Join Our WhatsApp Group

ZAWARCI Complete Hausa Novel Document by ZAWARCI


ZAWARCI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 111628



ZAWARCI

Reading Time: 9 Hours

Added On: 26, Oct 2023

Author: Jameela Musa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 612.1 kb

File Type: txt

Views: 862+

Download: 605+

Last download: 17 hours ago

Description/Story: Copied By
YAYA HAYAT
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
Cool novel, makeup and kitchen2⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen3⃣)


WHATSAPP NO:+2349030159301
[07:24, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 1⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*


*K*wance take a tsakar ɗaki sai muɗiɗɗiƙa take a ƙasa, yunwa kawai take damunta, ga kudaje sun cika ɗaki kamar toilet in daya shekara bai samu wanki ba,,,,, wasu zafafan hawaye suka zubo mata masu zafin bala"i, a bayyane tayi magana , wayyo Allahna, da ina can naci mai kyau , babu ruwana da wata yunwa ko ganin ƙazanta,,,, goge hawaye tayi da bayan hannu lokacin da taji mahaifiyarta tana kiran sunan ta,,,,,

*R*aihana baki ji na ne?""" umma ina zuwa, tsaki tayi , sannan tace idan ma baza ki zo, kin huta, dama wankau ne, aka kawo sunce yau suke so, idan zakiyi to kizo ki karɓa, idan kuma bakya yi ki faɗa masu, a daidai lokacin da ta fito a tsakar gida,,,,,,,

*T*ashin kayan wankin ta gani, ta gyara ɗaurin zaninta, sannan tace umma zanyi, umma ta kace da dariya, sannan ta taɓa hannu, tace yo kice ma baza kiyi ba, zama raihana tayi a ƙasa ta jayo wanki ta fara irgawa, sannan ta kalli yaron tace to wankin na ɗari da hamsin ne, yaron yace Eh, tace ga kuɗin, ya miƙa ma raihana ta ƙarba, tace bayan la"asar ka dawo ka ɗauka yace to yace sannan ya fita daga gidan,,,,,,,,,,,,,,

Umma tace to yanxun dai kafin ki fara wannan wanki, ki fara wanke kayan babanki sannan, raihana tace tou umma,

��������
������
*ZAWARCI*
��������
������
Saida ta wanke kayan babanta kala biyu, sannan ta fara wankin kayan wankau, yinin ranar nan haka ta yini ta wanke kaya,,,,,,

Lokacin da ta gama wankin hijabinta data gama koɗewa ta jawo daga saman iyiga, ta rataya a wuyanta ta fita tabar gidan............

Tana fita umma tayi dariya tace munafikar Allah, ai tunda dai *zawarci* kika zaɓa sai kixo mu zauna kice uwar da nake a gidan,,,,,,,,,

Raihana tana fitowa wani shago taje, suka gaisa da mai shagon, bayan sun gama gaisawa tace don Allah fulawa za"a bata kwata ɗaya, yace to, ya ana mata, tace don Allah ka bani bashin manja na hamsin insha Allah zan kawo maka , yace gaskiya raihana bakya san biyan bashi wallahi, tace kayi haƙuri wallahi zan kawo maka dana samu, shamsu yace, baia san ranar samu ba kenan,

Idan zaka bani kawai ka bani idan baza ka bani ka faɗa man, gaskia bazan bayar ba, tace to yanxn naji magana, ta ɗauki fulawarta da canjin ishirin ɗinta ta fito daga shagon,,,,,,,,

Sallama tayi ta shigo cikin gidan, matar babanta da ta dawo daga unguwa tace ina kika je ne?""""raihana tace fulawa na siyo gwaggo, cikin tashin hankali gwaggo tace waye ya baki kuɗi?""" tace nayi wankyau ne, tsaki tayi sannan taje inda fulawar take ta ɗauketa, tace wallahi saidai a ajiyeta da safe ayi fanke kowa ya samu, raihana tace gwaggo nifa nayi wankin nan na samu kuɗina gwaggo tace koma uwarki tayi haka za"ayi, ta ɗauke fulawar ta shige , cikin ɗakinta,,,,,,,

����
*zawarci*
����

Bayan ta ɗauki fulawar ta shige cikin ɗaki raihana ta miƙe ta nufi ɗakinsu, kwanciya tayi saboda tun safiya bata ci komai ba, ga azabar yunwa dama tana ji kuma tayi wanki har ta gaji, kuma hdama kowa dai yasan wankindasa jin yunwa,,,,,,

Raihana wasu hawaye suka zubo nata , abinda ta fara tunawa, hango tsareren gidanta, tayi da tsaruwarsa da kuma yanda yake a tsabtace, cikinta ta laluba, lokacin data tuna irin abincin da take ci, uhum Allah sarki rayuwa tace,

Tashi tayi ta fito tsakar gida dan ganin waye yake sallama, wai ance a bada wanki, raihana tace to ɗauki gashi can , ya nufi wurin data nuna mashi ya nufi wurin yana cewa wai mama tace a kawo maki kaɗin taliya?"

