Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

RALIYA-01
.
SHAFI'U DAUDA GIWA
.
SHIMFIDA
.
KANO 2003
.
AL”AMARIN ya fara samo asali ne tun a
yammacin wata laraba” wacce tazo daidai da
mako biyun karshe” na wani zangon karatu a
jami'ar Bayero dake birnin kano” duk inda mutum
ya duba a cikin makarantar dalibai ne birjik” suna ta yawace-yawace kamar kwari” suna hada-hadar
ganawa da malamai domin an riga an saba duk
lokacin da jarrabawa ta karato” to ba sauran
sukuni malamai sun shiga aiki kenan” tun safe
har dare”
.
Wadansu dalibai kuma suna zazzaune suna ta
faman karanta littatafai da takardun kasidun
darasi” da yawa duk suna warwatse ne a cikin
ajujuwan makarantar” wadansu kuma wadanda
basu son yawan hayaniya da cikowar mutane”
suna can saman benaye suna yin nasu karatun”
duk wanda ya shigo cikin makarantar yasan
cewar yanzu ba lokacin wasa bane” musamman
kuma da aka ji an fara kishi kishin cewar a
wannan shekarar za'ayi tankade da rairaya mai
tsanani” shi yasa ba banza tasa dubban daliban
suka dukufa karatu ba” suna bitar darussan
gindin wata katuwar bishiya” wata kyakkyawar
budurwa ce ke xaune rike da nata littafin” ‘yar
kimanin shekaru ashirin da hudu a duniya bayan littafin dake a hannunta” a saman bishiyar da
take xaune a karkashinta” wasu tsuntsaye ne”
‘yan gida daya masu kama daya su kimanin
ashirin jikinsu yana ta sheki a cikin ganyayen
bishiyar” tun xaman wannan budurwa a wurin”
tsuntsayen keta faman rera mata wakoki iri-iri a
cikin wani yare mai wahalar ganewa”
To amma kuma ko sau daya budurwar bata daga
kai ta dubi wadannan tsuntsaye ba” kuma ga
alama aikin banxa suke yi” domin kuwa koke-
koken su da wakoki basu sami karbuwa a xuciyar budurwar ba” wasu daliban idan suka ga haka”
zasu yi tsammanin duk saboda tsabar karatu
wannan budurwar tayi xuru a xaune bata ji bata
gani” to amma kuma a xahiri ba haka abin yake
ba” domin kuwa tana dai dakon littafin ne a
hannunta amma idanunta bashi suke kallo ba”
Hankalinta ya tafi can wata duniya mai nisa” ita
kadai tasan abinda take nunani a ranta” sai kuma buwayi gagara misali” masanin sirrin boye
.
“RALIYA” Sunan ta da wannan sunan kowa yafi
saninta tun tana karama” to amma kuma a yanxu
data girma ta xama ‘yar jami'a akwai wadanda
ke kiranta da Diamond ba haka kawai yasa
wasu dalibai ke kiranta da wannan suna ba”
akwai hujjoji kwarara”
Da farko dai Allah ya halicci “RALIYA” da
tsabagen kyau fiye da duk yadda xa.a misalta ta
domin kuwa idan mutum ya hangota daga nesa”
zai sami kanshi yana kallon fara ce sol” to amma
kuma da zaran ta matso kusa” sai ta rikida ta
koma ita ba fara ba sannan kuma ba baka ba”
fuskarta ‘yar matsakaiciya ce doguwa” wacce
bata cike kauri ba shiyasa ko a wanne lokaci ko
barci take yi” tana nan da annurinta” “RALIYA” ta more lallausar fatar jiki kamar kwalba” sannan
kuma Idanunta ba manya-manya bane” kuma ba
kanana bane” sun dan shige ciki kadan” da xaran
ta kalli namiji dasu sai yaji duk gwiwarshi ta saki
babu kwari ko laifi tayi ma sauyinta sai dai yayi
bambami a bayan fage” amma ba dai ya tare ta
gaba da gaba ba”
.
