wajen kallo cikin neman Janan. Ina kokarin kiranta a waya na hango ta acan inda ake parking motoci a gefen hostel din tana dago min hannu, murmushi na saki cike da murna da dokin ganinta na taka a nutse na tsallaka zuwa inda take. A tsakiyar wajen ta tareni, muka rungume juna cike da doki. Duk duniya, ita kadai ce naki jinta kamar wata yar uwata ta jini, kamar yadda nasan itama haka take a bangarenta.

Na kalli iNext din da naga ta fito daga ciki ina daga mata gira, "Ya Almu ya sake sabuwar mota ne hala?". Ta girgiza kai tana murmushi, "ina Almu na yayi arzikin sayen irin wannan abun? Yaya Bilal ne". Na dan zare ido cikin mamaki, "Holy Wow!! Yaushe rabon da in ga Yaya Bilal? Har na manta wallahi. Yau dai Allah ya nufa zamu hadu kenan!".
Tayi dariya da tasa dimples dinta suka lotsa, abinda yake burgeni da haliitar ta kenan. Tace "sosai ma. Allah ne yasa ban samu abin hawa da wuri ba, shine yace bari ya kaini tunda shima wajen FCE din yayi. Taho muje, muna kara makara". Na bi bayanta zuwa wajen motar.

Janan ta bude gidan gaba, ni kuma na bude baya muka shiga a lokaci guda, bakina dauke da sallama. Sansanyan kamshin freshener na cytrus da mix din strawberry ya doki hancina hade da sansanyan sanyin AC daya dumame motar. Muna tsakiyar watan May ne, saboda haka ba karamin zafi muke sha ba a garin na Zaria.

A nutse na gaishe da Yaya Bilal, ya juyo a kaikaice ya amsa tare da juyawa ya tashi motar muka bar wajen. Babu abinda na iya kararwa game dashi sai cewa faded jeans ne a jikinshi da T-shirt mai zanen zebra a jiki, sai sunglass da ya saka ya sakaya idanunshi.

A hankali yake tukin, tattausar kira'ar Sheikh Malam Minshawee tana tashi cikin suratul-Kahf, na jingina kaina da kujerar motar na lumshe idanuna, a can kasan zuciyata kuma ina bin kira'ar bi da bi. Yayin da a gefe guda, shi da Janan suke hira jifa-jifa. Har muka isa makarantar Kongo, inda zamu je, a bakin gate ya nemi waje yayi parking. Sai a baki-baki ma yayi parking din, saboda yadda wajen ya cika da mutane da ababen hawa. Muka mishi godiya muka fita, ya ja motar ya tafi, mu kuma muka tunkari gate din makarantar.

Ranar babban Shehin malami, ' Dr. Bilal Philips' yake zuwa yin wa'azi. Saboda haka, you can only imagine yadda wajen zai cika da mutane wai don ma na mata ne zallah. Duk da mun zo kusan mintuna arba'in kafin a fara wa'azin, da kyar muka samu wajen zama muka zauna.

Akan Matan da zasu shiga aljanna yayi wa'azin ranar. Kafin ya gama, jikin kowace diya mace dake wajen yayi sanyi saboda yadda ya dinga zano abubuwa da mu mata muke yi, muna tunanin ba wani abu bane, either ga junanmu ko ga mazaje da iyayenmu, alhalin abubuwan nan za su iya jagorantarmu zuwa wuta. Karfe sha biyu na rana aka gama wa'azin, saboda karancin abubuwan hawa da aka yi ranar, bamu samu mun koma cikin makaranta ba sai kusan karfe daya da rabi.

A dakina muka sauka, Janan tayi sallar azuhur, kafin ta gama ni da bana yin sallah na gama dafa mana jollop spaghetti. Bayan mun gama cin abincin, kan gadon muka hau, na kunna mana film din Pick the Stars, wani Korean Film, muna kallo. Bamu jima da fara kallon ba, barci ya daukeni.


"Na'ilah!".
"Uhmn?" na amsa cikin barci.

A hankali naji an kai tattausan hannu gefen fuskana an shafa cike da wani irin tenderness da yasa naji bugun zuciyata ya canza sosai. "I Love You, baby! So much!!".
Aka fadi a daidai saitin kunnena, cikin wata irin tattausar murya. A hankali na bude idanuna dake cike da barci, mutumin da ke zaune a gefen gadon da nake kwance, appears very blurry, bana iya ganinshi cikin rashin hasken dakin.

"Na'ilah?" naji ya sake kirana cikin tattausar muryarshi, na saki murmushi a tausashe ina amsawa, "uhmmn??".

