Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

taliya sannan tayi sos din kwai tafito duk ranta ajagule, zama tayi afalo taci abincin ta ganin har tagama bai fitoba yasata sadadawa taje ta dan labe amma tsitt kamar babu kowa acikin dakin, komawa falo tayi taci gaba da zama har magriba tayi sannan ta tashi taje tayi salla tasake fitowa lokacin suma su bilkisu sun tashi, tana kwance kan rug din salla da carbi ahannunta fahad na kusa da ita yana yimata maganar abinci, labewa husnah tayi tana saurarensu,

"Hajjaju me zakici to idan bazaki ci wannan fanken ba?"

Saida taja wasu sakwanni sannan tayi magana ahankali,

"Ni babu abinda zanci..."

"No, zakici wani abu gaskiya, zaki ci indomie?"

Daga masa kai tayi yatashi yafita, yana fita yaga husnah wacce babu zato taga yabude kofa yafito,

"Uhmmm ya fahad dama zuwa nayi in tasheku naga baku fitoba shine nace may be baku san lokacin salla yayiba....."

Fuskarsa babu yabo babu fallasa yace,

"Mun tashi, zo muje ki dafa min indomie...."

Hade rai tayi tajuya tana kunkuni,

"Tabdijam... Nice ma zan dafawa matarka abinci? Impossible wallahi bazai yuyu ba"

Jin abinda tafada yabashi mamaki,

"Husnah nikike fadawa haka ko? Wato bazan saki abu kiyi ba?"

"To ai naga bakai zaka ciba.... Matarka zaka kaiwa fa"

"To matar tawa ita kika yiwa bani kika yiwa ba? Zaki wuce muje kitchen ko sai nayi miki rashin mutunci"

Turje turje tafara yi tana buga kafa akasa ganin haka yasashi wucewa cikin kitchen din batare da yasake bi ta kanta ba, da kansa yadafa musu manyan indomie guda uku sannan yasoya kwai yajuye yanufi dakin Bilkisu tana kwance har lokacin tana tasbihi,

"Tashi kici abincin hajjaju..."

Yunkurawa tayi ta tashi ta dauki fork ta debo takai bakinta tafara taunawa kenan taji yace,

"Kanwarki ce ta dafa mik...."

Ai bai karasa ba yaga ta tsaya da taunar da takeyi ta kafeshi da ido,

"Wasa nake yimiki wallahi ni na dafa... Kin san dai ai wani time din ina girki a kd"

Jin ya rantse yasa ta cigaba da ci tana kunkuni,

"Ni kar ka kara saka wannan nonsense wife din naka cikin sha'anina..... Ban son raini..."

Murmushi kawai yayi yana kallonta gaskiya Bilkisu tana da bala'in son girma,

"Daina zagar min mata..."

Yi tayi kamar bata jishiba, fork yadauka shima suka cigaba da cin abincin tare, bayan sun gama ta hada tea tasha, shikam yana nan nane adakin kamar cingum har sukayi sallar ishah, sai bayan da yayi shirin bacci sannan yafita zuwa dakin husnah tana kwance cikin kayan bacci tana waya da Ruky tana bata labarin abinda yafaru wai har ita fahad zai ce ta dafawa wannan tsohuwar wife din tashi abinci? Ita kuwa tace bazata dafaba, zugata Ruky taci gaba dayi tana cemata wallahi karta yarda idan bahaka ba rainata zasuyi kuma bilkisu gani zatayi kamar yafi sonta, tana jin fahad ta katse wayar ta gimtse fuska, kallonta yayi shima fuskar tashi gimtse,

"Asma'u har ni zance kiyi min abu ki k'i yi ko? Dama kin rainani har haka ban saniba? Good nagode ba laifinki bane nawa ne...."

"Haba ya fahad kayi hakuri pls... Ni wallahi da kaine zakaci zan dafa maka..."