Zainaba tace a,a, banda hali, gwaggo data ke alwalla tace kaje kace a kawo, kumin dare tayi ta, yace to, ɗakar wankin yayi ya tafi,,,,,,,,

Gwago tace dan rashin imani ubanki yana can yana fama liƙewa mutane takalmi baza ki tausaya mashi ba?" wai mutum ya haifeka amma kana masa hassada, raihana tayi tsaki ta shige ɗakin su.........



����������
*ZAWARCI*
��������

Gwaggo tace uwarki da ita kike tsaki, shegiyar nan, idan kinki haushi ki fitar da miji kiyi aure,,,,,,,,,
[07:24, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 2⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*A* ɗaki rahaina tayi magana ƙasa ƙasa, tace wallahi ba uwata nayi ma tsaki ba, kuma maganar aure, idan Allah ya kawo man lokaci sai inyi,,,,,,

*U*mma kiyi mata magana ta bani fulawata yunwa nake ji taliya zan kaɗa inci da manja, raihana ce take ma mahaifiyarta magana,,, umma tace bazan mata magana ba, dana ce kada ki kashe aurenki ai cewa kikai ke ba"a sanki, to yanxun ana sanki sai ki zauna kiyi ta haƙuri tunda haka kika zaɓarma rayuwarki,,,, raihana tace umma haka zaki ce?"" Eh haka nace kuma haka ne,,,, uhum raihana tace sannan ta ɗauki buta ta fita daga ɗakin,,,,

��������
*zawarci*
����������
*R*aihana ta kalli wani jikan gwaggo da yake zaune yana cin abinci, da sauri taje inda yake, robar ta ɗauka ta zubar da abincin a ƙasa, tana faɗin tunda banci babu uban da ya isa yaci ko yasha a gidan nan harsai naci, idan kuwa ba haka wallahi ba"a nemi zaman lafiya ba,,,,,,,,

Yaron da raihana ta ɓare na abinci ya faɗi ƙasa ya fara burgima yana ihu yana ƙarawa, da sauri gwaggo tayo waje tana faɗin lafiya?""" raihana tace ina ma lafiya tunda baki nemi zaman ta ba a gidan nan, gwaggo ta tafa hannuwa tana sallalami , sannan ta riƙe haɓarta tace raihana, yanxun da ni zaki yi faɗa a gidan nan?""" raihana tace Eh, tana magana tana zaro idanuwa, tace udan har baki bani fulawata ba yau saidai gidan nan ya tashi saboda bala"i, gwaggo tayi dariya tayi guda, ayyuri yuriiiiii yuriiiiii, to uwarki ma ta buga dani tabarni danni nan da kika bakan gixo ce, dan idan har hadari ya taru saina tsotseshi,,,,,

Rainaha tace aikin banza wanda bakuyi imani da Allah ba baku da aiki sai neman asiri, kuma idan har ina a gidan nan wannan yaron babu shi babu ƙara cin bacci saidai yunwa ta kasheshi kowa ma ya huta,,,,,,,

Gwaggo ta sake sheƙwa da dariya sannan tace, ke yunwa zata kashe, kuma ni yanxun dana ga dama sai in mayar dashi gudan ubanshi, kuma ubanshi yana da abincin bashi dan ubanshi namiji ba kamar ubanki ba, wanda sai ƙato ya cire takallmi sannan ya wanke, raihana tace Eh a haka aka gani kuma aka aura,

Gwaggo tace lallai yarinya dani kike magana, tunda *zawarci* kika zaɓa haka zamu zauna dani dake a gidan nan aure ko saidai kiga anayi,, tana faɗin haka ta kama hannun jikanta ta shige ɗakin ta,,,,,,,,

Raihana tace karyar banza baƙin bakinki ya faɗa ma jikokinki,,,,,, itama daga nan bata sake magana ba, ta ɗauki butarta ta kona ɗaki,,,,,,,,
��������
*zawarci*
��������
Raihana baki kyauta ba, ummarta take mata magana, tace umma barta, ninan walkice daidai ƙugun kowa, umma tace rufa man baki, tunda kinsan halinta kika biye mata,,, umma tace to wallahi nidai saidai in bar maki gidan nan,

Raihana tace kiyi haƙuri, kada kibar gidan nan saboda ni, umma tace idan kuwa ina san zaman lafiya da tsira da rayuwata dole in tafi dan bana iya zama ina kallon wannan wulaƙancin wallahi,,,,,,,,,