"Na'ilah!!". Wannan karon naji an kirani da karfi. A gigice na tashi zaune, kaina ya bugu da bango. Da sauri na dafe wajen na maida kaina kan pillow ina hararar Janan dake zaune a gefena, tana kallona cike da alamun tambaya.

Harara na jefa mata tun karfina, cikin tsiwa nace "dallah can Malama meye haka, zaki katse min barcina mai dadi?".
Ta daga kafada, "maganganu kike yi cikin barci. Abin naki ya dawo ne?".

Na kara komawa kan katifar na kwanta, "Wallahi kuwa Jan. Yaushe rabon ma da inyi irin mafarkannan? Har na manta. Sai yau".
Janan tace "to sai ki kiyaye da addu'o'i dai. Is'haq yazo yana jirana a waje, bari in tafi".
Na duba naga yamma har tayi.

Na mike ina lalubar mayafi na, "muje in miki rakiya to!".

Ta tashi na rufa mata baya, dakin na rufe kasancewar abokiyar zama na bata dawo ba, muka sauka kasa ni da ita.
Har parking lot na rakata inda Is'haq yake jiranta. Ta bude gidan baya ta shiga, na maida mata kofar na rufe ina daga mata hannu, a haka suka tafi. Sai da na tsaya anan kofar hostel din na sayi yoghurt babbar roba mai sanyi sannan na koma daki.

Bayan na yi yan gyare-gyare da kimtse-kimtse na, arm chair na dauka na ajiye a gefen gadona na zauna, na dora laptop dina akan gadon na bude tare da cigaba da kallon da muka fara ni da Janan.

Sai bayan magriba Aylah, roommate dina ta dawo. Har zuwa lokacin ina kan system dina, ta min sallama na amsa, a gajiye ta zauna a gefen gadonta. Sai da ta huta, sannan tayi sallah. Taci sauran spaghetti din da muka bari ni da Janan.
Ni kam karfe bakwai tana yi, na kashe laptop din na mike. Kasa na sauka inda common room yake, na kalli serieses din da nake kallo a Zee World; Twist of Fate da King of two Hearts. Karfe tara na koma daki, ina zuwa shirin kwanciya barci nayi cikin riga da wando, na bi lafiyar katifa na kwanta.

Hira muka fara da Aylah, tana bani labarin abinda ya faru a wajen bikin da taje ranar. Wai mutumin mace ta biyu ce zai aura, wadda ta kasance kawarsu ce. Shine a wajen lunch party, matarshi ta farko taje da tawagarta, aka yi rashin mutunci dai yadda ya kamata.

"Dama duka yaushe ne Yayan su Afrah kawata zai sake aure, amaryar ta hadu da uwargidan a shagon saloon. Wallahi tsiyar da aka yi a wajen sai ta baki mamaki. Kaca-kaca suka yi wa juna. Bayan anyi auren kuma da sati biyu, ya dankarawa uwargidan nashi saki. Naji ance kusan watannninta biyu a gida, sai kwanannan ta koma".

Nayi ajiyar zuciya tare da girgiza kai. Abinda yawancin mata suke jin tsoro game da kishiya kenan, taje ta fitar dasu daga gidansu. Ko ta hana su zaman lafiya da miji. Ko ta zauna, haka zaka kare rayuwarka cikin tashin hankali, fargaba da takaici.

Aylah ta cigaba da cewa, "ni wallahi gani nake babu wani aibu game da wata kishiya. Ba abokiyar zama bace? Menene a ciki? Idan dai ka kwantar da hankalinka, tsaf zaku yi zaman lafiya da ita wallahi!'.

Na kada idanu, "baki san komi ba game da kishiya Aylah. Kiyi shiru kawai. Ina tunanin duk danginki babu wadda take zaune da kishiya ko?".
Ta daga kafada, "Anty Hanifa ce kawai, kuma suna zaune da ita lafiya lau".

A hankali murmushi ya subuce min, "to wannan sa'a ce tayi ba karama ba, ina gaya miki. Wallahi da tayi rashin sa'a, gabadaya sai ta girgiza family dinku saboda sanabe".
Aylah ta girgiza kai, "naa. Bana tunanin haka. Kada dai kice min, baki son kishiya Na'ilah?!".

Murmushi kawai nayi, na gyara kwanciyata tare da mata sai da safe.


Dare ya tsala matuka, yayin da barci ya gagari idanuwana. Zuciyata tayi wani irin nauyi, ji nake kamar an dauki wani gungumemen dutse an dora min a kai, numfashi ma sai da naji ya fara gagarata. A hankali na janyo wayata da headphone na hada, na kamo kira'ar Sheikh Malam Ahmad Suleiman na kunna. Idanuwa na lumshe a hankali, ina bin kira'ar a cikin raina.

