Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

AJININSA YAKE Book 2 Complete Hausa Novel Document by AJININSA YAKE Book 2


AJININSA YAKE Book 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 24541



AJININSA YAKE Book 2

Reading Time: 2 Hours

Added On: 06, Feb 2025

Author: Zulaihat Sani Kagara ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 120.23 kb

File Type: txt

Views: 138+

Download: 125+

Last download: 16 hours ago

Description/Story: Ajininsa yake 2-01
Posted by ANaM Dorayi on 11:39 PM, 11-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.
.Gaba daya tsarguwa ta kama shi, dole ya sake
kallonta, ya kirkiro murmushin karfin hali yace "
an dawo lafiya? tace "lafiya lau" shiru ya sake yi
yana tunanin me kuma zai sake cewa? ji yayi tace
" Ya wasan Polo? ya dan dube ta ya amsa, "
muna dan tabawa." Abba ya ce yayi sabon Jah-
Jah, shine ya-ce har Yakubu ya tsufa ne? yayi
dan Murmushi yace ai komai lokaci ne, mu ma
wata rana daina yayin mu za'a yi." ta ce "Gaskiya
ne. To ya antin tawa? Ya amsa "Tana gaishe ki."
"Ina amssawa." Tayi shiru kamar yadda shima bai
kara cewa komai ba. Wayar sa ta hau ruri, ya
jawo ta ya duba. Nan da nan ya dauka, "Hurul
aini." Da sauri ta daga ido ta dube shi yayin da
ya ci gaba da fadi" An dawo school din ne? Ta ce
na dawo, to yaya? Ya-ce "Muna tare da ita." "Ban
yarda ba". Ya ce kin san ba zan miki karya ba. Shi
yasa ma tun jiyan na kira ki na gaya miki." Ta ce
in da gaske ne, ban ita mu gaisa.' Kai tsaye ya
dubi Nusaiba, ko dama shi take kallo, kuma sai
taji kamar kishi zai kamata. Mika mata wayan
yayi ya ce "ga Zarah." Tana yar fara'a ta
amsa,............ Tayi mata sallama, haka kawai ita
ma taji kishin ya dirar mata, Ta daure ta amsa
sallamar, Nusaiba tace 'Ya school? Ta amsa,
"Lafiya lau, Kin ga Maigidan namu ko? Tayi dan
Murmushi, Ta ce "Na gan shi" Ta ce Zaki sha
surutu har sai kin gaji, ta dan saci kallonsa, don
ita bata ji surutun ba, Hankalinshi bashi kanta,
shi dayar wayar ma yake faman latsawa, tana
kallonsa ta ce "Yarima kam bakunta na
damunsa." Shi yasa ya dubeta ya tabbatar da shi
su ke, Ta janye idonta a hankali, tana mai
bayyanar da murmushi. Shi kuwa takaici ne ya
tokare wuyansa. " Wane shisshigi kuma Zarah ke
yi? ya tambayi kansa, wani asirtaccen tsaki yayi,
ya dauke kai, Nusaiba da Zarah kam hira ce ke
neman gocewa, basu ma san lokacin da
zukatansu suka saba da juna ba, kawai ji suke
sun amince da juna har suna dokin ganin junan
su.Domin a halin yanzu Nusaiba ke fadin,"To
yaushe za ki zo? Kodayake ni ce k'arama, ni ya
kamata in fara zuwa." Zarah ta ce,"Yanzu na ji
magana, to yaushe za ki zo? Ta ce,"Ki saurare ni
zuwa karshen satin nan, ki turo min lambarki, ni
ma zan turo tawa." Ta amsa, "O.K, zan turo miki.
Bari in bar ki da ogan, kar in yi laifi." Tana
dariya, ta ce,"Tsaya in mika masa ku yi sallama."
Haushi Zarah ta ba shi, don haka tana mika
