Join Our WhatsApp Group

FUTUHATU KHAIR Complete Hausa Novel Document by FUTUHATU KHAIR


FUTUHATU KHAIR

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 37177



FUTUHATU KHAIR

Reading Time: 3 Hours

Added On: 15, Sep 2023

Author: Xainab Y Hussain ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : © NAGARTA WRITERS ASSOCIATION©

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 214.93 kb

File Type: txt

Views: 479+

Download: 239+

Last download: 1 day ago

Description/Story: [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹
(August 2016)

Na Xainab Y Hussain✍🏻

{Huum,wannan labarin qirqirarrene,ba'ayi dan cin fuska ga kowaba,kuma duk Wanda ya juyan labari *Allah ya Isah*}


Aminci ya tabbata ga duk wanda ya karanta wnn littafin, sadaukarwa ga Daukacin writers baki daya.

Episode 1


Assalamu alaikum, kina ina matar gidan nan?nasan kina d'aki fito kiban kud'ina ,haba ace kullum yarinya sai uban cin bashi sai kaxo karb'a alallameka da dad'in baki.

Da fara'arta ta fito daga cikin daki,tace Adda Bena ce !sannu d xuwa kujera ta janyomata sannu ,ni bawani sannu gaskiya kud'ina xaki bani,murmushi Meime tayi tace dan Allah kiyi hakuri insha Allahu nan da sati xan baki wallahi maigidan ne kwana biyu ba ciniki shiyasa.kaji irin abin koh!nidai kawai sati na xagayowa xanxo na karb'a,shikenan Allah y kaimu, har Adda Bena ta fita sai ta dawo,Yauwa Miemi dama inason tambayarki wai me kikesawa a girkinki kullum unguwa sai ta cika da qamshi,dariya tayi tace maggin da kike siyarwa dashi nake amfani,Kuma ni tsayawa nake ina girki a hankali,Itadai Adda bajin maganar maganar Miemi takeyiba,miyaun tane yaketa tsinkewa tunda ta shigo takejin qamshi shiyasa ma bata tsawaita maganarta ba.


Miemi tasan halin Adda Bena shiyasa tace xauna Adda na xubomiki tuwo ne ,nasan baci kike ba,da sauri tace la aini mutuminane tuwo kamar kuwa kinasan yunwa nakeji ,haka ta xauna taci abincin ta tasha ruwan randa,sannan ta miqe tace Yauwa sati kikace koh tace eh, Allah ya kaimu haka tafita ita Kuma takoma d'aki.

Bacci yafara d'aukanta tajiyo sallmar megidanta Kabeer,da sauri tafito tana dariya tace Allah yau ka jima bacci har yafara d'aukana,turus tayi ganin shi da wata yarinya wadda batafi shekara 11 ba tayi baqi ga kayan jikinta sunyi datti,kallonsa tayi tace daga ina?dariya yayi yace before kice komai plx let her take a shower first, then sai kiyi complaine, kallonsa tayi tace banda ruwan d'umi" Kiyimata da nawa abinda yace kenan ya shiga d'aki.

Wayyo typing wuya,plx mama Hassy or Maman Bobo come nd join me plx😜😜😜😜😜😜
© NAGARTA WRITERS ASSOCIATION©
2 u futha love
*@ut@r h@jiy@*✍🏻
[11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹

(August 2016)

Zainab Y Hussain✍🏻

Episode. 2-5

``✍🏻`Hannun yarinyar ta kama suka shiga toilet,sannan ta fita ta d'ebo ruwan kanta tafara wankemata saboda gaba d'aya qasa had'eda datti sunyiwa kan yarinyar sallama,hakan yasa gaba dayan ruwan yatafi gurin wanke kan,kadan ta rage wanda dashine tayimata wanka, hannunta ta kamo suka shiga d'aki kayan make-up nata ta d'auko mai tashafamata akan sannan tayimata kwalliya dai dai.```