"To ke waye yace miki ita zataci...?" Wannan tambayarce ta so kada mata hanjin cikinta shiyasa takasa bashi amsa tayi shiru,

"Babu damuwa nagode, saida safe"

Juyawa yayi yafita tabi bayanshi da harara,daga shi har bilkisun haushinsu takeji. A falo fahad ya zauna ya kirasu mukhtar yana tambayarsu ya school sukace normal ne kawai yaci gaba da hutawarsa, dariya yayi sukayi sallama dashi ya wuce dakin Bilkisu bayan yaje ya rufe ko ina na gidan, kwance ya isketa cikin riga da wando na bacci masu dan kauri amma abubuwan dake tsokale masa ido gasu nan abayanne,dariya yaso yi saboda ganin ta jera pillow a tsakaninsu,

"Dan sammin kadan intaba dan Allah Bilkisu..."

Juya masa baya tayi nan tajishi yana dariya kasa kasa yana cewa,

"Yarinya jiya tasha....."

Juyawa tayi ta harare shi duk yawani bi ya hasketa da hasken dake wayarshi,

"Kafa dameni... Bacci nake ji"

Kashe hasken taga yayi,nan tagyara kwanciyarta tana mamakin shi wai ita yake kira da yarinya lallai yaga gadon baccinta dole yakirata da haka. Duk yadda taso kar yarab'u jikinta saida ya kwakumeta cikin dare dole ahaka sukayi bacci. Washe garima haka suka wuni cur adaki saida yamma tafita tashiga kitchen ta girka tuwon semo miyar kuka, aranar yabar dakinta yakoma dakin husnah duk haushinsa husnah keji saboda ganinta ya raina mata hankali yazo sai wani bacci yaketa faman yimata. Bilkisu dai saida tayi kwana biyar bataje aiki ba har saida taji ta garau, fahad shima bai koma makaranta ba acewarsa sai wani satin har lokacin bai sake attempting na kusantar ta ba amma sai dai tana shan dakuma haka zaiyita fakarta yana taba mata kirji gata ita kuma ba gwanar saka bra ba wani lokacin ko fita zatayi bata son tasaka amma yanzu tasan fahad bazai bariba dan ko jiya da tafito zata fita aiki yana falo kallo daya yayiwa gurin yagane bata saka ba janta daki yayi sakamakon husnah na wurin,

"Baki saka bra ba why?"

Musawa tayi tana ta turo baki, hannu yakai ta rike tana harararsa,

"Kibari naji mana tunda kince kin saka...."

Tureshi tayi tawuce gaban wardrobe ta dauko tawuce bathroom fita yayi yana dariya, lokacin da taje office khulsum tsokanarta tarinka yi tana cewa amarya take gashi nan har tafara wani shining gaskiya ko ita ta fahimci hakan amma tazaci ko Shea butter din da tafara shafawa ne na cikin lefenta. Ana gobe fahad zai koma kd adakinta yake shiyasa ranar ma yayi mata wayo saida yabarta tafara bacci sannan yaje ya far mata sosai yauma yaci galaba domin saida yafara rudata ya kasheta da soyayya sannan yayi abinda yayi niyyar yi, ranar ma sunsha kuka shikuma yasha yakushi da cizo amma bai hakuraba saida yayi abinda yaso shiyasa lokacin da yabarta bata da karfi ko na sisin kwabo, bai ma yarda yayi wanka adakinba dakin husnah yagudu can yaje yayi wanka yayi alwala yafito haushi da bakin ciki kamar zasu kashe husnah ganin yazo yayi wanka anan dan ko magana ma kin yimasa tayi. Saida karfe 6 tayi sannan yakoma dakin Bilkisu tana kwance har lokacin idanuwanta sunyi fici fici saboda kuka dan jiyama sosai ta dandana kudarta fahad fa babu damane a wannan fagen domin akwai rike wuta gashi ta fahimci irin mazan nanne masu dogon zango baya samun nutsuwa cikin karamin lokaci shiyasa take shan wuya a hannunshi, sunkuyawa yayi agabanta yadafa hannayenshi akan gadon yana kallonta,bige hannayen nashi tayi nan yafado mata, kallonta yayi yana murmushin rashin kunya,

"Kina bukatar kari ne?"

Harara ta watsa masa sannan ta yunkura dakyar ta tashi aranta tana tunanin wai meyasa yake yimata wayo ne har haka? Ita ina nata wayon yake tafiyane?