masa wayar, ya kashe, ya zira ta gaban aljihu.
Kashewa tayi?" Ta tambaya. Ya ce,"Uhm......... Ta
ce,"Anti na kenan. Da ji za ta yi kirki." Ya ce
,"Sosai take da kirki kuma tana da halaye masu
yawa wadanda kullum suke kara min son ta.
Iyayen ta talakawa ne iri na. Sai dai Allah yayi
mata baiwar da bai yi wa kowane mahaluki ba.
ZARAH, sunanta kadai ya kan sanya ni nishadi,
ballantana ita kan ta. Kar fa ki ji wani abu a rai,
ba wai ina fad'i bane, saboda wata manufa. No,
ina son ki sani ne, ba kowace mace zata yi abin
da Zarah tayi ba. Tun muna yara mu ke tare, sai
da biki ya zo gaf, sannan aka ce ga wata a hada
2, ina nufin kishiya, ko ke ce yaya za ki ji? Gaba
daya jikin ta yayi la'asar, ba don komai ba, sai
don tausayin Zarah d maganganun Naseer suka
sanya ta. A take nan ta ji kaunar Zarah na shiga
jikin ta. Tabbas Zarah tayi bajinta, kuma abar
tafa mata ce. Ta sauke numfashi. "Gaskiya ne, ko
ni ta burge ni, sannan bayanin ka a yanzu ya
sanya min kaunar ta cikin raina. Hakuri babban
Jari ne, kuma ita rayuwar duniya mai karewa ce,
shi yasa ni ma ban ga dalilin daukan ta da zafi
ba. Tsakanin mai kudi da talaka kuwa, wata
hikima ce irin ta Ubangiji. Ya kuma halicce mu ne
saboda mu taimakawa junan mu. Da ya so, da
gaba daya masu kudi zai hallice mu. Haka ku ma
daya ga dama, da sai ya aje mu dukkanmu a
talakawa. Mai hankali idan ya natsu, zai gane
dimbin dalilan da su ka sa Ubangiji ya bambance
ababen halitarsa. Saboda haka kar ka yi tunanin
komai akan zama na tare da Zaraha, wai don ni
na fito gidan wadata. Insha-Allahu za ka same ni
da irin halayen da ka ke so." Yayi dan shiru,
tunanin sa Nusaiba na da kalamai, sai dai ba su
wani girgiza shi ba, saboda ya saba jin kyawawan
lafuza a wajen Zarar sa A takaice ma dai ji yayi
kamar tana son tayi gasa da Zarah, don ya ce ta
ji yana yabon ta. Ya girgiza kai, ya ce,"Shi kenan."
Ya duba agogon hannunsa, ya ci gaba,"Bari mu yi
sallah ko? Karfe daya ta gota." Yana rufe baki,
ana kwala kiran sallah. Ta mike ta ce,"Za ku shiga
masallaci ne? Ya ce,"Sosai kuwa." Ta fice ta bar
shi yana zancan zuci, "Ka ji 'ya da a dakin ki za
mu yi sallar? Ya dan ja tsaki, sannan shi ma ya
fita ta kofar da suka shigo. Ita kuwa wajen Sageer
ta nufa, ta kira shi ya fito, ya iske Naseer a waje,
suka tafi masallaci. Nusaiba na sallamewa sallar.
Wayar ta ke ruri? Ta dauko ta, ta duba Kausar
ce, ta dauka tasa wa kunnen ta,"Ban son
wulakanci, ba za ki zo din bane? Ta ce,"Gaskiya
zai yi wuya. Wallahi lakcas sun yi yawa yau. Ko
wacce kuma na da muhinmanci da sai in tsero.
Sorryy kwata, ki ce da Jah-Jah gaisuwa na ke.:"
Ta dan ta6e baki, ta ce,"Ban fad'i." "Ai na ce
sorry. Ke ma kin san sbd karatu ne kawai.." Ta
ce,"Shi kenan, ni zan zo gobe, idan kin dawo ki
kira ni." "O.K Matar Jah-Jah. Tana murmushi ta
ce,"Kya ji da shi." Suka yi sallama. Kowa ya aje
waya.
Madubi ta nufa ta sake gyara fuskarta da daurin
dan kwalinta, ta suri waya ta bar dakin. Mariya
