Join Our WhatsApp Group

AURAN BABBAN MUTUM Complete Hausa Novel Document by AURAN BABBAN MUTUM


AURAN BABBAN MUTUM

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 74430



AURAN BABBAN MUTUM

Reading Time: 6 Hours

Added On: 11, Dec 2023

Author: Ummee Mukhtar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 441.01 kb

File Type: txt

Views: 1578+

Download: 1480+

Last download: 2 days ago

Description/Story: Oο»Ώ[31/08, 16:16] β€ͺ+234 905 934 3174‬: πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€



*AURAN* *BABBA*


Creating and writing by


*Ummee* *Mukhtar*




πŸ…Ώ1




Iyayen tsaye suke akanta kamar zasu cinyeta d'anya saboda tsabar fad'an da suke mata " Iyee tsakani da Allah meye ai bun Alhaj Sa'id da har zakice bakya sonsa mijin da kowace mace zatai burun auransa ga kyau ga k'ud'i," kawai dan ya kasance kusan sa'an babanki sekice bakya saonsa?



Mahaifinne yai saurin cafe maganar da cewa kaji zancen banza zata dinga yawo da shine? Ke ki saura reni aure ba fashi jibi idan Allah ya kaimu in yaso ki had'iyi zuciya ki mutu .




Larai na gane yarinyar nan rufin asirin da Allah ya aiko mana dashi shi takewa bak'in ciki 'dan ubanki kamar bamu muka haife kiba.


Dubi yanda yase mana k'aton gida ga mota ya bani ga shagunan daya bani har biyu ga uban mak'udan kud'i ko yaushe akan hanya" amma ace Zarah kirasa wanda zakiwa bakin ciki se iyayenki.




Zarah wacce akewa fad'a ta kifa kanta da jikin gado se kuka take na takaici da iyayenta suka kasance masu kakwad'ayin gaske" tayama tana 'yar shekara 17 za abata dan shekara Arba'in da tara kawai danya kasance me kud'i?






Ta share hawayenta tana me goge face d'inta wacce tai ja saboda kuka.





Malam hadi ne ya sunkuyo kusa da Zarah murya k'asa k'asa yace haba 'yata tinda mike baki ta6a bujirewa a binda mukace kiyi ba ' se akan wannan ?



Mun baki za6i daki kawo wanda kikeso kince yayi tafiya idan kin buga number sa batama shiga ,"ga wanna ya fito da k'arfinsa ze aureki, to Zarah zamusaki agaba kamar tv muna kallo ne?




Girgiza kai tayi Alamar a a , nan yai murmushi yace to yanda bazamu saki gaba muna kallo ba tobe kamata mun muki za6i kice ba hakaba.

Larai ce ta sunkuyo ta dafa kafad'arta tace ki hkr 'yata mun hango miki daular dake baki hango ba , nan de sukaita lalla6ata itako Zarah in banda sharar k'wallah ba abinda take wanda daga k'arshe tace ta yarda inde hakan ze sasu farinciki.




Nan gaba d'aya suka rungume ta suna sa mata Albarka itako taci gaba kuka .






Kwance take a d'aki tayi ruf da ciki idon yai ja sosai se kanta dake mata ciwo sosai , wayar ta jawo iphone7 tai dialing d'in wata number cikin kuka take magana Aysha ya zanyi ya zanyi Aysha kifad'amin se kuma kuka me tsuma zuciya.




Salati aysha tayi tace kiyi hkr gani nan zuwa yanzu.





Aje wayar tayi taci gaba da kuka .







Dake basu da nisa cikin minti 10 tak'araso gidan A tsakar gida ta tadda Larai wacce ke zaune tana shan farfesun kaji """ wani kallo taiwa Aysha na rashin kirki ,, cikin ladabi Aysha tace umma ina yini ",, fuska a daure ta amsa Γ…ysha tai ciki tana mamakin sauyawar umman Zarah,,,, tinda 'yarsu ta had'u dame kud'i take d'aga kai.





Nan tai ciki umman Zarah ta bita da wani shegen kallo tace wallahi bazata yuwuba da anyi auran sena raba Zarah da wannan 'yar matsiyatan dan bazata goga mana talauciba.







Zarah na kwance Aysha ta shigo da sauri Zarah ta tashi da gudu ta rungume Aysha se kuka.

