Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yayi yana cewa,

"Barka da zuwa hajiya khulsum"

"Yawwa haji fahad, ya kwanan amarya?"

Saida suka shigo cikin falon sannan ya amsa da,

"Gata nan muna bata hakuri, bai zauna ba yawuce bedroom yabar musu falon"

Kallon khulsum bilkisu tayi,

"Kekuma sai yanzu kika gadamar zuwa?"

"Kai labour yanzun bakiyi maraba da ganina ba?"

"Oho miki, ya gajiyarki?"

"Ahh gajiya ai tana tare dake hajiya, ni ai tajima da bin lafiyar jikina"

"Nima haka..."

"Gaskiyane amarsu, me kike tafasawa ne haka?"

"Wallahi girki ma na dora gashi can wai zanyi jalop din shinkafa..."

"To muje mana mu karasa, ah tashi muje"

Tare suka shiga kitchen din khulsum ta tayata suka hada komai, kayan marmarin da yakawo jiya sukayi blending dinshi suka hada banana milk shake suka saka a fridge basu kai ga sauke abincin ba Abba yazo fahad yafita yashigo dashi, kamarsu daya da fahad kuma kusan kansu ma daya dayake shima fahad din dogo ne, a falon suma suka zauna amma bilkisu tun kafin su shigo tasako hijab dinta har kasa wanda hakan ba karamin dadi yayiwa fahad ba. A mutunce suka gaisa sai lokacin takara raina girman fahad saboda koshi abban tagirmeshi kai dakyar ma idan maama kanwarta bazata fishi ba, mikewa Abba yayi zai tafi saboda yana son ya isa Maiduguri da wuri amma suka hanashi tafiya wai sai yatsaya yaci girkin amarya, dan dole yatsaya su bilkisu sukaje suka shirya table sannan tazo tace musu,

"Bismillah..."

"To godiya nake amarya" inji ya Abba,

"Ah babu komai..." Tafada tana murmushi,

"Ni gaskiya...ni gaskiya ban ganeba, ni meyasa ba agataleni" fahad yafada yana bata fuska kamar zaiyi kuka,

"Kai ai yanzu kagirma" Abba yafada cikin sigar tsokana,

"Allah ban yarda ba"

Daga bilkisu har Abba dariya sukayi ita dai tafiya tayi tabarsu saboda taga dramar tasu ba mai karewa bace kuma da alama sun saba, cikin bedroom suka shige itada khulsum suka basu waje suma suka kai nasu can, suna cin abincin khulsum na sake yimata tsiya har suka gama daidai lokacin shima fahad ya leko yace sun gama Abba zai tafi, hijab tasaka tafita sukayi sallama takoma wurin khulsum, shima fahad ta can yawuce bayan yaraka Abba, majalissar shayinsu yatafi wacce suke zama idan sun taso daga shago amma shi bawani ma cika zama yayiba sosai domin daga shago sai filin ball. Acan gidan amarya kuwa bayan fahad sun fita tareda abba babu jimawa su yaya asabe suka zo itada Anty Fauziyya fuska asake bilkisu ta karbesu takawo musu abinci da lemon da suka hada kuma babu laifi ta saki jiki da su kamar yadda suma suka sake da ita, suna nan tare sunata kallo suna hira har maman hudah tazo wato maama takawowa bilkisu kayan tarbar baki wanda yahadar da cincin, cake, alkaki sai nakiya da dubulan an dan samu tsaiko ne matar da aka bawa tayi bata gamaba sai jiya da daddare ta aiko dashi amma da tuni anjima da kawo mata,

"Ina daughter dina naganki ke daya??"

Dariya maama tayi ta zauna kan kujera suna gaisawa da su Anty Fauzy,

"Daughter ki yau tana wurin kakarta can nabarta,ya fahad baya nanne?"