Tsarki da godiya sun tabbata ga Ubangijin
Al'arshi gwanin tsara halittu” domin kuwa babu
wanda zaiga “RALIYA” ya dauka cewar
bahaushiya ce” saboda tafi kama da irin ‘yan
matan turawan yammacin duniya da ake gani a
hotuna da mujallu” bata cika kama da ‘yan matan
nahiyar bakaken fata ba” to amma kuma a zahiri
cikakkiyar bahaushiya ce ‘yar asalin jihar kano”
wacce ta taso a wani kauye kilomita hamsin daga birnin kano a karamar hukumar Garun Malam.
Daliban jami”ar sun sha rade-radi akan wannan
budurwa mai suna “RALIYA” domin kuwa wasu
samarin tuntuni sun tsinke da al”amarinta” sun
fara tunanin da wahala idan ba aljana ba ce ta
shigo cikin mutane tana karatu” domin kuwa
sanin kowa ne cewar ko da a jami”ar ‘yan matan aljanu “RALIYA” xata iya cinye gasar (miss campus) wato sarauniyar kyau ta jami.a”
Babu wani saurayi dake a jami”ar da zai ci karo
da Raliya koda a hanya baiji yana sonta ba”
ragowar “yan matan kuwa suna kinta ne kawai
saboda sun san cewar ta sami wani abu” wanda
koda miliyan dubu baza,a sayar masu ba a
duniya” shiyasa suke nuna mata kishi da kuma
kyashi” to amma kuma ya zasuyi tunda haka
Allah yaso ya ganta?
.
Ba dalibai kadai ke kaunar “Raliya ba” hatta
malaman makarantar su kansu labarinta sukeyi”
akwai lokuta da dama da “Raliya ke firgita
lakcarori da idanunta” domin kuwa idan malami
yana kan aikin bada darasi a cikin aji da xarar ya hada ido da ita a cikin dalibai duk sai yabi ya daburce”
wasu dalibai sun taba cewa” akwai wani malamin lissafi” wanda baya son shigowa darasi” idan babu “RALIYA” a cikin
ajinsu” wadansu kuma sun bada amanna da cewa
idan akwai “Raliya a aji” to malamai ba sa
yankewa kuma duk wanda ya shigo baya son fita”
.
TO amma kuma koda ace duk wannan zuki ta
malli ce” sanin kowane cewar “Raliya
tauraruwa ce a wannan makaranta” kuma duk
wani namiji dake kai da komo a makarantar tun
daga kan masu gadi har xuwa sama” su dukansu
suna mafarkin ace “RALIYA” ta xama masoyiyar
su idan so samu ne”
to sai dai kuma duk da wannan ni'ima da kuma
baiwa da Allah yayiwa wannan kyakkyawar
budurwa” sai kuma ya jarrabeta da kasancewa
cikin tsananin kuncin rayuwa da rashin galihu”
gashi kuma ita ba kula samari take yi ballantana ta dan rika yagar abin masarufi sau da yawa sai
wata kawarta da suka shaku mai suna SURI ta
taimaka mata sannan take samun sabulun da
xata wanke ‘yan tsummokaran ta shiyasa Raliya bata son shiga cikin mutane sosai domin kuwa
xamanta ita kadai musamman idan babu kawarta Suri ya fiye mata kwanciyar hankali” fiye da
komai a makaranta”
Sannan kuma wani karin abin al”ajabi ga lamarin
wannan budurwa shine” duk da samari da ‘yan
gayi masu xanxaro da motoci dake ta kawo mata
farmaki a kullum kwanan duniya domin ta xama masoyiyarsu” ita a nata bangaren tun tuni
zuciyarta tayi nisa da afkawa cikin xuxxurfan
kogin kaunar wani saurayi dake KAUYENSU mai suna RUFA'I
A xahiri tun RALIYA tana karama suke ta wannan
soyayya da Rufa'i dan kauye” gashi kuma yanxu
ta girma ta xama cikakkiyar ‘yar boko tana
karatun digiri” shi kuma Rufa'i tun tasowarsu ko
karatun firamare baiyi ba” to amma kuma ga
mamakin Raliya sai taji har yanxun tana kaunar
shi”
Da ace tuntuni ta sami karin masu goya mata
