Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

KASAITA 2 Complete Hausa Novel Document by KASAITA 2


KASAITA 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 29892



KASAITA 2

Reading Time: 2 Hours

Added On: 07, Jul 2024

Author: Maryam Kabir Mashi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 148.56 kb

File Type: txt

Views: 1642+

Download: 2488+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: *ƘASAITA BOOK 2*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 1


Ƙwana na yi ina juyi gudun kada ya je ya sanar a gidanmu, saboda na ga alama ba shi da kunyar kai ƙara, tun da ya kai ƙara ta ga Aunty.

Ganin an wayi gari lafiya, shi ne na yi wanka na saka kayana doguwar riga ce mai ruɓi biyu, ƴar Saudiyya za mu iya kiranta ko Dubai. Na fito daga gidan ko ɗankwali babu kaina na nufi bakin dutsen da nake hutawa na yi tsaye.

Lokacin kuwa ya nuna ƙarfe taƙwas na safe kawai wanda na ce na yafewa su Mansura rakiyata,ko kalaci ban tsaya yi ba. Ina tsaye nan ina ta saƙa abubuwan da na san ba zan samu ba,wato Yarima ya ji haushin maganar jiya ya ce ya sauwaƙe mini inje in auri Anwar, na ɗaga kaina jikin barandar ɗakinsa, sai na hango shi zaune a kujera ya ɗora ƙafafunsa a saman tebir ɗin gabansa.

Na juya abina, sai ma na tattaka na haye dutsen, tsayin minti sha biyar na yi sai na ji ina sha'awar shiga ƙoramar nan,ta hanyar tattaka duwatsun da aka jera layi da su, waɗanda suka yi cikin ɗan dajin inda ruwa nan ke nufa,su kuwa duwatsun babu ruwanka da taɓa ruwa idan dai har ka sa ƙafarka a kansu.

Nan take na saɓule takalman da ke ƙafata, na sulala cikin ruwan inda na dinga taka duwatsun a hankali, na yi tsaye a wurin ina ta waiwaigawa sai na hango barandar Faysal,ai kuwa juyawar da zan yi ina tsaki, sai na ga wani ƙaton miciji ya nufo inda nake tsaye, ta cikin ruwan nan kanshi a buɗe yana ta huci ban san lokacin da na yi baya da sauri ba ina ƙwalla ihu. Cikin ƙanƙanin lokaci ya tari gabana babu zancan iya motsi a yanda na ga yana hucin.

Runtse idanuwana na yi na dinga ƙara,tun ina ƙarar har ya kaini ga kiran Yarima. Saman ƙafata ya kai wa sara, sai dai naji gab,na yi wata irin ƙara, na buɗe idanuwana, sai kuwa na hango Yarima Faysal a guje shi da wasu a bayansa.

Sai na dinga cewa, "Maciji! Maciji!! Bai wani tsaya tattaka duwatsun nan ba sai dai kawai na ganshi da gudu a cikin ruwan, wanda ganin da nake masa dishi-dishi ne, daga nan kuwa sai dai na dinga jin maganganun mutane sama-sama, sai kuwa ji na yi ana jijjiga ni da kiran sunana da nake jin ana yi.

Ina jin ƙasa na juyawa da ni, sannan ina ji sama-sama Yarima na daka masu tsawa zan iya cewa ɗaukata ya yi cak ya koma gudu, amma daga nan ban ƙara sanin komai ba.

A hankali na dinga motsa idanuwana,alamar ina son buɗe su, ina cikin haka na ji Yarima na kiran sunana. "Yasmin! Yasmin!!" Sai na ji yana dafa goshina.

"Ta motsa?" Na ji an tambaya.

"Eh,tana motsa idanuwanta."

Na samu tsayin minti biyar a haka, amma na kasa buɗe idanuwana, amma ina jin abin da ake faɗa. Jin abu mai sanyi a goshina, shi ya ƙara taimaka mini na ji hular idanuwana ta saki daga nauyin da ta yi mini, idanuwana Faysal suka fara gani zaune gefen gado,yana ɗora mini abin nan mai sanyi da nake ji, sai na ga ya yi saurin jefar da shi ya ɗago kaina ya rungume a ƙirjinsa, ya yi wata irin ajiyar zuciya. Sannan na ji ya ce, "Ta tashi." Ya mayar da ni ya ƙara gyara mini ƙwanciya,sannan ya sumbaci goshina, bayan nan kuwa mutane suka dinga leƙowa suna yi mini sannu, idanuwansu kuwa jajir kamar suna ciwon idon Afolo.

Da ɗaiɗaya duk na fara gane fuskokinsu, amma matan,mazan ban san kowa ba,gwara ma ƴan na kusa da shi da ba su fi Biyar ba, ƴaƴan ɗakina kuwa har wannan lokacin kuka sukeyi.

Bayan kamar minti sha biyar duk suka fita,a inda Yarima ya miƙe shi ma ya ɗauki wayar hannu, ya fara daddannawa.

"Barka da yamma,eh, yanzun za ta yi minti ashirin, Eh, tana gane mutane, a'a ban duba ba, to yanzun zan duba. To sai kun zo,Mama da wuri don Allah yanzun ko, to zataji." Ya juyo ya yi mini murmushi.

Sannan na ga ya cigaba, "Barka da yamma, eh, Yarima ne. Eh,Mamee, yanzu ta yi minti ashirin da ɗaya,a cewa Daddy ya zo yanzun ta gan shi. To Mamee ai kamawa ta yi,to, to zataji, to sai kun iso, to a huta lafiya, eh tana ƙasa, eh, na san yanzun zata hayo,kin san ƙwana biyu bacci ina jin bacci ne ya ɗauke ta,a ɗakin ƙasa, to za'a taso ta, mungode."

Ya dawo ya zauna gefena ya matso kusa da ni sosai, sannan yasa hannunsa ya shafa gashin kaina, ya ƙara gyara mini gashina zuwa gefe, "Sannu." Ya ga dai ban amsa ba, sai na ga ya juyo sosai.

"Yasmin,kina jina? Yasmin?" Sai na ɗaga masa kai, sai na ga ya ɗan mayar da numfashi tare da lumshe idanuwa, ya yi saurin kai min sumbata a kumatuna.

Ya tashi a hankali sai na ga ya buɗe bargon da yake lulluɓe da ƙafa ta, sai a lokacin na tuna da cewa fa Maciji ya sare ni, nayi ƙoƙarin motsa ƙafar, na ji ta kamar dutse, ina kallo ya ɗaga ƙafar tawa a hankali, yasa hannu ya ɗan shafe ta.

"Ƙafar ta mutu ko Yarima?" Na faɗa da muryata irin ta marasa lafiya.

Ya rufe ya zagayo ya kama hannuna tare da zaunawa a gefena, wanda ƙafarshi ɗaya ya ɗago ta duka ya lanƙwashe ta har sai da gwiwarsa ma ta ɗan hau saman cikina.

"Bata mutu ba,za ki warke sosai ma." Ya sumbaci hannun nawa,a take sai na ji tausayinsa ya kama ni.

"A kawo miki abinci za ki iya ci?" Na girgiza kai.

"A'a,zaki ɗan ci ko yaya ne,ko abu mai ruwa ne." Ya miƙe.

"Bari inyi miki burush(Brush)."

Da saurinsa ya fito daga banɗaki da burushi na a hannunsa wanda saman shi ke cike da makilin, da ruwa a ƙaton kofi da wata silba a hannunsa, ya ajiye su gefen gado, sannan ya hayo gadon gaba ɗayansa, ya ɗaga ni ya jera filallika guda uku a bayana, na ɗago sosai, ya janye bargon jikina ya mayar da shi iya ƙuguna, ya gyara shi sosai, sannan ya sauka ya ɗauko kayan ya ɗora silbar a cinyata.

Ya kanga mini kofin a bakina, "Kuskure bakin tukunna." Na kurɓa, ya yi saurin ajiye ruwan a durowar gefen gadon, sannan ya ɗago silbar.

"Zuba a nan." Na zuba sai na ga jajawur yawun bakina, ga ɗoyi yana yi, kunya ta kamani, amma na ga shi bai nuna alamar ƙyanƙyamina ba, ya ƙara bani ruwan na kurɓa, na ƙara kuskurewa ya ɗago na juye.

Ya ɗauko burushin na ɗago hannuna na riƙe, "Zan iya."

"A'a, kada ki wahala fa."

Bazan wahala ba."

Ya ƙura mini idanuwa,sai ya lumshe su tare da yin murmushinsa, ya buɗe idanuwan tare da girgiza kai.

"No Yasmin, jikinki ba ƙarfi, ki yi haƙuri in kula da ke har ki warke,kina ga ya dace in bar yaran can su dinga kula da ke, alhalin ƙasa suke da ni, amma su ga wani ɓangare na sirrin matata? No,no,is not possible."

"Wallahi zan iya."

Ya miƙo mini burushin.

"Na amince da ke."

A hankali na dinga gogawa, saboda jikina babu ƙarfi sosai, amma duk da haka sai da naji na gaji sai da na ɗan tsaya hutawa, ya yi murmushi ya karɓa ya ƙarasa mini.

"Ya sunan ɗaya daga cikin yaran gidanki?"

"Mansura ko Muslum."

Ya miƙe da hanzari ya ajiye kayan a ƙasa ya leƙa barandar cikin falo, ya kira Mansura, da gudu ta hayo,a inda shi kuma ya dawo ya zauna.

Ya umarce ta da ta ɗauko masa mango juice a firji,ta tafi cikin saurinta, shi kuma ya shiga banɗaki da kayan ƙazantar wanke bakina a hannunsa.

Ko fitowa bai yi ba, sai ga Aunty ta ce, "Lah! Ina Yarima, bari in gaya masa kin tashi."

Sai ga shi ya fito. "Ta tashi?"

"Ta ɗan jima, abin da yasa ban ce a taso ki ba,ganin kin samu bacci shi yasa."

Ta iso ta zauna gefen gado.

"Ya jiki Yasmin?"

"Da sauƙi."

Nan suka ci gaba da zama ita da Yarima, har sai da ya ga nasha mango juice ɗin nan sannan Aunty ta matsanta masa da ya je ya yi koda wanka ne, da ƙyar ya amince.

Bai fi mintuna goma da tafiya ba, sai ga Mama ta iso, cewa take, "Barkanmu, barkanmu Yasmin,tare da Sarki muke yana ƙasa,kin san abun mata, shi ne na hayo in ga yanda ku ke tukunna." Ta juya ta yi baya, sai ga su sun shigo tare da Sarki tun da ya shigo na ga fuskarsa cike da walwala.

Sarki ne har gefen gadona,yana ta jinjina abin da ya faru, Mama ta ɗaga bargon da suka lulluɓe ƙafata, suka
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download KASAITA 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album