Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MUSABBABI Book 1 Complete Hausa Novel Document by MUSABBABI Book 1


MUSABBABI Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 61331



MUSABBABI Book 1

Reading Time: 5 Hours

Added On: 20, Jun 2024

Author: Habiba Abubakar Imam ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 322.45 kb

File Type: txt

Views: 537+

Download: 758+

Last download: 17 hours ago

Description/Story: MUSABBABI.

NA

HAJ. HABIBA ABUBAKAR IMAM

https://youtube.com/@HabibaAbubakarImam?si=H7yQptZbm29jaY6x


Page 1

Fateema Mahmud wacce aka fi sani da Afrah,
a sakamakon sunan kakarta ta wajen uba da
ta ci, nagartacciyar yarinya ce, kyakyawa
haifaffiyar garin Minna.
Mai cikar kamala, hakuri, juriya, sune
manyan halayenta na-gari abin koyi, sai kuma
tsantsar ilimin Islama da Allah ya wadata ta da shi,
domin tun tasowarta take kokarin koyon addininta,
har zuwa yanzu da ta mallaki hankalin kanta.
Ta zama cikakkiyar mace, domin tuni
ta
kammala karatunta na sakandire, tana zaman jiran
sakamako ne a yanzu. Idan akwai abinda ya ragi
Afrah a rayuwarta.
To ba zai wuce maraicin rashin uwa ba,
domin ta dandani dacin maraici tun tana
'yar
shekara biyu, kuma ita ce kadai
'yar da
mahaifiyarta ta haifa tare da mahaifinta Malam
Mahmud.
Bayan rasuwar mahaifiyarta ne, rikonta ya
koma hannun matar Babanta. Mama Hauwa, wacce
a matsayinta na uwargidan Malam Mahmud, tana
da yayyi guda biyar biyu maza, Mansur wanda shi

Page 2
ne na farko, a yanzu ma'aikaci ne a hukumar wutar
lantarki, wato (NEPA).
Yana rife da babban mukami, ya yi aure har
da 'Yarsa daya, sai Kabir, shi kuma ma'aikacin
banki ne, shi bai wuce watanni uku da aure ba, sai
Naja"atu da Sakina, su ma duk sun yi aure. Na'ima
ce ta rage, wacce take tsarar Afrah, duk tare suka
kammala makaranta.
Sai dai abu daya da Afrah ta rasa a gidan
mahaifinta, shine kulawa da kowace
"Ya take samu
na uwa, domin irin rikon da Mama Hauwa ke mata,
ba irin riko bane na amana.
Wanda maraya ya kamata ya samu ba'a
kowane mataki. Mama Hauwa na nuna bambanci
kiri-Kiri tsakanin Afrah da 'ya' yan ta,
Ko kadan ba ta kyautata mata, rayuwa take a
gidan tamkar ba
"yar gidan ba, duk da Malam
Mahmud yana iya kokarin sa domin ganin marainiyar
'Yarsa ta samu riko me kyau daga
Mama Hauwa.
Amma hakan ya kasa tabbata, domin Mama
Hauwa ta zama tamkar tauraruwa me wutsiya,
domin shi kansa Malam Mahmud din ta fi karfinsa,
ta kan yi duk abinda ta ga dama ko a gaban idonsa
ko a bayan idonsa.
Inna Halima wacce ita kadai ce kanwar
Malam Mahmud. kuma ita kadai ce take iya

Page 3
takama Mama Hauwa birki akan irin mugun rikon da take ma Afrah
Hakanne ma ya sa, kusan rabin rayuwar Afrah
take yi a gidan Inna Halima, domin duka ranar
juma'a. Can take tafiya, sai ranar lahadi take
dawowa gida, wannan dalilin ya sa Mama Hauwa
da Inna Halima ba sa shiri ko kadan.
Makarantar Islamiyyar da Afrah take yi, anan
kuma take koyar
da kananan yara, saboda
hazakarta. Ya Sayyadinsu Habib ya maida ita
Malama, a ajin haddar Kur' ani ta kananan yara,
tana daukarsu gun koyon Kur ani da Tauhid.
Malam Habib shine mutum na farko da Afrah
ta fara tsayawa da shi a matsayin masoyi, ta kuma
amshi tayin soyayyarsa, domin yarda da ta yi da
irin son da yake mata na tsakani da Allah da kuma
hanyar Ubangiji da yake doreta akai.
Hakan ya sa take da tabbacin cewa daga gare
shi za ta sami kyakkyawar rayuwa, ko ba kudì da
jin dadi, to idan har akwai Allah a cikin rayuwarsu,
to ya ishesu daga dukkan komai, don haka ta tsayar
da zuciyarta gun mutum daya, wato Ya Sayyadinta Habibu.

