Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



55****Washe gari da safe tana jinsa afalo yana harkar dake gabansa ahaka ta tashi tayi wanka ta dan shirya sannan tasake kwanciya cikin net,har wurin 9 sannan yashigo cikin dakin kai tsaye bathroom yawuce yaje yayi wanka yafito tana nan dai inda yabarta kwance tana satar kallonshi, ganin bai san tanayi ba yasata maida kallon nata gaba daya kansa, koda wasa ita bata taba zaton zata tsinci kanta cikin wannan yanayin ba wai yau itace ke yiwa fahad kallo na daban lumshe idanuwanta tayi wadanda kasala ta cikasu, tana ganinshi ya kammala shiryawa yasa dogayen kaya kalar ruwan siminti yana kokarin fesa turare yaji atishawar ta, juyawa yayi ya kalleta,

"Sannu.... Ko mura kikeyi ne?"

Jijjiga kai tayi idanuwanta na taruwa da kwalla,

"Ayya sorry...., idan zan dawo zan taho miki da magani"

Batayi magana ba taci gaba da binsa da kallo ji take kamar ta janyoshi amma bazata iyaba, har yakarasa shiryawarsa ya juyo ya kalleta batayi motsi ba,

"Ni na fita... Akwai wani abune?"

Shiru tayi masa tana matse kwallarta,

"Wai meyake faruwa ne? Ke kam sai kace dan ke kadai aka halacci kuka? Haba bakida aiki sai koke koke.... Dan Allah kirage yawan kukan nan....."

Tashi zaune tayi tana kallonsa amma batayi magana ba,

"Bari naje shago.... Nadawo aljihu na babu nauyi ne duk na kashe kudadena wallahi....."

Juyawa yayi yafita jin batace komai ba yana fita ta rafka tagumi tana shafar cikinta da hannunta guda daya, tunani take yi kila abinda ke cikinta mace ce kila kuma namiji ne, ohh Allah mai iko shi kadai yasani, tashi tayi tafita ta shiga kitchen domin dafaffen kwai take son ci, bayan ta dafa tafito tana kallon dakin husnah kwana biyu duk sai take jin gidan yayi shiru da yawa da husnah bata nan yanzu da ace tana nan tasan tana nan tana aikin yar mata da magana, har zata zauna tajiyo karar wayarta, ciki takoma ta dauko wayar tafito ta daga sannan ta nemi wuri ta zauna,

"Labour wai yau baki zuwa aikine? Waye kika ajiye wanda zaiyi miki voicing din labaran rana?"

"Haba kawata dama fa ina nemanki yanzu nake shirin kiranki.... Yau bazan shigoba bana jin dadi"

"To wallahi ki zo dai ki karanta labaranki domin yau copers din da kika saba jibgawa aikinki suyi miki duk basu zo ba..... Nikuma kinga ni nayi nasafe bazai yuyu asake jin muryata a na rana ba MD zaiyi magana"

"Dan Allah kawata kiyi min wallahi ina cikin matsala ne bazan iya zuwaba dama kuma ina nemanki fa.... Ina son mu tattauna"

"Shikenan Allah yakara sauki, wasa nake yimiki zanyi miki news din, anjima idan natashi zan shigo...."

Sallama sukayi ta dan kishingida tana bare kwan da ta dafa guda uku, daga karshe wai ta dan kunna kallo ko zata debe kewa. K'arfe biyu saura khulsum ta karaso gidan lokacin bilkisu na kwance kan kujera, zama khulsum tayi tana cemata,

"Bani abinci yunwa nakeji..."

"Ai kuwa sai dai kisha tea dan ban girka komai ba, bana jin sha'awar girki wallahi"

"To shikuma fa?"

"Shima tea din yasha kadai yafita"

Dariya khulsum tayi,

"Kina shagalinki kawata, wato girkima sai kin gadama zakiyi, koda yake bake kadai bace ai..."

"Nida waye da?"

"Au ina kanwar taki?"

Yamutsa fuska bilkisu tayi sannan tace,

"Bata nanfa kwana biyu, amma may be zata dawo... Ke ni ba wannan ba dan Allah shawara nake so kibani...."

"Allah yasa zan iya labour... Meya faru?"

