Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zuwa yanzu ta fasa kwanuka da dishes babu adadi ita dai bilkisu bata taba yimata magana ba saboda badashi tazo ba kayan hamood ne kawai dai ansiyane da sunanta. Satin wasila biyu da yan kwanaki bilkisu tasamu hamood akan maganar tafiyar wise, karkatar da hular kansa yayi ya kalleta,

'Gaskiya kiyi hakuri dan ko zata tafi ba yanzuba saboda amfaninta yafi naki yawa agareni domin awajenta nake samun nutsuwa..."

Daga haka yasa kai yafita dama lokacin ficewa zaiyi, wannan maganar ba karamin ciwo tayi mata ba dan har kuka tasata daga karshe ta rarrashi zuciyarta aranar da yamma sukayi waya dasu elmustapha suke fada mata saura kwana biyu su koma Sudan shiyasa ta daura aniyar zuwa gida gobe domin suyi sallama,tun adaren ranar ta sanarwa hamood shiyasa washe gari tayi asubancin zuwa gida domin 9 acan tayi mata koba komai zata samu sassaucin zaman kuncin da take ciki, kowa nagidan yazaci laulayi ne yamaida ita yanda take ayanzu ita kuma bata sanarwa da kowa ba, acan duk su hindu suka sameta shiyasa tasake cikinsu sunata cafta sai daf da magrib takoma gida tana shiga bedroom dinta tayi turus saboda gaba daya aburkice yake akwatunan lefenta babu ko daya sannan laptop dinta dake kan bedside drewar itama wayam gashi da alama komai nata mai daraja dake cikin dakin anyi gaba dashi......




*littafin Kamar da wasa na siyar© *HASKE WRITERS ASSO.*



*KAMAR DA WASA....!*



_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*32*


*Littafin kamar da wasa na saidawa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



***A mutukar razane tafita daga dakinta ta nufi na hamood shi dai bata ga wata alama dake nuna cewar anshigar masa dakinba sai dai bata da tabbas, sake fitowa tayi tanufi wurin mai gadi hankalinta atashe nan ta fara tambayarsa suwaye da waye suka shigo gidan amma yace mata babu kowa yau kwata kwata ma basuyi baki ba wasila ma tun safe itama tabar gidan har yanzu kuma bata dawoba haka shima hamood,

Cike da damuwa takoma cikin gida ta nemi wuri ta zauna afalo tana jimami duk kuwa da kiraye kirayen sallar da ta jiyo anayi a masallatai daban daban, to kenan barawon ko kuma barayin ta katangar baya suka shigo? Ta tambayi zuciyarta asirrance, bata samu ta motsa daga inda take zauneba su hamood suka shigo shida wise kamar kullum hannunsu sakale cikin na juna, mikewa tsaye tayi,

"Hamood yau gidan nan babu lafiya... Barayine suka shigo, gaba daya sun kwashe min kayana na lefe da laptop dina harda agogona na gold...."

"What....?" Yafurta da karfi, ai tun kafin tasake magana yanufi upstair da sauri gudu gudu, yana zuwa yashiga bedroom dinshi mintuna kadan yasauko hankalinsa amutukar tashe,

"Kai... To ai nima harda dakina suka shiga, kudin wata mota da na siyar shekaran jiya nazo dashi gidan nan sun dauke.... 7 hundred thousands cash..... Ohh my God"

Wani wulakantaccen kallo wise ta watsa musu su duka biyun kafin ta yi gyaran murya,

"Hmmmm haba dear... Wai kai baka gano game dinba har yanzu? Tab..."

Kallon wise yayi idanuwanshi sun fara yin jaa,

"Me kike nufi?"

"To ai wannan abune abayyane kuma afili... Kawai dai matarka sun hada baki da barayi sun shigo gidanka sun yasheka idan bahaka ba tayaya akan san kashigo da kudi? Sannan tayaya zasu iya haurowa gidannan har su shigo batare da anyi guiding dinsu ba.....?"

Zaro ido bilkisu tayi cikeda tashin hankali sakamakon jin sharrin da wise ke neman kulla mata, shi dai hamood bai sauraresu ba yayi waje da sauri,

"Ke mahaukaciyar inace? Me mijina yayi min da zan hada kai da wasu har in cutar dashi?" Bilkisu tafada tana huci,

"Karyar banza, mijina mijina... Mijinki a ina? Mijin da bai damu dakeba.... Sannan ni kika kira da mahaukaciya ko? To bari innuna miki ni din cikakkiyar mahaukaciya ce...."