baya don tabar wannan karatu nata” da tuni
tabar makarantar ta koma kauyensu” domin ta
kosa taga ranar aurensu ita da Rufa'i to
amma kuma kakarta ce kadai ke goyon bayanta acire ta daga wannan jami.a ta koma gida haka
nan tayi aure” ita kuma kakartata ganin ta tsufa
ba.a cika daukar shawararta ba” kome ta fada
sai ace rudun tsufa ne shiyasa sai ta wuni tana
masifa” babu wanda zai saurareta”
Yawancin dalibai suna yiwa RALIYA mummunar
fahimta” domin kuwa wasu sun dauka cewar
tsabar fadin rai gareta” shiyasa bata cika son
yiwa mutane magana ba” sannan kuma bata da
wasu tarin kawaye sai SURI ita kadae” to amma
kuma RALIYA bata da fadin rai” yawanci idan aka
ga ta xauna ita kadai to tunanin rabin ranta
Rufa'i take yi” sau tari tunanin wannan saurayi
nata dan kauye yakan buwayi xuciyar Raliya
har ma ta kasa yin barci” ko a halin yanxu da
take a xaune a gindin wannan bishiya mai
tsuntsaye tunanin da takeyi kenan” tunanin
masoyinta Rufa'i
Duk lokacin da Raliya kyakkyawa xatayi irin
wannan xama ta tambayi kanya shin anya kuwa
Rufa'i xai yi xaman jiranta har xuwa lokacin da
xata gama wannan dogon karatu nata?” Hakika
wannan wani abu ne mai wahala wanda wanda
bashi da tabbas” domin tun shekaru shida da
suka wuce tun Raliya tana sakandire Rufa'i ya
matsa a gaggauta ayi aurensu domin kuwa ya
gaji da xaman jira” tasan halin samarin kauyensu
da son aure” yanxu haka watakila Rufa'i ya sami
wata budurwa wacce yake so ya aura ita kuma
ya hankura da ita” wannan tsammani da raliya
take yi a xuciyarta yana ci mata tuwo a kwarya”
.
Wannan tsammani da Raliya take yi xai iya
xama gaskiya” domin kuwa baxata taba mance
da maganganun da Rufa'i yasha fada mata ba
idan ta koma gida hutu
“wai ke Raliya wannan wane irin karatu ne haka
babu ranar gamawa?” ki duba fa ki gani yanxu
tsararrakinki su magajiya da talatu mai fura duk sun haifi ‘ya’ya biyar biyar” amma mu muna nan
har yanxu bama asan ranar da xa.ayi auren ba”
kuma shi wannan karatu da kikeyi” don baki sani ba ne” amma duk kauyen nan namu xagin
babanki ake yi” kowa yana tir da wannan karatu
da kikeyi na ‘yan birni………….
Duk lokacin da Rufa”i yayi mata irin wannan
maganar Raliya bata cewa komae” domin kuwa
tasan cewar shi baiyi karatu ba” bai san dadin
ilmi ba dole ne yaga kamar aikin banxa takeyi
tana batawa kanta lokaci”
to amma idan a yanxu data dawo jami'a ‘yan
kwanakin nan gab da xa.a fara jarrabawa” saita
fara wadansu irin munanan mafarki marasa dadin
gani” haka kawai da xarar Raliya ta kwanta barci
sai tayi mafarkin wai ga jama.a nan sun cika
kauyensu makil ana ta shagalin bikin auren
masoyinta Rufa'i da wata yarinyar daban”
hakika wadannan mafarkai” sun tayarwa da
Raliya hankali matuka. Sannan kuma duk
hankalinta ya koma kauyensu”
.
Don haka ne yasa ta yanke shawarar tattara
inata’inata ta koma gida” da xarar taje xata
tsaya kai da fata” baxata sake dawowa jami”a
ba” domin kuwa akwai sauran shekaru uku a
gabanta” kafin ta gama karatun” Raliya tana
fargabar xaiyi wahala a cikin shekaru ukun nan
idan har mafarkan da takeyi ba xasu xama
gaskiya ba” to ita kam” gara ace ta rasa karatun
digiri data rasa wannan masoyi nata Rufa”i ko
banxa dai xata karashe rayuwarta cikin farin ciki tare da masoyinta
.