Dan shiru tayi na wasu sakanni sannan tace,

"Kinga wannan cikin da wata dabi'a yazo min wallahi.... Wai karfi da yaji kulawar fahad nake nema"

"Banfa ganeba.... Yimin gwari gwari"

Harararta tayi sannan tace,

"Ina nufin ina bukatar mijina, shikuma fushi yake tayi akan last time da yazo na hanashi kaina saboda munafurtata yayi.... Dan Allah tawacce hanya zan janyo ra'ayinshi batare da yagane ba...."

Khulsum najin haka me zatayi inba dariya ba, dariya tafara yi harda buga kafa akasa,cikin jin haushi bilkisu tace,

"Ya ina yimiki serious magana amma kina nema ki mayar da ita abun dariya?, dagaske fa nake yimiki..."

"Kin san me yabani dariya? Zamanku da fahad na burgeni, ke son girma shikuma Jan aji.... Labour kenan wallahi Allah ne ya kamaki, kin tuna lokacin bikinku, cewa fa kikayi ni yaron nan da yadage sai ya aurene me zai bani idan munyi auren?, wai ma tsaya idan aka ajiye masa ni ta ina zai fara?, yaron da ko gama balaga baiyi ba...."

"Dan Allah ni ya isheni, yanzu dai zaki bani shawara ko dariyar zaki cigaba da yimin? Kin dai san bani kadai bace cikina zai iya samun matsala idan har bai samu abinda yake bukata ba...."

Shiru khulsum tayi ta daina dariyar da takeyi,

"Kin san me labour? Ai ke yakamata kisan hanyar da zaki bi wurin janyo hankalinsa saboda kinga kowanne namiji akwai ta inda ake kamashi.... Wani ta girki, wani ta kwalliya, wani ta magana, wani ta kamshi ma kawai zai zo hannu... Yanda maza suke kala kala haka hanyoyin kamasu ma yake kala kala.....amma ke me mijinki yafi so?"

"Shima yana son abinci kuma gaskiya yanada son kamshi...."

Tsaki khulsum tayi sannan tace,

"Ashe ke da kin san ma abubuwan da yafiso shine bakiyi ba? To yanzu tashi zakiyi ki shirya masa lafiyayyen abinci sannan ki turare gidanki da dakinki da ke kanki da kamshi kinga yana dawowa sai kuyi evening show kawai...."

Dariya bilkisu tayi cikin murna tace,

"Yawwa mutuniyas kokefa.... Nagode bari natashi nabada himma...."

"Yakamata kam, yau dai ga ranar yaro tazo...."

Daga haka ta sabi jakarta tafita tana dariya. Bilkisu zagewa tayi ta gyara gidan tsaf ta turareshi da turaren wuta da freshener mai sanyin kamshi, shi kansa bedroom din ma yadda ta gyarashi abin kallo ne tasaka wani bedsheet pink colour da zanen heart atsakiya abin gwanin burgewa sannan ta danyi kwalliya da net din dake makale jikin gadon ta tattare shi yabada design mai kyau sannan gefe daya ga turaren wuta na stick mai masifar kamshi yana ci sai hayaki mai kamshine yake tashi ahankali. Ita kanta yau kwalliya taci cikin materia red colour dinkin gown gefe daya ta shirya lafiyayyen girkinta soyayyiyar shinkafa da salad kawai fahad take jira. Tana kwance kan doguwar kujera tana kallon wani film atashar African magic mai suna things i hate about you fahad yashigo, fuskarshi babu yabo babu fallasa ya nemi wuri ya zauna yana kallonta, matar nan fa dagaske kiba take hadawa bata wasaba,

"Sannu da zuwa...." Tafada idonta nakan tv amma fuskarta asake take sosai wanda har hakan yaso bashi mamaki, cikin basarwa yace,

"Yawwa ranki yadade...."

"Ga abinci can fa..."

"Ok sannu da kokari bari na dan watsa ruwa tukunna..."

