You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
kusanci da ita. Washe gari tana son taje kitso ta can kuma zata biya ta gidansu khulsum domin ta dubata saboda taga text dinta cewar bata da lafiya yau, shine yakaita duk inda zataje bayan tagama yakoma daukota, kallonshi tayi sama da kasa yana sanye da koriyar t shirt mai gajeren hannu da hoton tsintsaye ajiki anrubuta angry birds, sai bakin wando mai kyau amma dan tsiya an yanke gwiwar an wani tsagashi shiyasa ga gwiwarsa nan awaje ga wani dan banzan askin da ya sarkaba yanzu irin wadanda yan kwallo keyi ko musicians awani saisaye gefe da gefe amma kuma tsakiyar atara uban suma, ita duk ma ashigar tasa wannan askinne yafi yimata takaici,shi dai kallon tsaf yake yimata ta cikin bakin glass din dake fuskarsa kasancewarshi mai hasken fata glass din ba karamin kyau yayi masa ba dama yanzu baya raboda saka glass tunda yasai babur saboda iska da kwarukan dake fadawa mutum ido idan yana tuki,
Yanda take kare masa kallo haka shima yake kare mata kallon batare da ta saniba,
"Wai kai dan Allah sai yaushe zaka girma ne? Kullum kai kenan cikin shiga marar kan gado"
"To hajjaju wai yau kuma meye laifin shigar tawa?"
"Oho..."
Daga haka ta tattare skirt dinta ta hau machine din, juyawa yayi ya kalli kafarta duk kwaurinta awaje yau bata saka safa ba,
"Ranki yadade ki sake jan skirt din naki kirufe kafarki"
"Muje kawai ko naja ba rufewa zaiyi ba tunda ba zani bane"
Saida ya tura baki sannan yafigi machine din yaringa bin lungu wai dan kar yabi ta cikin gari mutane su ganta.
***
Ahalin yanzu basuda wani matsala a zamansu sai dai fa har gobe zamane suke yinsa irin na yaya da kani bawai mata da miji ba domin har yau dagashi har ita basu san menene aurenba suna dai zaune ne kawai tsawon watanni biyar da aurensu, tun ranar da yace mata yana jin tsoron kwana shi kadai yadawo kwana cikin dakin amma yana kasa ita kuma hakimar na kan gado,yau tunda asuba taga kiran maama tana dagawa taji tace mata ankai meenah asibiti ana zaton ko haihuwace, nan tayi maza tashiga kitchen domin hada abincin da zata tafi musu dashi asibiti dama shiyasa yanzu bata kashe wayarta da daddare saboda tana tunanin za anemeta saboda daga meenah har Hindu cikinsu yatsufa, fahad yana kwance yanata baccinsa bai san meyake gudana ba saida tagama komai tayi wanka sannan ta tasheshi lokacin karfe 6 nasafe, da kayan dake jikinsa ya dauki key zai fita ta dakatar dashi,
"Ba dai ahaka zaka fita ba ko?"
Fasa fitar yayi yaje yacire armless din rigar dake jikinsa yasaka jallabiya harda hula sannan yafita, suna tafe yana ta kunkuni,
"Wai sai anyi abu ace wani kagirma bayan har yanzu ayaronka kake tunda babu abinda ya canja... Hmmmm zan girman dai akwai lokaci"
Ita dai da yake hankalinta ma baya wurin bata san meyake yiba, wani private hospital ne mai suna al shaddad hospital aka kai meenah acan suka iske maama da mahaifiyar mijin meenah saida suka gaisa da fahad ya tambayi ya mai jiki sannan yatafi gida yaje yaci gaba da baccinsa, wani hukunci na ubangiji itama hindu babu jimawa aka kawota amma ita tana zuwa baifi da mintuna ashirin ba ta haifi yarta katuwa mace nan duk hankali yasake tashi ganin meenah shiru har lokacin tana can dai tanata fama, ammah kuwa da kokari har wannan lokaci bata zo asibitinba tana can gida dai tana tayasu da addu'a sannan tahada komai da ake bukata da abinci tabawa rabi mai aikinta da driver sunkai, su bilkisu kam babu wanda yabi takan abincin da aka kawo domin lokacin ana tunanin yiwa meenah aiki aciro yaron dan har anbaiwa mijinta takarda yasa hannu ba akai ga biyan kudin aikinba Allah ya takaita ta haifo yaronta namiji shima tubarkalla da girmansa.
