Join Our WhatsApp Group

ALWASHI Complete Hausa Novel Document by ALWASHI


ALWASHI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 83629



ALWASHI

Reading Time: 6 Hours

Added On: 21, Jul 2023

Author: Ummi Aisha ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : HASKE WRITERS ASSO

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 503.4 kb

File Type: txt

Views: 1964+

Download: 985+

Last download: 4 days ago

Description/Story: ๏ปฟ[6:37PM, 2/1/2018] ~Maman_twins๐Ÿ’ž๐Ÿ˜๐ŸŒน: ยฎ *_HASKE WRITERS ASSO_*
( _Home of expert & perfect writers_)


*ALWASHI....!*๐Ÿ’
_(Labarin Hafsat)_


_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_



_Dedicated to MISS XOXO_


_Sakon fatan alkhairi gareki k'anwata Feedohm marubuciyar ZAN RAYU DAKE,ina yimiki fatan alkhairi aduk inda kike, indeed i have no words to thank u, am deeply grateful....! The first page is belong 2 u dear!_



DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI.



*1*



****Gidane na marayu mai d'auke da tangamemen gate sannan ga katanga babba zagaye da gidan wanda tsawonta ma abin kallone,haka shima cikin gidan yake wawakeken gaske mai dauke da gine gine masu yawa wadanda suka hadar da ofisoshin ma'aikatan gidan da kuma wurin kwanan marayun da kuma duk wani abu na bukatarsu,

Duk inda ka hanga yarane zaune sunyi group group, masu wasa nayi sannan masu hira sunayi yayinda wasu kuma suke yan aikace aikacensu na yau da kullum,

Wasu yanmata ne guda biyu acan gefe su kadai wadanda akalla shekarunsu zasu kai shekaru 23,

Daya daga cikinsu tayi tagumi tana sanye da kodadden hijabi da wata kodaddiyar atamfa ajikinta haka itama dayar kayan jikinta duk sun gajiya,

"Hafsat wai wannan tagumin da kikayi na menene? Yau naga gaba daya yanayin naki sai ahankali tamkar wata marar lafiya..." Daya daga cikin yanmatan tafada bayan ta dafa kawar tata,

"Amina wallahi lafiyata kalau kawai dai ina tunanin makomar rayuwarmu ne acikin gidan nan, ba kasafai mutane suka fiya kulawa damu ba, hatta gwamnati tayi watsi da rayuwarmu sai lokaci zuwa lokaci take tunawa damu..." Wadda aka kira da suna hafsat tayi magana cikin karyewar zuciya,

"Amma dai hafsat wannan ai ba bakon abu bane awajenmu duba da tsawon shekarun da muka diba acikin wannan gida gashi har yau Allah bai kawo wanda zai daukemu ya fitar damu daga cikin gidan nanba ko muma mazamo yaya kamar kowa.."


"Amina kenan tayaya zamu zamo yaya kamar kowa alhalin babu wanda yasan asalinmu, Allah ne kadai yasan tushenmu dan haka kinga maganar amaida mu 'yaya ma bata taso ba.."

"Hmmm babu komai koma dai yayane Allah yana tare damu..."

"Kai yanmatan nan kutaso kuzo muje.." Muryar daya daga cikin ma'aikatan gidan marayun ta ratsa kunnuwansu wanda hakane yayi sanadiyyar katse musu hirar da suke yi,

Mikewa sukayi suka karasa inda take,

"Yawwa kuzo muje, wannan bawan Allahn ne yauma yakawo muku agaji kamar yadda yasaba..."

Batare da sunyi magana ba suka bi bayanta, gaba daya an tattaro yaran gidan antarasu wuri guda gefe kuma wata babbar motace anata sauke kaya daga kanta wadanda suka hadar da buhunhunan kayan abinci da tufafi,

Wuri amina da hafsat suka samu suka tsaya suna kallon irin uba uban kayan da ake saukewa,

Kowacce acikinsu addu'a take acikin zuciyarta kan Allah yasakawa koma wanene wannan mutumin da alkhairi domin yajima yana yi musu hidima,

Kayan da aka sauke daga kan wannan katuwar motar ba dan kadan bane domin bayan kayan abinci da kayan sawa harda barguna da katifu,

Suna nan zaune sunyi tsuru suna ganin tulin kayan da aka kawo musu har aka kammala sauke kayan nan wakilin wanda yabada kayan akawo ya mike yadanyi jawabi,


_Kamar yadda muka sani kuma muka saba, wannan bawan Allah Wanda mukafi sani da suna baya goya marayu akoda yaushe yana iya kokarinsa wurin ganin ya kyautatawa rayuwar marayu sannan kuma ya sadaukar da dukiyarsa wurin taimakon musulunci, kamar yadda nadade ina fada muku shi wannan bawan Allah matashine ba tsoho ba kawai dai Allah ne ya albarkaceshi da halin manya dan haka muyita yimasa addu'a akan Allah ya albarkaci rayuwarsa da dukiyarsa da kuma iyayensa...._

"Amin..."

Dukkan jama'ar dake wurin suka amsa cikin farin ciki domin wannan bawan Allah ba karamin taimako yake yiba saboda kusan agarin ma shine lamba daya wurin taimakawa rayuwar marayu.

Saida aka gama rabawa marayun kayayyakin da aka kawo musu akan idon wakilin wannan bawan Allahn dake basu gudun mawa wanda suka dade da rada masa suna da baya goya marayu,bayan gama rabon kayan tsaf sannan wakilin baya goya marayu yatafi, sukuma yaran kowa ya kinkimi kayanshi ya nufi wurinda zai adana su, haka suke gudanar da rayuwarsu cikin wannan gida wanda a lokuta mafiya yawa sukan shafe sama da watanni biyu batare da sun samu wani tallafi ba indai ba wannan bawan Allahn ne ya aiko musu ba gashi kuma duk wannan hidimar da yake yi musu basu taba ganinsa ba balle har su gane kamanninsa.


***

Kamar bazai taka k'asa ba haka yake tafiya, sanye yake cikin jar t shirt mai dogon hannu yasha d'amara da jar belt wadda ke d'amare ajikin bakin trouser din dake jikinsa, duk da wai ahakan sauri yake amma baisashi sauya salon tafiyar tashi ba,bak'in face din dake idonshi yadan gyara bayan ya maida hankalinsa kan agogon azurfar dake d'aure a tsintsiyar hannunshi, kamar koda yaushe fuskarshi babu alamun fara'a atare da ita,

K'ofar da zata sadashi da falon mahaifiyarshi ya bude ya shiga fuskar nan kamar zaice wayyo Allah dan tsananin fushi,

Ganin babu kowa aciki yasashi kara yin gaba, awani tsararren falo wanda aka tanada musamman domin hutawa ya isketa, tana zaune saman kujera daga ganinta bazata haura shekaru 45 ba aduniya, farace jajur mai dan jiki, tana sanye da wani leshi mai tsadar gaske, wuyanta da hannuwanta gamida kunnenta duk gwala gwalai ne sai walwali suke, haka yan yatsun hannunta ma duk sunsha zubunan gold,gefenta kuma wata yar matashiyar budurwa ce wacce zata kai shekaru 23 tana kwance tayi matashi da cinyar matar,

Sallama yayi wadda ba lallai su iya jiba domin aciki ciki yayita,

Dukkansu hankalinsu yana ga drama din da suke kallo atashar tauraron dan adam wanda har saida ya zauna sannan suka farga dashi.......



*_Ummi Shatu_*๐Ÿ‘Œ๐Ÿป
[6:37PM, 2/1/2018] ~Maman_twins๐Ÿ’ž๐Ÿ˜๐ŸŒน: ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_



*ALWASHI.....!*
๐Ÿ’
_(Labarin Hafsat)_







*_NA_*



*_UMMI A'ISHA_*







_Dedicated to Miss Xoxo_







*2*







***Fuska cikeda annashuwa mahaifiyar tashi ta kalleshi cikin fara,a yayin da shikuma sai faman cijar lebenshi nakasa yake yi fuska babu annuri,



"Yusleem.... Har anshigo?"



Mahaifiyar tashi ta tambayeshi da fara,a akan fuskarta,



Saida yasake hade rai idanuwansa na bisa screen din hadaddiyar wayar dake hannunshi sannan ya amsata dakyar,



"Ehh Mami..."



Wata fara,ar tasake yi sannan tayi magana,



"Nima dama tun dazu nake jiranka kazo saboda ina son ka sama mana visa nida surayya zuwa kasar chairo zan kaita medical check up..."



Shiru yayi batare da ya amsa ba yaci gaba da latsa wayarshi, idan da sabo to kowa nagidan ya saba da wannan mummunar dabi'ar tashi tayin shiru idan ana yimasa magana, ko mahaifiyarshi ce tayi masa magana sai yaga dama zai amsa gashi da shegen girman kan tsiya kamar shi yafi kowa,



Saida ya dauki fiyeda mintuna goma sannan ya daga manyan idanuwanshi wadanda suke tamkar kwai domin round eyes gareshi,surayya kanwarshi ya kalla wacce ke kwance akan cinyar mami tana sanye da English wears riga da skirt bakake kanta babu dan kwali,



Baiyi magana ba yasake mayar da kanshi kan screen din wayarshi,



"Mami...am dama ina son infada miki.."



Tattaro hankalinta gaba daya Mami tayi zuwa gareshi,



"To yusleem ina jinka.."



"Mami nasaki khadija yau da safe.."



Zaro idanuwa Mami tayi gamida dafe kirji, surayya kuwa dake kwance akan cinyarta zunbur tayi ta mike zaune, dukkaninsu kallonshi suke cikeda tuhuma gamida zargi iri iri,



"Nashiga uku ni siyama, innalillahi wa inna ilaihir raji'un...." Mami tafada tana tafa hannuwanta,



"Haba yusleem wai kai wanne irin mutum ne? Anya kuwa ba aljana ce ta aureka ba? Karfa ka manta ko watanni uku cikakke ba ayiba da bikinku kaida khadija amma shine yau kazo kake fada min wai ka saketa?



Yusleem mai ka dauki aure ne? Ka daukeshi ne a matsayin wasa, ko kuma abin wasa ko wasan yara?



Yusleem duk fa wannan dukiyar da kake ganin kana da ita bazata taba iya siya maka darajar da aure zai siya maka ba...!"



Dan jan numfashi tayi sannan ta dora,



"Kana yaronka dakai amma acikin shekaru biyar kayi aure sama da guda goma, haba yusleem wannan wacce irin mummunar dabi'a ce, ka mayar da sakin aure ba komaiba,saki da Allah ma baya sonsa amma kai kuma shine ka mayar tamkar sana,arka,



To agaskiya nidai nagama gajiya da wannan halin naka na auri saki, babu damar ka zauna da mace na koda shekara dayane?"



"Gaskiya Yaya bamuji dadin wannan labarin ba, yanzu anty khadijan ma ka saketa?"



Surayya ta fada idonta dauke da kwalla,ko kallonta baiyi ba bare tasa ran zai bata amsa,



Fada mami tasoma balbala masa ta inda take shiga bata nan take fitaba,



"Ni narasa gane kan wannan hali naka yusleem, kwata kwata baka dauki aure da daraja ba, sam baka son zama da mace, wannan wacce irin rayuwa ce,



Kuma bafa kowa kake watsawa kasa a idoba face ni tunda nice nake aura maka matan, yanzu abinda kayi ka kyauta kenan?"



Dan kishingida yayi kadan ya tsurawa wayarshi ido batare da yace komai ba,



"Dakai nake magana kayi min shiru, ka fada min dalilinka na auri saki, akalla ba a kasaru ba yusleem ka auri mata dai dai dai har guda goma sha..., baka da lafiya ne ko yaya?"



Saida ya dan shafi sajen fuskarshi sannan ya kalli mami,



"Mami ni lafiyata kalau sannan dama ai ban taba cewa ga wacce nake so ba, duk matan da nake aure kece kike samo min su ki aura min.."



"Wacce irin magana kake fada min yusleem? Dan bakai kagansu kana soba shikenan bazaka zauna dasu ba? Wannan dalilinne yasa ka dauki auri saki ba abakin komai ba?



Sau nawa ina baka dama domin ka fito da matar da kake so in aura maka amma sai kayi biris da maganar, kuma ni ai aganina nagama yimaka duk wani gata wanda yadace ace uwa tayiwa danta domin na nemo maka mata yan mutunci, yan asali, masu aji wadanda suka dace dakai amma daga karshe duk dai labarin iri dayane cewa ka sakesu, yanzu kaduba kaga yarinyar nan khadija da ka saketa ka rabu da ita, yarinya ce mai hakuri mai nagarta mai sanin ya kamata, yarinya kyakkyawa yar asali yar mutunci yar kawata hajiya fa'iza,ko wata biyar ba ayiba da bikinku amma kasaketa..."



Dan tsagaitawa mami tayi tana dubanshi cikeda bacin rai, har tsawon mintuna biyar babu wanda yasake magana acikinsu,



"Yusleem wai da me kake takama ne da har kadauki auri saki ba abakin komai ba?



Idan dan kyawun dakake dashi ne yasaka kake yin haka to ya kamata fa kasani akwai wadanda suka zartaka kyau amma basa yin haka,



Idan kuma dan arzikin dakake dashi ne to kasani akwai big millionaires suna nan ba irinkaba young millionaire ba kuma basa aikata wannan wulakancin dakake yi,



Inkuma kuruciyar da kake tare da itane yasaka yin wannan cin mutuncin to wallahi ka gaggauta farkawa daga wannan dogon baccin da kakeyi domin akullum shekarunka sake yawa suke bawai raguwa ba.."



Shiru mami tayi cikeda bacin rai tana huci saboda babatun da tagama yanzu,



Mikewa yayi sannan yayi magana ahankali,kamar mai ciwon baki yace,


"Kiyi hakuri mami.."



Ko amsa masa batayi ba yasaka kai yafice daga cikin falon, nan mami da surayya suka rakashi da idanu....




_*Ummi Shatu*_๐Ÿ‘Œ๐Ÿป
[6:37PM, 2/1/2018] ~Maman_twins๐Ÿ’ž๐Ÿ˜๐ŸŒน: ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*

_(Home of expert & perfect writers)_







*ALWASHI.......!*๐Ÿ’

_(Labarin Hafsat)_







*_NA_*



_*UMMI A'ISHA*_







_Dedicated to Miss Xoxo_




_Fatan alkhairi ga takwarar Nana Hafsat wato Hafsat Rano, this page tukwici ne agareki...!_





*3*







***Dafe goshi mami tayi cikeda damuwa bayan fitar yusleem,nan tayi shiru tana jin wani irin bacin rai yana ziyartar zuciyarta,



Sunfi mintuna biyar itada surayya batare da wani acikinsu ya iya yin koda motsi ba,
Mami ce tayi karfin yin magana cikeda damuwa,


"Narasa gane kan yaron nan, agaskiya abin nasa yawuce tunani, yawuce hankali, gaba daya zagayen jahar nan harma da mak'ota kowa yasanshi awurin auri saki, duk yabi yabatawa kansa suna..."



"Mami wallahi nidai ban yarda yaya yusleem lafiyarsa kalau ba, duk inda akaje aka dawo acikin abubuwa guda uku to abu daya yana damunsa dole,



Kodai aljana ce ta aureshi, ko kuma yana shaye shayen kwayoyi aboye ko kuma kwakwalwarsa ta dan tabu batare da mun saniba..., wallahi mami ki kaishi adubashi" surayya ta kareshi zancen hawaye yana bin kuncinta,



Jinjina kai mami tashiga yi tana kallon surayya amma sai dai kafin takai ga yin magana tuni karar wayarta ta cika musu kunnuwa nan mami ta dauki wayar jikinta asanyaye saboda ganin sunan wanda ke kiran,



Jiki asanyaye mami ta kalli surayya,



"Kinga ni ko? Hajiya fa'iza ce ke kirana mahaifiyar khadija, yanzu ban san me zan fada mataba, ban san irin fushin da take cikiba.."



Kiranne yakatse wani yasake shigowa,



"Mami ki daga kawai.." Surayya tace da ita bayan ta tsura mata ido,



"Hajiya siyama ina fata dai kinji cin mutuncin da danki yayi mana, koda yake nasanma da saninki zai aikata hakan,yayiwa khadija saki na wulakanci batare da laifin komai ba..." Jin abinda mahaifiyar khadija ke fadi yasa mami saurin katseta domin bata son amintakarsu da kawancensu yabaci ta wannan silar,



"Hajiya fa'iza dan Allah kiyi hakuri kijirani zanzo gidan, dan Allah karki yi fushi akan wannan abun da yafaru, kisani khadija yatace kuma bata da wani banbanci da yayan da nahaifa..."



"Ai hajiya siyama magana tariga da takare Allah yasa haka shine yafi alkhairi kawai kuma dama halin danki ne auri saki tunda ba akan khadija yafara ba, ita khadija kaddara ce kawai ta hauta har takaita ga aurensa..."



K'ittt mami taji hajiya fa'iza takashe wayarta bayan tagama wadannan maganganu,





"Yusleem bai kyauta minba, akansa zumuncinmu da muka dade muna yi da hajiya fa'iza yana neman baci.."



"Ai mami nafada miki wallahi acikin abubuwa guda ukun nan da na zayyano abaya akwai daya aciki wanda ke damunsa"



"Hakane surayya nima nayarda da batunki, indai kuwa hakane to yazama dole inbincike shi sosai har ingano matsalarsa..."



Shuru kowannensu yasake yi har na tsawon wani lokaci, surayya ce tafara mikewa ta nufi bedroom dinta ganin haka yasa mami itama tashi ta shiga nata bedroom din, mintuna kadan tafito cikin sabuwar shiga wacce tafi ta da,



Wani jan swiss lace ta dauro tayafa babban mayafi kalarshi,hannunta rikeda handbag dinta ta leka bedroom din surayya, kwance ta isketa da wayarta ahannu suna yin video call itada Abdul tana fada masa sakin da yusleem yayiwa khadija,



"Yawwa yaya Abdul ga mami..."



Karbar wayar mamin tayi tana kallon Abdul din,



"Mami haka yaya yasake karo wulakanci? Yanzu sury take fada min wai yasaki khadija yau.."



Ajiyar zuciya mami ta sauke,



"Abdul nikaina yanzu haka ban san da wacce kalma zanyi amfani da itaba wurin bawa mahaifiyar khadija hakuri duba da irin wulakancin da yayanku yayi, auren da ko watanni biyar ba ayiba amma wai yau har anyi angama..."



"Ni mami narasa meye matsalar...


Read / Download ALWASHI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

2 Comments On ALWASHI
avatar
aliyu-1-5-2

4 months ago

Reply

I appreciate it

avatar
aliyu-1-5-2

4 months ago

Reply

I appreciate it

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album