Daga haka yamike yawuce ciki nan tabishi da kallon sha'awa tana jin kamar tabishi, tana nan zaune yafito sanye da kananan kaya dukansu bakake daga rigar har wandon hannunsa rikeda p cap, wani bala'in kyau taga yayi mata ba kadanba bata taba sanin cewa fahad kyakkyawa bane sai yau,kallonshi kawai ta zauna tana yi sai take ganin kamar ma da biyu yake yimata wannan yangar da jan class din domin sai wani yatsine yatsine yakeyi kamar mace, da yake yau acikin shaukinsa take shiyasa take ganin komai nasa yau kyau yake yimata yana burgeta. Tana zaune tanata aikin satar kallonshi yagama cin abincin yamike yana kallonta shi fa yau yakula da fara'a ta tashi amma baisan dalili ba,

"Zan fita...."

Taji yafada, ji tayi kamar ta dora hannu aka tafasa ihu dan tsabar haushi, batayi masa magana ba yasa kai zai fice har yaje bakin kofa taji yajuyo yace,

"Amm namanta..., gaskiya yau dakinki yayi kyau.... Da ke dinma kanki, style din da aka yiwa dakin is something amazing..... I like ur style hajjaju..."

Daga haka yafice daga cikin falon, tana jin alamun tafiyarshi tafara kwalla, cikeda damuwa da bacin rai takira khulsum tana fada mata, dariya khulsum tayi sannan tace,

"Ohh my God.... What a funny.... Wato darling fahad yagano mu shine bazai bada kai bori yahau da wuriba har sai yabamu wahala? To inyasan wata ai bai san wata ba.... Bari inyi miki text, insha Allah bazai tsallake wannan tarkon namu ba"

"Are you sure...?" Inji bilkisu,

"Am 100% sure dear... Kijirani yanzu"

Daga haka takatse wayar tana jiran text din khulsum babu jimawa kuwa saiga text din yashigo, murmushi bilkisu tayi tana bawa kanta tabbacin zatayi fiyeda yadda khulsum ta shirya mata.

Har karfe 9 fahad bai dawoba sai wurin 9:30 sannan taji shigowarshi, tana kwance cikin net a kunnenta yashiga wanka yafito sannan yafita falo daga shi sai short nicker wanda tabada tabbacin abinci yaje yaci, yana shigowa yaji kamar nishin bilkisu da sauri yanufi gadon, kwance yaganta shame shame tanata faman sakin wahalallen nishi cikin wata atamfarta dinkin riga da skirt gaba daya kayan sun matseta sosai, dagota yayi yana tambayarta cikin rudewa,

"Bilkisu menene? Meke faruwa...?"

Kirjinta ta nuna masa da hannunta alamun ciwo yake yimata,

"Ciwon kirji kikeyi?"

Kai ta daga masa tana sake dago kirjinta tana sakin nishi, gaba dayanta ya dauketa ya saka ajikinshi yana cewa,

"Ai dolema dama kiyi ciwon kirji... Kallifa yanda kayan nan suka matse ki...., bari acire kawai"

Runtse idanuwanta tayi tana sake sakin wani nishin kamar gaske dan sai ka rantse da Allah ciwon takeyi irin sosai dinnan, baiyi wata wata ba yazuge zip din rigar yacire sannan yazuge na skirt din shima yacire shi kamar yadda yayi expecting daga ita sai pant yarasa meyasa bilkisu bata shiri da bra kamar wacce take mintsininta, kasa kawar da kansa yayi yadai yi kasa da murya yana cewa,

"Zaki sha maganine infita insamo miki?"

Kai ta girgiza masa cikin dakiya da muryar wahalar ciwo tace,

"A'a.... Kayi massaging dina may be i will be ok...."

Babu bata lokaci yafara abinda tace amma kuma bai dade da farawar ba shi kansa yaji al'amarin yafi karfin daurewa irin tashi shiyasa kafin ya farga har yasoma shiga cikin wani yanayi, daga shi har ita yau kowa yabaje basirarsa wurin kulawa da dan uwansa da samar masa da nutsuwa, bilkisu kam kasa kallonsa tayi daga karshe ma ta tsiri baccin karya tana jinsa yana yimata magana akan tatashi tayi wanka amma tayi shiru. Yau kam tayi baccinta cikin nutsuwa domin tasamu abinda take muradi dan ko juyi batayi ba saida asubah tayi sannan fahad yatasheta, wanka tayi tai salla shikuma fahad yafita masallaci, abin mamaki lokacin da yadawo kwance ya isketa kan rug din salla tana faman haki da nishi kamar wacce tayi race, yanzunma abinda yafaru daren jiya shine yasake faruwa, shar da ita ta shirya ta shiga cikin kitchen bayan takashe kan 80,tana tsaka da soya doya fahad yafito cikin shirinsa, manyan kaya yasaka shadda ash colour amma babu hula, a kofar kitchen din yatsaya yana dan kasa da idanuwanshi, daga ita harshi kunyar juna sukeji ta lura,

"Good morning sweetheart...."