Sai lokacin kowa yasamu nutsuwa, bayan an kaisu dakin hutu fahad yazo lokacin magriba takusa jariran dai ana ganinsu gasu nan gwanin sha'awa amma iyayen na can ana yimusu karin ruwa sunata baccin gajiya har cikin dakin da jariran suke bilkisu takai fahad ta fara dauko masa macen ta mika masa ya karba yana murmushi, kallon jaririyar yake tayi yakasa bada ita,
"Bazaka dauki dayan bane?" Yaji bilkisu tafada sai lokacin yabata ita yadauki namijin yana mai cigaba da kallon yarinyar, shi dai yana son ahaifa masa yar budurwa ko dan bashida kanwa mace ne oho, bata jaririn yayi yafita yana yimusu Allah yaraya, sai wurin 10 nadare yadawo yadauki bilkisu, washe gari aka sallami masu haihuwar suka tattara sai gidan ammah, dakin bilkisu nada aka sakasu, tunda akayi haihuwar nan bilkisu can take wuni,ana igobe suna suka sha lalle da kitso har masu jegon duk su hudun, da tayi niyyar kwana sai washe garin suna zata koma gidanta amma fahad ya uzzura mata nan Ammah tace tatafi inyaso tadawo da sassafe,
Tanata fushi taje suka tafi shi dai sai santin kunshinta yakeyi da yagani batare da yafito fili ya nuna mata ba har sukaje gida, kasa kasa yake kallonta yana hadiyar yawu, zama tayi bakin gado ta cire mayafinta da dan kwalin kanta hakan yasake saka fahad acikin wani hali, zama yayi agefenta,
"Hajjaju... Dan Allah nidai yau dinnan..."
Kallonshi tayi dama har lokacin bata huceba,
Dan matsawa kusa da ita yasake yi taja baya tana fadin,
"Menene haka??"
"Gaskiya yau yakamata.... Abani.... A..b..a..ni... Ha...kki..na"
Ita saboda yadda ya rarraba maganar ma sai takasa ganewa, nan ta kalleshi yawani matso jikinta sosai yana shafa sumarshi alamun kunya,
"Kace me? Me kace?"
"Cewa nayi yakamata yau abani.... Hakki... Na"
"A ina hakkin naka yake?"
"Ni na nasan a inda yake idan har kin bani dama kuma kin yarje min"
Wata uwar harara ta dalla masa ta mike zata bar wurin da azamarshi yariko hannunta shima yamike tsaye, daga idonta tayi ta kalleshi dayake yafita tsawo kafin tace wani abu jin hannunshi tayi akan waist dinta yamaida ita ta zauna bisa cinyarsa, kokarin yi masa masifa tayi amma ya hanata yin hakan ta hanyar hade bakinsu wuri guda, kokawar kwacewa tafara yi amma takasa saboda yanayin karfin ba daya bane, yana kokarin rabata da rigar jikinta taci nasarar kwatar kanta har ya balle bra din dake jikinta. Hannunta ya riko a masifance take kallonshi da fushi akan fuskarta,
"Dan Allah mai gado yau daya dai ki amince min..."
"Kasan Allah duk ranar da kasake yunkurin tabani ko tam..."
Idanuwanshi dake lumshe yabude ya kalleta,
"Me kike nufine wai? Amma dai ai kin san Shari'a ta bani damar yi ko da karfine ko?"
"Ok fyade kenan zakayi min, right?"
Girgiza kai yayi yamaida idonshi yarufe,
"Ni bazan taba yimiki fyade ba, da yardarki da amincewarki zan kusanceki...."
"Lallai yaron nan bakada kunya..."
