Join Our WhatsApp Group

JIHADI Complete Hausa Novel Document by JIHADI


JIHADI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 186980



JIHADI

Reading Time: 15 Hours

Added On: 28, Feb 2024

Author: Sameera Harouna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ZAMAN AMANA WRITER'S

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 1.02 mb

File Type: txt

Views: 325+

Download: 500+

Last download: 2 days ago

Description/Story: 06/08/2019 à 00:06 - Les messages envoyés dans cette discussion et les appels sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*JIHADI*
_Umar faruk_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_My Happiness *Amnoor*, barka da fara sabon novel mai sunan *matar farko* (dandab'asa), wannan novel kam namu ne domin damu ake, matan farko ba ba kamar su o'o ba, ina nufin momyn D....tasan sauran, su kam d'ogalawa ne.😁 Allah yasa ki gama lafiya kamar yanda kika fara lafiya._


💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
_My BK, nasan babu godiya tsakaninmu, to amma ya zama dole yaba kyauta, ina godiya BK ta Allah ya bar zumunci._
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘


🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾
_My Heenat, na rasa me zance ma, sai dai kawai nace Allah ya barmu tare, qauna ta gaskiya kam kina nunawa Sameera ita._🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾

_💘Mamien mu *(Maman Labyb)*, gaskiya ke uwace ta gari wacce ko wace d'iya ko d'a zaiyi alfaharin samunki a matsayin uwa, yanzu haka har na d'an fara kishi da BK ina ji inama nice 'yarki , to amma ba damuwa zan zauna a matsayin 'kawa kuma rabin ran d'iyarki._💘


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Bismmilahir-rahman-rahim_

1⃣


Da alama ranta a b'ace yake ga k'aguwa a zahirinta ya bayyana, sake kallon agogo tayi na karo ba adadi sannan ta kalli k'ofar douche d'in taja dogon tsaki tana magana k'asa k'asa "wannan wulak'anci dame yayi kama, sama da awa d'aya kina wanka, ki bani wani banzan serviette (towel) na rik'e kamar ke wata musaka ce."

Sake kallon agogon tayi sai dai kafin ta maido kallonta taji an bud'e k'ofar douche ana fitowa, da sauri ta kalleta amma saboda ganin santaleliyar budurwar ta fito daga ita sai d'an k'aramin silip (pant) d'inta ko soutien ( bras) babu yasa tayi k"asa da kanta, ita kam ko a jikinta takowa tayi ta zo gabanta ta karb'i serviette d'in ta d'aura a k'irji sannan ta karb'i dayan ta d'aura a kanta, gaban coiffeuse taja kujera ta zauna tana kallon madubi ita kuma mai aikin ta matso ta d'auki mai ta fara shafa mata, bayan ta gama ta shafa mata powder da pink d'in jan baki, ta fito mata da wani silp d'in da soutien ta bata ta saka sannan ta fito mata da riga da siket na atamfa, d'inki ne na yan zamani yayi kyau sosai gashi ya zauna a jikinta daram , mai aikince ta zuge mata zip d'in dake bayan siket d'in wanda ya kamata sosai komai nata ya fito masha Allah, d'an kwali ta kashe d'aurinshi sannan ta fito mata da sarka da yan kunnai da gani kasan sunji kud'i, sannan ta fito mata da jaka da takalmin da suka dace ta aje mata gabanta, sakawa tayi sannan ta d'auki turare ta fesheta dashi ita kam tana tsaye kamar gunki, tana kamalawa ko jiranta bata tsaya ba kawai tayi k'ofar fita abinta.


Binta tayi da harara tana fad'in "wannan zanso naga gidan aurenki , mijinki ne zai miki wannan hidimar ko kuma mai aiki zai samar maki."

Gyara d'akin tayi kamar yanda maishi zata buk'aci ganinshi sannan ta fito ta rufe mata d'akin.

Ba tare data kalli kowa dake kan table a manger (dinning) d'in ba taja kujera ta zauna, wata mai aikince dake tsaye kusansu ta matso ta fara zuba mata abincin, ta zuba mata fritte zata bud'a wani kwanon kawai ta d'aga mata hannu tare da kallonta cike da wulak'anci tace,

"Ya isa haka, ni ba jaka bace kamarku da zan zauna ina had'iyar abinci haka."