Taji yafada ahankali,

"Morning, how was your night....."

Jin abinda tace yasashi dan murmushi yana shafa keya,

"It was amazing....."

Shiru tayi tana dan murmushi batareda ta kalleshi ba,

"Yanaga kafito bayan gashi ina preparing break fast?"

Dan satar kallonta yayi suka hada ido,

"Ni ai azumi nake...."

Dariya abinda taji yafada tayi tajuya ta kalleshi,

"Dama ana daukar azumi bayan alfijir ya keto?, malam bakada azumi kawai katsaya kayi breakfast"

Murmushi yayi ya karasa shiga cikin kitchen din yatsaya abayanta yana taimaka mata, tare suka zauna sukayi breakfast din sannan yafita, tun da tasamu wannan dabarar shikenan kullum da ita take aiki babu dare babu asubah sannan babu rana sai yanzu take gasgata maganar khulsum da take cemata itafa ta godewa Allah da tasamu yaro sharaf ta aura wallahi zataji dadi domin duk lokacin da take son kasancewa dashi zai saurareta kuma bazai kosaba amma manyan mutane sai ahankali ga shekaru ga basir duk yagama dasu, yanzu kam ta yarda 100% auren yaro akwai advantage aciki kamar yadda shima auren babban akwai nasa advantage din. Koda fahad yakoma makaranta ma baya sati daya baizo gidaba saboda Bilkisu domin baya son ta bukaci wani abu shikuma baya nan, kullum yana hanyar kano wani abun mamaki har lokacin shi bai san ciki gareta ba. Ranar da yayi wani zuwa da yamma yan uwan husna sukazo suka kwashe kayanta ita bilkisu ma lokacin bata nan tana wurin aiki saida tadawo ta iske falon yayi wani fadi duk sai taji babu dadi, fahad ta kalla wanda ke aikin goge mata tiles din dake cikin falon saboda yau haka tafita bata dauke ko tsinke acikin gidanba,

"Wai bazaka dawo da husna ba kenan? Haba kai kuwa anayin fa fiyeda hakama kuma adawo ashirya.... Dan Allah kaje ka dawo da ita..."

"Bakiga laifin da tayi min bane?, to be honest with you, she highly disappointed me and ban jin zan sake zama da ita gaskiya...."

"Duk da haka u have to be patient... U have to forgive her... Remember bature yace without sins there is no forgiveness.... Dan Allah kayafe mata..."

Tsayawa kawai yayi yana kallonta, zuwa can yanisa yace,

"Ai yanzu ba laifina bane, itace lokacin da taje gida ta hada karya da kareraye ta fadawa mahaifinta shikuma yayi fushi akan wai zaluntar yarsa nakeyi dan haka tagama zaman aure dani.... Kin gani da ace time din ta fadi gaskiyar abinda yafaru may be idan aka bani hakuri bayan na huce zan iya dawo da ita amma sai taje ta harhada karya ta fada.... Gashi dai tana sona tana son zama dani har gobe amma babu hali.... Aurena da husna kawai mubarshi a matsayin kaddara"

"Allah yasa hakane yafi zama alkhairi...."

Daga haka ta mike tashiga bedroom din tausayi taji yabata saboda ganin yanda ya gyara dakin ya kintsa komai harda su turaren wuta, gaskiya fahad abokin rayuwa ne yanada halin manya komai nagidan yayi mata harda su wanke wanke, washe garin ranar yaje yasiyo babbar katifa mai round kamar gado yasaka adakin husnah ai bilkisu nagani tafara daure dauren fuska wato raba daki zaiyi da ita da zai wani kama yasiyo katifa? Wallahi bazai yuyu ba ai kuwa bai yuyunba, kwanansa biyu yakoma Kaduna bai dawoba sai ranar da ake sunan matar ya Abba wato nusaiba wacce ta haifi yaronta namiji, kasancewar exam yakeyi saida ya dan samu interval sannan yadawo gida sai ranar yasan bilkisu nada ciki saboda cikin yafito sosai ita kuma tasake kiba tubarkalla gaba daya kayanta sunki shiga dan dakyar tasamu doguwar rigar da ta shigeta, bra kuwa duk sunyi mata kadan sai wata kwaya daya itace take iya sawa itama tana dawowa zata figeta ta yar,

"Wannan rigar ai ta matseki..."