ta kira, ta tambaye ta maganar abinci, ta ce duk
ta shirya su a can falon. Kai tsaye can ta wuce.
Takalman su Naseer na kofar falon, don haka ta
shiga da sallama. Duk suka amsa. Kai tsaye wajen
abinci ta wuce ta bubbude kulolin, ta ce kowa ya
bi abinda yake so. Sageer ta za6i Frie rice, shi
kuwa dan gogon da kyar ya cusa lafiyyan
(Coleslaw). Sun dan ta6a hira zuwa karfe 3,
Naseer ya ce tafiya za su yi. Sageer ya ba su wuri
su yi sallama. Tsawon minti 2, bai ce da ita komai
ba, sai ta mike ta ce bari ta kawo masa sakon
Zarah. Shi ma ya tashi ya ce ta same shi a mota.
Suna tsaye jikin mota, ta fito da manyan
jakunkunan leda guda 2, cike suke da kayan
shafe-shafen mata. Ta mika wa Sageer ta
ce,"Leda 1 Zarah, 1 ta amaryar ka, don ni ban
yarda ba da ka ce babu ita. Dariya yake yana
fadin me zan 6oye miki? Kin san Allah babu ita a
halin yanzu sai an kammala karatu. Kin san taura
2 basa taunuwa a lokaci guda." Ta ce,"Gaskiya ne,
to mun gode, amma ki rike wannan, tunda dai
yanzu babu ita." Ta ce,"To lodawa Antina duka."
Ya ce,"Lallai Zarah ta gode. Allah ya saka da
alkhairi." Naseer ya dube ta tsakar ido, ya
ce,"Kayan nan sun yi yawa da kin rage." Ta dan
kada kai, ta ce,"Ba su yi ba, kuma ai Antina na ce
akai ma wa ko? Ya ce,"Shi kenan ta gode. Sai
wani lokaci." Ta ce,"Ni ma na gode, a gaida kowa
da kowa. Za su ji." Ya fadi yana shiga mota. Tuni
Sageer ke mazaunin direba. Ya tada mota. Mai
gadi ya bude get, suka fice, sannan ta wuce
gida." A falon sama ta iske Umminta. Gefen ta, ta
zauna ta ce "Wash! Na gaji." Aikin me ki ka yi? Ta
ce,"Haka kawai na ke jin kasala." Sun tafi ne?
"Eh, sun tafi yanzu." Ta dan yi shiru, kafin ta ce,"
O.k." Ta dan dafa kan ta." Ko dai yunwa ki ke ji?
Fuska yamutse ta amsa. "Wallahi kuwa. Don ko
dan ruwa ban kurba ba." Ta ce,"To maza tashi ki
je ki sami abinda za ki ci." Ta mike ta wuce, tana
jan takalma, da gani ta gajin da gaske. Umminta
tayi kasake, tana tunanin ya dace ace Naseer ya
shigo ya gaishe ta. Da ta rasa dalili, sai ta watsar
da zancan, ta kama abinda ke gaban ta.
Sageer ya ja na dogon salati. Da sauri ya dube
shi, "Menene? Ya ce," Zuwan duk bai da amfani."
Da aka yi me? Ya ce,"Ka san tamkar a kan kaya
na ke zaune cikin gidan nan, maimakon ka ce
min mu je mu gaida Hajiya....... Shi ma salatin ya
dauka ya dire,"Girman Allah na mance, abinka
da ba sabun ba. Gaskiya ba'a kyauta ba. Kuma
anyi abin kunya. Yanzu ka kira wayar Nusaiba, ka
ce ta ba Hajiya hakuri, mantawa mu ka yi. Ai
kowa yasan ajizani na Dan-Adam." Naseer ya ja
tsaki,"Zancan banza. Ni ina da lambar ta ne? Ba
ka amsa ba? Ya tambaya a firgice. Wani tsakin ya
sake yi. Sageer ya hau fada.Ka na ta tsaki,
wannan ai wulakanci ne, ka ma nuna zahiri ba ka
damu da ita ba, ai ko da ba'a sai ka ce ta
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download AJININSA YAKE Book 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album