Subahanallahi Zarah dan Allah kibar kukan nan nasan de Akan Auran nan ne ki hkr ba yadda zamiyi haka Allah ya tsara.




Fuska taf da hawaye Zarah ta ďago kai suna fukantar juna tace Aysha taya zan auri babban mutun nifa yarinyace ,,, babu wani so ko k'auna azuciyata game dashi """" ballan tana azo kan maganar shauk'i ta Auratayya nayi dashi nace nayi dawa ? Haba Aysha yaro se yarinya ni wallahi an cuceni tai maganar tana me kwantar da kanta akan cinyar Aysha....





Aysha tai ajiyar zuciya ta shafa kanta tace babu yanda zakiyi tunda sukace shi zaki aura kawai kiyi hakuri bakisan Abinda Allah yake nufi da hakan ba.


Nanta d'ago ka cikin sauri tace a 'a Aysha ban hango Alheri cikin auran nan ba sema tashin hankali.

A a don't say that cewar Aysha ai sanin gaibu se Allah .



Batun shauk'i kuma wallahi wasu manyam sunfi yara iya soyaiya """" Zarah tace au haka zakice?

Nan ta kama wani kukan da kyar aysha taita lallashinta akan cewa sanadiyyar biyaiyar dataiwa mahaifanta se Allah yasa abun ya zame mata Alkhairi.


Hira suka d'anyi wanda kusan rabi akan auranne wanda Zarah take cewa ita ba abunda zatai na harkar biki.





Ku biyoni yanzu aka fara😘

Ummulo
[31/08, 16:17] β€ͺ+234 905 934 3174‬: πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€


*AURAN* *BABBA*



*HIKIMA* *WRITTERS* *ASSO*🎁

Creatimg and written by

*Ummee* *Mukhtar*



πŸ…Ώ2


Misalin k'arfe biyar na yamma gidan ya cika da bak'i 'yan biki wad'anda sukazo daga k'auyensu wato cen dangin mahaifin Zarah """" har yanzun tana d'aki wani ciwon kaine ke neman kamata hayaniyar dataji tayi yawane yasa ta lek'o ta window nan taga mutane da yawa a farfajiyar gidan se farin ciki ake ",,wani guntun tsaki tayi ta koma ta kwanta tana cewa duk akan Auran Babban mutun kukewa zumud'i aikin banza kawai ""




Jitai ana cewa ina Amaryar takene kota tafi gyaran jiki?

Larai tace wallahi tana ciki inaga bacci take''' ke ni kuntuna mim ma yakamata da ace tayi gyaran jiki wallahi shaf na manta.



Wata wacce ake kira da maryam tace ah ai kinyi sakaci zaki kai yarinya gidan kishiya ace bazaki gyarata ba ?


Larai tai dariya tace ai gidan kowa daban ba abunda ze had'asu amma duk da hk zan gyarata duk da lokaci ya k'ure.






Su biyu suka mik'e suka nufi d'akin Zarah, tana jin tafiyarsu tai saurin kwanciya azuwan bacci take.



Da sallama suka shigo baba maryam tace aiko bacci take yanaga idonta ya kumbura kode batada lfy ne ? """" d'ayar tace gashi ta rame sosai Larai meke damum 'yan nan ,:::: ?


Larai tai saurin cewa wallahi zazza6i ke damunta amma ai baza a fasa auran ba saboda wannan.




Baba maryam tace yakamata ata sheta"""


Tashinta sukai ta bud'e ido a hankali kamar me bacci cikin nutsuwa ta gaida su jikinta duk a sanyaye kamar wacce ruwa yaci.




Lafiya lau zarah kinci abinci kuwa? Cewar baba maryam kai ta girgiza alamar bataci ba .




Ah maza Larai d'akko mata amarya ba cin abinci me a akai kenan """" ta gefen ido Larai a kalleta gamida galla mata harara wacce yasa Zarah saurin k'asa da kanta.






Abincin ta kawo mata sede ta kasa ci domin jitake yana mata d'aci spoon3 tai tace ta k'oshi .


Ba yadda basi ba amma takasa ci .


Ku kyaleta zataci anjima ne dama haka cin abincinta yake a tsintsnke.


Su baba maryan ne sukace ta tashi ta gyara taje gidansu kawarta su tafi gyaran jiki"" wani bak'in cikine ya zo mata wai ita wane irin gyaran jiki zataiwa wani tsoho.