Bata kara bi takanshi ba tawuce toilet yauma saida ta dage wurin gasa jikinta sannan taji dadi sai kunkuni taketa yimasa tana kiransa da mugu, shikuma ga rashin zuciya da zarar yaga wuri sai yayi tsokana aranar da yamma ya tattara yayi tafiyarsa kd kuma yace sai yajima basu ganshi ba, aranar da yatafi da daddare ita yafara kira awaya kafin husnah duk Bilkisu bata son hirar nan tashi saboda mafi yawanta baran baramace da rashin kunya aciki daga karshe cemata yayi wai dan Allah tacire kayan baccinta suyi video call, kawai mamaki fahad ke bata bata taba sanin dan air ne shi mai lasisi ba sai a yan kwanakin nan dan wata maganar ma idan yafada ita da ba itace tafada ba kunyace take hanata motsi, harda fushi yayi saboda taki yarda suyi video call bayan sunyi sallama tafita kitchen dafa Lipton da lemon grass taji husnah tafito falo tana waya da fahad wai dan Bilkisu taji saboda dama taji motsin fitowarta, dariya bilkisu ita abinma yabata wato ita husnah bata san kwantai ma tasamuba na hirar tunda saida yafara kiranta suka debe awa da awanni yana yimata magana shine ita dan ankirata yanzu harda su zuwa tura haushi? Bata kulata ba tawucewarta daki.

Tunda fahad yatafi tafara wata irin kiba ta lokaci daya ada ita yan shafal ce amma yanzu duk tabi tacike tako ina harda dan kumatu tayi acikin satikan da basufi biyu ba ga shining da fatarta keyi da wani lightening na musamman ita harga Allah ta zaci ko man da ta sauyane ya karbeta,su maama dukansu lokacin da suka hadu agida da suka ganta santin canjawar da tayi suka rinka yi hakama khulsum ita dai bata kawo komai ba. Ranar asabar tana gida babu aiki ranar khulsum taje asibitin su mijinta ta dawo tabiyo ta gidan, adaki suka kule suna ta shan chapter husnah kam halin nata data saba tayi taje ta labe musu tana jin hirar da sukeyi ta hamood tsohon mijin Bilkisu har khulsum nacewa taganshi rannan a asibitin su abban Khalifa sai Bilkisu tace may be maganin HIV yaje siya ita dai Allah ne yakareta da tuni ya yaba mata jaraba, ai husnah najin haka ta rufe baki cikeda mamaki, da gudu takoma daki takira anty juwairiyya tana fada mata abinda kunnenta yaji nan fa juwaira tarinka famfa ta tana cewa karta yarda wallahi taje gidansu fahad ta tada maganar dan duk yanda akayi iyayenshi da yayyenshi basu san da maganar ba waya sanima ko itama bilkisun tana da ita karta yarda tabar maganar nan, ai suna gama waya husnah ta shirya tsaf dama lokacin yammace ta sulale tafita tanufi gidansu fahad ita Bilkisu lokacin ma khulsum tatafi tabarta tsaye gaban mirror tana karewa kanta kallo tana so tagano kibar da su khulsum keta cewa wai tayi da kuma haske......


*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


54****Bilkisu bata san meyake faruwa ba sai sha'anin gabanta kawai take tayi tana sake kallon kanta bayan tafito daga wanka, dagaske kam ta dan sake murmurewa ba kamar da ba lokacin da tana tsaka da ramar nan kamar wata majinyaciya amma yanzu kayanta ma duk nema suke suyi mata kadan saboda matsarta sukeyi. Husnah kam lokacin da taje gidansu fahad iya ayiyah da mamuh tasamu kadai suna girkin abincin dare suna dafa tuwon biski miyar karkashi shiru tayi bata fadi abinda yakawota ba har magrib saida baba yadawo sannan tace wurinsa tazo dama karar fahad da Bilkisu takawo, tambayarta baba yayi mesuka yimata nan tafara kora jawabi,

"Baba dama ya fahad ne da matarsa..... Ni gaskiya munafurtata sukayi saboda kwata kwata ban san cewa Bilkisu nada HIV ba sai yau......"

Ai daga mamuh har ayiyah dake zaune awurin dukansu kirji suka dafe cikin razani da tashin hankali sukace,

"HIV...?" Suka fada cikin hadin baki,

"Ehh wallahi mama dama ashe tanada ita shine ta boye bata fada ba...."