Ja baya tayi kanta k'asa bata kalleta ba ita kuma ta fara cin fritte d'in, mahaifiyarta ce tace "mu kike so mu fara gaidaki kenan?"

Cike da nuna an takura mata tace "ina kwana."

Mamar ce tace "nice kad'ai a wajen?"

Kallon saurayin da suke fuskantar juna tayi, amma ganin wani kallo da yake mata tare da murmushi yasa ta zabga masa harara, maida kallonta tayi ga mahaifinta, d'auke kai tayi ta kalli mahaifiyar tata tace "ki tabbatar min jiya bai shigo cikin maye ba, ni kuma saina gaisheshi."

A tsawace uwar tace "ke, ashe baki da mutunci, wannan ba mahaifinki bane da zaki fad'a masa haka?"

A wulak'ance ta kalli uwar tace "shi kenan mutunci ne yake sashi shigowa cikin gida a buge? kinga nifa karki b'ata min rai da safiyar nan."

Duk da k'ok'arin rik'e hawayen da tayi saida suka zubo, cikin muryar kuka tace "ba laifinki bane, kiyi yanda kike so."

Tana fad'a ta juya ta nufi d'akinta tana zubar da hawayen takaici, ita kuma ko kulata ba tayi ba bare taji ba dad'i, saima mahaifinta data kalla tace "zaifi maki kyau ki daina saka damuwa a ranki akan wannan da baisan kina yi ba."

Tashi tayi ta bar abincin zata fita ,mahaifinta ne kalleta a marairaice yace "kiyi hak'uri mana gimbiyata, nayi alk'awari ba zan sake ba."

Kallonshi tayi ta kalli saurayin dake zaune kusanshi tace "ka fad'awa wannan wawan watak'ila shi zai yarda da abinda ka fad'a, amma bani ba *Khairat*."

Fita tayi ta nufi wajen motarta, d'aya daga cikin jami'an dake kula da mahaifinta ne ya taho shima a gadarance ya karb'i jakar hannunta da makullin mota ya nufi motarta dasu, dan in baiyi ba to masifa zaisha amma ba k'aramin d"aci ba abin ke mishi, har zata shiga mota taji saurayin nan yace "nine wawan?"

A wulak'ance ta juyo ta kalleshi tace "to da wa in ba kai ba? da wani ne wanda ya fika zama wawa a duniyar nan? ai kai kad'ai ne namijin dake zuwa gidan wacce yake ikirarin yana so kuma ya zauna zaman dirshan har da mik'e qafafu."

Nunashi tayi da yatsa tace "wallahi harka gama wa'adin daka dibarwa kanka ba zan tab'a kallonka a matsayin mutum ma bare harna fara tunanin soyayya da kai, désolé."

Tana fad'a ta shiga motarta ta bar gidan cikin matsanancin gudu, shi kuma taushe b'acin ranshi yayi da har yanzu yana ji a jikinshi zata iya zama tashi, a ranar da kuma hakan ta faru zata gane wanene shi.

********************

Kafin ta fara gudanar da komai saida tasa masinger ya siyo mata fritte mai had'e da soyayyen nik'akk'en nama da jus d'in albasa da moutarde, tasa *Habiba* ta had'a mata kakkauran tea da zuma sannan ta fara wani sabon petis de jeûner d'in, tana fara ci Habiba ta sake shigowa cikin ladabi tace "madame, manager ne ke son ganinki."

Kallonta tayi a wahalce tace "uhum, kice ya shigo."

Juyawa tayi dan cika umarninta, takai wata lomar bakinta taji shigowarsu, amma jiji da kai yasa ta kasa koda kallonsu da ido, tsaye sukayi a kanta hakan yasa ta musu nuni da hannu akan su zauna, saida suka zauna sannan ta kallesu gaba d'aya ta kuma kalli manager tace "kai kad'ai aka ce kana son ganina, yana ganku ku biyu?"

"Eh madame, wannan shine wanda za muyi magana akan ci gaban daya kawo mana."