"Banida kunya...? To bari infito amarar kunyar tunda har anyi min tambarinta"
Ja daya yayi mata sai gata kusa dashi bakin da ya kirashi da marar kunya yayi magani tareda ragewa kansa zafi bayan yayi fatali da sutturarta, sosai fa yau fahad ya jagwalgwalata daga karshe yabarta ba dan wai yakushi da dukan da takeyi yana shigarshi ba kawai dai ya kyaleta ne,rigarta ta jawo tasaka tana faman cika tana batsewa.
Daga haka ta mike tawuce bathroom cikeda fushi, juyi yayi ya baje sosai akan gadon yana maida numfashi ahankali.....
*Idan har kika karanta alhalin baki biyaba keda Allah domin yana ji kuma yana gani.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*24*
***Har tafito daga bathroom din bayan tayi wanka bai motsa daga inda yakeba, kayan baccinta ta dauka ta koma bathroom din tasaka sannan tafito fuskarta ahade babu fara'a,
"Malam dan tashi zan kwanta"
Batare da ya bude idonshi ba yace,
"Ki kwanta mana amma ni bazan iya tashiba yanzu jikina babu karfi saboda akwai abinda yashirya yi kekuma kin katse shi"
Batare da ta tanka masa ba dan taga abin nasa harda rainin wayo aciki tawuce can karshen gadon tayi kwanciyarta bata ko cire hijab din jikinta ba,
"Wallahi akwai matsala ajikinki billy, yanzu ke dan tabakin nan danayi bakiji komai ba? Dan Allah kibari ko dan romance mu sake yi...."
Ita mamaki ma fahad ke bata yanzu wato yasan komai kenan dama can ido yazuba mata bai nuna ba amma yana sane da komai, kunya taji tarufeta dan haka tayi gaggawar juya masa baya,
"Kinji..." Yasake yimata magana yana kallon bayanta,
Ganin bazata kulashi ba yayi shiru ya hakura ai ko wanka bai tashi yayiba daga nan inda yake kwance yacire rigarshi da wandonshi ya wurgar yazauna da iya singileti da gajeren wando, dayake yau itama adan tsorace take dashi bata matsa akan sai ankashe wuta ba ahaka suka kwana da haske, shi dai fahad kasancewar abun yana ranshi har mafarkinta yayi da asubah da yatashi kunkuni yayita yi shi kadai,
"Kaida hakkinka amma anhanaka anbarka da yin mafarki idan kayi magana kuma ace kayi rashin kunya..., ni bada yin abuba nida wanka da asubar nan....."
Tana jinsa tayi kamar bata jiba da tajiyo alamun wanka yakeyi bayan yashiga bathroom ficewa tayi tabar dakin tashiga kitchen tana mamakin wannan al'amari wato shi a wannan shekarun nasa har yasan yanda zaiyi da mace lallai, abu mai sauki tahada masa takai dining sannan taje daki zata shiga wanka yana baje saman gado jikinsa sanye da jeans da t shirt da wayarshi ahannu yana chaten da husna yar nacin tasa domin yau kusan kwana uku kenan tanata turo masa sako amma bai budeba sai yau kuma cikin rashin sa,a ashe tana online,
Tana harararshi tashiga wanka harda saka key, bayan tafito sanye da hijab ta kalleshi,
"Malam dan fita zan shirya"
"To ranki yadade"
Yana fita tasawa kofar key tashirya ta dauki duk abinda zata bukata tafita ta sameshi akan kujera yana kwance,
"Bari naje gida sai zuwa dare zan dawo, kayi zamanka basai ka kaini ba zan hau napep"
"To shikenan Allah yatsare"
Fita tayi aranta tana mitar dalilin dayasa bata siyi motaba ma tun wuri, shi fahad murna ma yayi da bashi zai kaita ba domin yasan idan ya dauketa sake famo masa tabon abinda ke damunsa zatayi, haka yawuni agida ranar jikinsa duk babu kwari sai la'asar yafita yaje gidansu acan yaci abinci sannan yatafi dama yasamu su ayiyah suma suna shirin tafiya gidan sunan. Su bilkisu kam yau kansu yasai kayuwa domin suna yayi suna, yara sunci sunan ammah da abba macen yahanazu zasu kirata da Minal namijin kuma lukman zasu kirashi da sultan, gida ya cika dam da dangi da abokan arziki su iyallo da baki baya shiru cewa bilkisu tayi yanzu kuma saura ita itama nanda yan watanni suna so suzo suna, batace komai ba taci gaba da harkarta dama ammah tatura akirata tazo surukanta sunzo iyayen fahad nan taje taji dasu.