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un..... HIV kuma? To aini koda wasa mahaifinta bai sanar dani hakaba... Sannan shima fahad din baiyi min maganar ba"

"Nima baba bai fada minba dan lokacin bikinmu ma da nace yayi test sai cemin yayi wai yayi shi bashida matsalar genotype da sauran cutukan zamani dake hana aure..."

"To yanzu shi fahad din yasani? Ina nufin yasan matar tasa tanada HIV?"

"Wallahi baba yasani, da saninsa kawai boye muku yayi dan karku hanashi zama da ita, kuma kowa yasan mijinta nada shima yanada HIV din amma ahaka ya fahad yace wai sai ya zauna da ita"

Shiru dukkaninsu sukayi na wucin gadi shi baba ma gaba daya yarasa abinda zaice sai hada zufa yakeyi lallai kuwa idan hakane fahad kuruciya na yawo dashi, waye yafada masa ana irin wannan makauniyar soyayyar akashe kai?

Su mamuh kuwa har yanzu basu daina salati da sallallami ba, kallon husnah baba yayi sannan yace,

"Asma'u abinda nakeso dake kitashi kitafi gidanki kije ki zauna, shikuma zan kirashi zaizo, idan yazo zamu san matakin da zamu dauka"

Sunkuyar dakai tayi cikeda ladabin karya tace,

"To shikenan baba.... Nagode Allah yakara girma"

Sallama tayi dasu mamuh suna cemata ta tsaya tatafi da tuwon biski tace a'a bata iya ciba, cikin jimami tatafi tabarsu kowa yayi shiru suna tunanin mafita.

Bilkisu na falo sanye da doguwar riga yar kanti tana kallo husnah tashigo tawani dauke kanta bata kalli inda bilkisu takeba tawuce daki jimm kadan tafito tashiga kitchen tana cewa,

"Su tsohuwar guzuma dai ankusa abar gidan da aketa tunkaho dashi ana huhhura hanci..... Ashe ana makale da kabari salamu alaikum..."

Ita Bilkisu sam bata gane abinda husnah ke nufi ba shiyasa da taji hayaniyarta na neman damunta tatashi takoma daki ta kwanta taci gaba da kallonta, lokacin kwanciya nayi tai azamar kashe wayarta saboda bata son nacin fahad. Ranar juma'a da yamma saiga fahad yadawo mamaki abin yabawa Bilkisu saboda shi da yayita cewa sai sun nemeshi kafin su ganshi amma shine yakasa hakuri yadawo? Hamdala tarinka yiwa Allah da ba adakinta yake ba yana dakin husnah dan haka suje can su karaci fitinarsu, shi kuma lokacin da yaga Bilkisu mamakin yar kibar da yaga tayi yarinka yi sai taba mata kumatu yake wadanda suka fara luhu luhu gashi ba laifi komai na jikinta ya sake dan bunkasa,wani zumudi yafara yi na son sake kasancewa da ita kawai yana son yasamu dama ne amma ahalin yanzu babu dan ranar husnah ce shiyasa yana fita Bilkisu tatashi tarufe dakinta tayi kwanciyarta. A bangaren husnah kuwa ko da wasa bata nunawa fahad ga abinda wai taje ta shirya ba lafiya lafiya suka kwana amma da safe tun kafin yatashi daga bacci baba yakirashi awaya yace anjima kadan yana son ganinshi shida su bilkisu, tunanin duniya fahad yayishi wai ko zai samu yagano dalilin da yasa baba ke nemansu amma sai yakasa, juyawa yayi yakalli husnah yafada mata cewar ta shirya anjima zasuje gida baba na son ganinsu daga nan yamike yafita, dakin Bilkisu yashiga har lokacin ita bata tashi daga bacci ba tana tunkunkune cikin bargo, zama yayi gefenta yaja kumatunta nan tabude ido ta kalleshi,

"Kitashi ki shirya zamuje gida baba na kiranmu..."

Gabanta taji yafadi,

"Lafiya?"

"Ehh to lafiyar kenan dai...."

"Allah yasa..."

Sake jan kumatunta yayi sannan yatashi yafita, tashi itama tayi tashiga wanka.