Sake kallon saurayin tayi wanda idonshi ke kan kallon yatsun hannayenta da take cin abinci dasu, jan lallen da suka sha da dogayen akaihu na kanti wanda suma ta lullub'esu da pink couleur d'in vernie, sosai suka birgeshi duk da dai ya tsani mai su d'in, maida kallonta tayi ga plate d'in abincinta taci gaba da ci har saida ta gama sannan ta d'auki bidon (gora) d'in ruwa ta zura hannunta ta tagar dake bayanta ta wanke hannu ta juyo da nufin aje bidon d'in ta d'auki lotus dan goge hannu, karaf idonta suka sauka akan gayen nan daya kasa d'auke idonshi akan kyakyawar hallitarta, da sauri ya d'auke idonshi tare da had'e fuska tamkar hadarin gabas, dan tunda ta fara aiki anan take tak'ama wajen mahaifinta ne ya lura tana da raini shi kuma ba zai d'auka ba, saida ta goge hannun ta tsaya ba yare data zauna ba ta kallesu tace "ina jinku."

Hannu manager yasa a jaka ya fito da takalma ya mik'a mata yana fad'in "wannan shine sabon sanfarin da wannan ma'aikacin namu ya fito mana dashi, shine nace kafin muci gaba da bugawa sai mun samu izininki."

Karb'a tayi bayan ya gama mata bayanin ta kallesu da kyau, tabbas sanfurin ya birgeta dan kuwa basu da maraba dana maza harda gidan babban yatsa, ga kuma tudunsu shima kamar dai na maza, ajesu tayi qasa ta cire na qafarta tasa wad'annan, su kam kallo suka bi qafar da ita yayin da saurayin ke ma qafar kallon qurilla wacce tasha jan lalle sai dogayen akaihu itama data saka masu kamar dai na hannuwa, ganin yanda suka zauna a qafarta suka mata kyau yasa ta cire ta zauna a kujerarta tace" kuje kawai ku ci gaba da bugawa, ku bar min wannan zanyi publié a Internet nasan zamu samu masu so."

Cikin farin ciki bayan sunyi godiya suka tashi zasu fita, muryarta ta tsayar dasu tace "fasahar waye?"

Juyowa sukayi manager kuma yace "wannan ne madame." ya fad'a tare da nuna na kusa dashi.

Saida ta fito da wayarta a jakarta sannan tace "meye sunanka?"

" *Umar Faruk*." ya fad'a a daqile.

"Zo nan." ta fad'a kamar ta kira yaronta.

Kamar ba zai zo ba saida manager ya sake cewa "madame na kiranka."

Takowa yayi tare da k'ara d'aure fuskarshi, saida ya tsaya gaban tebur d'inta yana kallon idonta, jujjuya kujerar ta fara yi tana juyawa da ita ta fara magana "karka bari mu sake had'a ido da kai da sunan had'arin kallo, karka sake bari na maka magana so d'aya har sai an maimaita maka, karka bari na sake jin raina ya b'ace a kanka, sannan karka sake kallon min bayana idan na juya."

Tsaye ta mik'e tare da d'aukar lotus d'in data goge hannu ta saka masa shi a aljihun gaban riga tace "ka aje min shi, gobe zan tambayeka."

Zaune tayi tace "zaka iya tafiya."

Saida ya gama mata kallon raini kafin ya gyara tsyuwarsa yace "idan baki son ana kallonki, to ki zama kamilar mace ta yanda ba zaki rinjayi shed'anun dake cikin zuk'atanmu ba bare har mu kalleki , ni kaina nasan nayi zunubi kuma dole na nemi gafarar ubangijina akan hakan, sannan ki sani ni ba d'anki bane da zaki takani yanda kike so, haka kuma talaucina bai k'ask'antar dani izuwa matakin dake kike k'ok'arin d'orani a kai ba, ina fata kin fahimta."

Yana fad'a ya juya bar bureaux d'in, ita kuma ta bishi da kallo tare da tunanin koya masa hankali.

Kasancewar bata jima da fara aiki a wajen ba yasa har yanzu akwai rashin sabo, yanzu haka tattara kayanta tayi Habiba ta biyota dasu ta nufi gida saboda bacci kawai take so tayi.