Har bayan suna da kwana biyu kullum sai taje gida amma a napep domin shi fahad bai kara daukarta a babur dinsa ba acewarsa saiya warke. Bayan sati uku da sunansu meenah zasu koma gidajen mazajensu ranar bilkisu taje gidan zasuyi sallama da masu jego dama tun yamma hadari yake haduwa amma taki tafiya saida duk suka tafi suka barta bayan sallar isha fahad yazo ya dauketa, ai tun ahanya yayyafi yafara jikasu kafin suje gida sunyi jalaf da ruwa ga hanyar babu haske ga uban gudun da fahad ke shekawa ganin idan tayi wasa tana iya fadowa yasata kankameshi, bayan sunje gida inbanda sanyi babu abinda suke ji daga shi har ita,kayan bacci tasaka yau babu maganar wanka ta kwanta, shigowa dakin shima yayi yana digar da ruwa ya kwashi kayan da zai saka yaje falo ya canja yaje yakwanta kusa da ita, tashi tayi kafin tayi magana ya rigata,
"Ki taimaka min wallahi yau sanyi nakeji kuma duvet dinnan naki yafi wancan blanket din nawa dumi... Zazzabi ma nake ji fa"
"Malam wallahi bazai yuyuba...."
Yabude baki zai sake magana kenan sukaji wata tsawa mai mutukar karfi dan hatta dakin da suke ciki saida ya girgiza, bata san lokacin da kankameshi ba shima haka, jikinta gaba daya rawa yake ga ruwa da ake kwararawa kamar da bakin kwarya, ahaka suka yi bacci suna kwakume da juna har asuba, shine yafara farkawa har lokacin ruwa akeyi, kallonta yayi tana bacci cikin kwanciyar hankali rungume akirjinsa tayi matashin kai da kirjin nasa,
"Su hajjaju iyayen son girma amma kuma ana tsoron tsawa...."
Pillow yajawo zai kwantar da ita akai domin ya fahimci tana fashin salla duk da boye masan da take tayi domin idan bata salla bata son yasani idan asubah tayi saita tashi taje tayi alwala sai tazo ta zauna kamar irin ta idar da salla dinnan tana tasbihi bayan kuma tun lokacin da ya fara kwana adakin ya fuskanta saboda duk lokacin da zata tashi sai yafarka domin abu kadanne ke farkar dashi abacci,
Bude idonta tayi wanda ke cike da bacci kamar jaririya ya kwantar da ita ya mike, ga mamakinta sai taji tana bala'in jin sanyi bayan yatashi babu jimawa ciwon kai yasata agaba, sam fahad bai san abinda yake faruwa ba har saida rana tayi duk da har lokacin anata yayyafi yashigo dakin da niyyar yin alwala tayi masa magana,
"Dan Allah ko zaka samo min maganin ciwon kai"
Matsawa yayi kusada ita ya dafa goshinta,
"Da zazzabi?"
"A'a iya ciwon kanne"
"Sannu, Allah ya sawwake bari naje na samo miki"
Sai bayan da yatafi sannan ta janyo wayarta ta kunna ta tura masa text domin pad dinta yakare abinda ya hanata ma wanka kenan tun dazu,
Yana gidansu wurinsu ayiyah zai karba mata abinci text din nata yashigo yana dubawa yaga tace,
_Dan Allah ka dan taho min da pad._
Murmushi yayi aransa yana cewa,
"Wato baza dai afada min baki da bakiba wai kunya akeji hajjaju kenan"
Saida yajira aka karasa abincin rana sannan aka zuba ma bilkisu cikin food flask, maryam yadauka zasu tafi da ita domin ta ragewa bilkisu aiki tunda yau suna gida ruwa ya hanasu zuwa makaranta, ta wani chemist suka fara biyawa yashiga domin siyo mata maganin ciwon kan kuma cikin sa'a yaga harda pad dinma gashi nan ana saidawa kala kala, guda biyu ya siyo mata yakarbo mata maganin suka wuce shida maryam. Har yakoma tana kwance rikeda kanta wanda ke azalzalarta, afalo yabar maryam yashiga cikin bedroom din ya taimaka mata ta tashi zaune,
"Kiyi wanka sai kici abinci kisha maganin ko?"
Kai ta daga masa tana jiran yafita daga dakin sannan sai tatashi domin tana kyautata zaton tayi staining, tun kafin ta koreshi ya fahimta dan haka yamike yafice bayan ya ajiye mata maganin da pad din agefenta, lallabawa tayi ta tashi cikin sa'a taga staining din bai taba bedsheet dinba iya kayan jikinta ne, wanka tashiga tayi da ruwa mai dumi wanda ke cikin babbab tea flask dinta, har lokacin kanta bai sarara mata ba, body spray kadai ta fesa ta saka kaya riga da wando na Pakistan, ta lallaba tafita falo, yana kwance a kujera maryam na mopping din falon ganinta yasa bilkisu fadada murmushinta,
"Maryam daga zuwa kuma sai aiki"
"Ehh anty, ina wuni? Yajiki?"
Zama tayi akujerar nesa da fahad tana amsawa, da kanshi yatashi yaje ya dauko mata abinci da flate yakawo mata, saida tafara hada tea tasha sannan tabude abincin, dashishi ne yaji kayan hadi da albasa ga mai nashe nashe ai kuwa taji dadin ganin dashishin nan domin taci da yawa dama yau bata ci komai ba, kwanciya tayi bayan tasha magani bacci yayi gaba da ita sai lokacin fahad yasamu yafita yabar maryam atare da ita, koda yaje shagonma hankalinsa na gida domin bini bini sai yakirata yaji yajikin nata har magrib tayi bayan yayi salla ya koma gida yadauki maryam ya maida ita gida daga can ayiyah tabashi tuwo yatafiwa da bilkisu. Tsawon kwana biyu ta dauka tana fama da ciwon kan kafin tasamu sauki tafara fita aiki amma da ko aikinma bata zuwa, khulsum har gida tazo ta dubata haka ma maama masu jegone kadai basu zoba tahanasu tace taji sauki basai sunzo ba kowa yadauka laulayin ciki tafara basu san bahaka bane. Shi dai fahad yanata iya kokarinsa na ganin sun zama abu daya amma taki amincewa shikuma baya son yanuna mata karfinsa shiyasa yake kyaleta, yauma kamar kullum saida sukayi rikici daga karshe ya sauka kasa yayi shimfidarshi ya kwanta wai yayi fushi,can cikin dare tafara jin nishinsa yana murkususu kamar bazata kulashiba amma sai taje inda yake ganinsa tayi duk ya jigata sai gumi yake baccin da basu komaba kenan domin abin ya tsananta zuwa asuba yasamu ya lafa masa, bayan gari yafara haske yatashi ya dingisa yayi alwala yayi salla yana dafe da gefen mararsa na hagu, akwance agida yawuni ranar gashi yakasa cin abinci sai ruwan tea kadai yake sha bilkisu tayi tayi akan yaje asibiti yaki daren ranar halin da yashiga har yafi najiya babu shiri ta dauki wayarsa ta dangwala dan yatsanshi tashiga neman contact ya abba takira lokacin karfe 12 nadare yana tsaka da bacci yadauka,
"Kanina ya akayi?"
Cikin tashin hankali bilkisu tayi magana, dama abban yazo gari yana nan cikeda tashin hankali shima yasako kaya yafito ko cikin gida bai shigaba saboda kowa na gidan yayi bacci. Bilkisu na can tanata fama dashi domin kuka yake ta yimata wiwi yana rike mararsa ahaka Abba yazo gidan yasoma kwankwasawa da azamarta taje ta bude shida salim ne sukazo a motar ya baffa ai basu jira komaiba ahaka suka daukeshi sukayi kama kama, itama dogon hijabi kawai tasaka ta daura zani tabisu,asibiti mafi kusa suka je wani dan karami na kudi, wajen karfe dayan dare Dr yafito yace aiki za ayiwa fahad domin k'arine a mararsa kuma yagirma dole sai ancire nanda zuwa safe za ayi masa aikin matsawar sun biya kudin aikin amma ahalin yanzu aunyi masa allurar da zata sakashi bacci dan yasamu saukin ciwon,azaune su bilkisu suka kwana da ita da Abba da salim, zuwa asuba Abba yasanar da gida abinda yake faruwa kafin gari yagama wayewa su baba duk sunzo dasu ayiyah har su yaya asabe sun zo nan aka biya duk wani kudi da ake bukata,wurin karfe 9 nasafe ake sa ran yimasa aikin shiyasa kowa ya zauna yana zaman jiran tsammani,kafin lokacin da za ayi masa aikin anty kubra da anty juwairiyya suka zo dauke da abincin da suka shiryo amma dayake hankali ba akwance yakeba babu wanda yakula balle har yaci.
Karfe tara da wurin rabi aka shiga da fahad theater ayiyah sai addu'a akeyi itada mamuh abin tausayi, tunda aka shiga dashi basu suka fitoba sai sha biyu na rana kallo daya zakayi masa kagane amutukar wahale yake sannan yajigata,sai faman baccin wahala yake, wani daki aka kaishi gado biyune adakin amma daya gadon babu kowa akai, wuni yayi yana bacci bai farfado ba sai la'asar sai lokacin hankalin kowa ya dan kwanta yanyameshi akayi kowa nayi masa sannu bilkisu dai daga dan baya ta tsaya saida kowa yagama sannan tamatsa itama bayan taga fitarsu mamuh yarage saura abba da salim kadai, duk wanda yayi masa sannu sai dai yadaga masa kai amma baya iya amsawa, koda bilkisu ta matsa idanuwanshi yazuba mata wadanda suka sake girma sakamakon dan fadawar da yayi,
"Sannu... Yajikin.... Allah yabaka lafiya"
Kai yadaga mata sannan ahankali yakamo hannunta cikin nashi yana mai yimata alamar da ta zauna agefenshi, batayi musuba ta zauna tana kallonshi, lumshe idanuwanshi yayi har lokacin yana rike da hannunta, sunata zaune ahaka har anty Fauziyya tashigo ta kirata wai tazo inji ayiyah, tashi tayi tafita bayan yasaki hannun nata, koda taje ayiyah matsa mata tayi tasata agaba dole sai taci abinci domin wuni guda bata ci abincin kirki ba, daurewa tayi taci abincin tuwon shinkafa miyar wake bayan tagama ci tayi alwala tayi salla sannan takoma cikin dakin tare dasu Mariya wadanda suka biyo anty fauziyya suka taho tare.
"Sannu ya fahad....." Inji su mariya kai yadaga musu sannan yamaida kallonsa ga bilkisu hannu ya mika mata amma sai taki kamawa saboda ganinsu mariya awurin gaban gadon taje ta zauna amma sai ya dan dungureta koda ta kalleshi sai taga yana yimata alama da ta zauna asaitin kanshi matsawa tayi ta zauna tana zama yamaida kansa kan cinyarta yana ciccije lebe sakamakon amsawar da wurin da akayi masa dinki yayi hannunta ya damke cikin nasa yana rumtse idanuwa duk sai yabata tausayi domin tasan abinda zaisa kaga namiji na kuka to bafa karami bane abin ahaka suka kasance har wani baccin ya dan daukeshi kowa ya leko yaga ayanda suke baya shigowa saiya koma shiyasa duk nauyi da kunyar duniya tataru ta dabaibaye bilkisu musamman ma da taga su ayiyah sun leko amma sai suka koma har magrib yana kan cinyarta saida ya farka sannan abba yataimaka mata ya kwantar dashi saman pillow, salla taje tayi daga can tazauna wurinsu ayiyah har karfe 9 nadare suna asibitin da su ayiyah zasu tafine lokacin da mijin anty fauziyya yazo daukarsu sukace bilkisu ma tatafi gida sai su mariya subita su tayata kwana shikuma fahad abba yakwana awurinsa, turo baki fahad yayi ya bata rai yana kallon mamuh wadda itace ke tsara hakan, kallonshi ya mayar kan bilkisu ganin ta mike daga kujerar da take kai azaune acikin zuciyarshi yanata masifa,
"Ga matata ga komai maimakon abarta mu kwana tare shine kawai za awani ce ya Abba ya zauna ya kwana awurina, ni wallahi mamuh baki kyauta minba..."