Sallamar babansu raihana , umma taji ta tashi ta fito tana mashi sannu da zuwa, ya amsa cikin kulawa, itama raihana fitowa tayi ta mashi sannu da zuwa, ya amsa sannan yace Allah yayi maki albarka, daga ɗaki gwaggo tace ba amin ba, sannan ta fito tsakar gida taci gaba da cewa kace Allah ya tsine mata albarka, wannan da kake gani, tana nuna rainaha da yatsan ta, tace to wallahi bakai sa"arta ba, saboda lalatattar yarinya, baba ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu, yace bana san irin wannan kalamin daga yau, gwaggo tace dama haka zaka ce tunda an shanye ka sakarai mai matacciyar zuciya, duk gwaggo take wannan maganar , baba bai sake magana ba ya nufi ɗakinshi,,,,, raihana da umma suma ɗaki suka koma,,,,,,,,

������������
*ZAWARCI*
����������

*T*unda asuba, gwaggo ta fito daga ɗaki ta fara jaraba, tana masifa tana zage zage, babu wanda yayi mata magana, taci gaba da cewa idan banda munafircia matsa ma yarinya ta fito da miji tayi aure sai a barta ta zauna, kuma tana da nasu santa, to tunda *zawarcin* kika zaɓa sai kizo ki zauna,

Raihana dai daga ita har umma babu wanda yayi magana , haka ta kari masifarta ta koma ɗaki,,,, ,,,,,

Bayan hantsi ya fito baba ya fito dan tafiya wajen sana'ar sa, kuma gwaggo batayi wannan famke ba, kuma batayi komai da fulawar raihana ba, haka baba ya fita daga gidan baici kuma baisha komai ba,,

Gwaggo bayan fitar baba itama gyalenta ta yafa itama fita tayi tabar gidan,,,,,

Wata maƙociyarsu tayi sallama ta shigo, bayan gaisuwa tace raihana ga dakan tashshi raihana tace to, da ƙarfe nawa kike so?""" tace bayan azahar, to Allah ya kaimu lafiya, nawa za"a bada?"""inji matar, raihana tace tiya nawa ne?"" biyu da rabi ce, raihana tace to ki bada abinda kikai niyya, tace to, ɗari biyar ta ciro ta bawa raihana, tace ta riƙe sauran canji, godiya raihana tayi, matar ta tashi ta fita, itama raihana fita tayi ta nufi shago, gari da suger ta siyo sannan tayo gida............

*zawarci*
[07:25, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ������������
����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
������������
����������
��������
������
����

*page* 3⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��


*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*S*allama raihana tayi ta shigo gida, umma ta amsa mata, kusa da umma raihana taje ta zauna, garin ta ajiye sannan taje ta ɗauko kofi da cokali, wurin ta dawo ta ɗauki garin ta haɗashi, bayan ta gana , ta miƙawa ummarta tace ummana sha ki rage man, umma tace ni bana sha, raihana tayi juyin duniya tace bazata sha ba,,,,,,,,,,

*R*aihana ta ɗauki garin tasha, bayan ta gama sha ta tashi ta fara dakan tashshin da aka kawo mata,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������

*B*ayan raihana ta gama dakan tashshi ta kwashe, bayan ta gama kwashewa ta zauna a wurin tabaryar da tayi dakan tana hannunta, ta jingina kanta da ita, hawaye masu zafi suka zubo mata, ta runtse idanuwanta, abinda ta fara tunawa shine,,,

�� ��
*gidan mijinta*
�� ��

*R*aihana ta fara tunawa, wata rana, da sallama ya shigo gidan ko inda yake bata kallaba, shi kuma cikin farin ciki ya shigo yana faɗaɗa murmushin shi, yace raihana barka da gida, tsaki tayi, ita babu sannu da zuwa kuma bata ansa sallamar ba,,,,,,uhum ajiyar zuciya zainaba tayi sannan a bayyane tayi magana tace rabon *zawarci*

������
*zawarci*
������
Idanuwanta ta sake runtsewa, abinda ta ƙara tunawa, raihana zanyi tafiya, ta sake hango lokacin da ta taɓe baki, sannan tace sai wani magana kake man saman kai babu girmamawa, idan zakayi tafiya ina abinda ya dameni"""",,,,,,, murmushi yayi sannan ya ciro kuɗi har dubu ishirin ya ajiye mata a gabanta,,,,,,,,, wasu hawaye suka ƙara kwararowa daga gudan raihana, tace *astagafurulah*

*zawarci* baiyi ba, abinda raihana ta faɗa kenan, sannan ta gige hawayenta, tace abinda nafi ƙarfi yanxun shine yafi karfina,,,,,,,,,, ***

