Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

maganar bikin fahad, shi dai baba yace zai karasa gina masa gidanshi wanda yafara hakama yayunshi maza guda biyu wadanda ke zaune a gombe da zamfara sunce zasu bada kyakkyawar gudun mawa lokacin da baba ke sanar dasu awaya sauran yan uwansa mata kuma sukace zasu taimaka masa wurin yin lefe. Yanzu kam fahad ansamu nayi domin can wurin aikin yake wuni duk da dama ginin yadan deboshi da fadi shiyasa dole sai baba yasaka masa hannu. Kasancewar yau ba ayi aikinba yasashi zama agida domin hutawa, yana kwance adakinshi duk jikinsa ciwo yake kamar shine yake aikin ginin, alamun shigowar text yagani duk tunaninshi husna ce amma da yabude sai yaga sabanin haka domin bilkisu ce taturo masa da,

_Salam idan kasamu time kazo zaku gaisa da kakarmu._

"Tofa.. Wata sabuwa nifa kunyar gaishe gaishen nan nakeji amma ya na iya? Ai idan naki zuwama sai na fuskanci hukunci"

Shi kadai yaketa maganganunshi daga karshe ya yanke shawarar kiran salim domin yarakashi da daddare. A lifan din salim suka tafi bayan sallar isha, kayan marmari suka tsaya suka fara siya mata sannan suka karasa gidan, awaje suka jira har bilkisu ta fito fuskarta dai babu yabo babu fallasa, kasancewar yasan hali shine yafara gaisheta ta amsa sannan suka gaisa da salim wanda take kallonshi ta gefen ido aranta tana jin damuwar wai wadannan zata nuna ranar bikinta amatsayin abokan ango,

"Muje ko" daga haka tawuce gaba suna binta abaya har ciki, iyallo jaraba ana zaune dakin baki ana sharbar tuwon shinkafa miyar taushe wanda tasa aka yimata ga tv ana kallo jin baki zasu shigo yasata yin lullubi ta rufe tuwon,

Cikin barkwanci da tsokana irinta kakanni ta taresu,

"Barka da zuwa angona, ina fata dai nima ka tanadi nawa dakin dan kafarka kafata"

Murmushi fahad yayi yayi shiru bai amsa ba sai salim ne yace,

"Dama ai dakunan mata biyu yayi harda naki wanda yamafi nata kyau"

Ai kuwa nan ta cafke tana cewa bata yarda ba shikuma salim yabiyeta sunata yi, daga fahad har bilkisu basa cewa komai shiru kawai sukayi sai dai murmushi sunfi minti talatin wurin iyallo daga karshe suka ajiye mata tsarabar da suka kawo mata harda na cin goro fahad ya ajiye suka fita, godiya da albarka sun shata wurin iyallo daga nan suka gaida ammah suka fita domin shi Abba yau baya nan, a compound din gidan suka tsaya yayinda salim yafita yabasu wuri, kallonshi tayi yasha coffee din yadin kufta da hula da takalmi sau ciki sannan ta dauke kai, ita kam hijabi ne ajikinta har kasa, shiru sukayi dukkaninsu na dan wani lokaci.

"Mai gadon zinare ya ake ciki? Kinji dai yanda su Abba suka yimana wai aure nanda 2 months nikuma gani mai karamin karfe"

"To ai basai ka takura kanka ba kawai kayi abinda ya sawwaka.... Tunda aurene na wucin gadi" takarasa maganar acikin zuciyarta,

"To Allah yasa bazaki rainaba"

"Babu matsala kayi dai dai karfinka"

"To shikenan, sai gani nagaba,nabarki lafiya, I luv u!!"

Bata amsa masaba yajuya yatafi yana daga mata hannu.


*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*



*KAMAR DA WASA....!*


*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*14*



*Littafin kamar Dawasa na siyarwa ne,yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta, ku kuma masu fitar min da book dan Allah ku hakura haka tunda ai kunyi na zumunci.*


***Wasa wasa lamari sai kara girmama yake domin biki yanata matsowa, a bangaren fahad komai yana tafiya daidai domin hatta lefenshi yakusa kammala danma yana baiwa su yaya asabe matsala saboda komai idan suka siyo suka saka idan baiyi masaba sai ya canja idan anyi magana yace shi matarshi babbar yarinya ce yar gayu ba karamar yarinya bace, tun abin yana yimusu ciwo musamman Anty Fauzy mai zuciyar tsiya amma da ta fahimci inda ya dosa saita daina damuwa daga karshe ma duk abinda zasu siya sai sunyi snapping dinshi sun tura masa ta whatsapp yagani, baba kuwa duk atamfofin da aka zuba cikin lefen shine yabada domin cewa fahad yayi yaje shagonsa yadubo duk atamfofin da suka yimasa dama sana'ar baba kenan shago gareshi a kwari na atamfofi zalla kala kala, duk da kayan sauran kadan su gama haduwa har yau bai siyo akwatuna ba saboda yace da kanshi zai siyo kuma da kudinsa, kowa agidan lamarin auren nan na fahad dariya yake bashi har baba ganin abin suke yi tamkar wasa wai fahad ne zaiyi aure, shi dai yanzu ta ginin gidanshi yake domin burinshi kawai yanzu yaga gidan ya kammala.

Bilkisu kam ta cika famm haka kawai lamarin auren nan ke bata haushi gashi kullum saita gwada number hamood amma shiru kamar koda yaushe bata shiga, yau kam amare duk sunzo gida harda maama dama hudah na gidan wurin bilkisu tun ranar da ta raka iyallo gidajensu hudah ta dankafe mata dole sai tare suka taho,

"Adda muma fa mun kwadaitu da son muga big Broz domin anty maama tace yahadu karshe ga class..." Inji meenah,

"Ehh wlhi meenah anty maama cemin tayi wai duk yafi mazajenmu kyau.... Gaskiya Adda labour kina bada kala..." Hindu tafada tana dariya,

"Yara kudai kubari zaku ganshi, wallahi big guy ne har wani suna fa ake fada masa amma ba zakuji abakina ba...."

Ai maama tana rufe baki bilkisu tatashi tabar musu wurin ta shige kitchen domin idan tazauna suka cigaba da haka tana iya make wata aciki.

Yammacin yau yammacine da jama'ar cikin garin kano da kewaye ke mararinsa domin yazo da sauyin weather, sabanin zafi da ake fama dashi kwana biyu yau garin a lullube yake da ni'imar ubangiji sansayyar iska ce ke kadawa ko ina ga sararin samaniya yayi luf luf gwanin sha'awa tamkar hadari domin da alamarsa kadan kadan, kowanne mahaluki yau yanayin yayi masa dadi ciki kuwa hadda fahad wanda fitowarsa kenan zuwa shagonsu bayan yataso daga wurin aikin gina gidansa da akeyi sai yanzu yasan lallai magidanta na kokari domin shi duk da ana taimaka masa agida amma yanzu haka account dinshi duk ya kusan yasheshi sai dan abinda ba arasa ba, yana tsaye yana yanka kayan wasu dalibai wadanda zasuyi bikin gamawa wato anko, yana yi yana cewa aransa,

"Danma dai Allah baya hana bawansa hanyar samu amma da ba haka ba sunana sorry..."

Maganar su hamza da yajiyo daga cikin shago itace ta dakatar dashi daga zancen zucin da yakeyi,

"Kayan Prince.... Kayan prince"

Ko bai waiwaya ba yasan husnah suke nufin ta taho, shi sunan nan takaici yake bashi wallahi yarasa yanda zaiyi da husnah, kamar yanda ya tsammata abayanshi ta tsaya tana murmushi murmushi dariya dariya,

"My prince... Sannu da aiki"

Aciki ciki ya amsa kamar koda yaushe,

"Yauwa"

Kallonshi tayi daga sama har kasa,p cap ce akanshi dark blue agaban p cap din anrubuta harrafin p da bakin rubutu,sai bakar t shirt mai dogon hannu wadda aka rubuta prince agaban rigar sannan ga bakin trouser yasaka da bakin takalmi na kamfanin Nike,

"Yau kayi kyau my Prince.."

"Nagode"

"Gobe me zaka ci in dafo maka?"

"Ai kawai ma kibarshi saboda ba lallai infito shago ba"

"Haba ya fahad... Meyasa?"

"Ina zuwa wani wurine, yanzu ma fita zanyi....ina so inje inga half soul"

Yakarashe maganar acikin ranshi, duk da yace fita zaiyi amma dan naci bata tafiba har saida yagama yanka kayan nan ya kullesu yakai cikin shago yana gaba tana biye dashi har shagon su salim, key din Babur dinshi yakarbo domin dagaske bilkisu yake son gani yanzu da yamnacin nan,

"Inhau muje ka saukeni a school"

Girgiza kai yayi,

"Bana daukar mata a machine sai dai inbaki kudin napep"

Zumbura baki tayi tatafi batare da tace masa komai ba ita ala dole tayi fushi shi kam murmushi yayi yabuga babur din yabashi wuta yaje ya wuceta a kofar plaza. Bilkisu tana zaune hindu tana kitse mata kanta wanda yafi sati uku atsefe mai gadi yashigo kiranta danma kitson manya ne baifi saura biyu agama ba,mamakine ya isheta jin wai ana sallama da ita bata san fahad bane domin lokacin da yazo yanata kiran wayarta amma shiru kasancewar tabar wayar adaki, agaggauce Hindu ta karasa mata ta shiga daki domin dauko mayafi, dukansu mikewa sukayi wai zasuje su gano yayansu, ita dai batace musu komai ba ta kama hannun hudah,

Har tafita bai sakko daga kan Babur dinba yana kai yana duba wayarsa yana dariyar tsokanar da yayanshi Abba keyi masa, ita tafara fitowa fuska ba yabo babu fallasa su meenah na biye da ita,

"Yaya fahad sannu da zuwa"

Sai lokacin yasan fitowarsu Babur din yaja zuwa kusa dasu yana kallon gimbiyar tashi da ta wani dauke kai tana shakar iskar dake kadawa,

"Uhmm son girma kamar gyambo" yafada aranshi afili kuma yace,

"Yau amare ne agidan... Yakuke"

"Lafiya lau ya fahad, ai yanzu amarci sai ku kaida adda labour" inji meenah,

"Wai hakama zakuce?"

"Ehh mana ya fahad gashi kuma wallahi kun dace da juna" inji hindu,

"Shine ai, abin nasu kamar shiri ita baka shi fari...." Meenah tafada tana dariya,

"Gaskiya dai wannan hadin yayi daidai..." Inji mama,

Tana jin duk uban surutun da suke zubawa amma batace musu uffan ba har sukayi suka gama ita abinda yakara kular da itama yayan da taji suna cemasa, gashi sunzo sun wani saki baki sai zuba suke kamar kanyar da bata da zaki. Sun jima awurinshi sannan suka shiga cikin gida amma banda hudah wacce ke makale da ita, saida yaga shigarsu gida sannan ya daga ido ya kalleta yana mikawa hudah hannu babu musu kuwa ta taho wurinshi ya dauketa yadora gaban Babur dinshi,

"Ina yini adda..."

Duk da bataso yin dariya ba amma saida tayi saboda yanayin yanda yayi maganar,

"Lafiya lau... Ya kake?"

"Alhamdulillah, ya mutanen gida?"

"Kowa lafiya"

Shiru sukayi yakoma yiwa hudah wasa wacce keta danna horn din jikin Babur din nashi, ji yake inama ace yarshi ce shida bilkisu wai... Da Allah ne kadai yasan irin farin cikin da zai tsinci kansa aciki,

"Lafiya kuwa naganka babu ko waya?"

Kallonta yayi sai kuma ya girgiza kansa yana murmushi,

"Mutum bazai zo yaga matarshi ba saida wani abu?"

Duk da maganar ta ratsata amma saita dake ta sake kallonshi aranta tana cewa, "yaron nan naga yana nema ya zake dayawa fa"

"Uhmm? Ni kawai ji nayi ina son inganki saboda nakwana biyu bamuyi tozali da fuskokin juna ba... That's all"

"To nagode, yanzu dai ai gashi kaganni, inada dan uzuri agida wanda nakeyi sai kuma kafito dani"

"Nifa ko baki koreni ba dama tafiya zanyi amma kafin sannan, zan nemi alfarma"

"Allah yasa zan iya"

"Dan Allah pics dinki nakeso ki turo min, sannan ki daure kifara kulani online murinka chat"

"Pics kuma? Me zakayi da pics dina?"

Murmushi yasake yi yasauke hudah kasa sannan yazaro dubu daya ya danka mata a hannunta,

"Nidai kawai ki taimaka kibani babu ruwanki da abunda zanyi dashi... Shikenan nabarki lafiya, kizama cikin aminci da kwanciyar hankali"

Babur dinshi yabuga yayi gaba yayinda ita kuma tabishi da kallo,

"Jishi kamar wani babba sai zaro magana da iya shiryata"

Daukar hudah tayi tashiga cikin gida, kamar yadda ta tsammata su Hindu anbaje anata zuzuta haduwar da fahad yayi da kuma yaba hankalinsa ita dai batace uffan ba tawuce daki ta ajiye mayafinta tasake fitowa tana zama khulsum na shigowa, har lokacin su maama hirar fahad suke,

"A'a kaga amare"

Dariya sukayi gaba dayansu, meenah tace,

"Anty khulsum ai yanzu kune amare gashi nan sai budada kamshi kuke" takare maganar da yiwa khulsum alama da ido,

Saida Ammah tabar wurin bayan sun gaisa sannan ta maida hankalinta Kansu meenah,

"Wai me kukeso kuce minne? Wacece amaryar? Ni ko wa?"

Dariya mama tayi,

"Kar dai kice kema baki saniba?"

"Wai me kuke magana akaine? Menene ban saniba?"

"Maganar auren adda labour mana, anfa samata rana nanda 2 months bikinta ai ni nazaci ma anko kikazo fitarwa"

Gimtse fuska khulsum tayi ta kalli bilkisu,

"Lallai kawata, abin har yakai haka? Kullum muna tare dake amma shine kika kasa sanar dani maganar bikinki? Nagode"

Daga haka tamike zata tafi, janta daki bilkisu tasoma kokarin yi amma tana turjewa daga karshe dai saida su maama suka saka baki sannan tayarda suka shiga dakin,

"Kawata kiyi hakuri dan wallahi ni auren nan ganinshi nakeyi kamar da wasa..." Nan takwashe komai ta fada mata amma ta boye mata kudurin dake cikin zuciyarta

Dariya khulsum tayi tace,

"Nidama tunda naji yace wai ke zaiyiwa dinki ni bazai yimin ba nasan akwai wata akasa"

Kai mata duka bilkisu tayi tana cewa "bana son sharri malama"

"Allah dagaske guy din yana mutuwar sonki"

Sun dade tareda khulsum suna tsattsara abubuwa da dama domin hatta anko atake anan khulsum ta fitar dashi tace pink din net da blue din head yayinda ita kuma amarya zata saka blue din kaya da pink din head su Hindu murna suka shiga yi suna cewa wallahi yayi sosai ayi hakan ita dai jinsu takeyi bata tankawa domin tunaninta gaba daya yana ga hamood.

Shi dai ango shirinsa yake ba kama hannun yaro domin gidanshi har anyi roofing anyi wearing da komai yanzu fenti da saka kofofi dasu tiles yarage kudine ma ya yanke masa shiyasa aikin yatsaya. Kwana biyu atsakani ya dan kwanta zazzabi saboda baya samun zama yanzu ga dinkuna duk sunyi masa yawa danma yabaiwa hamza wasu yarage masa, har yayi dan zazzabinshi yagama bilkisu bata saniba domin ba waya sukeyi ba shine ma yake kiranta ita kuwa ba kiranshi takeyi ba saida dalili, ranar da yaji dan dama dama bayan sallar magrib yashirya yaje wurinta, yau kam a guest room aka saukeshi ba a compound ba kamar yadda aka saba domin yazo kenan abba kuma yadawo shine yabada umarnin akaishi guest room dinshi, har lokacin kanshi bai gama daina yimasa ciwo ba ga jikinsa babu wani karfi sosai, yana nan zaune Rabi ta kawo masa ruwa da juice da wani dan madaidaicin food flask, bai taba komaiba har gimbiyar tashigo tana sanye da milk colour din doguwar riga da mayafinta wannan fitinannen kamshin nata yana biye da ita, ayanda ya lura tana kaunar dogayen riguna sosai domin tafi sakasu fiyeda riga da skirt ko zani, har ya amsa sallamarta tanemi wuri ta zauna akujerar dake kallon tashi idonshi na kanta,

Yasan muddin idan bashine ya gaisheta ba to sai dai idan bazasu gaisa dinba shiyasa yakatse shirun da gaisheta, ta amsa kuwa fuskarta babu yabo babu fallasa,

Shagwabe murya yayi ya langabar da kai yana kallonta,

"Bawan Allahnnan har yayi zazzabinshi yagama baki saniba bare kiyi masa sannu.... Dama haka akeyi?"

"Ayya to aini ban saniba, baka fada minba"

"To ai baki nemeni ba, har yanzu ban gama warkewa ba, tabani kiji..."

Murmushi tayi ta dauke kai,

"Kai yarone, kuruciya na damunka wallahi akan me zan tabaka?"

Murmushin shima yayi,

"Au hakane yarintar? Shikenan"

"Kasan me? Maganar biki a ina zaka zauna ne?"

"A ina zamu zauna dai, can ne transformer uku sabuwar unguwar nan amma gidan bawani babba bane dai"

"Ba matsala indai dakunan sunkai biyu zuwa uku"

Gyara zamansa yayi yana kallonta,

"Daki dayane kwal..."

"Daki daya fa?"

"Ehh mana"

"Hmm lallai, to kai a ina zaka rinka kwana"

Dariya tambayar tabashi da kunya lokaci guda shiyasa ma baice komai ba, itama share maganar tayi kamar yadda yashare amma aranta cewa take,

"Ai kuwa yaro garama tun wuri kanemi wurin kwana amma banda inda nake"

Ganin lokacin sallar ishah yayi yasashi yi mata sallama domin tafiya, abubuwan da takawo masa baici ba tayi masa packaging dinsu tabishi dasu, bai musaba yakarba yatafi, yana zuwa gida dakinsu kawai yabude yasaka kayan aciki yayi alwala yawuce masallaci, bayan an idar tare da baba suka shigo gidan baba na tambayarshi abubuwan da yanzu ginin nashi ke bukata, kamar koda yaushe nan suka baje atsakar gida suka sha hirarsu har 9 nadare sannan yashiga daki bayan yarufe kofar gida. Wanka yafara yi sannan ya dauki sakon da bilkisu tabiyoshi dashi, farfesun kayan cikine yasha kayan kamshi da lemon kankana mai dankaren sanyi sai ruwa, duk da yasan zaiyi wuya ace itace ta girka amma yana fatan hakan shiyasa ma yazage ya cinye tas, saida ya dan zazzage cikinsa sannan ya kwanta, wayarshi yadauka yakunna recording din da yayi na programs dinta nan muryarta radau ta bayyana, haka yarinka bi daya bayan daya yana saurara.....




*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!*



*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


*15*

*Kamar da wasa na siyarwa ne duk mai ra'ayin karantawa ta biya saita karanta, masu fitar min da book kuma kusani Allah yana ji kuma yana gani sannan yana jiran kowa a madakata*


****Akwana atashi alamari sai kara matsowa yake bilkisu ji take kamar tayi hauka domin har yau bata samu hamood ba amma tasawa ranta ko ranar dauren aure ne hamood yadawo mata tilas tafasa auren fahad ya aureshi, duk wasu shirye shirye tuni anfara su domin fita kunyar jama'a musamman ma bakin da za agayyata, su Hindu kuwa kusan kullum suna hanyar gidan abin nema yasamu, amaryar dai kawai tana binsu ne amma har cikin zuciyarta bata son wannan auren kawai dan dai ta gujewa jarabar iyallo da auren ya mudan ne.

Ango fahad kam abangarensa komai yana tafiya daidai yanzu hakama adaren jiya salim ya rakashi yaje kasuwa suka siyo akwatunan da za azuba lefen aciki, saida yaduba mai tsada ajin farko wanda baza araina ba sannan yabiya kudin danma yasamu ragi kasancewar shagon baffa ne yayan salim,akwatuna guda biyar yasiyo har dan kit na shida kalarshi pink mai haske sosai sai walwali da kyalli yake, dakin mamuh yakai domin acan ake tara kayan wanda kusan yanzu komai yagama haduwa sai dan abinda ba arasa ba, kowa saida ya yaba da wadannan akwatunan domin sunyi mutukar kyau, shifa yanzu wani girma yake jin yazo masa saboda zaiyi aure. Daren ranar baiyi bacci da wuriba sai wurin 2 nadare, washe gari bai fita shagoba sai yamma dan har saida yayanshi Abba yadawo ya iske shi agida,yana dakin yana baje akatifa amma ba bacci yakeyi ba idonshi biyu,

"Kaga ango... Saura wata nawane?"

"Saura yan satittika fa, saura sati nawa zakace ba wata nawa ba?"

Dariya Abba yayi yanemi wuri ya zauna bayan ya cire rigar jikinshi,

"To Allah yanuna mana ashe abin yazo"

"Yazo gaskiya domin saura kiris"

Dariya Abba yayi saboda shi gaba daya kallon abin yake kamar a mafarki wai fahad ne zaiyi aure. Da yamma yana shago yayiwa bilkisu text ya sanar da ita za akawo lefe nanda kwana biyu domin ayiyah tace yakamata akai kayan haka nan tunda yan uwa da abokan arziki sun gama gani, dawo mishi da reply tayi tace Allah yakaimu, wani text din yasake tura mata wai wanne colour din fenti zai yiwa gidan nanma tadawo da reply tace light purple. Bayan faruwar haka da kwana biyu aka shirya kai lefe tun ana igobe za akawo lefen iyallo aka sauka itada yafendo domin akarbi komai dasu, yan uwan ammah kuwa sai ranar da za akawo lefen sukazo da safe, anyi hidima iya hidima sannan annuna bajinta domin anyiwa baki tanadi na musamman, mamuh da anty Fauziyya da Anty asabe ne suka kawo lefen sai maman su salim da matan yayun su fahad guda biyu juwairiyya da kubra,

Acan gidansu bilkisu kuwa gida cike yake da mata ita kam tana daki ita da khulsum bayan sun dawo daga aiki, su maama kuwa ba zama ana can ana raping din soye soyen da za abaiwa baki tun safe suke aiki itada su Hindu ammah bata saka musu ko hannu ba sai dai tazo taga me ake ta komawarta daki wurin baki. Misalin karfe biyar na yamma baki suka karaso hajiya iyallo da guda da shewa ta taresu nan aka soma shiga da akwatina falon ammah inda yan karbar kayan suke, sosai lamarin ya kayatar domin kowa sun girmama kowa, gwaggo badiya kanwar ammah me bimata itace takawo tukwicin dubu talatin ta basu,basu bar gidanba sai jikin magriba dauke da garar arziki nan kowa ya raja'a wurin kallon kayan banda su meenah dake can dakin bilkisu suna tasu shaftar ita kuma Hindu na kwance tunda suka gama wadannan soye soyen kanta ke juyawa,

"Amarya kodai da bayani ne?" Inji khulsum, dariya maama tayi tace,

"Ai ba ita kadai ba har dayar itama dazu tagama amanta yanzune ta warware..."

Caraf meenah tayi tace,
"Kai Anty mama kiji tsoron Allah.... Maine fa yahau min kai"

Ita dai bilkisu na zaune tana jinsu tana bin kowa da ido bata uhm bare um um, tasan da ace hamood ne yakawo mata lefe yau ai da farin cikin da zata tsinci kanta aciki Allah kadai yasani amma bata fitar da ran hakanba agaba tunda idan da rai to da rabo.

Sai dare suka samu zarafin kallon kayan bayan mutane sun baje domin hatta yan uwan ammah adaren suka tafi yanzu sai su iyallo, bilkisu na saman kujera sukuma su khulsum suna gaban akwatunan suna kallon kayan daya bayan daya, saida suka gama tsaf sannan ta raka khulsum tatafi da tadawo dakinta tawuce bata koma wurinsu maama ba domin ita kadai tasan abinda take ji.

Ango dai abangarenshi yagama komai duk da har wata yar rama yayi kadan saboda stress danma yanada mataimaka, ko shago yanzu ba sosai yake zuwa ba, shiyasa lokacin da salim yakai musu labarin wai fahad zaiyi aure abin yabasu mamaki duk sai suka fara zargin to ko husnah zai aura amma sai salim yace musu a'a wannan watace daban basu ma santa ba. Saida biki yarage saura sati daya yana shago yana dinka farar shaddar da zai saka ranar daurin aure saiga husna, daga cefane take tabiyo ta shagon dama arana takan zo shagon nan sau biyu ko sau uku,

Su biyune ashagon daga shi sai kanin hamza dake koyon dinki, sauri yake yagama yatafi gida domin ayiyah na nemansa,

Zama husna tayi gefenshi dayake akan benci yake,

"Prince... Yakake"

"Lafiya husna, ya karatu?"

Kayan dayake dinkawa ta kalla sai kuma ta kalli bakar ledar dake gefen keken da tarin invitation card aciki, babu bata lokaci takai hannu ta dauko kafin ya fauce har ta matsa tana karantawa tiryan tiryan, idanuwanta ne suka cika da kwalla ganin sunanshi baro baro ajiki domin harda saka Prince in bracket, ai cefanen da tashigo dashi shagon nan tatafi tabarshi tana kuka fahad yanata kiranta amma taki ta ko waiwayo, duk kuma yau sai yaji tausayinta ya kamashi ganin akanshi take wannan kukan, duk da yana saurin yaje gida amma hakura yayi yakira Salim dan ya rakashi school of nursing wurin husnah, kayanta da tabari yadaukar mata yatafi mata dashi, yakirata yafi sau biyar amma bata dauka ba tana kwance tanata kuka yan dakinsu kawayenta sai rarrashinta sukeyi amma taki yin shiru fiyeda mintuna talatin kenan take kukan nan, ganin taki daga wayarshi sai yatura mata text akan tayi hakuri tazo yana son ganinta, wannan shine karo nafarko da yazo wurinta har cikin makarantarsu amma ita kullum sai taje wurinshi kaf kawayenta babu wanda bai san prince ba yan dakinsu kuwa da sunanshi suke kiranta saboda kowanne bango dake jikin dakin sunanshi ne rubuce da marker, idanuwanta sunyi jajur tafito tazo wurinshi suna tsaye shida salim amma shi yana kan roba roba din Salim da alama shine ya tukosu yakawosu,

Wani sabon hawayene yazubo mata lokacin da sukayi ido hudu dashi,

"Husnah menene abin kukane? Meye zaki tada hankalinki?"

Harara ta watsa masa batare da tayi magana ba, murmushi Salim yayi yasa baki cikin sigar lallashi yace,

"Kiyi hakuri husnah, kedai prince kikeso to ko yayi aure karki duba aurensa kawai kidubi soyayyar da kike yimasa saboda rayuwa tsarice daga ubangiji tayuyu ke ata biyu zakizo, wannan ba matsala bace, ki kwantar da hankalinki dan Allah..."

Kalaman Salim sunyi nasarar dan rage mata radadin da takejin zuciyarta nayi amma har lokacin taki koda kallon fahad, har Salim yagama tsarata tasauko bata kalli fahad ba, da zai bata ledar ta wacce ta baro ashago bata kalleshi ba ta karba, tura babur din yayi yamatsa kusa da ita kamar zai takata ai kuwa babu shiri takai masa duka duk da idan tayi masa irin wannan hade fuska yake yau murmushi yayi yace,

"To ki dan kalleni mana husnah tah..."

Ai kuwa kalmar tayi mata dadi shiyasa babu bata lokaci ta dan warware harda su kyalkyala dariya ganin haka yadauki Salim suka tafi, shidai yasan baya son husnah amma yau yana tausaya mata domin tanuna masa iyakar soyayya tun ranar da tafara zuwa shagonsu taganshi tafara sonshi duk da fada yafi yawa cikin mu'amular tasu saboda ita bata kunyar tabashi agaban kowaye ko yanzu kafin su baro wurinta saida ta dafashi ta hanyar dora hannunta kan nashi,

"Gaskiya akwai matsala fa, dan wallahi yarinyar nan dagaske take sonka"

"To ya zatayi sai dai tayi hakuri tunda nidai aure zanyi"

"Sai ka kara da ita"

Dariya fahad yayi,

"So kake bilkisu ta korene daga gidan kenan"

"Kaida gidanka taya zata koreka"

"Allah

Please Login or Register in order to submit comment