Join Our WhatsApp Group

NAMIJIN DUNIYA Complete Hausa Novel Document by NAMIJIN DUNIYA


NAMIJIN DUNIYA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 96571



NAMIJIN DUNIYA

Reading Time: 8 Hours

Added On: 08, Feb 2024

Author: Fenerh ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 517.39 kb

File Type: txt

Views: 741+

Download: 852+

Last download: 7 hours ago

Description/Story: 🌻🌻NAMIJIN DUNIYA🌻🌻





*WRITTEN BY FENERH*


https://chat.whatsapp.com/FxikBhpweXTLMbrEVc6xdS
Join our free page group



"Bismillahir Rahmanir Raheem.

"Alhamdulillah muna godiya ga Allah akan dukkan ni'imomin shi agarenu, tsira da Aminci su tabbata agareshi fiyayyen Halitta Annabin mu Muhammad S.A.W da Ahalin sa da kuma sahabbansa .

Page 1️⃣

Sokoto state

............ Y'an mata ne sanye da Uniform birjik a harabar katotuwar makarantar ta y'an matan, wato WTC tanbuwal dake Karamar hukumar sokoto, kowacce ka kalla kayan tane a gaban ta Alamar hutu suka samu na zangon tsakiya. Gefe daya hankali na yafi karkata wurin wasu y'an mata su uku kyawawa masha Allah masu dibar yanayi farare dasu, saidai daya a cikin su data so ta darasu haske ga wani irin sihirtaccen kyau Idan ganta zakace filloce Yanayin jikinta,daya daga ciki kalleta tace "Amrah ni yau Idi bai san munyi hutu bane da har yanzu bai zo daukar muba? taja tsaki tareda cewa, " ni ai ba hutun da na tsana irin wannan wallahi domin nasan shugaban mugayen yana gari. "Yeeeeeeh!. Dayar ta buga tsalle tareda saka ihu har saida suka toshe kunnuwan su, "Nimrah bakida hankali ne ki ke mana irin wannan ihun? Duk kinsa ana kallon mu? . " oho nidai ina farin ciki yaya NAZIR zai dawo yau she rabon da mu hadu dashi shekara kusan biyar fa nasan yanzu ya kara kyau da haduwa. Tafada tana lumshe idanun ta Alamar shauki. "Mtswww iska na wahalar da mai kayan kara wallahi, meye abun burgewa a wurin miskilin mutumin nan mai shegen fadin rai da nuna shi kamar yafi kowa. "Kai, gaskiya kinfada ra'ayinki ne Nimrah akan Yaya Nazir domin kuwa ko hasidin iza hasada yasan shidin NAMIJIN DUNIYA ne. "Fada mata kedai Farha ni bansan me yayi mata da zafi ba ta tsane shi tun tashin mu. "Ba wani tsana tawa da tashi bazasu taba haduwa ba har abada. Nidai duk duniya banda zabi sama dashi da Allah zaiyi ikon shi ai ni shar wallahi. Nimrah ta fada. "Kin haukace kuwa, yanzu sai a wuce su Aunty FARIDA dasu Aunty Sadiya a hada shi dake Y'ar tatsitsiya ko?. " Ai abun rabo ne a bare Gyada a tsinci mota. "Impossible kenan. Amrah tafada. "Ai wallahi kudai ku tayani Addu'a Allah ya tsanan ta rabo...... Tsit tayi ganin motar gidan su data kunno kai, sukayi saurin tashi suna daukar jakun kunan su da trolys dinsu, Idi driver ya fito da sauri " kuyi hakuri iyayen gidana holdup ya rikeni a hanya tun Asuba na fito. Yafada cikeda fara'a, Amrah bude motar kawai tayi tareda shigewa baya ta cire hijabin da ya takureta saboda zafin da ya takureta domin ita mutum ce mai tsananin jin zafi kanta ta girgiza tareda baje sumarta dama ko kamata batayi ba, Farha ta shigar musu da duka kayan booth ta shigo bayan ta zauna a gefen Amrah, Nimrah kuwa ta kame a gaba, ya dauki hanya sunata zabga hira su uku, ita kuwa Amrah jingina tayi a jikin mota ta fara bacci domin ita batada jimirin Tafiyar mota ko nan da can ne yanzu zata fara bacci. Tafiyar kusan hour guda sukayi suka shiga cikin birnin shehun,