"Ehh yafita" bilkisu tabata amsa tana harararta kasa masa saboda haushi suke bata idan taji sunce mishi yayan nan wallahi, ganin tasake samun yar tayin hira su anty fauzy suka yimata sallama suka tafi, ledoji ta cika musu da kayan zakin da maama takawo mata ta rakasu har kofar gida anan suke sanar da itama gidajensu zasu wuce basai sun koma gidan ayiyah ba saboda dama sun rigada sunyi sallama, wurinsu khulsum takoma bayan taga tafiyarsu nan hira ta barke bare yanzu sai su kadai har magrib suna gidan ta hanasu tafiya tace sai fahad yadawo. Bayan sallar magrib kuwa babu jimawa sai gashi yadawo yana rikeda CD flate din bikinsu da yakarbo, maama yaya sama yaya kasa ta ringa kiranshi dashi dama suna shiri sosai musamman ma dayake tana kamada bilkisu fari kawai tafi bilkisu duk dinsu ma sun fita haske saboda ammah suka biyo ita kadaici ta dauko kalar abba tayi baki amma bakin shima bawani can dayawa ba sai dai baza asata alayin farare ba, ganin yadawo suka yimusu sallama suka fita ai harda fahad arakasu kofar gida bayan sunga tafiyarsu suka koma ciki lokacin babu wuta saida fitilar wayarshi yayi amfani ya haska musu suka shiga ciki, tana shiga taga wayarta dake kan kujera tana kara tana dauka taga su elmustspha ne,kamar yadda tazata saida tagaji da surutunsu dakyar sukayi sallama ta kashe wayar tana kallon fahad wanda ke jiranta ta kammala wayar,

"Yadai?"

"Akwai abinci ne?"

"Da akwai guntu, kacinye ma kawai"

"To kekuma fa?"

"Karka damu zansha tea ya isheni"

"Shikenan..."

Dining yanufa ita kuma ta kishingida jikin kujerar tana dora rayuwar duniya a ma'auni na zahiri ba badini ba. Har ya gama cin abincin yadawo cikin falon bata bar tunani ba saida yazauna ya murza yatsunshi guda biyu asaitin fuskarta sannan ta dawo hayyacinta ta kalleshi,

"Ranki yadade lafiya kuwa?"

Ajiyar zuciya ta sauke,

"Lafiya lau kawai dai nagajine wallahi"

"To kije kici abinci mana ki kwanta ki huta"

"Gaskiya kam haka yakamata inyi bari natashi"

Tea taje ta hada tadawo falon ta zauna tasha zafi kuwa yace muje zuwa daki tashiga domin wanka zatayi ta kwanta tana cire kaya yadanno kai bayan yaturo kofa, tukwicin harara yasamu shiyasa cikin azama yafada toilet yayi alwala yafito bai yadda ya kalli wurin da takeba yafice daga dakin bayan yadauki abin salla,

"Haka kawai wai mutum da halal dinshi amma ayita nuna masa fin karfi da iko..." Haka yaketa fada cikin kunkuni lokacin da yafita falo, abin sallar ya shimfida yatada kabbarar sallar ishah. Dan neman fada bai shiga dakinba saida ya daidaici ta kwanta domin yaga yadaina ganin haske sai duhu alamun takashe fitilar data kunna, tashi yayi ya dauki abin sallarshi yanufi cikin dakin yasan bata son haske gashi tun yana salla aka dawo da wuta amma ita bata saniba,yana shiga ya lalubi makunna ya kunna nan wani fitinannen haske ya gauraye dakin, dan karamin tsaki taja tayi saurin rufe jikinta,

"Wai dan Allah menene haka? Shigo min dakin da kayi cikin wannan lokacin bai isheka ba har sai ka kunna min haske..."

"Yi hakuri dama nazaci ko baki san andawo da nepa bane..."

"To da aka dawo da ita me zanyi mata? Ko nace maka ina bukatane?"

"Ni na san abinda zakiyi da itane madam.... Nidai kawai na fada mikine"

Banza tayi masa ta juya baya tayi kwanciyarta,

"Malam idan kagama nidai ka rage min hasken nan ya takura min..."

"Nima ai kin takura min..." Yafada cikin kunkuni, bata bi takanshi ba ta mayar da idonta tarufe, saida yagama jula jularshi sannan yakashe yashiga wanka, acan yashirya yafito yana ta kukkumbura baki kamar tana ganinshi, acikin duhun ya kwashi kayan shimfidarshi yayi falo yaje ya shimfida a position din jiya sannan yakoma ya dauki pillow irin daukar nan na ehh ina cikin fushi dan kawai fincikar shi yayi yai gaba,

"Ahh malam menene haka? Karka yaga min pillow mana..."

Yaji tace yana daf da isa bakin kofa,

"Sai anyaga din" sai dai shi tashi maganar yadda bazata jiyoba yayi, bude kofa yayi yafita yaje ya kwanta,

"Haka kawai dan kinga kin fini shine zakiyita takura min.... Allah sai nima na rama wata rana tom"

Shi kadai yake maganarshi har yagaji yahakura yayi shiru, yauma kamar jiya raba dare yayi yana chaten daga bisani yasauka yayi addu'ar bacci.....


*Book dinnan na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta.*



*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA....!*


*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*21*



***Yau anyi sa'a bai tashi da daddare ba saida asubah lokacin har anshiga masallaci, alwala yashiga yayi yafito anan cikin bedroom din yayi salla sai bayan da ya idar sannan yakoma makwancinsa yasake dora wani sabon baccin dan har bilkisu tatashi tayi wanka tashirya yana bacci saida ta shiga kitchen sannan yatashi, da kanshi ya nade shimfidar da ya kwana yashigar cikin dakin ya ajiye komai a muhallinsa sannan yashiga wanka ganin shi kadai ne adakin yasashi fitowa daga shi sai dan karamin wandonshi iya cinya dan baima kai rabin cinyar ba, lokacin ita kuma tana kitchen tana girki sai ta tuna jiya maama tace mata da dasu Hindu zasuzo amma sunce zasu mata yau ita kuma ta manto almiskinta da wani turarenta Arabian night a handbag din meenah wannan dalilin ne yasata cewar bari ta dauko wayarta takira meenah ta tuna mata kar akuma manto mata su yau ma. Tana fitowa falo taga baya nan alamar yatashi kenan, bedroom din tashiga itama kanta tsaye, tana shiga yana fitowa cikin sauri yayi baya zai koma bathroom din ita kuma fita tayi daga dakin takoma falo ta tsaya ita bata wuce kitchen dinba haka kuma bata koma dakin ba saida ta daidaici yagama kintsawa sannan ta bude ta shiga, yana gaban mirror yana taje sumarshi da cumb yasa bakin jeans da bakar t shirt mai gajeren hannu, ta cikin mirror din suka hada ido yaturo baki yana kallonta,

"Gaskiya daga yanzu idan zaki shigo kema ki rinka taking excuse.... Haka kawai kinzo kin wani kalleni"

Ita maganar tashi ma dariya tabata, wucewa tayi ta dauki duka phones dinta saida tazo saitinshi sannan ta tsaya,

"Kai excuse din kake nema kafin kashigo min daki? Kafara tukunna sai nima infara"

Tura mata baki yayi yana shagwabe fuska,

Ta cikin mudubin yake binta da kallo tana jujjuya masa baya lokacin data doshi kofa domin fita kasancewar dinkin jikinta riga da skirt ne wanda ya dinka mata lokacin bikin kannenta, karasa fesa turarenshi yayi ya ajiye gaban mirror dinta sannan yafita, afalo ya tarar da ita tana yin waya da meenah tana tuna mata sakonta dake cikin jakarta domin tana sa ran gobe zata fara salla, zama yayi yana jiran tagama, kitchen tawuce taje ta kwashe dankalin da take soyawa ta soya kwai sannan ta debo zuwa kan dining, bai jira anyi masa tayiba yataso yazo ya zauna,

"Sannu da aiki, ina kwana?"

"Yawwa katashi lafiya"

Ta amsa masa tana zuba nata dankalin acikin flate tana gamawa ta tura masa sauran gabanshi,

"Lafiya lau hajjaju.." Yafada yana lankwasa yan yatsunshi suna yin kas kas,

"Wai kai meyasa baka iya ninke kayaba idan kacire? Sai kawai ka rinka watsa min su cikin drewar any how?"

Dakatawa yayi da hada tea din da yakeyi ya kalleta yana shafa sumarshi,

"Ranki yadade wai dan Allah meyasa banida wahalar laifi ne awurinki....? Allah yabaki hakuri zan gyara"

"Ba maganar bakada wahalar laifi bane, ai gaskiya ce"

"To shikenan dai tunda ai nabaki hakuri"

Daga shi har ita babu wanda yasake magana cin abincinsu kawai suka sa agaba, itace tafara tashi nan yabita da kallo dama tun dazu jikinta yake bata irin kallon kurullar da yake yimata sannan tasha kamashi yana satar kallon kirjinta lokacin da suna cin abinci shiyasa tawuce bedroom tasako hijab har gwiwa tazo taci gaba da hidimominta, baki yatabe yatashi bayan yagama da komai na wurin,

"In kinyi hakuri ma ni gidan zan fice inbar miki yanzun nan..."

Yafada acikin zuciyarshi, tana tsaye tana shara da standing broom duk da falon babu wani datti, kusa da ita yazo yatsaya,

"Ranki yadade ni zan fita neman kudi, dinkuna ne kecan suna jirana sunfi kala ashirin gara naje na dan rage..."

"Allah yabada sa'a, amma cefane fa wazan bawa ya siyo min?"

"Bari idan naje shago zan aiko yaro ya kawo miki"

"Shikenan"

Fita yayi yaji shiru batace komai ba sai yakara dawowa,

"Yadai?"

"Uhmm ai banji kinyi min addu'a bane"

"Adawo lafiya, Allah yabada sa,a"

"Amin hajjaju, wallahi har naji dadi, i luv u irin wujiga wujiga dinnan"

Ita dariya ma yabata kawai ta girgiza kai taci gaba da shararta, saida tagama komai nata sannan tayi baki wasu mata guda biyu wadanda makotanta ne amma da dan tazara tsakaninsu sai dai duk kana iya hango gidajensu daga kofar gidanta, sosai ta karbesu da fara'a da kuma sakin fuska da zasu tafi ta dibar musu kayan zaki cikin leda tarakasu kofar gida sannan tadawo ta zauna tama rasa me zatayi gashi laptop dinta na wurinsu meenah duk yau zasu kawo mata da tana nan da ta dan rage zaman nan haka dan dole dai sai kallo ta kunna.

Fahad gidansu yafara zuwa ya iske su maryam nata shiri wai gidansa zasu tafi bai hanasu ba dan yaga jininsu yahadu da na bilkisu, bayan sun gaggaisa dasu ayiyah yatafi shago ai yana shiga aka fara tsokanarsa,

"Ga ango ga ango"

Dariya yayi yarinka binsu daya bayan daya suna gaisawa, kayan da ya yanyanka yaciro zai fara hadawa,

Bai jima da zuwaba saiga husnah jikinta ma farin uniform ne da alama daga lecture tafito ashe ko jiyama saida tazo dubashi taga bai fito ba,

Zama tayi agabanshi ta kura masa ido lokacin da yake dinki wani kyau na musamman taga yayi shiyasa kishi ya turnuketa nan da nan,

"Husnah ya makaranta...?"

Badan tasoba tasaki ranta gudun karya gane amma shi tuni yakaranci yanayin da take ciki domin dama yasan bakin kishinta akansa,cikeda son yasake kular da ita yace,

"Baki tambayi matata ba"

Tabe baki tayi ta dauke kai, yana kokarin juya rigar da yake dinkawa tarike rigar tana kallonshi,

"Prince katsaya mana mugama hirar sai ka cigaba da dinkin"

"To husnah ai yanzu ma hirar mukeyi"

Turo baki tafara yi daga karshe ma dai tashi tayi tafice daga shagon ita adole tayi fushi, habibu kanin hamza dake koyon dinki ashagon ya aika yabashi kudin cefane yace yayi yakai masa gidanshi ai kuwa nan su hamza suka cigaba da tsokanarshi. Acan bangaren bilkisu kuwa yau bata da matsalar kadaici domin bayan su mariya sunzo babu dadewa su Hindu suma sukazo kuma yinar mata zasuyi cur, lokacin da aka kawo cefanen da fahad ya aiko ma meenah ce takarba ta dora musu girki, yau yanayin da bilkisu take jinta na farin ciki yafi gaban kwatantawa danma maama bata nan da abin sai yafi haka, ayanda ta fahimta daga meenah har Hindu duk ciki garesu nan dadi yasake kamata domin tana bala'in son kannen nan nata kamar yadda suma ke sonta, dama tabawa meenah tace ta dafa duk abinda takeso nan meenah tace shinkafa da miya zatayi ai kuwa Hindu tace bazai yuyuba taliya da miya za adafa saboda ita tunda tasamu ciki ta daina cin shinkafa ita kuma meenah tace itama bata cin taliya yanzu sai shinkafa kadai, dariya abin yabawa bilkisu tace to duk su kwantar da hankalinsu sai adafa shinkafa da taliya kowanne daban mai son shinkafa yaci mai son taliya shima yaci ita kam gaba daya zataci shinkafar da taliyar dahaka dai tasamu nasarar raba wannan fadan. Sai la'asar fahad yadawo gidan domin yana son zuwa filin ball, yana zuwa su mariya na shirin tafiya yadauko dari biyu zai basu su hau napep bilkisu ta hana tashiga bedroom dinta ta dauko dari hudu tabasu tace kowa yadauki dari bibbiyu sannan ga naira dari su biya napep din, yana shiga falo yaga su meenah,

"Ya fahad sannu da zuwa..."

Shifa idan suna cewa yayan nan jin kansa yakeyi asama yana huruwa,

"Gaskiya munyi fushi sai yau zaku zo mana, maman hudah tun jiya tazo"

Dariya Hindu tayi,

"Ayi mana afuwa ya fahad insha Allah sai kunma gaji da ganinmu agidan nan"

"A'a bazamu gaji dakuba, koda kuwa zaku zo kullum"

Ahaka bilkisu tashigo ta samesu abincinsa ta dauka ta kai masa daki tafito tana cemasa,

"Ga abincin ka can kashiga kaci"

"Nagode hajjaju"

Tashi yayi yawuce ciki, shinkafa da taliya da salad yagani, dama yunwa yake ji shiyasa babu bata lokaci yazuba yafara ci saida yakoshi sannan yashiga wanka agurguje domin yaga kamar yakusa makara, kayan ball dinsa yasaka dark blue yadauki combos dinshi a hannu yafita, sallama sukayi dasu Hindu dan yasan dakyar idan zai dawo yasamesu, sai bayan da yatafi sannan bilkisu ta dauko jakar kudinta tabawa su meenah su kirga mata tanata basu labarin abubuwan da suka kasance lokacin da tana gidansu fahad gaskiya abin ya kayatar dasu bama ita kadaiba dan abinda suka lissafa kudin da aka tara mata dubu talatin da bakwai da dari biyar har dari biyar din da ta baiwa su mariya dazu dubu talatin da takwas kenan, dubu biyar biyar tabasu harda na maama tace itama akai mata.

Daf da lokacin sallar magrib suka tafi ji tayi kamar ta rikesu ta hanasu tafiya amma babu damar hakan domin mijin meenah ne yazo daukarsu zasu bi su ajiye Hindu, ciki takoma tarasa me zatayi saboda babu wani sauran aikin da yarage ma agidan domin su Hindu sunyi mata komai kafin su tafi sai dai dan girkin dare da zata yiwa fahad wannan kuwa indomie ma zata dafa masa, dadinta ma daya da wuta shine tasamu damar fara kallon sabon series din da Bollywood ke nunawa mai suna zahba walam ya'ood, tana tsaka da kallon fahad yadawo, wanka yafara wucewa yayi sannan yazo yayi sallar magrib daga nan bai kuma fitaba sai salim da yayi masa waya wai zaizo yagaida anty amarya kafin ishah kuwa sai gashi shiyasa tare ta dafa musu indomie din da dafaffen kwai,kan dining takai musu lokacin suna kallon ball atashar sport +,daki tawuce da yar guntuwar tata indomie din acikin flate taje ta zauna taci koda tagama ma anan tayi zamanta ta bude laptop dinta tashiga YouTube domin yin kallo, sai wurin 9 sannan salim yatafi, duk da haka bata koma falon ba taci gaba da zamanta adaki daga karshe tayi shirin bacci ta kwanta bata san lokacin da fahad yazo yayi nasa shirinba dan yau bai kunna fitila ba.

Haka suka cigaba da zama idan zai shigo daki wai dole sai yayi knocking tabashi izini shima idan yana ciki idan zata shigo sai tayi knocking yabata izini ahaka har sukayi 2 weeks kuma lokacin ne zata fara fita aiki duk da cewa acikin sati biyun nan rana daidai ce da baza suyi baki ba su ayiyah ma itada mamuh sunzo sunga daki sunyi fatan alkhairi, ranar friday maama tazo dama ranar bilkisu bata fitaba amma shi fahad yana shagonsu yan shagon nasu su tj sun hura masa wutar wai dole sai yau sunje gidanshi sunci girkin amarya, daga karshe dai text massage yayi mata yace,

_Princess dan Allah ki taimaka kiyi girkin mutum biyar wallahi yan shagonmu sun dameni wai sai sunzo.... Pls hajjaju._

Lokacin da taga sakon bata yimasa reply ba amma tafadawa maama abinda yaturo ai kuwa maama tazage ta tayata suka shirya shiryayyen girki duk da cewa unguwar ba asaida abubuwa amma saida bilkisu tafita da kanta ta samo almajiri ta aikeshi can bakin titi yaje ya iyo mata siyayyar duk abinda takeso bayan yakawo mata tace anjima can yazo yakarbi abinci,

Bayan sun gama girkin wanka tashiga tayi tasha doguwar riga ta atamfa ta danyi kwalliya sama sama, tana kitchen tana zuba musu abincin itada maama wacce ke daki tana salla suka shigo, fuskarta asake ta karbesu ta kalli fahad dake wani jin kansa asama shi ga mai gida murmushi tayi,

"Sannu da zuwa, table is ready"

"Thank you sweet heart"

Basu hau dinning dinba domin yayi musu kadan sai anan tsakiyar falon suka baje ba karamin dadi fahad yajiba domin girkine na fita kunya su bilkisu sukayi shi white rice and vegetables stew ga hadadden salad yasha dafaffen kwai abin dai ba acewa komai sannan ga drinks agefe mai dan Karen sanyi kowa saida abin ya burgeshi, tafiya tayi wurin maama tabasu wuri bayan sun gama ya leko cikin dakin suka gaisa da maama yakara gaba bashi yadawo ba sai magriba saboda yau babu zuwa filin ball ita tarasa me yake ji a ball dinnan da kullum sai yaje ranar juma'a ne kawai baya zuwa. Ranar litinin tafara fita aiki sai dai wannan karon karfe uku take tashi sabanin da, zamansu da fahad normal babu wata matsala tayanda take so yake bida ita kullum kuma afalo yake kwana aikin gida kuwa wannan almajirin data samu shine yake yimata shara da mopping idan da aike ta bashi amma fa har yau fahad bai san dashi ba saboda lokacin da almajirin zaizo baya nan wani lokacin kuma kafin yatashi daga bacci dasafe zaizo yayi aikinsa yatafi amma banda falon sai tace wannan yabarshi zatayi yau dai da Allah yayi za ahadu fahad na gidan baije ko inaba dama weekend ne yana da dinkuna ashago amma baya jin zai fita yanzu sai yamma yana kwance afalo daga shi sai three quarter iya gwiwa da riga armless yana kallo sai yaji anbude gida anshigo harda sallama tashi yayi yafita jin muryar namiji yana fita yaga saurayi zaiyishi atsaye hakama ahaife kilama yafishi ahaifen,

"Lafiya? Ya akayi?"

"Ehh nazo aikine.. Nine meyiwa hajiya aiki"

"Aiki? Aikin me?"

"Shara nake yimata da iyo cefane"

"To daga yau karka kara zuwa na sallameka, karka yarda ka kara dawowa"

Saida yaga tafiyar almajirin sannan yarufe gidan yasa sakata yashiga ciki, yau kam babu maganar neman izini kawai yafada mata daki tana kan gado da bra ajikinta da skirt tana kwalliya da alama daga wanka tafito,

"Menene ma'anar wannan abun da kikayi maigado? Ya zaki kawo min almajiri gidana batare da sanina ba..."

Tuni ta dauki hijabinta tasaka tana kallonshi,

"Almajirin ne wani abu? Yaron da na girmeshi"

"Ke kike ganinshi yaro amma ni awurina ba yaro bane, ya zaki dauko wanda ko atsaye yana daidai dani, ai sai akasa banbance dani dashi wanene mai gidan, wannan ma ai tsaf zaiyi min duka"

"To yanzu me kakeso ayi wai?"

"Ai narigada na sallameshi..."

Har yajuya zai tafi tariko rigarshi,

"Da ka koreshi din to yanzu wa zan rinka aika?"

"Ni ki aikeni mana, ai gara ni kisani aikin kuma kiyita aikena da ki kawo min wancan gardin ki ajiye min agida wanda ko adake tsaf zaiyi min duka yanda nake dan kadan dinnan dani..."

Sakinshi tayi yafita yanata yi da bakinshi wanda kusan rabi kishine acikin maganganun nashi. Aranar da yamma suka shirya sukaje gidan Anty Fauziyya suka gaisheta acan sukayi sallar magrib sannan suka dawo gida da zummar gobe ma zasu jewa yaya asabe da su anty kubra. Yau da zaiyi wanka da daddare rasa kayan baccin da zai saka yayi saboda shi baya maimaita kaya idan yasaka guda daya sai anwanke yake sakawa gashi tunda yazo gidan sakawa kawai yake yana tarawa ba awankewa dama ayiyah ce keyi masa wankin inner wears dinshi manyan kayan kuma wanki yake kaiwa to yanzu babu ayiyah, tsayawa yayi agaban drewar din bayan yarike kugunshi da hannunshi guda daya......


*Dan Allah idan har kin san baki siyaba to karki karanta.*



*_Ummi Shatu_*


© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*22*


***Shagwabe fuska yayi ya juya ya kalli bilkisu wacce ke sanye da hijab ajikinta amma aciki sleeping dress ne riga da wando iya gwiwa,hankalinta gaba daya yana kan system din da take dannawa,

"Wai yau wanne kayan zan saka...?"

Dagowa tayi ta kalleshi sannan ta maida kanta kan laptop dinta,

"Da nice nake fada maka wanda zaka saka?"

Shiru yayi mata zuwa can yayi kwafa,

"To wallahi yau karki fito bayan na kwanta dan babu mamaki tsirara zan kwana..."

Tabe baki tayi,

"Kayi duk yadda kaso..."

Jallabiya ya dauka daga cikin kayansa yanufi bathroom yanata kukkumburo baki,

"Wai haka kawai mutum yanada mata amma komai shi zai yiwa kansa..."

"Magana kake yine?"

Yaji tafada yana kokarin shiga toilet din,

"Ni ba dake nake ba"

Tana nan zaune tana aikinta yafito sanye da jallabiya kalar ruwan kasa har lokacin bai daina kumbura ba, kayan shimfidarshi ya diba ya fita zuwa falo bai sake komawa cikin dakin ba sai asubah daga nan bacci yakoma bayan yayi sallar asubah bai tashiba sai karfe 9, wanka yayi yasa three quarter da t shirt ya tattaro kayan baccinshi da kananan kayanshi yakai tsakar gida, duk sai wani cika yake yana batsewa tana ankare dashi, yajima tsaye kan kayan yana kallonsu kafin yaje ya dauko bucket da sabulun wanki yazo gaban fanfo ya debi ruwa yafara wanke kayan yanayi yana yarfe hannu kamar wanda ake yankar naman hannunshi,

"Hajjaju yanzu idan wani yazo ya iskeni ina wanki bazaki ji kunya ba?"

Karasa ajiye kayan wanke wankenta tayi tana kallonshi,

"Au wai kai da nufinka ni zanyi maka wankin?"

Langabe kai yayi yasake bata fuska,

"To ai mata masu neman aljanna har wanki suke yiwa mazajensu"

Dariya ita abun yabata ma amma ta dake ta wucewarta daki, dakyar ya samu ya wanke kayan Amma fa ji yake kamar yayi wani gagarumin aiki gashi ko breakfast baiyi ba, falo yaje ya fada saman doguwar kujera yanata ajjiye numfashi. Saida yahuta sosai sannan yatashi ya yi breakfast lokacin karfe goma da kusan rabi, yana gamawa yasake kwanciya, wurin 12 na rana yakwaso kayan mashi yazauna domin gogesu, yana yi yana jin wakar breaker awayarshi,

"Gaskiya ni ba dan gata bane..., inyi wanki da kaina kuma gugar ma arasa mai taimako

Please Login or Register in order to submit comment