********************


Tunda ta shiga gidan taga guardcord (bodyguard) d'in mahaifinta kuma taji shiru dan haka ta shiga babban falon da zai sadata da nata d'akin, duk da ba bak'on abu bane a wajenta amma dai ta tsorata, tunda taji sautin tasan mahaifinta ne ke dukan mahaifiyarta, da gudu ta nufi d'akinshi ta jefar da jakarta, bata tsaya komai ba ta kutsa kai cikin d'akin ai kuwa bata tsaya ba wajen kaiwa mahaifiyarta d'oki , saman gadon ta fad'a ta rumgumo mahaifiyarta tana k'ok'arin kare jikinta, tunda ya ganta ya jefar da wayar hannunshi ya fara zare ido, yana kakkare jikinshi saboda daga shi sai gajeran wando, kama mamanta tayi suka sauko daga gadon ta d'auki rigarta a k'asa daya ketata da qarfi ta rufe mata jiki, tana rik'e da mahaifiyarta ta kalleshi sai k'yabta ido yake tace "wallahi idan ka sake dakar min uwa, to ka sani justice (kotu) ce zata rabani da kai, dan ba zai yiyuba ka dinga shak'o giyarka kana zuwa kana narkar min uwa ba."

Tana fad'a suka fita daga d'akin saida ta kaita har d'akinta ta d'auko mata riga doguwa ta sauya ta d'auko mata maganinta ta bata tasha sannan ta kwantar da ita tana rufeta tana fad'in "banga abinda kike tsinta a gidan nan ba da ba zaki barshi ba, amma da nayi magana sai kice saboda ni kike zaune, ni zan kula da kaina ki koma wajensu Mammie ki zauna."

Tana fad'a ta juya itama ta koma nata d'akin ta cire kayan jikinta ta watsa ruwa sannan ta d'auki kayan data fi jin dad'in zama dasu a cikin gida ta saka, wando ne na jeans fari tas sai dai iya cinyoyinta ya tsaya sai kuma riga ta dan sauko har cibiya amma k'ananan hannuwa gareta, kwance tayi ba jimawa bacci ya d'auketa.

*******************

Tana tashi bayan la'asar brush tayi kawai ta fito bata damu dayin sallolin dake kanta ba, a falo ta zauna saman lunstumemiyar kujerar dake kai tana kallon tv, mai aiki ce ta kawo mata abinci tana ci mamarta ta fito rik'eda carbi , zaune tayi tace "kinyi sallah?"

"Nayi." ta fad'a dan karta sake damunta.

_Wannan yarinya ba dai k'arya ba_

Haka suka kasance wunin ranar ba wani dad'i, sai dai takalmin data d'ora a internet sun samu masoya, anan wasu manyan 'yan kasuwa suka ce suna son dayawa akan sari, anan suka tsayar akan gobe zasu zo ma'aikatar tasu sai suyi magana, kasancewar manyan mutane ne yasa tace wa mahaifiyarta ta tasheta k'arfe takwas na safe danta shirya da wuri, cikin dare sosai tana kwance tana chat taji motsi a falo, lek'owa tayi abin mamaki *Mujahhid* ne yake shiga d'akinshi cikin tsananin maye tare da wata budurwa, tsaki taja tace "dubunka ta cika, wallahi saika bar gidan nan tunda bana ubanka bane."

Komawa tayi d'aki ta ci gaba da abinda take har bacci ya d'auketa da ecouteur a kunne tana sauraren wak'ok'i iri iri.

*********************


*Da safe* zaune take a tsakiyar wani faffad'an gado na alfarma cike da magagin bacci da har yanzu bai saketa tace "nifa wallahi kun takura min, wai dole saina tashi ne?"

Sake komawa tayi ta kwanta taja wata kakkabrar zanin rufa ta rufe, matar dake tsaye gefenta ta sake yaye zanin tana fad'in "dole ki tashi, ke da kanki kika ce na tasheki takwas daidai saboda bak'in da zasu zo."

Tana jin haka ta tashi firgigit tana zare ido tare da kallon mahaifiyar tata tace "k'arfe nawa yanzun?"

Tab'e baki tayi tace "08:20."

Ai kuwa kamar zata bige uwar haka ta diro daga kan gadon ta nufi k'ofar fita, ta bud'e k'ofar matar tace "ina kuma zaki je da wannan kayan?"

Ko saurarenta ba tayi ba kawai ta fice abinta, da gudu ta sauko daga matakalar benen, tsinkayar mahaifinta tayi a farfajiyar gidan d'aya daga cikin masu tsaron lafiyarsa ya bud'e masa mota yana daf da shiga, da gudu ta k'arasa tana kiran "papa, papa."

Tsayawa yayi ya juyo yana kallonta, sai dai bashi kad'ai ba harda masu tsaron lafiyarsa dake cikin tenue d'insu na sojoji su...


Read / Download JIHADI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album