Page 3

Yau asabar ne Afrah tana gidan Inna Halima, yau
gyara take mata na gidan gaba daya. Inna Halima
tana gefe a zaune, duk inda Afrah ta yi, tana bin ta da
kallo, tana matukar sha'awar yarinyar da halayenta,
domin duk inda ake neman yarinya me hankali
wacce ta rike maraicinta, aka sami Afrah, to an wuce wajen.
Tana matukar jindadin kasancewa da Afrah, a
duk sanda ta zo gidanta, ta daina aikin komai,
duk abinda za ta yi Afrah, ta kan dauke mata, hatta girki
ba ta yi, ta kan dauke mata komai.
Inna Halima. na tsaka da yin wannan tunani
aka bugo kofa da Karfi. Musaddik ya fado cikin
gidan, tamkar wanda aka jefo ba tare da sallama ba, Inna Halima ta mike tana kallonsa

'Musaddik". Ta Ambaci sunansa da karfi, a yayin
da Afrah ta yi saurin ja da baya, domin kar ya
bugeta.

Musaddik nagartacce,kuma kyakkyawan
matashi. wanda ya hada komai da za ka iya kiransa
da jarumin matashi, sai dai kallo daya za ka yi
masa.
Ka san ya rasa wani ginshiki na rayuwarsa,
wanda ya hana shi damar da za'a kira shi da
mutumin kirki, ba shi da natsuwa, da ganinsa ka
ga wanda ya yi nisa a shaye-shaye, ko a yanzu ba'a cikin hayyacinsa ya ke ba.

Page 4

"Inna abinci na ke so,yunwa nake ji” ya fada da wata irin budaddiyar murya
Inna Halima ta yi ajiyar zuciya,
sannan ta kalli Afrah ta ce
"'Afrah aje tsintsiyar nan,
ki zubo ma yayanki abinci.”

A hankali ta yi kasa da
tsintsiyar, sannan a sanyaye ta wuce kicin.
Inna Halima ta maida kallonta ga Musaddik,
wanda yake tsaye ya nannade kafafun wando
tace "Zo ka zauna"
Ta nuna masa tabarmar da ke shimfide, ya
wuce da takalmi da komai ya zauna akan tabarmar,
ba ta damu ba, domin ba yau ya saba yin hakan ba,
ta ja kujerar da ta tashi akai, ta koma ta zauna tana
kallonsa. Tana saka abubuwa da dama a ranta.
•Har zuwa lokacin da Afrah ta dawo dauke da
faranti cike da shinkafa da miya da ta dafa,a
hankali ta aje a gabansa, sannan ta juya ta wuce
Zuciyarta cike da tsananin tausayin Musaddik da
halin da yake ciki. Musaddik yace
"Inna na kan so na zo cin abinci gidanki duk
ranar sati, saboda na san Afrah tana gidan nan, ina jindadin abincinta, komai rashin gyaransa”
Maganar Musaddik ta katse mata tunani da take
yi ta juyo da idonta tana kallon sa, a yayin da Inna Halima ta jinjina kai tace