Haka yaketa fada acikin ransa amma afili babu bakin magana domin tamkar andinke masa bakin baya iya magana gashi duk jikinsa kamar ba nashiba musamman ma daga mararsa zuwa babban yatsunshi na kafa,
Jin kowa nayi masa sallama suna tafiya yayi saurin yiwa salim alama da ya kira bilkisu,
"Hajjaju oga fa yana magana"
Murmushi tayi ta koma da baya tana cewa,
"Lallai salim kaima din hajjajun zakace"
Tana zuwa yayi mata alama da ta sunkuyo taji, duk atunaninta magana zaiyi mata akunne amma tana mika fuskarta saitin tashi taji yabata hot kiss a kumatunta mikewa tayi tana harararsa shima harararta yayi murmushi ne ya subuce mata batare da ta shirya ba, hannunta ya riko yana yimata alama da wai shima tayi kissing din kumatunshi,
"Dan Allah kaga ni sakar min hannu gasu can ni kadai suke jira kar kasa azargi ko wani abu mukey...."
Murmushin karfin hali taga yayi kafin yagirgiza Mata kai alamun bazai sakar mata hannun ba, hannunshi tayiwa kiss tana kokarin fita abba yashigo ganinsu ahaka yasashi saurin komawa da baya, hararar fahad tayi,
"Kagani ko...."
Bata saurareshi ba tafice daga dakin, binta da kallo yayi yana yimata dariya acikin zuciyarshi, dama ita kadai ake jira tana zuwa suka tafi,itada maryam da mariya aka sauke agidanta tana shiga wanka tafara yi sannan tayi sallar ishah domin batayi ba a asibitin acikin wannan daren takira maama da ammah duk ta sanar dasu rashin lafiyar fahad da asibitin dayake kwance ahalin yanzu sannan takira khulsum wacce har tafara bacci itama tasanar da ita, dayake jiya batayi isasshen bacciba shiyasa yau tunda ta kwanta bata tashiba sai da asubah duk da hakama ta makara sallah domin har masallatai sun jima da idarwa......
*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan har kinada bukata ki siya ki karanta domin yana dauke da dunbin darrusa na rayuwar da muke ciki yau, ka karanta halak dinka yafiye maka alkhairi akan karanta hakkin wani.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*25*
***Kitchen tashiga bayan ta idar da salla sukuma su mariya suna kokarin gyara mata gidan, saida ta shirya lafiyayyen abincinta tazuba a flask wanda zata kai asibiti sannan ta zubawa su mariya suka ci daga nan tabasu kudin napep saboda sai sun koma gida sannan zasu shirya su tafi makaranta danma dai sunyi wanka agidanta da sunje gida uniform kawai zasu saka, bedroom tashiga bayan ta sallami su maryam sun tafi, tana kokarin daura towel idonta yakai kan wayar fahad dake ajiye saman bedside drewar tana karar neman agaji, koda taje gaban wayar sunan husnah tagani ajiki nan wayar takatse wani kiran yasake shigowa, ko kadan bataji tana sha'awar daga wayarba har tayi tagama sai lokacin ta dauka ta jona masa a charge kasancewar akwai wuta. Wanka tashiga tayi tafito ta kintsa adan hanzarce sannan tayi breakfast kafin ta hada komai wanda zata tafi dashi tarufe gidan tatafi, shatar napep ta dauka yakaita har asibitin lokacin karfe bakwai da wurin rabi,iya ya abba ne kadai awurin da alama babu wanda yazo tunda yanzu garin yawaye, saida suka gaisa ta tambayi yamai jiki sannan tashiga ciki, idonshi akan kofa shiyasa tana shigowa idanuwansu sukayi arangama da