*Huum! ko kefa keda kike son yarinya gashi Allah yabamu daga sama,kallonsa tayi tace hakane amma ya akayi kasameta?nifa banson kwashe kwashe dan Allah baibamu d'a ba,ai baya nanufin yamanta damu bane,komai lokacine.*

```Haba Miemi xanyi miki qaryane,Wllh kinji na rantse kwana wajan uku ina ganinta awajan,damagaran tana bin mutane wad'anda suka rage abinci tana ci,koni sai dana bata nawa,jiya kuma dawowata daga abalak naganta wasu suna dukanta wai sunsiya abinci kafin su wanke hannu su dawo ta cinye,ni na biya kud'in sannan nayimata fad'a na tambayeta gidansu tayimun shiru nayimata magana amma batacemun komai ba,shine nakaita gidan mai unguwa,daxu ina fita na had'u da mai unguwa yake cemun gaskiya yara sunyimasa yawa saboda haka nasan yadda zanyi da ita,haka na d'auketa muka tafi kasuwar tare,muka dawo tare kuma ,kinji yadda akayi na sameta```


*Hawaye ta goge tace Allah sarki yarinya kyakywa komai ya fito da ita daga gida ko kuma bata tayi Amma kuma kamar ba 'yar qasar nan ba,dan batayi kama da 'yan Niger ba,tafi kama da Larabawa ko Fulani,wallahi nasami 'ya,hannunta ta riqo tace ya sunanki baby,kallonta kawai tayi ganin haka yasa tayimata alama da hannu ya sunanki,itama da hannu ta rubutamata sunan ta BILKISU.*


Kallonsa tayi tace ko bata magana ne,kai ta d'aga masu,Allah sarki insha Allahu zan riqeki kamar 'yar dana haifa,Shimi ta d'aukomata tasa mata,sannan ta zubamata abinci da kanta take bata har ta qoshi,sannan sukayi alwala sukayi sallah.


*Wacece Miemi da mijinta Kabeer*

*Miemi matace gurin Kabeer auren saurayi da budurwa sukayi,shekarar su shida da aure Amma Allah baibasu haihuwa ba 'yan Nigeria ne,garin Maiduguri,Miemi ta kasance mace mai hankali da mutunci batada hayaniya kyakyawar gaske batada abokin fada kowa natane mjinta dai dai gwargwado yana kulawa da ita komai takeso yanayimata batada k'iwa ko lalaci kaf unguwarsu ansanta wajan iya sarrafa girki,tana iyakar qoarinta wajan kula da mijinta,basuda shi sosai amma sunada wadatar zuci,mijinta d'an kasuwane sannan kuma ayanxu yana neman aikin gwamnati Ba inda baijeba amma baisamu aikin ba, kuma ga kasuwar yanzu bata ci sosai, dalilin dayasa kuwa lokacin daya saro kaya daga Nigeria zuwa Niger Allah ya saukar da lbtila'i akan kayan babu abinda yayi saura akayansa,wuta ta cinye,wannan dalilin yasa ayanzu abubuwa sukeyimusu wuya duk da haka bazaka je gidansu ba karasa abin sawa abakinka, ba,gwanace wajan iya sarrafa turaren humarah,da turaren daki,tanasamu dai dai gwargwado.kasuwanci ya kawosu qasar Niger,suna zaune a garin abalak,ita da mijinta*

®NWA®
_Jinjina gareki Namecy ta Xee Maman Khady._
*2 U Futha Luv👯*
*@ut@r h@jiy@*✍🏻
[11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹
( August 2016)

@ut@r h@jiy@✍🏻

Page 5 - 10

```Janyo BILKISU tayi jikanta,tace kiyi hakuri bansan komai ya fito dake gida ba amma insha Allahu nixan zamemiki UWA,kinji BILKISU, kai tad'aga alamar to!.Dawowar sa daga masallaci kenan,ko gida baishigaba yaji anmasa sallama amsawa yayi had'e da juyowa,a'a Alhaji ne sannu ina yini'malam Kabeer ya gida da iyali,alhamdulillha yace,Alhaji yace wato gaskiya nayaba da hankalinka kuma dama nadad'e ina San ganinka wato rumfata ta kasuwa,nasan kasan tafi shekara da rifeta dalili kuwa baya rasa nasaba da irin ta'adin da akayi mun,shine nakeso Idan ba damuwa mezai hana ko gobe indai ashirye kake kaxo kaganta Idan zaka iya jurewa xan d'oraka akai saboda tafiya xanyi Kuma Wllh babu wanda nayadda dashi kamar kai,Kuma koda xaka xuba kayanka aciki Ba matsala, fatana ka riqe gaskiya,kaje kayi shawara gobe da safe naji yadda kukayi,Allah yabamu alkhairi,abinda yace kenan ya tafi. ```