Cikin jin haushi ta kalleshi,

"To ya zanyi? Kana ganima ahakanma ita kadaice ta shiga jikina"

"Allah yabaki hakuri, fito mutafi"

"Amin", tafada cikin fada, dogon hijabi tasaka tafita suka tafi yana rakata gidan sunan yawuce kasuwa kananan atamfofi yasiyo mata guda shida yawuce shago duk ya yankasu ya dinka mata doguwar riga samfarin maternity saboda duk na cikin lefenta masu tsadane bazai yuyu abata ba. Tunda cikinta ya tsufa fahad ke cikin zulumi sai kace shine mai haihuwar kullum addu'arsa Allah yasa kafin yakoma makaranta ta haihu, cikin ikon Allah yana gida suna tsaka da bacci ta tashi da daddare saboda azabar ciwo, tashinsa tayi sai faman ciccije baki take yi tana cemasa bayanta da kwankwasonta ciwo, gaba dayama rasa abinda zaiyi yayi daga karshe yakira mamuh yafada mata lokacin karfe 2 nadare, kafin su mamuh suzo duk ta jigata sai faman rokarshi gafara takeyi wai ya yafe mata mutuwa zatayi duk ta rudashi hankalinsa yatashi,bai taba sanin haka mata ke wahala ba wurin haihuwa sai yau lallai duk dan da baibi mahaifiyarsa ba yayi asara domin wahalar haihuwa kadai abar dubawa ce. Su mamuh na zuwa suka wuce asibitin haihuwa mafi kusa amma na kudi, c s za ayi mata saboda bazata iya haihuwa da kanta ba, acikin daren aka yimata aka ciro santaleliyar jaririya mai kamada fahad sak, komai na yarinyar irin nashine ba tayiwa bilkisu karar ko farce ba, mamuh nata faman tsokanarshi amma yaki kulawa saboda shifa ta matarsa yakeyi, da yake anyi aikin cikin nasara lafiya lau bilkisu ta farfado washe gari duk yan uwa suka cika asibitin amma banda ammah ita kam har aka sallamesu ana igobe suna bata zo ba. Ranar da suka koma gida bayan angama yiwa jaririyar wanka tanata faman tsaga kuka mamuh tace Bilkisu ta dauketa tabata tasha, daya dakin tashiga wanda fahad ke ciki domin nata su maama ne cike harda khulsum da sauran yan uwan fahad, yana kwance yana dan baccin gajiya, jin kukan baby yasashi tashi yana tambayar bilkisu mai yasameta? Zama tayi gefen katifa tana kokarin shayar da babyn, ido ta runtse tana cije lips saboda zafi tarasa wannan zafin ko na menene,

"Sannu baby... Tsaya in tayata"

Banza tayi dashi ashe shikuwa da gaske yake dan shima matsawa yayi ya dan janye kafafun babyn ya dora kansa bisa cinyar Bilkisu, tarasa sai yaushe fahad zai daina fitina, tashi tayi tafita ta mayarwa da mamuh yarinyar domin za agasa mata cibiya, yana kwance adaki yana jin mamuh na yimasa dan biki tana cewa ina sabon shiga masu 'ya wanda dan za ahuda mata kunne harda kwallarshi?. Washe gari aka radawa yarinya suna Bilkisu dan fahad yace tunda yaga wahalar da bilkisu tasha wurin haifar yarinyar nan dolene yasaka mata sunanta, su meenah ne suka zaba mata sunan da za arinka kiranta dashi wai Hanfa, washe garin ranar da akayi suna yakoma makaranta yabar bilkisu anata kwaskware kwaskware dan gyara jiki shikam yana cike da farin ciki yanzu baida aiki sai na dora hoton yarshi akomai nashi shiyasa bilkisu har tafara kishi, ada ita yake kira da baby amma yanzu tunda yasamu wannan jaririyar yamaida sunan kanta. Bayan sunyi arba'in harda wasu kwanaki yazo tunda yazo yakama yarinyar ya nanuke ajikinshi bilkisu duk haushi ya isheta daga karshe binsa dakin nashi tayi ta samesu kwance yadora hanfan akan kirjinsa, ture hanfa tayi ta maye wurin tana turo baki,

"Ai wurinane....."

Dariya yayi ya daga hanfa sama yana cewa,

"Baby kinji momynki na kishi....."

"Ni ba momy bace..."

"Oh sorry baby i mean..."

Sake rukunkumeshi tayi,

"Nima sai ka dagani..."

Kwantar da hanfa yayi ya dauki bilkisu yana dagata. Kallonta yayi yana murmushi ita kuma tana feeding din hanfa,

"Kema fa harija ce baby..."

Harararsa tayi, "kamanta..."

"Dagaske kinfini jaraba ni kawai juriya nafiki, ke kinada son abun amma bakida juriyarshi,da kanki zaki nema amma mintuna kadan zaki fara yiwa mutum raki kina kukan kin gaji...."

"Ni garama da ka tuna min, planning nak....."

Bata karasa ba taga yawani zabura kamar ta caka masa allura,

"Baby p me? Lallai sai yau nayarda kema karamar yarinya ce...., gaskiya koda wasa ban amince ba soo karma kifara"

"To sai muyi na musulunci ai..."

Kallo yakafe ta dashi zuwa can yace,

"So kike ki kasheni ne? Bazan iya wannan wahalar ba dan zan iya mutuwa, wannan ai muguntace...."

Duk ta yadda ta bullo masa sai ya bulle dan dole ta hakura, idan kagansu da yar yarsu kuwa abin gwanin ban sha'awa ammafa kowa acikinsu kishi yakeda ita, shi bazai ga ana feeding dinta yayi shiruba sai yace ai nashine ita kuma wai bazai kira daughter dinshi da baby ba sai ita, cikeda begen juna yakoma makaranta dama semester din karshe ne, ranar da yakoma da daddare yakirasu video call yana kwance adakinsa kan katifarsa sukuma suna kan gado bilkisu rungume da ita,

"Hy daughter...." Yafada yana murmushi,

"Hy Daddy...." Bilkisu ta amsa tana dariya,

"My daughter how are u?"

"Am fine Daddy...." Bilkisu tasake amsawa tana dariya, hira yaci gaba da yiwa hanfa ita kuma bilkisu na amsa masa daga karshe yabata fuska ganin bilkisu ta sauya mata maman da take bata zuwa dayan,

"Baby kuma yaza abata nawa?"

"We are sorry Daddy... Kadan zaka sammata kagafa kwarewa tayi..."

Haka suka cigaba da gudanar da rayuwarsu cikeda kaunar juna da tattalin juna, har fahad yakammala karatu lokacin da zai gama bilkisu hutu ta dauka a office tabishi kaduna cikeda jin dadi da farin ciki yarinka nunasu awurin friends dinshi da abokan arziki yana cewa ga familynshi idan badan shine yafada ba da tabbas dayawa bazasu yarda ba saboda ko da wasa baiyi kamada mai iyali ba.

BAYAN WASU SHEKARU.


Wata matashiyar mata nahango kyakkyawa wacce ke cikin kwalliya ta alfarma tsaye tana rarraba idanuwa a filin tashi da saukar jirage na Malam Aminu kano, tana sanye da jar atamfa ta yafa jan mayafi sannan komai nata ja tayi amfani dashi tana ta faman duban agogon dake daure hannunta,sake daga idonta tayi akaro na biyu nan tahangosu suna saukowa daga matattakalar jirgi, murmushi tasaki yayinda nima na waiga domin kallon wadanda take yiwa murmushin, wani kyakkyawan saurayi nagani rikeda hannun wasu yara guda hudu, biyu maza biyu mata, biyu kansu daya suma biyun kansu daya, dagudu yaran sukazo suka rungumeta suna kiran "oyoyo mommy"

Kallon matashin saurayin tayi ta dan bata fuska,

"Daddy kai wallahi tafiya dakai jidaline... Duk kunbi kun sakani doguwar tsaiwa wurin nan"

Ido ya kanne mata guda daya sannan yace,

"Wai ai duk acikin so ne..."

Da key din hannunta tayi amfani wurin bude musu motar nan yaran suka kwasa dagudu suka shige,

"Dadina dakai yarinta, har yau baka girma ba"

"Waye yaron? Kibari muje gida zan kamaki"

Dariya tayi takama kunne guda daya,

"Am sorry ya fahad"

Wata dariyar yasake yi cikeda farin ciki, hannunta yakama suka nufi cikin mota yana bata labarin dinner din da zata rakashi yau da daddare ta wani friend dinshi, sau dayawa idan yace ta rakashi party ko dinner sai tace a'a ita bataso suje tare ayi masa dariya kowa yana tafiya da yar karamar yarinya yar kasa da 25 amma shi yadebi tsohuwa duk lokacin da tafadi haka sai yayi dariya yace Shifa har yanzu yakasa ganin girman da taketa kurin tana dashi saboda kallon mitsitsiyar yarinya yake yimata her age is just a number, kuma ako ina baya kunyar nunata amatsayin matarshi duk inda zaije tare da ita yake zuwa, ko wannan umarar ma da sukaje da yara har ita yaso sutafi duk da last time iya su biyu sukaje sukasha soyayyarsu suka barwa ammah yaran,to wannan zuwan amma aiki ya hanata kasancewar tazama babbar jami'ar gwamnati mai kulada harkokin yada labarai shikuma ma'aikacine a asibitin koyarwa na mal Aminu maganar dinki kuwa tun shekarun baya yadaina domin bilkisu takafa ta tsare ita kadai yake yiwa dinki ahalin yanzu amma yanada babban shago da yabude yazuba ma'aikata sukeyi. Kowa yasan irin shakuwa da soyayyar dake tsakanin ma'auratan, lokuta da dama su maama na gulmarsu idan suka hadu suce sun rasa wannan irin kauna ta adda labour da ya fahad duk sunbi sun bata junansu da shagwaba kullum cikin yiwa juna shagwaba suke kuma duk fahad ne ya koya ma Bilkisu, ita dai Bilkisu babu abinda zata cewa fahad sai fatan alkhairi domin ya zame mata wani babban jigo acikin rayuwarta, guy din yayine tako ina yanada yakana da kunya da kawaici ga iya soyayya shiyasa baya taba gundurarta sannan yana respecting dinta takowanne bangare baya taba treating dinta kamar karamar yarinya sai ta bangaren love, itafa yanzu da zataga wacce karamin yaro da babba zasu fito neman aurenta da zata bata shawarar ta auri yaron domin sai yafi kulawa da ita, abangaren fahad shima hakane kwata kwata baya sha'awar auren karamar yarinya acewarsa wacce ta girmeka tafi kula dakai zatayi treating dinka kamar baby amma kananan yaran nan babu abinda suka ajiye sai rashin kunya, ahalin yanzu dai yaransu hudu da bilkisu hanfa da Muhammad fahad sai Mimi da Awwab, to muna addu'ar Allah yaraya su amin.

Alhamdulillah anan labarin kamar da wasa ya kammala ina addu'ar ubangiji Allah ya taramu cikin ladan nidaku yakuma yafe mana a inda nayi kuskure. Hakika ban taba sanin inada dunbin masoya har hakaba wallahi sai yanzu, tabbas kun nuna min kauna da kuma soyayya, da yawa daga cikinku wadanda suka siyi book dinnnan ban sanku ba banma taba tunanin kun san da niba, ina mutukar godiya hakika soyayyarku wallahi itace abar dubawa agareni bawai kudin da kuka siyaba domin mai sonka shi zaiso kayanka nagode Allah yabar zumunci,sai mun hadu cikin kundin haske wato gamayyar alkaluman marubutan haske gaba daya, zanzo muku da wani labari mai salo daban akan darajar malami da amfaninsa cikin alumma, sai mun hadu da yardar Allah taku ahar kullum Ummi A'isha.



*_
*_Ummi Shatu_*






An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko

Please Login or Register in order to submit comment