Page 5
"Ba kai kadai ke jin dadin girkin Afrah ba,
kowa yana yabawa, tun daga kan yara har zuwa
maigidan kansa.”
Ya yi dan murmushi, a yayin .da yake cin
abincin, ya dan waiwayi inda Afrah take wacce
Ke cigaba da karasa shara ya ce,
"Haka ne Inna, shi ya sa ni ma
na kan kwaso yunwata zuwa gidanki.
Don na san idan na ce kwadayin girkinta zai
dinga kai ni gidansu kullum, za mu sami matsala
da Mama Hauwa, don na san farantina ba zai
dinga cika ba kamar yadda yake cika a gidanki."
Gaba daya suka yi murmushi, a yayin da ya
maida hankali kan cin abincinsa. Inna Halima kuma
tana zube masa da ido, tana matukar tausayin
Musaddik da kuma rayuwarsa wacce bata taba
tsammanin zai koma haka ba. Duk tsananin
Kamun kansa ilimi da cikar kamalarsa.
Amma rana tsaka rayuwarsa ta koma haka. a
lokacin da ya kamata ace rayuwarsa ta inganta,
babu wanda zai ga Musaddik ya yarda ya kuma
amince Musaddik din da ne, lamarin yana da
matukar daure kai.
Inna Halima ta yi kasa da murya à hankali, ta
fara yi masa magana "Musaddik, anya ka na ganin
wannan rayuwar da ka dora ma kanka za ta kai
ka ga hanya madaidaiciya, wannan wace irin rayuwa ce?
Da mutuncinka da darajarka, rana tsaka duk ka
kore wannan, ka koma ka na Kaskantarciyar

Ku dakace ni

YAR GIDAN IMAM

bazan yarda da rashin yin comments ba don wallahi ina iya barin yin posting din idan bakwa comments.
MUSABBABI

NA

HAJ HABIBA ABUBAKAR IMAM


https://youtube.com/@HabibaAbubakarImam?si=8hYIJhGWi10v_gOI

Page 6
rayuwa mara dadin ji ko gani, shin meye dadin
wannan rayuwar?
A hankali Musaddik ya cire cokali a cikin
abincin, fuskarsa gaba daya duk ta canza ya
shiga cikin damuwa, ya ce a sanyaye,
"Inna babu wani
dadi ga rayuwar da na ke ciki, hakia inda ina da
ikon canja hanyar da na biyo, da na yi gaggawa
na canja, domin ko kadan ban jin dadin rayuwar.
Amma na rasa dalilin da ya sa na kasa yaki da
zuciyata na daina, duk da ina kyamar abinda na
Ke aikatawa ni ma,”

Inna Halima ta jinjina kai fuska cike da
tausayinsa tace
"Ka yi yaki da zuciyarka ne, ka
dage ka kori shaidan, domin hakika shine yake yi
maka huduba, ka tuna irin gata da arziki da ka taso a ciki Musaddik kayi tunanin irin girma da
kamalarka da dubban jama' a suke gani a da, sannan
ka tuna irin ilimi da hangen nesa da ka ke da shi
wanda a yanzu duk sun tattara sun gudu, a
sanadiyyar tsarin rayuwarka da ka canja, ka duba ka
ga yadda ka maida kanka, hakika lamarinka na
damun mu, yana kuma daure mana kai kwarai da gaske
Afrah da ke tsaye gaba daya sai ta juyo ta dora
ma Musaddik idanunta wadanda suka cika da
hawaye, zahiri tana daya daga cikin wadanda
lamarin yayanta Musaddik ke damu, ta kan shiga

Page 7
dimbin damuwa da tunani idan ta tuna halin da
yake ciki, Sannan ta kan rasa inda zata sa kanta, idan ta
kasa gane dalilin canjawar Musaddik, mutumin
da ya taso da nagarta, kamala, natsuwa, ilimi da
matukar hangen nesa, tana daya daga cikin
wadanda rayuwar Musaddik ke matukar burgewa.
Yana matukar ba ta sha'awa, rayuwarsa da
yadda yake tafiyar da lamuransa, abin a tsaya a
kalla ne a kuma yi koyi da su.amma meya kawo wannan canjin?.
"Inna kada ku gaji,
ku yi ta tayani da addu'a don Allah".
Furucinsa ya Kara dasa tausayinsa a zuciyar
Afrah. Inna Halima ta ce
"Addu'a muna nan muna
yi Musaddik. Allah ya shiryeka, ya dawo da kai
hanya madaidaiciya, ba za mu gaji da yi maka
addu'a ba."
Ya
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MUSABBABI Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album