*Da sallama ya shiga gida Miemie ya tarar ita d'aya,kallonta yayi yace duk jiranane haka,to gani na dawo,ko kallonsa batayiba,tace haba dan Allah wannan wane irin hali KA tsiro dashi, naji daxu saboda BILKISU ka dad'e yanzu kuma saboda wa kajima?hum Miemie kenan Wllh ana idar da Sallah natawo Alhaji RAHEEM ne ya tsaidani,wani Alhaji Raheem din,mutumin dabaya kula kowa shine zai tsaya yimaka magana,kawai dai ni nasan bazan juri wannan sabuwar halayyaarba,Shikenan amma ya inamiki magana kina magana haba dan Allah wallahi abinda kike zargina dashi ba haka yakeba,me xanyi da wata Seemby yarinyar baqa da ita,gani da kyakyawar mace agida ina zan tsaya kula wata Seemby,itace dai take sona, amma ni kece tawa,so don't be compuse fell free I'm Ur's, no more add any wife again insha Allahu ,u ar OK agurina,Huum to ya kukai meyacemaka,Yauwa Matata,kince in xauna dai baxaki barni atsayeba,dariya tayi hannunsa ta kama tace Idan ma acinya kakeson xama bismillah,wa rufan asiri karna karyaki inrasa ina xankai larurata,barni dai inxauna a qasa,suduka sukayi dariya,nan dai ya labartamata yadda sukayi da Alhajin,yace to mekike ganin xancemasa Eh ko A'a?,Nidai banda abin cewa sai fatan Allah yasa shine FUTUHATUL KHAIR dinmu,(mabud'in alkhairi) Ameen yace daga nan suka tashi wanka sukayi sannan ta d'auki BILKISU suka shiga daga ciki.*



Safiya nayi bayan sunga al'adar dasukeyi,ya shirya yace Miemie ni yakamata naje,ko shine xaiyi kirana,a'a kai zakaje tunda lokaci yabaka yace Idan ka amince sai kaje kayimasa bayani,Allah yasa alkhairi, Ameen yace.Yauwa Miemie Idan BILKISU ta tashi wane kaya xatasa,ko kafin ta tashi ki wankemata nata ,tav nifa Wllh a shara nasasu,sun yayyage,to! Yanxu ya xa'ayi?au Allah yasa Lokacin da Aunty Hassy taxo tamanta kayan babynta har kala 3 bashine nakewa indi xakaje katafi mata dashi,yanxu kuwa BILKISU tasamu kaya.kayi sauri 8 hartayi,plx kayi addu'a Allah yabadadinki*,Ameen yace sannan ya fita.

Tunda yafita taketa addu'a Allah yasa wannan abin yaxamo solar arziqinsu,Haka tayini tana addu'a,lokaci lokaci tana duba BILKISU amma ko motsi batayiba,wajan 2:30 ne tayi juyi ,ganin haka yasa taje tanad'an buga bayanta wai ta tashi, kafin ta tashinne taji wayanta da sauri ta d'auka mijintane da sauri tayi picking hamdala taji yayi yace Miemie Allah ya amsa addu'anki Wllh har kayana yace da d'akko dama Kuma sauran sati biyu kud'ina suqare na hayar teburin,yanxu kuwa kinga abinci ma harda rabin kaza,aka kamun nakasa ci,tunani nake mekikaci keda 'yarki?,dariya tayi me had'e da qwalla tace kajika,ninaci abincin na qoshi kaine dai baka ciba,'yata Kuma sai yanxuma tayi juyi,tashinta dai xanyi yanxu,a'a kyaleta kinsan kwana nawa tayi ba bacci Sai Allah to ki kyaleta ta tashi dan kanta,kawai dai kiringa juyata,sai na dawo mexan siyamiki,kinga yadda naketa ciniki,Kuma yace Idan na qara kud'ina afarashin dayaban nawane kud'in,na riqe Wllh bakiga ba kamar na shekara ina ciki. Allah dai yasa albarka,Ameen.