Fita sukai daga dakin yayinda sukace tai sauri ta fito.



Laraice abaya ta juyo tace wallahi idan kika sake kowa ya fuskanci bason auran nan kikeba sena 6ata miki kebank'i ma na tsine mikiba tinda ba k'aunata kike ba Arzik'i na binki kina guje masa.




50k ta wurga mata tace gashinan daga cikin ku'din da Alhaj Sa'id ya bayar domin ki gyara jikin ki """ kinsan 150k yaba da to nasan wannan zasu isheki ,,da kallo Zarah ta bita yayinda Larai tai ficewarta .




Kuka Zarah tasa harda shure shuren k'afa tana cewa an cuceta.






Wanka tayi tasa riga da siket na atamfa se hijab ko kwalliya ba taiba tazo ta fice daga gidan babu wanda ta gani saboda duk suna daya bangaren.











Tafiya take amma kamar bayi takeba saboda yanayin takunta shine ze tabbatar maka akwai a binda kedamunta .


Wata majalisar samari tazo wucewa suna ganinta sua hau nunata oh kaganta nan yarinya da ita amma wai tsoho zata aura sa an babanta .


D'ayan yai dariya yace eh mana Ai kasan ance kud'i hana magana idan kanadashi balarabiya zaka iya aura . D'ayan yace kai wallahi kwadayi ma beba suka kwashe da dariya.

Da gudu ta wuce su tana kuka ta fad'a gidansu Aysha .



Aysha na tsakar gida umanta bata nan da sauri ta tasa kanta kan
K'afar aysha tana kuka.



Aysha ta d'agota ce menene Zarah dan Allah kidena sa kanki a damuwa kada wani ciwon ya kamaki.



Zarah cikin kuka tace kowama yasan Auran kwadayi za ' min Aysha ya bazanyi kukaba ?


Nan taita bata hkr akan komai mewuce wane .



Kud'in da ummanta taba ta tafi to dasu " Aysha ta dubi kudin tace wannan fa ?


Hawaye Zarah ta goge tace wai gyaran jiki zani kome zan gyara oho.




'Yar dariya aysha tayi tace ah bari mu tashi muje afara yau zuwa gobe shaken an kada lokaci ya k'ure duk da yariga yak'ure.






Harara Zarah ta watsa mata tace malama ba inda zani wallahi kawai na fitone de dan kar ace banje ba.







Kallon ta Aysha tayi tace aike ko ba gyara wallahi da kyanki ko baki kwalliya kullun k'ara kyau kike musamman yanzu da kika samu Alhajin nan irin cimar dayake kawo muku gaba d'aya kin koma kamar wata shuwa Arab.




Ga rayuwa data sauya muku kun koma kamar damacen kud'in masu kudine ki godewa Allah.







Zarah batace komai ba se daga cen tace kawai ni kurkur zan ganbad'a ajiki da fuska shine zesa taga kamar naje .




Dariya sukai Aysha tace kin kawo shawara.





Nan suka had'a madara da kur kur se lemon tsamj kad'an wanda suka matsa ciki gaba daya suka shafa jiki da fuska .




Seda yai kamar 20mnts sannan suka wanke .




Wani suka had'a daban kurkurne da manja shima suka shafa daga baya suka wanke.



Sosai zarah ta k'ara haske damacen farace sol gata da gashi hanci kuma ga ido fari tas kamar madara.



Ba doguwa bace baza kuma a sata a sahun gaeru ba tanada jiki me kyan k'ira Allah ya hore mata mazaunai da dukiyar fulani dede misali wanda yake jan hankakin 'yan maza , .se d'an k'armin bakinta wanda aduk sanda take magana seya burge me kallo.






Aysha chocolate ce tanada kyau dede azanci.


Aysha kallon Zarah tai tace saura abu daya .



Tace me kenan? Aysha tace baki lalle ajiki ba duk da nasan jikinki damacen me laushine ga shinan ko a ido aka kalla.







Tsaki tayi tace bazan ba .


Dariya Aysha tai tace wallahi sekinyi so kike ta ramfoki baki jeba?





Zarah Tace kuma hakane fa.




Lallan suka sa a tasa nan ma sukazuba kurkur kadan suka juya suka dora a wuta minti biyu ya tafasa suka sauke suka zuba man zaitun sannan suka.shafa ajiki.


Ruwa me dumi Aysha ta dora Zarah ta fara shiga tai wanka """ bayan ta fito aysha ta shiga.