To say that na tsani kishiya, is an understatement.

I despise her! Na tsaneta with all my being.

Tunanin zama da kishiya kadai a cikin raina, yana sa jinin jikina tafasa, zuciyata zafi kamar ana diga ruwan dafaffiyar dalma.

Allah Ya gani, bana son kishiya. Ina kuma da yakini a cikin raina, ko zan mutu tuzuruwa, sai dai hakan ta faru, amma ba zan taba zama da kishiya ba!!.

And why not, you might ask?!

A shekaru na bakwa a cikin rayuwata, na dandana zafin kaidi irin na kishiyar uwa, a wani unfortunate dare, da na kira 'bakin dare'.

Ranar mahaifina yake sake aure, kyakkyawar bafulatanar mata, fara doguwa, tsayi wanda ta tafi gabadayanta ta mike, babu lankwasa ko duk'awa, har yau ina mamakin dalilin da yasa Baba ya aureta.

Idan kyawune, mahaifiyata tana daya daga cikin kyawawan cikin danginsu, kasancewarta ruwa biyu, shuwa-arab da barbanci, yasa ta kasance mace daya tamkar dubu. Kyawu, ladabi, biyayya, iya girki, kwalliya, kada ma ayi maganar tsafta, don gani nake duk duniya, babu na biyun mahaifiyata a tsafta.

Saboda haka, dalilin auren Babana da bafulatana Ramata, kazamiya mara kira, still remains a mystery, yet to be solved to me.

Bana taba manta ranar da aka kawota gidanmu, ina ta murna an kawo min wadda zan kira Anty na. Masu kai amarya sun shigo da habaici, suka tafi da bakaken maganganu a bakinsu, duk mahaifiyata da abokanta yan dannar cinya suna jinsu, amma suka kauda kai kamar basu ji ba. Wannan abu ya bakanta musu rai.
Wata daga cikin kawayen Mama da ta kasa kau da kai, ta tanka musu. Ba bata lokaci suka hau zage-zage, kamar dama jira suke yi, ko kuma da guzirin zagin suka shigo. Da kyar aka ba Iya Lami hakuri, su kuma suka tafi.

Bayan tafiyarsu babu jimawa, suma yan dannar cinyar suka mana sallama suka tafi, suna ta kara ba Mama na hakuri. Ni kam ina zaune muk'u a lokacin, ina jiran Mahaifina ya dawo. Bai dawo ba har barci ya daukeni.

Can zuwa cikin dare, hayaniya ta tasheni. Ba wai kuma normal hayaniya ba, kukan mahaifiyata ne ya tasheni wanda nake jiyowa yana tashi daga can dakin Babanmu.
Kasancewar gidanmu dakuna hudu ne, biyu suna kallon biyu. Dakin Mama shi yake kallon na amarya da Baba.

Daga tagar cikin dakin Mama na leka, ina hangen ta tsugune a gaban Baba. Matar da aka kai mishi a matsayin amaryarshi, a zaune a gefenshi kamar zata hau cinyarshi, tana ta wani firirita. Ban jiyo abinda suke cewa ba, daga karshe dai na ga Mama ta tashi ta fado daki da sauri.

Babu bata lokaci ta hau lalubar mayafi, ta yafa nata, nima ta miko min nawa. Ina tambayarta 'Ina zamu je Mama?', amma saboda tsabar kuka da take yi, ta kasa amsa min. Hannuna kawai ta kama ta ja muka fita daga dakin.

A bakin kofa, mahaifina ne a tsaye, kamar wanda yake jiran ta fito. Muna fita, ya kamo hannuna ya rike. Har yau ina tuna maganganun daya fada mata clearly,
"Kada ki kuskura kiyi tunanin zaki tafar min da diyata, yadda itama zaki je ki koya mata rashin kunya da rashin mutunci ko? To ba dani ba, yadda kika zo gidannan zikal, haka zaki tafi!".

Wani kukan ya sake barkewa daga bakin Mama, cikin rishin kuka, magana na fita da kyar, tace "haba Malam, ta yaya zaka ce in bar maka yarinya yar shekara bakwai a hannun wannan azzalumar mata ta ka?".
Ina tunanin hakan shi ya kara tunzira Baba, ya bude baki ya hau zazzagawa Mama masifa kamar wanda yake amayo kalmomin. Ban taba ganin tashin hankali irin na ranar ba.

Tunda aka haifeni, ban taba ganin sa'insa tsakanin iyayena ba. Tun tasowata, iyakarsu kawai: 'Yana yi kaza, to. Yana kada kiyi kaza, to Malam'. Ganin wannan abu a ranar nan, was a first. And definitely not a good...


Read / Download A ZATO NA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album