Raliya taji an girgixa kafadarta da karfi” ta farka
daga dogon tunanin da take yi sannan ta daga
kanta taga kawarta suri” a tsaye a kanta ta dafe
kugu tana yi mata murmushi.
.
.
KU KASANCE DA
TASKAR GIDAN LITTAFIRALIYA-02
.
RALIYA wanne irin tunani ke kuwa kikeyi haka?"
Ina ta faman yi maki magana amma koki dago
kai ki dubeni"
raliya tayi ajiyar xuciya" sannan ta rufe littafin
da ta rike a hannunta" kwata kwata ta mance a
gindin bishiya take xaune"
"ke ma kin san tunanin da nakeyi suri"
Raliya tace da ita a sanyaye sannan ta sake
kurawa wata shadda idanu wacce ta sauko daga
saman bishiyar ta sauka akan wani tsohon famfo
dake kusa da inda suke"
Suri ta xauna a kusa da kawarta Raliya" sannan
tace da ita cikin damuwa"
"Raliya waeke da gaske kike yi barin makarantar
nan xakiyi saboda kawai ki koma gida ki ga
masoyinki"? Ki tuna fa yanxu lokacin jarrabawa
ne" kowa ya mayar da hankali wajen karatu"
gaskiya nidai ban baki goyon bayan ace kin bar
makaranta a irin wannan lokaci ba
RALIYA" ta dubi kawarta suri cikin nutsuwa"
dogowar budurwa mai yawan kiriniya da kuma
rashin nutsuwa a wajen magana" wankan
tarwada mai yawan barin gashin kanta a waje"
Raliya tace da ita"
"Ba wai naki in bi shawararki bace suri" nasan
cewar abinda kika fadi mani gaskiya ne" to amma
kuwa ya xame mani dole in hankura da karatun
nan tunda dai ko da ace na tsaya makaranta
yawan tunanin Rufa"i baxae taba barina inyi
karatu ba" ballantana har inci jarrabawa"
Dalili na biyu kuwa shine" ke kinfi kowa sanin
halin da nake ciki a makarantar nan suri" ba wani abu nake xuwa dashi ba" da xan iya rike kaina a
makarantaar nan" dole ke nake dorawa"
dawainiya dani" kina tsammanin xan
iya jurewa inta xama a haka kullum a wahalce
suri?" gaskiya baxan iya ba"
Suri tayi farat tace da ita"
"To ai kece Raliya wallahi wani abin ma laifinki
ne" na sha nuna maki hanyar da nake bi ina
samun kudi" amma ke sai kice wai ba halinki
bane" to muda mukeyi halin mu ne Raliya?" ba
dole ke sa mutum yayi wani abin ba?" ni inda ace nice nake da wannan kyan naki to da na gama
hayewa tsanin arxiki a duniya"
wannan kyan da Allah ya baki Raliya na samun
hutu ne amma ke baki san darajar shi ba" kin
tsaya kina wahalar da kanki a banxa" ni bansan
lokacin da xaki goge ki xama cikakkiyar 'yar birni ba Raliya"
Raliya ta dubi suri cikin damuwa tace"
"Na sha baki amsar wannan maganar suri" ni ban
dauki duniya a bakin komae ba" nasan cewar
maganr kyau" hakika ni kyakkyawa ce kuma na
godewa Allah daya yi mani wannan baiwa" Amma
a gaskiya ni baxan taba ampani da wannan dama
in bata rayuwata ina biyewa maxa 'yan iska dake
bata 'yan mata ba" don in tara kudi a duniya" ni
nasan cewar komae nufin Allah ne" da arxiki da
talauci duk nufi ne na Allah"
Idan Allah ya nufa xan sami wani abu a duniya"
to ba saina bata rayuwata zan kae irin wannan
matsayi ba" domin ban isa in ba kaina wani abu
da ubangiji bai nufeni da samu ba" Na gwammace
dai in hakura in koma kauyenmu in auri
masoyina Rufa"i dake can yana xaman jirana"
Suri tayi tsaki ta kawar da kanta tace"
"Ai ke dama haka kike Raliya. Sai kije kiyi tayi" in
banda lalacewa tayaya xa.a ce kinyi karatunki"
kin xauna kin goge a birni kowa yana sha.awarki"
amma ace kin koma kauye kin auri wani wanda
bai yi karatu ba?" haba Raliya gaskiya ki rabu da
wannan Rufa"in in dai ba sammu yayi maki ba" ki
tsaya ana birni ki more rayuwarki" ga samari
masu kudi da motoci wayayyu suna binki kina
sharesu kullum"
ke ba matar kauyawa bace malama" xaki fi macin da miloniya dan birni" ba wani dan kauye ba wai shi Rufa"i. Rufa"in me dan Allah?"