Umman Aysha ce ta dawo suka gaisa da Zarah tana tsokanarta Amarya kinsaha kamshi.


Nan zarah tace zash tafi da aysha a gidansj zata kwana .


Tace ai bakomai kuje Allah yai muku albarka.





Ahanya Aysha tace kinga yanda kika kara haske kamar gyaran jikin gaske kikaje?


'Yar dariya sukai nan Zarahta d'akko 30k daga cikin kudin ta bawa aysha .




Aysha tace mezanyi da wannan ? Zarah tace baki nai " ni kuma? Cewar aysha ai ban ta6a rik'e irin wannan kudin ba ko ummata bata da wannan kud'in.



Zarah tace shiyasa na baki kuma umman ma zan bata nata kinga ko jari kwaja
tinda mahaifinki ya rasu Aysha.





Rungume juna sukai Aysha na kuka tanai mata godiya.










Suna shiga gidan kai tsaye d'akin Zarah suka wuce dan ita bataso ma kowa ya ganta.











Ummulo😘😘😘😘
[31/08, 16:19] β€ͺ+234 905 934 3174‬: πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€πŸ‘³πŸ»β€β™€



*AURAN* *BABBA*


Creating and Writting by

*Ummee* *Mukhtar*

*HIKIMA* *WRTS* *ASSO*🎁


*SADAUKARWA* *GA* *DUKKAN* *MASOYA* *WANNAN* *NOVEL* *ALLAH* *YABAR* *ZUMUNCIπŸ€—πŸ˜˜*


πŸ…Ώ3




Suna shiga d'aki zama sukai a kujerun dake d'akin suna kallon juna gamida murmushi Aysha tace Allah yasa de kada umma ta gane bamu jeba """"" Zarah ta cire hijab gamida warware dogon gashinta wanda ya zuba har baya ta zauna kusa da Aysha tace karki damu bazata ganeba .



Wata jaka ta dakko dake cikin drower ta zuge kud'ine a ciki fal wanda zasukai kimanin dibu d'ari uku da hamsin Aysha tai saurin zare ido """" tace ke wannan kud'in fa ?

Wani dan guntun smile Zarah tayi gamida yin tagumi tace zaki d'auki dukansu ki kaiwa ummanki """ Aysha tace wa? Rufamin asiri ai in aka ganni da wannan kud'in cewa za ai mutun na siyar nasame Su.




Dariya Zarah tayi wacce rabon datayi irinta harta manta domin yanzu bak'in ciki ne lullu6e a zuciyarta gameda Auran nan .



Tace ok ni zan kai mata da kaina amma ko kin manta mutumin nan d'an siyasane yana daya daga cikin masu baiwa shugaban k'asa shawara kin tina?



Aysha ta gyad'a kai tace hakane.



Zarah tace to su kud'i ba wani abu bane a gunsu dan haka kema kici naki rabon domin kuwa kud'immune .



Dariya sukai Aysha tace gaskiya zakiji dad'i 'yan nan wannan idan kikai wata daya nazo gidanki wallahi zan iya kuwa ganeki?



Duka Zarah takai mata tace eh saboda kinsan zan koma kamar dodo ko?


Nan Aysha tace no ba haka nake nufiba zade ki k'ara kyaune hajiyata.



Suna cikin magana Larai ta shigo kafin tai magana se taga Zarah k'ara wani haske da kyau""" fuska a sake tace kai masha Allah kin ganki kuwa nagode miki 'yata ai shima ya dad'a ganinki da kyau.


Motsi Zarah takamayi da bakinta Alamar tana k'unk'uni domin ta tsani taji an had'ata da Alhaj Sa'id.

Nan ta juya kan Aysha tai mata wani kallo na raini tace au kema gyaran jkin kikayi ?


Cikin sanyin murya Aysha tace eh umma.


Baki Larai ta ta6e ta kalli Zarah fuska a tamke tace kinajina gara ki k'ara gogewa da wayewa domin nan gaba kad'an zakifara mu amala da matan masu kudi gogaggun matan 'yan siyasa to karki da wasa nide...


Read / Download AURAN BABBAN MUTUM

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

2 Comments On AURAN BABBAN MUTUM
avatar
hausa

5 months ago

Reply

Yes Thanks

avatar
abasu-kala

5 months ago

Reply

Replying to hausa

Aha

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album