Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_


*KAMAR DA WASA....!*


_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_


_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI._



*1*


"Masu sauraro kamar kullum anan shirin namu zai dasa aya ayau kun dai ji mun tattauna akan wata babbar matsala wato ta yadda zakaga saurayi da budurwa sun kwashe shekaru suna gudanar da soyayya amma abin haushi arabu batare da anyi aureba shin laifin waye? Mazan ko matan? kafin inyi sallama daku ina mai janyo hankalin masoya da arike amana, gaskiya da kuma kulawa sannan aguji karya da yaudara domin hakan ba abune mai kyau ba sannan daya daga cikinsu yana raunata soyayya kuma ya illatata, anan zanyi sallama daku sai Allah yakaimu sati nagaba inda zaku jini acikin wani sabon shirin naku mai farin jini wato *Sakon na masoya ne...* kamar kullum nice taku mai gabatar da shirin wato *BILKISU LUKMAN ALIYU* Nabarku lafiya...."

Ahankali yake zare earpiece din dake kunnenshi sakamakon jin wakar _Sulken so...._ ta maye gurbin zazzakar muryarta, cikeda takaici ya kifa kansa asaman keken dinkin da yake zaune akai yana dinka wata kyakkyawar doguwar riga ta mata, tunani yake aransa yanzufa shikenan bazai sake jin muryarta ba sai wani satin indai ba shirye shiryenta na baya wadanda yayi recording zaiji ba domin hatta wannan wanda ta gabatar ayau ma yayi recording dinshi yana nan ajiye cikin wayarshi. Babu zato babu tsammani yaji wani abu saman sumarshi mai kamada almakashi, hannu yasa domin yakamo abin amma yaji anjanye ahankali yabude lumsassun idanuwanshi yatashi zaune, kamar yadda yayi zato husna yagani tsaye sai faman yi masa murmushi take, maimakon ya mayar mata da martanin murmushin da take yimasa sai ya daure fuska kamar ta kawo masa sakon mutuwa.

Bata damuba tabawa kanta masauki da wata kujerar roba wadda ke ajiye agaban keken dinkinshi, bata damu da yanda sauran abokan aikinshi wadanda ke zaune akan kekunansu suna gudanar da ayyukansu yanda zasu dauketa ba domin idan da sabo tasaba, zama tayi ta tallafe kumatunta da hannuwanta tana kallonshi kamar yadda yayi sai dai shi sam ba ita yake kallo ba domin yafada duniyar tunani.

"Prince..., Prince....ina dinkin yarinyar nan?"

Sai lokacin yadawo hayyacinsa sakamakon maganar tj abokin aikinsa da ta daki dodon kunnuwansa, gefenshi ya duba ya ciro wasu kaya acikin leda ya mika masa,

"Wai meke damunka fahad?"

Kallonta yayi adage sannan cikin rashin kulawa yace,

"Mekika gani fa?"

"To ai naganka ne kamar wani marar lafiya" tayi maganar cikin kalar tausayi,

"Lafiya ta lau..." Yabata amsa yana kokarin mikewa tsaye, wata leda ta mika masa tana langwabe kai,

"Please my prince ga uniform dina ka dinka min kaji"

Batare da ya kalleta ba ya karba ya jefa cikin wani kwali dake girke gefen kekensa,wani food flask dan madaidaici mai kyau ta sake mika masa,

"Ga abinci na kawo maka"

Karba yayi ya dora saman keken dinkinsa sannan ahankali kamar wanda tayiwa dole ya furta,

"Thank u"

Jingina tayi tana kallonshi shi kuma yana kallon wayarshi, babu abinda kake ji sai karar keken dinki wanda sauran abokan aikinshi keta faman aiki. Scissors din da ke ajiye kan kekenshi ta dauka ahankali ta kai kan tararriyar sumarshi,

"Inyi maka aski?"

Sake daure fuskarshi yayi yakai hannu ya doke almakashin,

"Kibari bana so, nafada miki bana son wasan banza"

Murmushi tayi tana sunkuyar da kanta,

"To kayi hakuri"

Baice mata komai ba yatashi da niyyar fita nan itama ta mike tana kallonshi ganin haka yasa shi yafasa fitar yawuce can wani lungu kusa da wata drawer ya kwanta, duk da tana son su fita tare amma haka tayi hakuri tawuce tatafi ba don taso ba.

Yajima kwance awurin yana jin sauran yan shagon sunata gulmarsa shida husna amma bai tanka ba har saida lokacin sallar la'asar yayi sannan yatashi,alwala yayi ya shiga masallaci duk da yana son ganin salim abokinshi amma sai yashare yashiga salla wanda acan din yahadu da salim din.

Yana fitowa daga salla keke napep yatare yanufi gida, atsakar gida ya iske mahaifiyarshi tana wanki koda yakarasa kusa da ita kamar yadda yazata kananan kayanshi take wanke masa.

"Ayiyah wankinne dai?"

Murmushi tayi tajuyo ta kalleshi,

"To ai ba komai nakeyi ba shiyasa nace gara inwanwanke maka sauran kayan ma na hadasu zuwa gobe zan bayar akai awanko maka"

"Godiya nake Ayiyah tah, Allah dai yabar min ke"

"Amin autana, maza kaje ga abincinka can a falo na tanadar maka"

Yunkurawa yayi ya mike daga tsugunnen da yake hakan yayi daidai da fitowar mamu,

"D'an nema kadawo ashe?"

"Hajiya mamu wallahi nadawo, kina daga ciki kenan?"

"Andai ji kunya, gandamemen saurayi dakai amma baka iya wanki ba"

Kafin yayi magana ayiyah tayi caraf ta cafke zancen ta hanyar bawa mamuh amsa,

"Tunda yana da masu yimasa ai ko ya iya bashida amfani"

Wata shewa mamu ta saka tana karasowa inda suke,

"To nidai naga yanda za ayi duk ranar da akayi masa aure"

"Yakuwa za ayi? Matarsa ce zata rinka yimasa"

"Idan ta iya ko?"

"Sai ta koya" inji ayiyah, jan yar karamar kujerar tsugunno mamu tayi ta zauna kusa da ayiyan, shi dai bazai iya cigaba da kallon wannan dramar tasu ba shiyasa yawuce dakin ayiyah fuskarshi shimfide da murmushi domin idan da sabo yasaba ganinsu ahaka kusan tun tasowarsa ahaka yake ganinsu bai taba jinsu suna fada ba kai idan baka saniba baka taba cewa kishiyoyine dan ko yanzun ma da suka gama wannan rahar hira ya jiyosu suna yi kuma da alama wankin mamuh take taya ayiyah. Zama yayi saman daddumar dake shimfide cikin falon yasoma bude kwanukan dake jere reras awurin wanda yasan shi aka tanadarwa domin kullum haka ayiyah keyi masa kamar wani mai gida, funkaso da miyar taushe yagani sai shinkafa da wake da manja da salad sannan ga zubo nan mai sanyi da kankara aciki cikin wani madaidaicin jug, hannun riga ya nade yasoma zuba shinkafa da waken domin kusan abubuwan nan na soye soye irinsu waina, sinasir, funkaso duk ba damunshi sukayi ba dan haka yazage yaci shinkafa da wakensa yayi dam yasha sanyayyen zobonshi daga haka ya mike ya fito,su ayiyah har sun kammala wankin sun fada wani aikin kuma sunayi suna hira shiyasa ma ko ganin fitowarshi basuyi ba, dakinsu ya nufa wanda yake cikin soron dake hanyar kofar gida yabude yashiga daga shi sai yayanshi Abba adakin amma yanzu abban baya nan yana can jami'ar Maiduguri wato unimaid yana karantar computer science dan haka sai shi kadai adakin yanzu, kayan jikinshi yarage yabar gajeren wando kadai bayan ya Kara kofar dakin, kan dundumemiyar katifar dake malale adakin yahau ya kwanta bai kai ga rufe idanuwansa ba yajiyo alamun karar shigar sako cikin wayarshi, akasalance ya mika hannu yadauko wayarshi kirar Galaxy S10,BILKISU shine password din kan wayar tashi nan yabude yasoma duba text din duk da baiyi saving number dinba yagane husna ce domin har ya haddace number dinta saboda yanda take damunsa arana sai ta kirashi akalla sau biyar ko fiyeda haka banda text massages kai idan takira ma taji shiru abune mai sauki yaganta ashagonsu ta biyo sawunshi yarasa gane kan wannan yarinyar gashi ta tsani ta ganshi da wata mace suna ko maganane alhalin kuma shi aikinsa na matane tunda dinkin mata shine sana'arshi. Sakon yabude yasoma karantawa kamar haka... _"Ya fahad yakake, ina fata lafiya kake, abincin yayi dadi?"_ murmushi yayi ya ajiye wayar bayan yasata a silent domin shi sai yanzu ma yatuna da wani abincin da ta kawo masa dazu saboda can yabaroshi ashago bararrajewa yayi saman katifarshi domin yin bacci duk da yasan ayiyah ta hanashi wannan dabi'ar ta baccin yamma amma babu yanda zaiyi ne sakamakon yagaji dayawa gashi ya jima bai samu isasshen bacci ba kullum yana kan keke yana dinki.
***
Murmushi tasaki ahankali wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hakoranta sannan ya bayyanar da kyawawan beautiful point dinta wadanda ke kara kawata kyakkyawar fuskar da Allah yayi mata. Wayar dake makale a kunnenta take jujjuyawa cikeda annashuwa,

"Yes half soul, yanzu dai kabari sai nakoma gidan kawai sai naturo maka...."

Dan Jim tayi tana sauraron abinda yake fada bata kai ga bashi amsaba tamike daga kujerar datake zaune wacce ke rukunin kyawawan kujerun dake zagane cikin zungureren office din wanda ke dauke da kayan alatun more rayuwa banda na'urar sanyaya daki wacce ta cika dakin da sanyi wanda bazai cutar da jikin dan adam ba, jakarta ta dauka wadda take ajiye bisa dogon teburin da ke tsakanin rukunun jerarrun kujerun masu fuskantar juna, hakan yayi daidai da shigowar khulsum kawarta,

"Noorul kalb ga khulsum ta shigo zamu tafi ni ina ganin kawai kabari sai naje gida din kawai sai muyi waya ko?" Batare da khulsum tajiyo amsar da yabata ba taga tayi murmushi sannan ta amsa da,

"Zataji half soul, me too"

Daga haka ta katse wayar tana kallon khulsum,

"Wai har kin kammala voicing din?"

"Tun yaushe, ina can inata jiranki amma najiki shiru ashe kina nan kina soyewa"

Murmushi tayi ta saba jakar hannunta suka doshi kofa domin fita daga office din,

"Nima fa yanzun nan nagama fassara labaran kasuwancin nan kin san yanada wahala shine kuma hamood yakirani,namanta ma yace yana gaisheki"

"Ina amsawa, am yawwa kafin namanta wai ke mekike shirya mana ne abikin nan?"

Juyawa tayi ta kalli khulsum sannan ta harareta,

"Me zan shirya muku kuwa, ko nice amaryar da zakiyi min wannan tambayar? Ban son wulakanci"

Murmushi khulsum tayi ta dafa kafadarta,

"Bakece amarya ba amma ai kece babbar yaya kuma uwar biki kinga kuwa yazama dole kiyi wani abu"

Lumshe idanuwanta tayi sannan ta budesu bayan yanayin fuskarta ya sauya cikin sakannin da basu gaza biyu zuwa ukuba,

"Ni yanzu duk ba wannan ba wallahi abunda ke damuna guda dayane zuwan Grandma dinmu iyallo, yanzu tana zuwa zatabi ta uzzurawa mutum ta daga masa hankali, tun lokacin bikin mamaa take damuna gashi yanzu bikin Hindu da meenah yazo, ni wallahi ji nake kamar inbar gidan sai angama bikin nadawo"

Murmushi khulsum tayi bayan taja ta tsaya kamar yadda taga tayi,

"Labour kema fa da laifinki gaskiya, why not bazaki baiwa hamood dinki damar yafito kuyi aureba tunda kuna son juna? Haba dan Allah, shekara da shekaru kuna abu daya sai kace wasu wannan..., ai yakamata yanzu ace yabaro kasar Chinan nan yadawo kunyi aure inyaso sai ku koma tare idan bai gaji da zaman canba"

Saida ta sake bata fuska sannan ta kalli khulsum,

"Zanyi miki rashin mutunci idan kika kara kirana da labour dinnan, nafada miki bana so"

"Atoh kiyi min mana wayasa lokacin da kina secondary school din da aka baki labour prefect din kika karba? Ai da sai kice bakya so abaiwa wata"

Dariya tayi ta dauke kanta daga kallon khulsum,

"Kin san me kawata? Hamood shima burinsa yanzu kawai yaga yadawo Nigeria munyi aure, kuma nanda 3 months fa zai dawo, sai dai shi yafi son yayi komai na aurensa dakanshi, baya son uncle dinsa yayi masa acewarsa lokaci yayi da yakamata uncle barewa yahuta tunda tun yana dan 7 years yake yimasa wahala sannan dukkan karatunshi da wanda yayi a Nigeria da wanda yayi a outside duk shine yake sponsoring shiyasa yace sai yadawo yasamu aiki tayadda zai iya yiwa kanshi aure sannan zai kai maganar gaban uncle dinshi"

Dan karamin tsaki khulsum taja,

"To kuma sai me dan yafadawa uncle dinshi yanzu? Minister nefa, ai yanada kudin da zaiyiwa samari goma irinsa aure"

"Hakane khulsum amma kigane wani abu guda daya, abunfa da kunya kuma da nauyi ace tun kana dan karami mutum ke dawainiya dakai sannan ka girma nanma kace komai shi zaiyi maka alhalin bashi ya haifeka ba kawai zumunci ne"

"Ehh to hakane kuma da wannan dan wannan, to Allah dai yadawo dashi lafiya musha biki"

"Amin, yanzu dai tunda magrib takusa ni ina ganin mubari zuwa gobe sai mu shiga central market mu siyo kayan da zamu saka abikin dan gaskiya basaka ankon nan nasu zamuyi ba tunda nasune suda friends dinsu"

"To shikenan babu damuwa Allah yakaimu, Allah kuma yasa mutashi da wuri daga aikin nan"

"Amin,Kuma wallahi commitment dina yawa gareshi goben nan dan har dinki nake son kaiwa ga sauran siyayyar yaran nan da ban karasa ba ta kayan kitchen dinsu"

"Babu komai dai kawai Allah yanuna mana goben komai mai saukine"

"Amin ya Allah"

Daidai lokacin suka tare wani mai keke napep suka shiga domin tafiya gida.


*_Ummi Shatu_*
[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO*_ _(Home of expert & perfect writers)_


*KAMAR DA WASA...!*


*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*2*


***Har suka kusa zuwa gida magana daya suketa yi shine maganar zuwan kakarsu iyallo,

"Mai gado Allah kina bani dariya yau dinnan" khulsum tafada tana tuntsurewa da dariya,

Harararta Bilkisu tayi daidai lokacin da suka isa kofar gidansu bilkisun yayinda gidansu khulsum ke can wata unguwa daban gaba da ta su Bilkisu,

"Banida lokacinki sai anjima saura kuma gobe karki fito da wuri"

Daga haka tafice daga keke napep din tabar khulsum na yimata dariya, ji tayi kamar kada ta shiga gidan sakamakon ganin motar ya mudan da tayi, sam ita ta tsani takura da naci amma babu yadda ta iya dole tashiga tana tafiya sadaf sadaf, atsakar gida ta hangoshi zaune kan farar kujerar roba yadora daya kan daya yayinda ammah ke cikin kitchen suna yar hira dashi,

"Sannu da aiki ammah..."

Daga haka tanemi wucewa dakinta, maganar amma ce ta dakatar da ita,

"Ke mai gado, bakiga yayanki bane zaki wuce baku ko gaisa ba?"

Juyowa tayi tadawo da baya, fuskarta babu fara'a,

"Yaya mudan ina wuni? Anzo lafiya? Yasu iyallo?"

Ta hada gaisuwar gaba daya lokaci guda, murmushi yayi ya amsa mata yana yi mata wani kallo mai cikeda sha'awa,

"Lafiya lau mai gadon zinare, ya aikinku?"

Tana tafiya take amsa masa da "lafiya"

"Manyan yan jarida kenan, ku da anganku anga labarai"

Bata amsa masa ba ta soma cuku cukun zaro key din dakinta daga cikin handbag dinta adaidai lokacin taji sallamar Hindu da minah har da mamaa wacce ke rikeda hannun yarta hudah yar kimanin shekara daya da rabi, yarinyar na hango Bilkisu ta kwace daga hannun mamaa tatafi da gudu wurin Bilkisu, dakatawa tayi daga bude kofar da takeyi ta dauketa fuskarta dauke da fara'a,

"Hudah na oyoyo daga ina haka?"

Kafin hudah tayi gwarancinta su mamaa suka karaso,

"Adda maigado yau baki taso da wuriba" inji mama,

"Wallahi fa mamaa aikinne sai ahankali, daga ina kuke?"

"Bakin kasuwa mukaje suka kai nadin gwaggwaro"

Murmushi tayi tawuce dakinta tana cewa,

"Amaren kamshi kenan"

Akan gadonta ta ajiye hudah ta kunna mata cartoon awayarta ta bata sannan ta zage ta fada wanka, tana wankanne meenah ta shigo sadaf sadaf ta dora mata wata farar takarda akan sallayarta tafice.

Bayan tafito doguwar riga kawai ta saka marar nauyi ta dauki hijabinta domin tanata jiyo kiraye kirayen salla daga masallatai daban daban, hudah kuwa tana zaune tana kallon cartoon dinta sai dariya takeyi,

Kan sallaya tahau har zata fara sallar idonta yakai kan farar takardar da meenah ta ajiye dauka tayi ta warware ta tafara karantawa,

_Adda labour yaya mama ce tace wai baza abamu komai bane na hadin amare? Wai kibada kudi zata siyo mana kaza ta dafa mana_

Murmushi tayi ta yaga takardar ta watsa ta cikin dustbin, dama kusan duk lokacin da zasu tambayeta abu indai na kunya ne sai dai su rubuta mata sai su ajiye mata wurin da zata gani ko su tura mata text, ko pad zasu tambayeta sai dai su rubuta mata shiyasa kafin lokacin ma yayi take siyo musu ko tabasu kudin su siya domin tana mutukar kaunar kannen nata saboda suma suna sonta sannan suna bata girmanta tsakaninsu babu reni hatta mamaa da tayi aure harda baby bata yimata reni bare rashin kunya, sallar magrib tayi bayan ta idar ta kara da nafila, tana kokarin shafa addu'a mamaa ta shigo,

"Yarinyar momy kallo takeyi awayar momy?"

Mamaan tafada lokacin da take zama agefen gadon Bilkisu,

"Ai kin jita shiru, nawane zai isheku dafa kazar?"

"Adda labour yafi dubu biyu zuwa uku?"

"To shikenan zan baki kafin ki tafi, shekaran jiya fa har naturawa wannan matar da tayi miki hadin kayayyakin nan lokacin bikinki kudi suma tayi musu kuma nasan itama harda kazar zata dafo musu"

"To shikenan ai iya natan ya isa tunda yama fi kyau nifa na bikina har na haifi hudah yana jikina..."

Harararta Bilkisu tayi,

"Ban son fitsara"

"Yi hakuri Adda maigado subutar baki ce" daga haka ta shige bathroom domin yin alwala.

Daukar hudah tayi ta fita domin yunwa take ji, atsakar gida ta iskesu saman katuwar tabarma wata na sallah wata kuma ta idar rashin ganin ya mudan yasata zargar kila ko yatafi, zaunar da hudah tayi tashiga kitchen, faten doya da wake shi akayi da rana yanzu kuma da daddare tuwon shinkafa ne miyar zogale, tuwon ta zuba ta dauko tadawo wurin hudah ta soma bata itama tana ci da haka har amma tafito ta samesu. Zama tayi kusa da ita tana tsokanar hudah,

"Acici kinzo zaki cinye min abinci nida mijina, to maza kiyi kibar min gidana...." Ta karashe maganar tana jan kunnenta daya, rike kunnen da taja hudah tayi tana guduwa jikin bilkisu, janyeta tayi tana kallon amma,

"Zo baby na rabu da amma kinji, maza ci tuwo idan baki koshi bama inkaro miki"

"Badai tuwo na ba tunda ba ita ta tuka minba"

Kowa na wurin saida yayi dariya saboda jin abinda tace, mamaa ma fitowar tayi tana dariya nan tasamu gefen tabarma ta zauna,

"Yawwa mai gado wai nikam meyasa kikeda taurin kaine? Meyasa duk ranar da dan uwanki mudassir yazo bakya sakar masa fuska ku gaisa? Iya gaisawar ce fa kadai daga ita shikenan babu wani abu, dan Allah ki gyara"

"To ammah insha Allah" daga haka taci gaba da cin tuwonta tana sauraren zantukan da su mamaa keyi wanda baya rasa nasaba da shirye shiryen bikin su Hindu lokaci lokaci ta kan dan saka baki harta kammala cin tuwon tatashi taje tana wanke musu hannu itada hudah daga nan dakinta tawuce tabaje akan gado bayan ta dauko yar madaidaiciyar laptop dinta, tana ji yara suna go slow din shigowa dan kiran hindu da meenah wanda ko ba afada ba tasan angwayen ne masu kiran. Aikinta taji gaba dayi na rubuta takardar neman hutu har na tsawon sati biyu wato (casual leave) saboda bikin su meenah domin tana bukatar isasshen lokaci so take idan biki yarage saura kwana uku saita nema kamar dai yadda tayi abikin mamaa. Har misalin karfe 9 saura idonta na kan laptop din tana wani aikin daban, shigowar mamaa ce ta katseta ta tashi zaune tana gyara hudah wacce ke makale ajikinta tana bacci,

"Adda maigado faruk yazo zamuje mu tafi, ko inbar miki hudah ta kwana?"

"Ke wai ban hanaki fadar sunan mijinki kai tsaye ba, tunda ga yarku ai gara kirinka sakayawa da abban hudah wallahi idan kuma baki gyaraba wata rana sai kinji sunan nan abakin yarki"

"Wallahi Adda bana fada agida anan ne dai nake fadar sunanshi"

"Nidai na fada miki ai, dauketa kutafi da ita kinga gobe zan fita aiki kuma idan nafita bazata yarda da kowaba sai kuka zata ishi mutane dashi da dai weekend ne sai kibarta"

Daukar hudah mamaa tayi suka fita bayan bilkisu tasaka hijabinta, atsakar gida suka samu ammah da Faruk mijin mamaa suna gaisawa. Yana ganin bilkisu ya soma dariya yana cewa,

"Barka da fitowa babbar yaya, anwuni lafiya"

"Lafiya lau faruk ya mutanen gida, ya aiki"

"Lafiya lau anty mai gado"

Dunguma sukayi gaba dayansu suka fita banda amma,suna fita tun daga compound din gidan kamshin turaren su hindu ya budadesu suda angwayensu kowacce suna tsaye agefe itada angonta suna hira,

Dukkaninsu saida suka matso suka gaisa da bilkisu kafin takoma gida, tana shiga daki ta iske miss called din hamood zama tayi gefen gadonta tana kokarin bin kiran yasake kiranta nan ta daga bayan ta lumshe idonta tana saurarensa, kamar koda yaushe sun shafe lokuta masu yawa suna hira har saida bacci yaci karfinta sannan sukayi sallama.

Washe gari da sassafe ta shirya tafita domin tana da zuwa dauko rahoto kamar yadda tasaba, ko khulsum bata nemaba ta kwashi kayan aikinta itada driver suka tafi,bayan ta dawo daga daukar rahoton taje tayi voicing saida ta kammala komai sannan tasoma neman kawar tata, news room taje acan ta iske khulsum tana fassara labaran da

Please Login or Register in order to submit comment