®NWA®

*2 u Futha Luv*
*Maman Khady sannu da typing ,Allah yabar qauna ,Ayiya yar basaja kema sannu,Hassy ,Sahaf ina gaisuwa, Anker hala pharm yayi seezing phone dinki*
😜😜😜😜😜
[11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹


(August 2016)

@ut@r h@jiy@✍🏻

Page 11

Ajiye wayar tayi,hawaye ta goge,tace ya Allah kasa wannan yarinyar tanada rabon ganin danginta,Allah ka bawa mijina abinda yaje nema,janyota jikinta tayi, ahaka itama bacci ya d'auketa.Sallamar dataji ne tayi salati sannan tafita waje,Adda Bena ce da *Maman fadeel*suka shigo lale Bena ce sannu ku shigo Wllh bacci nakeyi,sannu, *Maman fadeel* ce ta tab'o Bena tace amma gaskiya wannan matar 'yar gayuce kinji gidan qamshi,lallai dole kice ga inda xa'ayi mun had'in humrah,tana turaren wuta,ke babu abinda batayi,tafiyar ta sukaji da sauri suka canja hira.


*Ruwa ta kawomusu da alkaki* zama tayi suka gaisa,sannan Bena tace kinga wnn 'yar uwatace a katsina take,aure ya kaita Ghana,yanxu biki zasuyi jiyan nan tazo take cewa Maiduguri zata za'a had'awa amaren Turaren d'aki,shine nace mata basaita wahala ba akwai maiyi,yanzu muna son kwalba *goma sha biyar*amaren uku ne sannan da kwalbensu xaki had'a nawa xa'a baki, ajiyar xuciyata ta saki tace Bena ko nawa kikawo xanyi, bakwason gishirin wanka,ahaf komai xaki had'a fatanmu yayi kyau da qamahi ,karkuji komai insha Allah xanyi yadda kuke so,tom Ga deposit kafin ki gama xa'a ciki, *dubu d'ari*suka ajiye,Ita kuwa Ummu fadeel gaba daya Miemi ta burgeta yarinya da ita amma ta iya gyara kanta.


Fitar su kedawiya tajiyo motsin BILKISU da sauri tayi cikin d'akin hannunta ta kama brush tayimata sannan wanka,abincin ta ta d'akko abaki take bata,tana janta da wasa har suka gama.

Rayuwa sabuwa komai yayi farko xaiyi qarshe,yanxu su Miemi basuda matsala komai ajiyewa Kabeer yake,gashi Kuma sunsa BILKISU a makarnata,komai suka tava alkhairi yake zama,Idan kaga Miemi baxakace itace ba, rayuwa sabuwa,Kullum basuda abin qauna da tunani da dubawa Sai BILKISU, sukance wannan yarinya itace mabudin alkhairinmu,daga nan suka sa mata FUTUHATUL KHAIR.

® NWA®
*Ummu fadeela, Xee Mamsn khady ,Sahaf ,qauna zallah,Allah yaqara had'a kanmu*
2 U *FUTHA LURV*
[11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹
(August 2016)
Na Zainab Y Hussain✍🏻
Page 12-15

✍🏻Shekara kwana gamai yawan rai,yanxu FUTHA shekara ta biyu a qasar Niger,rayuwa yayimata dad'i kyanta da farinta kullum fitowa yake,ayanxu haka tana aji uku a qaramar secondary schoo,da taimakon Alhaji Raheem yasamu akayiwa futha primary certificate.Allah mai baiwa gata da qoqari,komai aka tambayeta xata bada amsa dai dai,amma da rubutu,tunda babu bakin magana,Maruqiyarta kuwa,Meemi babu abinda yacanja gameda yadda take kula da Ita.



Lokaci da dama suna xuwa gida Nigeria, danginsu Meimi sai san barka,sun d'auketa matsayin jika ko 'ya,amma 'yan uwan Kabeer kuwa duk lokacin da sikaje,da kuka take dawowa,saboda komai nasa since akan matarsa yake qarewa,da 'Yar tsintuwa,itakuma ba haihuwa saidai taci,ta kwanta,addu'ar Miemi da 'yarta FUTHA bai wuce Allah yabawa Auntyna baby ba shiyasa a unguwar ake sonta, batada hayaniya,yaro duk qazantarsa tana daukan shi, kuma batada rowa,had'in turare kuwa,ba Wanda bata iuaba tanda karambani wajan iya abinda bata iyaba abinci kuwa indai ba makaranta itace take yi, batada fushi, Idan kaga fushinta,to akan anhanata aikin gida ne,kamar wanke wanke ko shara,tunda yanxu sunada almajiri,shi yake komai,Ita tafi son tayi komai da kanta kamar yadda taga RASH agidansu itace kewa hajiyansu komai,amma Ita QURRATU AYN batada aiki saina danna waya,shiyasa bata qawa da Ita.


Duk da bata magana,amma haka ta keda qawaye sosai, dan lokacin da sukaje Nigeria,kowa sonta yakeyi,amma tafi riqe sunan,CANDY da KHAIRAT (panisau),saboda sune suka ringa kulata,har islamiyya tare suke tafiya,FIDDAUSI sodangi ce kawai bata kulata,shiyasa ko sunje bata ma zuwa indai take.


Tunda safe ta tashi wanka tayi,ta d'ora girki,harta gama Aunty Miemi bata fito ba, shiru shiru,ganin haka yasa tayi tafiyarta tunda before ta kwanta bacci Abban ta kebata kud'in break,yaudai gata nan ne,coz of she doesn't see her Aunty, shiyasa take so silent, even taking lesson in the class she can't stay to understand what d teacher do for us, tunanin ta one,meyahana Aunty fitowa,har aka fito break she's not fell well ajikinta,RASH ce taxo ta xauna dafata tayi, da sauri ta jiyo,tana share hawaye,alama tayi mata,me ke damunki,fad'amata tayi,murmushi tayi,tace yanzu ke dan kawai bata fito ba, shine kikaxama lazy yau,Abbanki ya fito tao,Kad'amata kai tayi,alamar a'a,dariya CE ta kwacewa RASH tace ke banda abinki, mata natare da mijinta,dan basu fitoba,shine xaki shiga damuwa,Plx kiyi shiru lafiyanta lou,bacci maybe ya kwashe ta, amma nasan badan bacci ba,da xata fito koh,kad'amata kai taqarayi,yauwa to kiyi shiru, yanxu tawo muyi break kinga yau masoyinki nayi miki,d'an malele,da sauri ta tashi tana dariya,wushiryarta me kyau ga dimple d'inta dasuka qarawa fuskarta kyau,yauwa yi sauri kada ANEE taxo kinsanta cinye duce,haka suka xauna,Rash namata magana mai dad'i har aka tashi.



Da saurinta ta shiga gida,Aunty Miemi tagani akwance ga robar miyau agabanta,da gudu taje tayi hugging d'inta,tana shafa kanta,alama tayimata,cewar bakida lafiya,?kai da kad'a,tace FUTHA banda lafiya,nadad'e inajin motsi acikina,jiya Kuma banyi bacci ba,kinsan tun kwanaki nake cemiki,abinci nake yawanci,bansan meke damunaba,ko wani abun ne acikin, shiyake cinye abincin bansaniba,hannunta ta jijjiga,ranar dai daga 'Yar har uwar akwance suka yini,sai da magrib ne da Abban ya dawo, yagansu ahaka, shine ya rarrashesu abinci kuwa kad'an FUTHA ta iyaci,Miemi kuwa ai Har saidata qara d malt,sannan taji daidai.Safiya nayi kuwa,asibiti suka tafi,gwajin farko doctor ya tabbatar musu da shigar ciki har wata hud'u,farinciki,murna ko ban fad'aba su suka SAMI matsuguni axuqatan wadan nan bayin Allah, kabbara kawai yake,Miemi kuwa kamar amafarki takejin wai ciki gareta.


Xokaga d'oki daga uban d'an har FUTHA, family d'insu ma,murna suke,aure shekara bakwai,sai wannan karan Allah yakawo rabo,cikinta nada wata takwas tafara musu wasu xantuka,sai ana...


Read / Download FUTUHATU KHAIR

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album