K'arfe 8 nasafe suka gama shirunsu tsaf a niyyar fahad yasamo musu napep su tafi gaba daya amma sai husnah tace ita kawai suje a machine din fahad inyaso sai tahau napep, wannan dalilinne yasa tafiyar tasu ta bambanta kafin suje tuni husnah taje tasake tsara karya da gaskiya harda su kukanta wai fahad baya adalci yafi son Bilkisu kuma itace take bashi umarni komai sai abinda tace shi zaiyi yanzu ma adakinta yake amma maimakon yasamo musu napep su taho gaba daya sai yaki yace wai Bilkisu zai dauko ita kuma taje tahau napep, kowa dake zaune wurin abin baiyi masa dadiba nan baba yashiga bata hakuri, tana nan zaune tagama kukan munafurcinta sai gasu fahad, su mariya najin Bilkisu suka fito sukaje da gudu suka rungumeta abin yasake baiwa husnah haushi,duk da tahada karya da gaskiya tafada hakan bai hana su ayiyah yiwa Bilkisu kyakkyawar tarba ba. Saida aka gama gaisawa sannan baba yacewa fahad,

"Fahad meyasa baka adalci tsakanin matanka? Haka ake zaman aure ko mu haka kataso kaga munayi a wannan gidan?"

"Baba menayi?"

"Asma'u maimaita abinda kika zo kika fada mana....."

"Baba tsoronta yakeyi sai abinda tace masa yakeyi, kuma ma ashe tsohon mijinta yanada HIV amma ahaka ya fahad ya aureta shiyasa lokacin bukinmu da nace muje muyi test yaki zuwa yace wai yayi anan...."

Hangame baki fahad yayi cikeda mamaki ita kuwa Bilkisu har tafara halin nata na saurin kuka,

"Bilkisu abinda tafada gaskiya ne wai tsohon mijinki nada HIV"

"Ehh gaskiyane baba..." Bilkisu tafada cikin kuka, kafin baba yayi magana fahad yace,

"Amma baba ai ita bata da ita.... Wallahi kawai tada zaune tsaye ne irin na husnah....."

"Ba tada zaune tsaye bane gaskiyane nidai kawai aje ayi test dan kaima kila kana da ita" husnah tafada tana hararar fahad,

"Ya isa, kai fahad katashi ka debesu gaba daya kuje kuyi test inyaso abinda duk sakamako yanuna ku kawo min...... Ku tashi kuje"

Sam abinda baba yafada bai yiwa husnah dadiba ita so tayi ace suna zuwa iyayen su rufesu da fada sannan suce fahad sai yarabu da ita, Bilkisu kam sai faman hawaye takeyi tana kukan zuci ahaka suka tashi suka fita, kallon bilkisu yayi cikin fada yace,

"Daina yimin kukan nan, kar na kara jinsa...."

Share hawayenta tayi tai shiru husnah na bayansu, juyawa yayi ya kalleta,

"Ke kuma tunda kin zama uwar mutane sai ki kaimu asibitin da yadace...." Tasan gatse yayi mata amma duk da haka sai ta fadawa mai napep asibitin da zai kaisu, lokacin da sukaje asibitin babu mutane dayawa dayake private ne kuma weekend ne, nan aka debi jinin kowa amma bilkisu saida fahad yariketa sannan tabari aka dauki jinin har lokacin kuka takeyi kadan kadan. Sun dan jima suna jiran result sannan aka kawo musu gaba daya suka tafi ko budawa basuyi ba,gidansu fahad suka koma suka kaiwa baba result din shi da kansa yabuda yagani sannan yadago yana kallonsu,

"To kamar yadda sakamako dai ya nuna kowannenku lafiya kalau yake.... Allah yakara rufa asiri, sannan wannan kar yakawo fitina atsakaninku kubarshi amatsayin kawar da zato"

"Baba ni so nake tafada mana a Inda taji ance bilkisu tanada HIV"

"Ai zancen duniya baya buya..." Husnah tafada tana murguda baki,

"A'a fahad, abar maganar nan haka kaji, kar Ku kara tada maganar nan...
Allah yayi muku albarka"

Nasiha sosai su baba suka yimusu sannan suka yi musu sallama suka tafi, tunda suka koma gida fahad ke rarrashin bilkisu sai dakyar yasamu ta hakura tayi shiru ta daina kuka, ita tarasa me ta tarewa husnah agidan nan da bata kaunarta ko lokacin da suke zaune lafiya agaban fahad ne take yimata magana amma idan baya wurin ko kallo bata isheta ba. Tsabar abinda husnah tayi fahad baiji dadinsa ba aranar yabar kano yakoma kaduna ko sallama baiyi mataba shi da titsiyeta yaso yayi sai tafada masa munafukin da yace mata bilkisu nada HIV amma kuma sai baba yace abar maganar. Tunda yakoma kd yadaina daukar wayarta idan tayi masa massage ma baya yimata reply daga karshe kawai sai ta shirya tabishi can kawai sai ganinta yayi da dan akwatinta dama dakinshi shi kadai ne, yanata daddaure mata fuska amma daga karshe dole ya hakura yasakar mata fuska yace ya hakura komai yawuce amma karta kara, duk zuwanta ya takura shi baya samu suyi hirar soyayya da bilkisu kamar yadda yasaba yimata ita kuma batama san husnah na wurinsa ba ita dai taga bata nan kwana biyu. Saida husnah tayi sati daya awurin fahad sannan tadawo gida tana dawowa ta hau yada habaici tana yiwa kawayenta waya tana cewa daga wurin oga take acan taje ta huta sosai abin ya taba zuciyar bilkisu aganinta ai wannan munafurcine fahad yayi shine ko yafada mata husnah na wurinshi nan itama tadau fushi dashi shiyasa lokacin da yazo weekend basu rabu da dadiba saida fada kwata kwata baisan laifinsa ba amma taki sakar masa fuska wannan karon ko yar karar da akeyi masa ake barinsa yayi katobararsa ba abarshi yayi ba bare abarshi yayi abinda ya gadama duk da tasan illar hana kai ga miji wannan karon kam hanashi kanta tayi saboda taji haushin abinda suka yimata shida husnah. Husnah kam tun lokacin da tadawo daga wurin fahad tafara amai da tofe tofen yawu sosai abin ya tayar mata da hankali saboda tana zargin cikine, ai kuwa tana yin test taga shine zancen zuci tafara yi,

"Tabdijam ina.... Wallahi bazan haihu yanzu ba intsufa ga wahalar karatu,ita matarka ma da take tsohuwa bata yarda tayi ciki ta haihu ba sai ni yar yarinya dani? Wallahi cikin nan zubar dashi za ayi tabdijam... "

Abinka da kuruciya duk sai tabi ta yadawa kawayenta wai cikine kuma ita bata so nan suka yita zugata suna cewa idan tabari ta haihu yanzu wallahi fahad daina yayinta zaiyi tunda ga matarsa nan ita taki yarda ta haihu sai gayunta take ci,

Tana komawa gida da daddare sukayi waya dashi har zasuyi sallama sai tace masa,

"Ya fahad.... Tunfa rannan naketa amai da tashin zuciya kuma da nayi test ashe cikine.... Nikuma gaskiya ba yanzu ba.... Kawai azubar...."

"Baki da hankali dama? Azubar fa kikace, husnah wai meyake damunki ne?"

"To ita anty meyasa ita baka yimata cikinba saboda ita kafi so? Nikuma nice zan wahala kenan..."

"Ohhh Allah.... Husnah ki shiga cikin hankalinki, haihuwa bata Allah bace? Ai ba yin kaina bane... Koda wasa karki kuskura ki attempting zubar da cikin nan idan kuma bakiji ba wallahi kika zubar zaki sha mamakina dan sai nadauki mummunan mataki akanki...."

Ummi Shatu_*????
Duk da wannan maganganun da yayi mata bata yarda ba azatonta wai barazana ce yayi mata shiyasa taci gaba da yi masa maganar itafa zubar da cikin nan zatayi ji yayi gaba daya auren yafita akansa daga bilkisun har asma'un fushi yake dasu saboda kowaccensu mai laifice awajensa, ita kuma husnah kishi da rashin wayo yarufe mata ido takasa ganin sudden changes din dake tattare da bilkisu itafa kawai idonta yarufe gani take bilkisu da biyu taki haihuwa saboda karta tsufa irin rashin dabarar da matan yanzu keyi wai aki haihuwa gudun kada atsufa. Ranar laraba yazo kano kuma aranar yake son komawa daga bilkisun har husnah sama sama yagaisa dasu dan ita bilkisu ma ko ganinsa bata yiba tana can wurin aiki sai awaya yakirata, ita kuma husnah tana gida, shi baida dabi'ar binciken wayar mutane amma yau yayi akan husnah saboda yana zargin kamar zugata kawayenta keyi ai kuwa zarginshi yazama gaskiya dan yaga chat dinsu da Fa'iza tana tambayarta wai cikin yazube tace a'a wannan maganin baiyi mata aikiba sai ciwon mara da yasata shine fa'iza ta tura mata sunan wani wai ta gwadashi mana yafi wancan karfi, ranar husnah ta raina kanta domin yi yayi kamar zai dafata yacinye nama danye saboda masifa daga karshe yace wallahi idan ta zubar da cikin nan abakin aurenta kuma kar su Ruky da Fa'iza su kara zuwar masa gida, da bacin rai yakoma kaduna itama bilkisu fushin take yi akan nada wai yazo ko yaje yaganta yayi tafiyarsa, washe gari da rana ya kirata wai dan Allah tayi masa taimako duk ranar da kawayen husnah sukazo ta fada masa da to ta amsa masa amma acikin zuciyarta tace babu ruwanta bazata zama munafuka ba. Bilkisu fa kiba kullum karuwa takeyi ga haske sannan fatarta har wani kyalli da sheki takeyi yanzu duk kayanta dakyar suke shigarta tun bata daukar maganar khulsum dagaske na wai cikine da ita har tafara dauka dan taji period dinta shiru gashi har pad tasiyo guda biyu ta ajiye amma kemadagas yaki zuwa gabanta ne yafara faduwa wanda sam bata San dalili ba, acikin satin fahad yazo nan dinma aranar zai koma fada sukayi kaca kaca da husnah akan cikin nan bilkisu na jinsu kamar zai doki husnah tsabar ransa yabaci bai ko yiwa bilkisu sallama ba yayi tafiyarsa abinda yasake kular da ita kenan, yana tafiya husnah ta aiwatar da kudurinta ta zubar da cikin ai kuwa tasha wuya kamar zata mutu dan azaba, ranar friday sai gashi lokacin husnah bata gama warwarewa ba daga ta'asar da tayi shiyasa yayi saurin ganewa tun kafin ya tambayeta tafara shirya masa karya wai kawai mafarki tayi wata mata mai kamada bilkisu tana dukan cikinta da tabarya tana farkawa taji tana bleeding sai kuma ciwo yasata agaba, fada fahad yashiga surfawa yana cewa kar ta yarda tasaka bilkisu cikin shirmenta ta hada kayanta tatafi gidansu shi yagaji da wannan masifar tata ai dama yafada mata karta zubar da cikin nan amma saida ta zubar. Bilkisu na daki tana jinsu amma bata fitoba saboda ba asata cikiba kar ace munafurci ne, aranar itama tayi gwaji da pt strip din da tasiyo tun kwanaki biyu da suka wuce amma tsoro yahanata yi, tun agwajin farko yanuna mata ciki baro baro, rufe baki tayi tana mamakin to meyasa takasa ganewa tun farko? Yanzu shikenan tayi abun kunya wai itace dauke da cikin fahad ajikinta to ko itama zubarwar zatayi? Masifar da yayita yiwa husnah ce tafado mata nan tsoro yashigeta to ai ko babu komai ma lokacine yayi wanda zata nunawa husnah cewa ita ba juya bace sannan babu abinda yasamu mahaifarta ras take tunda gashi tadau ciki. Duk da cewa husnah ta tafi yaki sakar mata fuska dan tun lokacin da ya bukaceta tahanashi yake fushi ita kuma yanzu tun ranar da tayi pregnancy test dinnan take jin wata matsananciyar bukatarshi kamar me amma ko cikin dakin nata bai kwanaba afalo ya kwana haka yabarta da juye juye da kwalla kun san mai ciki idan taso abu bata samuba.....





*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan

Please Login or Register in order to submit comment