.
Raliya tace"
"Nidai ina son abina hakan nan! Gaskiya suri ki
daina kushe min saurayi meye haka?" wannan ma
ai rainin arxiki ne" ki daina kushe mani shi
gaskiya bana so"
suri tayi murmushi sannan ta dafa kafadar Raliya
tace"
"Lallai Raliya kinyi nisa" ai an har fushi kikayi har
kina wani kakkareshi" sannu malamar soyayya"
sai ki gafarceni ban san cewar ba.a kushe maki
rabin rai ba"
Raliya ta saki ranta da taga suri tayi fushi tace
da ita"
"Ba haka bane suri" kiyi hankuri" abin da yasa
kikaga na nace akan kaunarsa" alkawari ne mai
karfi tsakanina dashi" tun muna yara" kuma kinga
dai bai kamata ace na karya alkawari ba suri"
shiyasa kikaga na mace akan kaunarsa" wannan
ita ce hujjata"
Suri tace.
"To ae shinke nan" tunda kina ganin haka yafi
dacewa da rayuwarki baxan hanaki ba Raliya" mu
dai muna nan cikin birni xamu xauna a cikin
ni"ima da daula" Babu komai kawata" watarana
idan na xama miloniya xanxo kauyenku in da kike
domin in ganki"
Raliya ta harareta" sannan tace"
"A gidan wa xaki ga miliyan din kina fama da
wahalar makaranta"? Kedai suri baki rabuwa da
daukar aradu ta ka"
Suri tayi dariya sannan ta kurawa shuke shuken"
dake a wajen idanu"
koraye shar dasu a cikin fararen duwatsu kamar
tutar nigeria" tace da Raliya cikin sanyin murya"
"Nasan cewar dama xakiyi mamaki Raliya" to
amma kuma bari in rantse miki kiji da kunnenki"
Wallahi gobe i yanxu na gama hayewa" domin
kuwa na mallaki kudi nawa na kaena dala na
gugar dala" dalar amurka har miliyan hamsin"
.
WANNAN wani sirrine a tsakanina dake wanda
bana so kowa ya sani daga ni sai ke Raliya"
"Raliya ta dubi kawarta shekeke har cikin
idanunta" tasan suri da son wasa" to amma
kuma a wannan karon babu alamar wasa ko
karya a fuskar saru" duk a ina xaki sami
wadannan kudade ke da kike a makaranta?
Suri ta sake yi wani makararren murmushi
sannan ta hade fuskarta tace da Raliya"
"Gaskiya wannan wani sirri ne mai girma" to
amma kuma baxan boye miki ba Raliya. Akwai
wani mutum da yake sona kuma yana matukar
kashe mani kudi" kome nace ina so shi yake saya min sunanshi JARMAI amma a gaskiya baxan boye miki ba JARMAI rikakken ƁARAWO ne"
Bashi ya fada mani ba" to amma kuma yasan
cewar na sani" jiya ne da yaxo nan makaranta ya dauke ni a mota muka fita shine yake sanar dani cewar yaji kawunshi tare da wasu mutane suna hirar sirri da daddare cewar akwai wasu makudan kudi da xasu fitar a boye daga matatar man fetur kawun Jarmai masoyina shine babban mai lura
da kudi na cibiyar tace man fetur na kasa"
Kuma a gidanshi Jarmai yake xaune" shine yake so idan sun xo da kudin ya sacesu basu sani ba"
ya kawo mana mu gudu dasu mubar kasar" to
amma kuma ni tuni na yanke shawarar cewar
idan har yaxo da kudin na gansu to sun xama
nawa"
.