��������
*zawarci*
��������

*R*aihana ta janye taɓaryar gabanta ta jingina da bango ta mike,,,, a daidai lokacin da gwaggo tayi sallama ta shigo,, raihana ta amsa, gwaggo ta cire gyalenta ta rataya a igiya, sannan tace raihana wani mutum ne a kofar gida yake maki sallama, raihana tace naji, ɗakin ummanta ta shiga, ta ɗauko kwandon wanka, ta duba taga babu sabulu a ciki, tsaki raihana tayi tace kai Allah kasa mu dace, saman window ta duba ta ɗauko wata ledar omo, ta zuba ruwa ta shiga wanka,,,,,,

��������
*zawarci ne*
��������

*T*ana fitowa wanka alwalla tayi ta shige ɗakinsu, umma ina man yake?"" in shafa umma tace babu mai ya ƙare fa, raihana tace yanxun ya zanyi a daidai lokacin da take zama saman tabarma, umma tace ɗauko waccan ledar ina da sauran man gyara ki murza , ajiyar zuciya raihana tayi sannan ta miƙe taje ta ɗauko ta shafa, fuskar nan ta ɗauki ƙalli, da kafafuwanta, kuma babu powder, ta kalli kanta a madubi, tace rayuwa kenan, girgiza kanta tayi hawaye masu zafi suka zubo mata, umma ta kalleta tausayin raihana ya kamata, saboda raihana bata san wahala, amma a fili tace haba har kin gaji?"" ai baki komai ba, lokacin dana faɗa maki kiyi haƙuri ki zauna ai cewa gani kikai gara ki dawo gida,,, haushi ya ishi raihana bata sake magan ba, ta ɗaga ƙasan katifarta ta ɗauko wata ƙoɗaɗɗiyar atamfa tasa, da habar zaninta ta goge fuskarta ta fice daga ɗakin,,,,,,

������
*zawarci*
������
Tana fita umma tace kinga da yanxun kina gidanki kina yin rayuwarki yanda kike so, kinzo ki liƙe nan sai wahala kike sha,,,,,

Fitar raihana wani mutum ta hango tsaye bakin bishiyar kofar gidansu kamar ya fiddoshi daga cikin ƙasa, raihana tayi tsaki sannan ta nufi wurin shi cike da masifa, tana zuwa babu ko gaisuwa tace malam yadai?"" yace nine dama nazo ina sanki, to naji kana do na, sai mi kuma?"" maganar aure ce, raihana tace to daga yau kada in sake ganin ƙafarka nan kaji na faɗa maka?"" tana faɗin haka bata jira abinda zaice ba tayi cikin gida, a zaure ta tsaya, tace banda iskanci da shara da bola dan taƙamar kana *zawarci* kowa sai yaxo, tsaki tayi sannan tace shege ƙazamin banza, ...............


Hhhhhhhhhh
��������
*zawarci*
��������
[15:01, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 4⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*gargaɗi a bisa wata ƙungiya, da bama buƙatar saka sunan ta, dan haka muna roƙonsu dasu guji juya mana littafi ta ko wace fuska, idan kunnne yaji ���� gangar jiki ya tsira* ����‍♀

��������
*zawarci*
��������

Sallama tayi a daidai ƙofar ɗakin ummanta ta shige, har kin dawo?""" Eh kawai tace, inda ta ajiye tashshin data daka ta wuce ta ɗauka , sannan tace umma zan kai mata saƙon nan, umma tace sai kin dawo , to tace tayi gaba,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

*zawarci*
Raihaina tana fita umma tace Allah ya baki miji kiyi aure raihana ki huta da wannan rayuwa, ,,,,,,,,

*R*aihana tana fitowa maƙotansu ta shiga, gidan badiyya, sallama tayi ta amsa mata tace raihana ki shigo mana, raihana tace to, ta shiga, ta samu wuri ta zauna, suka sake gaisawa, sannan raihana ta fidda tashshin ta bata, godiya tayi , sannan tace bara inxo,,, fitowa tayi taje kicin ta zubo ma raihana abinci,,,, sannan ta dawo ta ajiye mata, murmushi raihana tayi danma kada a ɓata lokaci kawai tace tana azumi,,,,,,,,,,,,

������
*zawarci*
������
*B*adiyya tace Allah sarki azumin mi kike?"" murmushi raihana tayi tace ramuwa nake, badiyya tace to Allah ya bada lada, amin raihana tace, sallamar mijinta suka ji, raihana tana zaune taga badiyya ta tashi cikin sauri ta fita,,,,, tana kallon ta tana zuwa ta rungumeshi tana oyoo yoo barka da...


Read / Download ZAWARCI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album