Kafin Bilkisu tayi wani yunkuri sai jin abu tayi agoshinta tauuuu take hankalinta ya bar jikinta na wucin gadi, jin duka kawai tayi tako ina, ita ba ma'abociyar fada bace domin rabonta da dambe harta manta,ko lokacin da tana yarinya batayi rayuwar fada ba bare yanzu shiyasa wise tasamu galaba akanta kafin hamood yashigo tayi mata laga laga duk ta kumbura mata fuska ga goshinta dake tsiyayar da jini sakamakon kwada mata flate din silver da tayi awurin, dakyar hamood ya iya banbare Bilkisu daga hannun wise wacce keta faman gwarata abango duk ta yayyaga mata kayan dake jikinta, cikin bedroom dinta ya turata ya rufe sannan yazo ya kama Bilkisu yashigar da ita dakinta dake sama, suna shiga tafashe da wani irin kuka mai cin rai gamida ban tausayi.


****

Sosai jikin fahad yayi kyau kuma ya samu sauki sai dai har gobe akan magani yake kullum sai yasha wasu kwayoyin magani kanana guda uku, yana kwance shi kadai acikin daki domin ya abba yakoma makaranta wayarshi na hannunshi ya tsurawa pic din Bilkisu ido wanda aka yimata ranar bikinsu,

"Wai dagaske Bilkisu kin barni...? Dagaske shikenan narabu dake? Dan Allah Bilkisu kidawo gareni,ki tasheni daga wannan mummunan mafarkin da nakeyi.... Dan Allah ki tasheni kice mafarkine ba gaskiya ba, Bilkisu kice min duk abubuwan da suka faru acikin mafarki ne, wallahi ina sonki.... Ina sonki Bilkisu....."

Salim dake tsaye akansa kawai ido yazuba masa yana kallonsa aransa yana tambayar kansa wannan wacce irin jarrabawa ce abokinsa ke fama da ita? Wai har yanzu yakasa daina son Bilkisu, ohh Allah....,

Fauce wayar dake hannun fahad yayi sai lokacin fahad din yayi firgigit alamun dawowa daga duniyar tunani, kan screen din wayar salim ya kalla hoton Bilkisu ne rangadadau gashi nan tasha mutukar kyau girgiza kai salim yayi yazauna kusa da fahad wanda ke goge hawayen idonshi cikin dabara gudun kada salim din yagani sai dai kashh ya makaro domin salim din yajima da ganin hawayen da yake zubarwa tun lokacin da yashigo cikin dakin,

"Kasan Allah? Zaka kashe kanka abanza akan wata aba banza wai ita soyayya.... Ya zaka zauna kayita kukan zuci da na fili akan so? Wallahi idan baka daina wannan tunanin ba kadai ji abinda Dr yafada maka ko jiya da na rakaka yace idan har baka bar damuwa da tunane tunane ba wannan hawan jinin naka zai janyo maka ciwon zuciya...."

Sake goge hawayen yayi da bayan hannunshi yakawar da kanshi gefe batare da ya kalli salim ba ya runtse idanuwansa,

"Salim wallahi nayi kokarin yin hakan amma nagaza, nakasa cireta araina, nakasa daina tunaninta, nakasa daina ganinta acikin mafarkina, nakasa salim, nakasa, nakasa daina sonta..... Meyasa Bilkisu zatayi min haka?"

"Kai ai banza ne wallahi, anfada maka haka ake so? Anfada maka haka ake soyayya kamar za amutu idan aka rabu? Wallahi ka maida hankalinka, matar da tajima da mantawa ma dakai shine zaka zauna kana westing din time dinka abanza kana tunaninta..."

Tashi zaune fahad yayi yana fuskantar salim,

"Malam karka sake ka zage ni ko ka zagar min mata..."

Dariya salim yayi wacce tasake kular da fahad,

"Lallai kuwa, kasan wani abu? Ai dai pics dinta kake zama kullum kasaka agaba kana kallo ko? To insha Allah daga yau zaka daina, kai wai mekakeson jawowa kanka ne? Ciwon zuciya ko tabin hankali? Anya wannan bilkisun ba asiri tayi maka ba kuwa? Wallahi karaba kanka da soyayya..."

Daga haka yamike zai fita daga dakin,

"Dallah malam ban wayata..."

Juyawa salim yayi ya kalleshi,

"An hanaka, ai wallahi ko zan baka wayar nan sai nagoge hotunan Bilkisu gaba daya...."

Tun kafin yakarasa fahad yadaka tsalle yabishi amma ina bai iya cimmasa ba domin aguje yabar gidan har kofar gida fahad yabishi ganin bazai iya kamashi ba yasa ya hakura yatsaya yarike waist yana haki gashi baya son fita cikin unguwa ahaka domin daga shi sai gajeren wando da t shirt, cikin gida yakoma yashiga daki yayi wanka yashirya sai faman fushi yake, aransa yana cewa idan har salim yagoge masa hotunan Bilkisu to zasu samu babbar matsala, yana shiryawa yana tunani, adaki yayi sallar la'asar sannan yashiga cikin gida wurinsu ayiyah, mariya na shirin tafiya islamiyya yayinda maryam tuni har ta dade acan, dundu ya zuba mata yana fadin,

"Uwar nauyi kullum kece karshen tafiya makaranta kiga maryam tajima da tafiya amma ke sai kinyi makarar da kika saba..."

"Ya fahad Allah hadda na tsaya yi idan naje ban iyaba dukana za ayi.."

"Wai zaki wuce kitafi ko sai nayi ball dake..."

Dasauri tawuce tabar gidan bayan tasaka takalminta, falon mamuh ya leka tana kwance tana jin shirin wasan kwaikwayo mai suna madubi hoton kowa wanda ake gabatarwa atashar freedom radio,

"Mamuh dan Allah me zan samu? Allah yunwa nakeji"

Dagowa tayi ta kalleshi,

"Au ai nazaci baka janye yajin aikin cin abincin da kakeyi ba, shiyasa yau ban raba dakai ba tunda naga ko anbaka baci kakeyi ba..."

Dariya yayi yasaki labulen bayan yakarasa shiga cikin dakin,

"Nidai dan Allah abani wani abu inci kar kuma ulcer ta kamani"

Mikewa zaune tayi tana rage karar sautin radion ta,

"Ai dole abaka abinci dan auta, gaka kuma shagwababbe.... Ohh su fahad ankasa daina baci..."

Shidai yana jinta baice komai ba har ta miko masa kwanon abincin, dan waken fulawa ne subil subil dashi kanana kanana nan tamiko masa robar yaji da ta mai da maggi, dama yau ayiyah bata nan tana can kura tatafi biki kuma sai gobe zata dawo,

"Wai mamuh dan Allah meke rage damuwa ne? Menene maganinta?"

Saida tagyara zamanta takashe radion da take sauraro gaba daya sannan ta amsa masa,

"Fahad hakuri da addu'a sune suke jagorancin maganin kowacce damuwa, duk abinda yasamu bawa mutukar zaiyi hakuri kuma zaiyi addu'a to da yardar Allah zakaga ubangiji ya yaye masa damuwarsa... Kowa na duniya da kagani yanada damuwarsa daban wacce ke damunsa sai dai kawai fadane bazai yiba amma idan da ace wani zai fito yafada maka damuwarsa sai kaga kai taka damuwar bata kai kazauna kana damuwa ba... Hakuri da addu'a sune mafita acikin rayuwa"

Rufe kwanon dan waken yayi yana gyada kai alamun gamsuwa, kallonsa tayi tana harararsa,

"Meke nan kayi? Wai kana nufin har kaci?"

Ashagwabe yadaga kai yana bata fuska saboda yasan halin mamuh yanzu sai tace sai yacinye shikuma yanzu kwata kwata baya iya cin abinci sosai domin ba dadinsa yake jiba,

"Wallahi sai ka cinye abincin nan fahad... Shiyasa dama ban bayar ankai maka dakiba dan ba lallai kaciba kokuma kaci kwaya biyar kabaiwa almajirai sauran kazo kayi karyar kaine ka cinye..."

Tamkar zaiyi kuka yanata yamutsa fuska yasake jan kwanon gabansa yana ci, mamuh sai kara yimasa Nasiha take cikin hikima kan muhimmancin hakuri da kuma yarda da kaddara, kamar yadda tace saida ya cinye dan waken nan tass sannan yatashi cikinsa acunkushe dan tsabar koshi, ai fasa hawa babur dinsa yayi sai akasa yafita, shagonsu yaje fuskarsa babu yabo babu fallasa dama yanzu haka yakoma bai cika walwala ba, yana saman tebur din da suke yanka dinkuna tj yana yanka wani swiss material shikuma fahad yana guiding dinshi yanda yadace yayi yankan salim yazo, sallamarsa kadai fahad ya amsa daga nan yadauke kai dariya salim yayi yadafa kafadarsa,

"Abokina ga wayarka..."

"Ai da ka rike gaba daya kaga saika kasheni da hujja..."

Dariya maganar tabawa salim ya kalleshi,

"Ga dai mai neman kasheka can shiyasa nagoge hotunanta dan nafuskanci wallahi sonta na iya zama ajalinka idan har kayi wasa..."

"To idan tazama ajalin nawa sai me? Ina ruwanka?"

"Da ruwana mana tunda mu zata jawa asara kullum baka da aiki sai dai kasa hotonta agaba kullum kayita kallo kana hawaye... Allah prince kashiga hankalinka karage son nan da kake yimata saboda ina tsoron kar ciwon nan naka yasake tsananta..."

Banza fahad yayi dashi yawarci wayarsa yasoma duba folder din da hotunan Bilkisu suke amma duk empty wato salim dagaske yake yagoge din kenan? Goshi yadafe yana jin bacin ransa yana karuwa, duk maganganun da salim keyi masa baya tankawa dan yadau fushi sosai dashi daga karshe ma bar masa wurin yayi yasauka kasa yashiga masallaci yayi kwanciyarsa sai da lokacin salla yayi sannan yafita yayi alwala, bayan an idar da salla yafito salim na bayansa yamika masa hannu suyi musabaha amma yaki, shi salim ma dariya fahad kebashi wallahi, sanin idan yaje gida tunanine zai addabi ruhinsa yasashi tunanin inda yadace yaje kamar yaje wurin husnah sai kuma yatuna ashe sufa yan school of nursing 6 nayi ake rufe musu gate bashiga ba fita, majalissin marigayi sheikh ja'afar yaje inda wasu dalibansa guda biyu ke gabatar da darasi kowacce rana daga bayan sallar magrib zuwa lokacin sallar ishah sosai hakan yadebe masa kewa bayan an idar da salla yatashi zuciyarsa wasai sai dan abinda ba arasa ba, salim sai kiran wayarsa yakeyi amma yaki dagawa daga karshe kuma kiran husnah yashigo itama bai dauka ba har saida kiran yakatse sannan ya kirata, a dakalin dake kofar gidansu yazauna sunata waya da husnah basu taba doguwar waya irin ta yauba har wurin karfe 9,baya son shiga gida yanzu domin yasan muddin sukayi ido hudu da mamuh sai tasashi yaci tuwon dare shikuma akoshe cikinsa yake, yana kokarin tashi yaya Auwal yafito daga cikin gidan wato babban yayansu mijin anty fauziyya,

"Lahh.... Yaya yaushe kashigo gari?"

"Ba tun dazu naketa jiranka agida baka shigo ba... Wai yanzu me kake shiryawa ne?"

"Yaya karatu fa zan koma"

"A ina?"

"Wai da maryam abacha nakeson tafiya ko Ogun state ance akwai wata private university acan..."

"Kai dalla rufewa mutane baki, kaje kayi applying a federal university Kaduna kacike D E saboda karka makara, kaga kusa da gidane kacike duk course din da ranka keso...,sai da safe"

"To shikenan yaya agaida su anty"

Daga haka sukayi sallama yawuce shikuma yaci gaba da zama awurin yana jin baida mafitar da tawuce abinda yaya auwal din yafada yazama dole yabar garin kano koda zuwa kadunan ne.......



*_Ummi Shatu_* wane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!.*



_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*




*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



*33*



***Cigaba yayi da zama awurin bai shiga gidaba har saida yaji sauro ya takura masa da cizo sannan yatashi yashiga ciki, bai shiga wajensu mamuh ba yashige dakinsu kawai yayi shirin bacci ga mamakinsa sai yau yaji baccin ya kauracewa idanuwansa domin aduk dare yasaba yasa hoton bilkisu yayi ta kallo har sai bacci ya daukeshi amma yau gashi babu salim yagoge masa komai,

Juyi yayi cikeda takaici sannan yaja wani guntun tsaki, haka yayita juye juye yana faman zuba tsaki har wurin karfe 12 ganin baccin yaki zuwa yasashi kiran ya abba bugu uku zuwa hudu kuwa yaji yadauka,

"Kanina bakayi bacciba? Ina fata dai ba damuwace ta hanaka bacci ba?"

Sai da yajuya daga kwancen da yake zuwa rigingine sannan yayi murmushi mai dan sauti,

"Ya Abba wallahi al'amarinne sai ahankali yau fari gobe tsumma...."

"Fahad hakuri zakayi fa, kayi kokari karage damuwa kaga condition din da kake ciki ayanzu haka...."

"Insh Allah, yanzuma kasa bacci nayi shine nace bari natabo abokin kwanana inji ya yake ciki...." Yakarashe maganar cikeda tsokana hakan yabawa Abba dariya,

"Ni test guda biyu gareni gobe shiyasa nazauna ina dan taba boko....."

"Allah yabada sa'a, yi bokonka nima bacci zanyi.... Saida safe"

"Shikenan amma pls karka yawaita tunani.."

"Insha Allah babban yaya..."

Daga haka sukayi sallama yajefa wayar karkashin pillow ya lumshe idanuwansa, yasan har yamutu bazai daina son bilkisu ba domin sonta acikin jinin jikinsa yake mutukar za arabashi da sonta to sai dai arabashi da numfashinsa wannan dalilinne yasashi yin mafarkinta awannan daren irin mafarkin da bai taba yiba wai ga mutane nan cike dam akofar gidansu bilkisun koda yaje sai yahango bilkisu tsugunne a tsakiyar mutanen ta hada kanta da gwiwa ba aganin fuskarta agabanshi wani yazo ya kama hannunta yatafi da ita alhalin fahad yanata kiranta fuskarsa sharkaf da hawaye amma bata ko waiwayo ba, shiyasa lokacin da yafarka da asubah jikinsa jike sharkaf da gumi duk kuma asanyaye, haka yatashi babu kuzari yashiga toilet, bayan yafito yana kokarin saka jallabiyarsa yaji baba na buga masa kofa, fita yayi suka fita masallacin tare, sai da yadawo daki yakwanta bayan yadawo daga masallaci sannan mafarkin da yayi yasoma dawowa cikin kwakwalwarsa,

"Meke faruwa da bilkisu.... ?" Shine tambayar da yake ta yiwa zuciyarsa, kasa komawa bacci yayi haka yazauna shiru yanata sakar zuci zuwa can yajawo wayarshi yasoma bincikar ajiyayyun muryoyin da ya adana nata amma su dinma wayam babu ko daya kwafa yayi da dukkan karfinsa yana jin haushin salim na sake turnikeshi,

"Wato har voice din nata ma duk yahada yagoge? Sai nayi maka wulakanci salim.... "

Daga haka yakunna radion wayarshi ko zai dan debe kewa yarage kadaicin da yake ciki, har ya dan fara bacci sama sama yaji kamar amafarki acikin radion ana cewa,

_"Zamu yi amfani da wannan damar wurin taya abokiyar aikinmu wato Bilkisu Lukman Aliyu murnar daurin aurenta tareda zankadeden angonta wato ma'arufi sha guda Hamood Ahmad barewa, muna addu'ar Allah yabasu zaman lafiya yakawo kazantar daki....!"_


Shiru yayi yana saurare har aka kammala sanarwar wasu zafafan hawayene suka ziyarci fuskarsa yana sake maida hankalinsa kan wakar nazifi asnanic wacce ke tashi,

_Na barki ya zan da raina.... Ban kwana...,sai watara na cewar bakina...., ban kwana...., amma kamarki ni ban mancewa.....,ban kwana, ko dare ko ko da rana, sai wata rana nasake fada ban kwana sai wata rana rabin jikina... Ni dake ayau muyi ban kwana sai wata rana rabuwa ba mutuwaba yar uwa rabin raina ban so muyo rabuwa.....!._

Kashewa radion yayi nan yadaga wayar da niyyar bugata da bango amma kuma ko me yatuna oho sai yafasa ya cillata gefenshi,hawayen takaici yaci gaba da zubarwa har na tsawon wani lokaci.

Yana nan kwance jikinsa babu kuzari yaji wayarshi tana vibrating kamar bazai dauka ba sai kuma yajawo yadauka yana goge hawayen idonshi,

"Yan mata...." Yafada muryarshi asanyaye, jin abinda yace yasa husnah murmusawa,

"Ya fahad ina kwana...?"

"Morning dear, how was ur night?"

"Fine sweet heart, dama nakiraka ingaidaka ne...."

"Nagode, me kikeyi yanzu?"

"Na shirya ne zan fita lecture amma ba zama zanyi ba saboda ina son zan shiga kasuwa insiyo lace zan kawo ka dinka min,ranar friday zanje Kaduna..."

"Bari nayi wanka zanzo inrakaki.... Idan kin fito daga lecture din just call me"

Daga haka yatashi ya shiga wanka domin yanzu ya kudurtawa ransa mantawa da bilkisu tunda har itama tamance dashi to babu amfanin yazauna yana damuwa akan wanda bai damu dashiba,da yardar Allah wannan zai kasance karo na karshe da zai zubar da hawaye akan soyayyarta. Wanka yayi yashirya yasha turare sannan yashiga cikin gida yanata kokarin danne damuwarsa sunata raharsu da mamuh ya karya da wainar shinkafa miyar taushe da ruwan zafi yana gamawa yatashi yafice, cikin plaza yaje ya ajiye babur dinsa sannan yataka da kafa zuwa school of nursing domin daga nan din zuwa can baida wani nisa yana hanya husnah ta kirashi tana sanar dashi gata nan fitowa,

Yana zuwa daf da gate din makarantar ya hangota sanye cikin uniform dinta fari tass da dan farin hijabinta marar girma sosai sai bakin toms akafarta da side bag dinta itama baka, jingina yayi da jikin bangon gate din yana kallonta tana tahowa gareshi tana magana awaya, tana zuwa ta tsaya gabanshi suna kallon juna kowannensu fuskarshi dauke da murmushi ahaka tagama wayar tana kallonsa sanye cikin kananan kaya jar t shirt da bakin wando da bakar p cap sai jan sau ciki akafarsa da jan agogo yana sakale da earpiece acikin kunnenshi, sosai yau dinnan yatafi da ita over duk da idanuwanshi sun danyi luhu luhu, can kasan makoshinta tafurta,

"Prince kayi kyau sosai..."

Saida ya lumshe idanuwansa sannan yabudesu akanta,

"Kin fini yin kyau ai..., muje ko"

Tare suka jera akafa suka nufi plaza har shagon da zata siyi leshin saida tazabi wanda yayi mata aka fada mata kudinshi tana niyyar ciro kudin fahad ya biya, shagon sayar da kayan dinki suka shiga yasai duk abinda zai bukata wurin dinka mata leshin, suna daf da shagonsu salim ya kalleta,

"Bakya bukatar kayan kwalliya.....?"


"Inada kayan kwalliya prince..."

"Turare fa? Ko kina dasu muje akara wasu"

Shagon su salim suka shiga nan fahad yayi tamkar ma bai san salim dinba saboda wani irin dauke kai yayi yana zaro wasu turaruka yana dorawa saman teburin dake gaban salim din,

"Nawa wadannan turarukan?"

Dariya salim yayi,

"Koma nawane ai kaima kasan dole inrage muku tunda budurwarmu za asiyawa..."

Harararsa fahad yayi yana motsa baki kamar mai son cewa wani abu amma baiyi magana ba,

"Husnah kiyiwa saurayinki fada yabar gaba dani, daga kawai nayi masa fadan gaskiya shikenan yake fushi dani...."

"Ayya ya fahad kayi hakuri ku shirya..."

Kallonta yayi nan suka hada ido tayi saurin janye nata domin ba kowacce macece zata iya jure kallon kwayar idanuwanshi ba domin akwai wani sirri na musamman aciki duk da idanuwan nashi farare ne tass,

"Babu ruwanki husnah kirabu dashi ai yasan laifin da yayi min babba ne...."

"Tom shikenan nidai nazama yar kallo tunda kunfi kusa da juna..."

Dariya salim yayi yana saka musu kayan acikin Leda,

"Abokina ashe yau soyayya ce tatashi shiyasa naganka cikin farin ciki...."

"Oho maka dan sa ido kawai..."

Da wasa da dariya suka rabu suka haura sama shagon su fahad, atake ya yanka leshin yana kallonta,

"Me Zan dinka miki? Riga da skirt ko da zani?"

"A'a kayi min da skirt"

Murmushi yayi ya dan harareta,

"Da zani zanyi miki zaifi yimiki kyau..."

Matsawa tayi kusa dashi inda yake kokarin karasa yankan kayan,

"Ya fahad banfa iya daura zaniba...."

"Ohhh husnah case... Zan rinka daura miki to"

Kafadarshi ta dan buga tana turo baki, tare sukayi yankan suka koma ciki duk inda yayi tana biye dashi kamar jela yan shagon sai dan kus kus sukeyi duk da dama sun saba ganinta wurin fahad dan indai kaganta ashagon to wurinsa tazo, har azahar suna tare lokacin sallah nayi duk suka fice sallah sai ita kadai bayan an idar fahad ne kadai yashigo amma duk sauran sun wuce sabgoginsu yana zama ta matsa tana karkade masa sumarsa,

"Ya fahad wani abune fari akanka..."

Hannunshi yasa ya kade wurin sannan yaci gaba da dinkin tanata yimasa hira zuwa can ta nisa tana niyyar yin magana yayi saurin janye hannunshi wanda allura taso datsewa,

Hannun tayi saurin kamawa tana shafa masa wurin daga ido yayi ya kalleta,

"Husnah meyasa bakya jin magana ne? Na hanaki tabanin nan amma kinki yarda nanfa ba bayelsa bane..."

"Haba ya fahad kuma dan na tabaka menene? Ai is nothing,normal..."

Saida yataka keken taku biyu sannan yadakata ya kalleta,

"Kina son wata rana nayi disvirgin dinki acikin shagon nan ko? Idan bakya so to kidaina tabani amma idan kika cigaba da tabani komai na iya faruwa dan zan iya baki baby batare da andaura mana aureba, kiyi hakuri har muyi aure sai ki tabani son ranki... Harma sai ankai level din da zakiji na isheki baki son tabanin...."

Ai tana jin abinda yafada tayi saurin rufe fuskarta ta hanyar kifa kanta kan keken da yake dinki, murmushi yayi yana cizon lips dinshi yasan dama dole taji kunya amma shi iyakar gaskiyarshi yafada mata domin idan ba haka yayi mataba to zasu cigaba da taba juna daga karshe har lamarin yayi kokarin kazanta,

"To ki daga kanki inkarasa hada miki intafi gida yunwa nakeji..." Yafada yana murmushi,

"Bari naje nakawo maka abinci...."

Kafin yayi magana tatashi tafice cikeda kunya dan har lokacin bata yarda ta bude idanunta ba, tana fita kuma saiga salim shi yaci gaba da tayashi hira har yan shagon suka dawo kafin 3 yagama dinka mata hadaddiyar skirt da riga yana kokarin mikewa sai gata tashigo itada kawarta hafsa tasha kwalliya cikin doguwar riga ta atamfa da dan mayafi, ahankali yafurta,

"Kinyi kyau princess......"

Murmushin jin dadi tayi ta ajiye masa abincin tana furta,

"Thank you"

Basu wani bata lokaci ba takarba tatafi yau dai yayi niyyar cin girkinta shiyasa yakira salim awaya yazo suci tare, jalop din macaroni da dankali yaji sadden sai kamshi yake tare sukaci shi dai fahad tsakura kawai yake saboda baya zagewa yaci abinci yanzu. Sosai al'amarinsa da husnah aka samu cigaba domin yana sakar mata fuska yanzu sabanin da ammafa har gobe bai taba jin sonta yana yawo acikin jininsa ba kawai dai yana biye mata ne kuma yanajin shakuwa mai karfi tsakaninsu.Duk da baya son karatu kusa da gida yacike D.E kamar yadda Yaya auwal yace yanzu kawai zaman jiran admission yakeyi.

***

Bilkisu kam ranar da sukayi fada da wise tayi kuka kamar me dakyar hamood yashawo kanta ta canja kaya yakaita chemist aka yimata plasta awurin aka manne da audiga da bandeji, suna dawowa kuma yakalleta yana fadin,

"Shawarar da zan baki babu ruwanki da shiga sabgar wise domin ita dambe awajenta ba komai bane sannan tafi karfinki saboda harda maza dambe take...."

Cikin masifa da jin haushi bilkisu ta kalleshi,

"To

Please Login or Register in order to submit comment