RALIYA dake sauraronta kamar wacce ke kallon
mahaukaciya tace da suri"
"to amma ke suri" idan ma ace duk wannan
labari da kika fada mani gaskiya ne" alal misali"
me xakiyi da irin wadannan kaxaman kudi a
duniya?" ina xaki kai miliyan hamsin.....?
SURI ta kalli Raliya cikin rainin hankali tace"
"lallai ke cikakkiyar bakauyiya ce Raliya" ke in
banda abinki a ina kika taba jin kudi sunyi wa
mutum yawa a duniya" tab!
Bari kiji in fada maki" idan kina da kudi a duniya
dole ne ki xauna tare da mutanen da ake ganin
kimarsu a duniya" sannan kuma xaki je wurare
da mutane kejin labari a duniya"
Xaki ci abinci da wasu kejin labarinshi har su
mutu ba xasu taba ganin irinshi ba" koda a hotone" ko aure kikayi dole ne mijinki ya kalleki da
mutunci fiye da kowacce mace" saboda ya san
cewar kema kin dogara da kanki"i dan baki da
kudi a duniya" kina cikin rububi Raliya" babu
wanda yasan kinxo ko baki xo ba"
RALIYA tayi dariya domin kuwa ita har kullum
tana daukar suri ne a matsayin wata birkitacciya
mara kamun kai" tace da ita"
"to bayan kin gama xuwa wuraren da kike so"
sannan kuma kin gama ganin irin mutanen da
kikeso a duniya" sannan kuma kin gama cin
abinci da kike jin labari...." to maganar mutuwa
kuma fa suri" ita kuma nawa xaki kashe ki boye
mata a duniya?
SURI taji gabanta ya fadi ras!! Ta bata rai ta kalli
kawarta Raliya a fusace" bata san lokacin da
takai mata duka a baya ba"
RALIYA ta tashi tana dariya ta nufi dakin
kwanansu" suri tabi ta a guje" 'yan mata biyu
suka haye saman bene da gudu sannan suka
shige cikin wani daki"
.
SHIMFIDA TA BIYU"
.
Ba abinda yafi batawa mutane rai irin ace an
dauke wuta da daddare" musamman kuma a irin
wannan lokaci da aka sheka ruwan sama da
yamma" duk inda mutum ya jepa kafa" ruwa ne
ke cin gudu akan hanyoyi" don haka mutane da
dama suka hankura da fitowa cikin daren domin
shakatawa" tun kafin karfe goma tayi kafa ta
dauke" kamar an sawa mutane dokar ta baci"
Wasu halittu kuma sunji dadi da irin wannan
yanayi" kamar su mujiya uwar 'yan bakin jini"
wacce zata fito a cikin daren tayi shawaginta ako
ina a sararin samaniya" ba tare da sauran
tsuntsaye axxalumai irin su shaho sun ganta sun
takura mata ba" sannan kuma dangin kwaro anan
ma an samu shinge" domin kuwa duk da yake
cewar halittune ma.abota son haske" a wannan
karon sun firfito ako ina a cikin daren" suna marin bangon gidajen mutane babu wanda ya kula tasu"
Idan kuma aka dawo bangaren mutane suma
baxa a rasa wadanda wannan dare ya burgesu ba suke a cikin nishadi" musamman ALHAJI ELBASHIR
wanda yake takai komo a cikin falonshi na sirri da
ya kebe don ganawa da manyan bakinshi" tun
kafin ayi sallar isha'i yake ta inda-inda yana jiran
xuwan abokan shi guda uku" ko kuma ace
abokan satarshi beraye masu malum-malum"
Wadanda suka mara mishi baya" suka wawure
makudan kudi daga asusun man fetur na kasar
nigeria har dala milyan hamsin" A halin yanxu
wadannan kudi an fitar dasu" suna nan a cikin
falon a boye" duk duniya ba wanda yasan wannan sirri" daga wadannan axxaluman mutane barayin
dukiyar talakawa da kasa ke dauka tana yi masu
aiki" sai kuma JARMAI wanda ya rabe a
kwanakin baya yaji mutanen suna kus kus" da
daddare akan wannan mahaukaciyar dukiya da
xasuyi awon gaba da ita kowa ya dibi nashi
kason yaje ya xuba a bankin da yake ajiya"
Elbashir yana nan a tsaye yana duba agogo" har karfe sha daya ta cika har da minti hudu" saiya ji motsin mota.....