Sai da motar ta shiga wangame miyar harabar gidan kafin Farha ta bugata tace " toh bayan mota sai ki tashi mun iso. Bude idanun ta tayi tareda yin mika ta bude gefen ta ta fita, hijabinta a hannu ta tana karewa harabar gidan nasu kallo,tsaki tayi ganin sabbin motoci har guda biyu tasan ko na waye, harda basu harara tayi gaba,
Farha tabiyo ta janye da akwati daya tana cewa " ya naga kina hufar gefen Mami? Mu tafi masaukin mu mana gefen hajajjaju mu kwashi jallof mai daddawa. "Bazan jeba yau. "Saboda me tom bayan can muka saba zama? " nace miki bazanje ba ko dole ne mtswww. Tayi gaba suka bita da kallon mamaki, Nimrah ta ce " duk saboda yaya NAZIR ne yasa taki zuwa gefen hajjo yau, aikin banza shida ke sha'anin gaban shi ina yasan ma tana wani tsanar shi. " no Nimrah ba zancen tsana kawai jinin su ne bai hadu ba kinsan shi baya raina abun fada ne. Wucewa sukayi abinsu Idi driver ya biyosu da sauran kayan, tun daga harabar gefen hajjo suka fara jiyo hayaniyar yayyun su mata, don haka da gudu suka karasa suna " yeeh mundawo, ina kike kakus tamu? Fadawa sukayi falon hajjo na kasa sun zagaye ta suna jiran ta gama kwaba ramar ta Suci, ita kuma tana mita, " ni yau duk dadin bakin ku kunbar cimin rama duk ku gama iya shegen ku kubar min daki. "Haba kakaras tamu ai mudake bata baci munsan zaki bamu. " ai sai kuyi zancen kuke so. Shigowar su Farha da Nimrah yasa dakin ya kara rikicewa, sun rukun kume ta kamar zasu karya ta, " kai karasa ni zakuyi ku cika ni bansan hauka. " hajjon mu munyi kewar ki ne shiyasa muka fara nufoki. " toh ai fa kundawo, ina waccen mai murdadden halin kuma yau? Amrah ta wuce gefen Mami. " toh kuma yau? Toh ta sauka kalau.

Wata Uwar tsawa ya buga musu yana fitowa daga dayan dakin dake falon hajjo, tsayuwa yayi tareda binsu da kallo one by one, sanye yake da tree quarter na camou kala mai haske sai wata irin armless blue agaban ta dauke da Alamar sojan sama wato air force Army, Hmmm what a Man, nafada a zuciya ta domin ban taba cin karo da namiji mai irin zati da kirar shi ba, gashi kyakkyawan gaske fuskar shi ba suma ko daya sai askin kanshi punk saisaye yayi matukar haduwa, hannayen shi zube a cikin pocket din wandon shi, fuskar shi kamar hadari ya taso, " All of you out.
Je Kaga ruwan Y'ar tsere tuni suka arce hajjo nacewa " kai karka korar min y'an hira kai ba tayani zakayi ba sai dai ka zauna kana latsar waya kamar mai aikin sirri. Ai su tuni sun ware ya zauna tareda dora kafa daya kan daya yafara sana'ar da ta tsana "sai ko ka cinye wannan uban Ramar da kasa suka tafi suka barni da ita.
Dago kai yayi ya kalleta cikin miskilanci yace "I don't understand you at all hajjo, inaji kina korar su tareda fadar bazaki bari suci miki Abu ba, na tai makeki na korar miki su kuma kina wata magana daban. Yafada yana kama hab'a,
" karkayi unstan din don kanin tsohon ka, toh tun ba a haifi ubanka ba nake zaune da y'an boko, na da' masu ilimi mai inganci ba irin naku ba na yanzu sai shirmen turancin banza da wofi.
Jikoki na suna zaune muna nishadi ka kora su sai ka tashi ka barmin gida duk nasan kame kamen da kakeyi kallon ka kawai nakeyi ka gama kwana kwanar ka ka dawo dai dai ko inyi ma ungulu da kan zabo Uhm.Kallon ta yayi tareda cewa "kiyi hakuri tun tuben harshe ne bazan karaba.
"Kama 'kara mango pa. Wata irin dariya ce ta kama shi unexpected ya mike tareda fita yana cewa " natafi cikin gari indawo hajjo a ajiyemin tuwon masara da miyar guro. " adawo lafiya ka turomin yaran nan suzo su tayani cin wannan ramar kartayi kwantai.fitar shi yayi batareda ya amsata ba, ita kuwa taci gaba da mita, " kayita nuku nukunka ka gama.

Kamar jira suke kuwa yana fita gidan suka koma suka ci gaba da shabtar su suna cin ramar da hajjo ta kwaba, Amrah kuwa tunda ta isa dakin Mami ta tarbeta cikeda murna tareda bata Abinci lafiyayye tace taje tayi wanka ta huta ta kyale shirmammun can, sundawo ko hutawa basuyi ba sunje su damar mana tsohuwa, ki huta kije ki gaida mutan gidan ko.
Gyada kai tayi tareda hayewa kan gado bata ko sha'awar zuwa side din Ummin ta saboda ba wata sakewa a tsakanin su da ita, don haka ko hutu akayi duk Rayuwar ta tafi a dakin hajjo da kuma Mami, da side dinsu Nimrah.

Ba ita tabar side din Mami ba saida su Nimrah suka shigo suka jata domin gaida mutanen gidan, dakin Ummi suka shiga tana zaune a tsakiyar falon rike da d'an karamin yaron ta mai kimanin shekara shida tana biya mai hadda cikin suratul mulk yana biyawa gwanin burgewa, sukayi sallama a natse saboda bata son rawar kai duk sun san halin ta don haka tuni suka sawa kansu natsuwa, zubewa sukayi tareda gaida ita, Kallon su tayi cikin sakin fuska tace " Allah ya muku dawowa? " eh Ummi ya gida. Suka fada baki daya, ta amsa a dunkule tareda mikewa tace " kunci Abinci " munci Ramar hajjo mu Ummi Akwai mai dadi?. Nimrah tafada tana mikewa domin nufar kitchen, saboda basuda shamaki a duka sasan, Farha tabita yarage Nimrah da brother dinta Imran Wanda ya haye kafarta yana zuba mata surutu,
Dago kai Ummi tayi tareda Kallon ta tace "iya shege ne yasa kika ware yau a cikin y'an Uwan ki baki koje kin gaida Hajjo ba?. " yanzu zanje Ummi Idan na fita daga nan.

Saida sukaci dambun shinkafar da Ummi ta hada yaji zogale da yajin kuli suka fita, tareda nufar gefen su Nimrah,
Momyn su Nimrah na zaune itama tareda su Aunty FARIDA da aunty Sadiya, sun hakikance sai hira suke zubawa kamar kawaye, Wanda hakan na matukar burge Amrah domin ita batada wannan saken a wurin Ummi, gaida ita sukayi tareda zama tana tanbayar su ya karatu? Suka amsa dukan su kafin Amrah ta gaida su Aunty FARIDA, "Ke kuwa kin shigo ina kika shige daga dawowar ku? "Ina wurin Mami ne. Tabe baki Aunty Sadiya tayi kafin tace " Hmmm kinadai da cusa kai dayawa in banda salon iyayi kinsan ya Naz yadawo meye na zuwa gefen Mami?.

"Toh uwar y'an korafi, Wanda kikasan sai dole ke kaishi part din ma meye don taje can, ai na fara yiwa Abban ku magana, bai kamata ace har yanzu su saka mai ido ba wani zancen Aure ba, don haka ya fito cikin ku biyu ya zabi daya tunda gida bai koshi ba ba akai wa d'awa ba. Nimrah tayi saurin cewa " kudai Aunty Sadiya wallahi iskace ke wahalar da mai kayan kara, dazu daga mu harku kamar awaki haka yai waje damu daga gefen hajjo, kuna kallon ya karo wulakanci yanzu, Karku je ku nemi miji ku tsaya jiran ya NAZIR. Dariya Farha ta kunshe ganin y'anda suka hayayyako mata kamar sa cinye ta d'an ya,

Haushi ya ishi Amrah, don haka ta mike tareda fita ta bar musu sasan su, don inda sabo duk ta saba da halayen nasu, daga Momy harsu Aunty Sadiya, ita bataga abun daga hankali ba akan wannan mutumin da bai san darajar kowa ba sai kanshi, Idan kagan shi yana magana su Abba ne ko Ummin ta,
Hajjo ta samu zaune tana lazami,saida takai karshe tace " toh Allah yayi an leko ni Y'ar ganin dama, keda Naziru ai sai Hakuri, dariya tayi harda kyakyatawa domin tasan tun tasowar ta Idan kana so kaga fushin shi toh ka jira hajjo ta Kira sunan shi. "Hajjo ina rama ta? " tana Masai ai yanzu, wayace kiki zuwa tun dazu?sai ki jira Idan iyayen ki sunzo na hada musu tasu sai kici. Bata wani saki jiki sosai da zama sashen ba gudun kar ya dawo suma hadu,

Koda su Abba suka dawo suka hadu duka a babban falon gidan bashi a wurin sai Su kamal da ya kabir kannin shi, karfe tara ta gudu gefen Mami tayi kwanciyar ta, itada Farha suka bar Nimrah a gefen Hajjo.
Kwance suke suna hirar school itada Farha, ta juyo tareda Kallon ta tace, " kinsan y'anda kike yi akan yaya NAZIR yafi. "Why yau kike ganin dai dai nakeyi?
"Saboda Akwai kura, waincan mahaukatan su uku a daki daya ace suna hauka akan mutum daya, bai kuma san ma sunayi ba. "Ya rage nasu ai banda wannan lokacin. "Amma Amrah me yasa kike wana ya kamal ne ko dazu ina kallon y'anda duk hankalin shi yaje kanki a falon Abba ke kuma kin share shi, please help my brother. Wani irin kallo ta watsa mata, " kema kina nuna son kai, me yasa kike son ya kamal bayan Ya NAZIR ma yayan ki ne? " no shima ina son shi sai dai sakin fuskar ya kamal yasa muke shiri. " mubar wannan zancen good night. Ta juya mata baya batareda tana jin bacci ba kuma ta rasa dalilin rashin jin baccin,

Wasa wasa sun kwashe sati biyu a sokoto suna shan hutu Wanda saura sati biyu su koma school saboda saura sati daya hutun nasu ya kare, ta mugun 'ka'gara ta koma school saboda tayi mugun takura this time, duk don gudun haduwar ta dashi,
Wanda shikuma yayi busy wajen shirya lafiyayyar walimar samun lambar yabo na matsayin shi na kwararren matukin jirgin na sojan sama, kusan kullum suna harabar gidan shida zugar abokan shi domin Allah yayi shi mai jama'a, ne sosai Allah yayi shi mai farin jini a duk inda yake.

Sai shirye shirye akeyi har a cikin gidan, tana kwance tana nazarin biology book dinta su Nimrah suka shigo da kaya a manyan ledodi, zubewa sukayi akan gadon da take kai, " ga dunkunan mu da Yaya Nazir ya mana na walima. Wani irin kallo ta watsa musu kafin tace " hope bani a ciki? "Idan muncire namu zaki Iya daukar naki kimayar mai ai kinsan sashin shi ko.
Tana Kallon su suna daga fitinannun materials din da sunji kudi da kuma lafiyayyan dinki, harda takalmin su da jakun kuna y'an waje, Mami ce ta shigo tareda cewa " kowa ya gwada nashi Idan baiyi ba a mayarwa tailor ya gyara, Amrah kinji, takalmi dai kowa size din shine.
" toh Mami mungode. " aa ku godewa yayan ku bani ba. Tafita, Amrah ta ture na hannun ta, doguwar rigace hannun ta net dauke da fulawoyi a jiki, material din navyblue, ya hadu yana shining da walwali, sai kodawa sukeyi tareda planing y'anda zasu shirya gobe, " nifa ba wani lalle ko kitso da zanyi sai kace taron Aure, ya cika bidi'a. " yafa isheki malama ke komai sai kinyi complain,Farha ta fada, Nimrah tace " ki...


Read / Download NAMIJIN DUNIYA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album