.
.
Ku kasance tare da
RAHMERT KHALEEL ZAZZAU
da zata zo muku da shirin FILIN RAHA da misalin karfe 8pm na yammacin yau lahadi idan Allah ya kaimu.
.
.
ƙarfin gwiwar da zaku bani a cikin kwamen hakan shi zai bani damar kawo muku shafi biyu 2 a duk rana akasin yanzu shafi ɗaya nake kawo muku.
.
NAKU A KULLUM
SADEEQ SHEHU SHARIFF
ƊAN MUTAN YOBE.
( JARMAN TASKA )
.
LOADING PAGE 03RALIYA - 03
.
ELBASHIR yana nan a tsaye yana duba agogo"
da karfe sha daya ta cika dai dai harda minti hudu" sai yaji motsin mota a waje" yayi sauri ya leka ta
gilashin tagar falon" yaga mutane uku sun fito
daga cikin mota daya da suka shigo tare" ko
wanne a cikinsu yana fama da katon ciki" kamar
an kifa musu kwarya" sai nishi suke cikin
manyan
riguna" sun kwashi haramun duniya na barci ba.a
gane ba" gashi yanxu da kowa ya farka ma basu daina ba""
Lokacin da barayin xaunen suka halarta shiga
cikin gidan Elbashir" basu ankara da wasu
mutane guda biyu dake boye a cikin filawoyin da
suka xagaye gidan ba" koda yake dai zaifi kyau
idan aka ce dasu ifiritai" domin kuwa ba don
suna
da hannaye da kafafuwa kamar sauran mutane
ba" to ba abinda zai sa a sakasu a cikin sahun
'yan adam" wannan halittu guda biyu sun kure
akan wata sana.a wacce suke ci suke sha da ita shekara da shekaru" kuma basu taba yin wata nadama ko jin tausayin wannan muguwar sana'a ba"
Shiyasa koda Elbashir ya tuntubesu da xancen
wasu bakinshi guda uku da xasu kashe mishi yau da daddare" basuyi wani faragaba ba" tuntuni suke nan a rakube suna xaman jiran xuwa mutanen" suna duba agogo lokaci-lokaci suna yin tsaki a fusace" domin kuwa sun fi so in xasuyi kisa" nan da nan suke so su gama" basa son xaman bata lokaci"
Lokacin da abokan Elbashir suka gama shigewa
cikin gidan" sai ifiritan mutanen buyu suka dubi
juna a cikin duhu" daya yace"
"daya xaka kashe ka bar min biyu" ko kuwa in
kashe daya ka gama da biyun?"
Ragowar dayan ya shafi kan guntuwar bindigar
dake hannunshi sannan yace"
"Bar min biyun kawai ka dauki wannan mai jar
rigar da hula" ni xanyi maleji da biyun dukansu"
yakamata ace su goma ne kaga da xa.a samu
aiki da yawa" amma dai yafi babu"
Ifiritan suka tunshire da dariya cikin shake
murya"
don kada a jiyo su" sannan sai suka fito daga
cikin filawoyin rike da bindigoginsu 'yan kanana"
tsawonsu da girmansu duk iri daya ne" haka
kuma xuciyoyinsu da sana'ar su kayan dake
jikinsu ne kawai suka bambanta"
Daya yana sanye da bakin wando da shudiyar
singileti mai hannu"
Daya kuma yana sanye da koren wando da kuma bakar riga mai hoton damisa a bayanta" basu tsaya jiran komai ba" sai suka shige cikin gidan ransu a bace"
.
************* ********** ******** **********
.
Suri tana tsaye ita kadai a saman benen" ta dafa
karfen matari tana kallon jepi jepin masu gadin
dake gilmawa rike da cociloli a hannayensu" da
kuma sauran daliban dake dawowa daga cikin
gari suna shigowa makarantar" wadanda ruwan
da akeyi da kuma sahun daminar bai hanasu fita
kallon sinima ba" da kuma xuwa hira wajen 'yan
matansu da basu kwana a cikin makaranta"
Iskar daren ya busa da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment