Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Wannan littafi mallakar Azizat Hamza ne. Ba a yarda wani ko wata su sarrafa shi ta kowani siga ba, ba'a yarda a karanta shi a youtube channels ba, ba'a yarda a kwafa ko a juya labarin ba tareda hakkin marubuciyar ba.
©AZIZAT HAMZA 2022


Wannnan littafi ƙirƙirarren labari ne. Allah ya yafe min kura-kuren da suke ciki Amin.


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM.


001 Ɓarauniyar nama.

Duk ranan Lahadin karshen wata akan yi Family meeting a gidanmu. Wannan family meeting da ake yi ya banbanta da wanda ake yi na gaba ɗaya iyalen marigayi Alhaji Muhammadu Ubandoma wanda ya kasance Kakanmu, Duk wanda ya haɗa jini da familyn Ubandoma walau ta wajen mace ko namiji duk ana haɗuwa ayi meeting ɗin dashi, ana yin meeting ɗinne bayan wata uku-uku, watau sau huɗu kenan a shekara.
Kai akwai wani meeting ma da Hajiya Kaka ke shiryawa tsakanin 'ya'yanta duk sanda ta ga dama, musamman ma idan wani gagarumin abu na alkhairi koma na sharri ya samu 'yayan Hajiya Sadiyya. Matar nan ta kwana biyu da rasuwa amma har yanzu Hajiya Kaka ba ta dena kishi da ita ba.

Yau ma kamar kullum shirye shiryen meeting ake yi kuma Mama ce ke da girki dan haka duk wani kanshi da ke tashi a gidan daga kichen ɗin sashenta yake fitowa.
Karfe goma na safe zuwa shabiyu na rana ake meeting ɗi, dan haka duk wanda ya san yana cikin list na masu tayata aiki to dole ya kasance a kitchen a wannan lokaci.

A gidanmu wajibi ne a kammala abin karyawa kafin karfe bakwai na safe. Wannan jazaman ne dan kuwa in dai mace ta bari yara suka makara zuwa makaranta saboda bata yi abin karyawa da wuri ba tabbas za ta haɗu da fishin Alhaji, in tai haka fiye da sau ɗaya kuwa tabbas za ta bada bayani idan aka zo meeting na wannan wata.

Ina cikin masu aiki a kitchen amma tsabar lalaci sai da aka kusan gamawa na shigo kitchen ɗin. Anty Firdausi ta ce maza na fita na bar musu kitchen tunda iskanci ne ya hana ni fitowa tun ɗazu.
"Anty Firdausi Allah Hajiya Kaka ce ta sakani aiki a ɗakinta" na faɗa ina zumɓura baki.

Mama da ke faman tsame nama a cikin mai ta daka min tsawa "zaki samu abunyi ne ko sai na zo na ɓallaki a wajen"

Na shiga kitchen ɗin da sauri ina faɗin " Mama mi zan yi?"

"Uwarki za ki yi. Shashasha kawai"
Na yi raurau da ido hawaye na shirin zubo mini, ba dan komai ba sai dan bana iya juran a zageni da uwata koda kuwa a zahiri ba wai ita ɗin ake zagi ba, amma in dai za a yi zagi da uwa to kodai na yi kuka ko kuma na fusata na fara masifa. Mama ce tayi zagin dan haka ba halin masifa.

"Maza ki je ɗaki ki fito min da kulolin Alhaji"

Na tura baki ina faɗin 'wai sai ayita cewa mutum uwarshi bayan baiwar Allah ta jima a cikin kasa'

"Mi kike faɗa wai?"

"Mama ban fa ce komai ba"

"Karya nayi kenan"

"Mama to kullum ki dinga ɓoye kulolin Alhaji a ɗaki kaman da gwal aka yi su"

"Sahala zan ci mutuncinki a gidan nan"

"Sahla sunana" na faɗa tareda ficewa da gudu.
Ban kawo mata kulolin ba sai da na tabbatar ta ɗan huce, lokacin dana shigo da su ma masifa take yiwa su Anty Firdausi akan tun ɗazu basu gama haɗa zoɓo da kunun aya ba.

Ni dai ban yi wani aikin wahala ba illa ɗauko wancan miko wannan. Da aka gama komai kuwa aka barni da su Safiyya da Nasiba muna zuzzuba zaɓo a cikin gorunan ruwa na swan water.

*
Idan za ka saci nama sai ka kware a abubuwa guda uku. Kowa ya san abu na farko amma na biyu da na ukun ba kowa ya iya ba. Na sha kama su Yaya Sulayman da su Yaya Abbas dama su Anty Firdausi suna satan nama amma ni dai ban taɓa gwadawa ba, sai dai idan an sata na gani nima a bani kaso na. Ashe dai su ɗin sun kware ne a abubuwan nan guda uku shiyasa Mama ko Ummi basu taɓa kama su ba.
Da farko dai sai ka iya takunka wajen shiga kitchen yadda ba za a ji karan buɗe kofarka ba balle aji na buɗe tukunya musamman idan ka taki sa'a ba a riga an kulle kitchen da key ba. Idan aka kulle kitchen to tabbas sai dai ka hakura ko kuma kayi karya da ɗaukan wani abu idan ka shiga sai ka idda nufinka.
Kowa zai iya buɗe tukunya. Amma ba kowa ke iya rufewa ba. Wato ka rufe ba tareda an ji ka ba, sannan ka rufe ka maida shi daidai yadda ka same shi a da. Da wannan koda wanda ya rufe tukunyar ya shigo ya gani zai ga kamar ba a buɗe tukunya ba balle har ayi tunanin an saci nama sai dai idan anzo rabawa aga nama sun kasa, ayita mamaki ana masifa.
Idan ka kai matakin nan ka kusa tsira kenan, ka kusa zama gwani.
Mataki na uku shine ka san yadda zaka iya naɗe tabarmar kunyarka da hauka idan har aka kama ka hannu dumu-dumu a cikin tukunya. In ba ka iya kare kanka ba tabbas za ka sha dukan tsiya.

Na san dukkan matakan nan amma ban taɓa gwadawa ba, ni dai ku barni da tsame nama a abincin Hajiya Kaka. Ana cewa tsofi basu cika damuwa da ciye-ciye ba amma Hajiya Kaka kam ta fita zakka. Dan in har zamu yi faɗa to baya nasaba da na cinye mata nama ko abinci ne. Kowanni irin abinci aka kawo wa tsohuwar nan sai ta kai baki. Balle yanzu da Anty Rafee'ah ke yin cake da meat pie wallahi duk a nan kuɗinta ke karewa. Koda yake nima har dani a kwaɗayin..

Tunda Mama ke tsame naman kaza a cikin mai nake jin yawuna na tsinkewa. Na san karshe ba abun kirki za a raba mana ba. A gidan nan kaf babu wacce take rabo tsakani da Allah, rabbon gaskiya irinna Anty Rafee'ah. Ita fa duk ranan girkinta ci ake yi a koshi sosai, ga girkinta daɗi.

Da aka gama komai aka ce mu je mu shirya. Mama ta kulle kitchen ta wuce ɗakinta dan ta yi wanka.
Wallahi fiffike ɗaya na yi niyyar ɗauka. Ban je da niyyar ɗaukan nama dayawa ba kamar yadda sauran su ke yi. Amma komai nawa daban yake dama.

Kwaɗon da aka kulle kichen ɗin da shi ya samu matsala, dan haka wani lokaci sai ka gama kullewa sai kaga ashe bai kullu ba, idan baka lura da kyau ba sai ka tafi ka barshi a haka. Ta nan masu satan nama ke samun dama. Nima a yau ɗin na samu dama dan kuwa Mama bata kulle da kyau ba. Na faki ido na yi sauri na buɗe kitchen ɗin na shiga da sauri, na nufi katon roban da aka zuba naman kajin a ciki na buɗe shi. To abunka da ba sabo ba maimakon na ɗauki duk wanda hannuna ya taɓa sai na sa hannuna cikin naman ina kokarin nemo fiffike, ni a tunanina idan na ɗau fiffike babu wanda zai gane an saci nama. Na ɗauko wani fiffike sai naga kaman ya faye girma dayawa za a iya ganewa. Na maida shi ina neman ɗan karami.

"Asirinki ya tonu. Yau dubunki ya cika a gidan nan. SAHALA"

"Mama Allah ba abinda kike tunani bane"

Saukar mari na ji a fuskana. Ta kamo hannuna muka fito daga kitchen ɗin sai masifa ta ke tana kiran mutanen gida kafin kace me Ummi ta shigo falon Mama tana tambayar mi ya ke faruwa.

"Sahala na kama a kitchen tana satan nama"

Ummi ta kama tafa hannu " dama kece ke shiga mana kitchen kina tsame mana nama a tukunya. Shiyasa ko a kasan gado na ɓoye nama bana tsira da shi"

"Wallahi ba haka bane. Su Anty Firdausi, su Abbas su Hanifa ke sace muku nama ba niba"

"Ai Maman yara ki kaita wajen Alhaji kawai dan idan kika bari Hajiya Kaka ta ji zancen nan ma shashashantar da shi za ta yi, gara a kaita gaban Alhaji ya mata hukunci a gaban kowa"

Ni kam dai Sahla bani da sa'a.

*
Karfe goma da minti biyar aka buɗe meeting da addu'a sannan aka shiga karanto jadawalin meeting ɗin. Meeting ɗin dai ya karkata ne kan Anty Firdausi wacce take shirin gama sakandare school bana sai kuma batun su Abban Egypt da za su zo hutun sallah. Da aka gama faɗin mahimman abubuwa sannan Alhaji ya tambaya ko akwai wani mai korafi ko wata matsala ko shawara. Caraf Mama ta ɗaga hannu ta ce Alhaji ina da magana. Alhaji ya bata izini.

Ina zaune a kasan kujera kusa da Hajiya Kaka. Koma mi za ayi dai na san Hajiya ba za ta bari ayi min bulala a gaban kowa ba kamar yadda Alhaji ya saba hukunta yara.

"Alhaji na kama ɓarauniyar nama a gidan nan. Da za a dinga magana ana cewa bama saka isashshen nama a miya yau dai na kama mai satan mana nama"

Kafin Alhaji yai magana Ummi ta fara nata haɗin.
"Alhaji, Sahala ta jima tana mana sata a kitchen. Ba dama ka kauda kai sai ka nemi abu ka rasa. Ranan wallahi abinda ta tsame min a tukunya yafi rabin kaza"

"Allah Karya su ke min. Alhaji Allah ban taɓa satan nama ba. Hajiya Kaka kawai na ke ɗaukewa nama"

"Na kama ki kina sata kice karya muke miki"

"Mama ai ban riga na cire hannuna a roban ba balle kice sacewa zan yi, kika sani ma ko kuda nake son cirewa a ciki. Alhaji Allah su Firdausi da su..."

"Yi mana shiru" Mama ta daka min tsawa.

"Kai Aishatu. Ki bar min jikata. Idanma ta saci naman ke kika siya ne da zaki bi ki ɗagawa mutane hankali. Ke kuma Zainabu yaushe kika dena siyarda kayan abinci da zaki tsalma bakin ki cikin maganan nan"

" Hajiya Kaka zancen nan fa tun ina Amarya ne fa"

"Ya isa!" Alhaji ya daka tsawa

"Zo nan Sahla"

Na mike daga gefen Hajiya Kaka na karisa gaban Alhaji.

"Faɗamin gaskiya kin ji. Na san ba kya karya Uwata"

Na ɗan sunkuyar da kai kasa nace "Alhaji, Allah fiffike ɗaya zan ɗauka shine Mama ta ganni. Da Mama tana bamu nama kamar yadda Anty Amarya ke bamu ai ba zan je na ɗauki fiffike a bayan idonta ba ko?"

"Haka ne" ya faɗa yana gyaɗa kai.

Irin kallon da Alhaji yaiwa Mama yasa ta fara Salati tana faɗin wai sharri na mata.
Alhaji bai min komai ba amma lokacin da Alhaji ya kai Hajiya Kaka ganin likita na daku a hannun Mama.
Ni dai Sahla a komai bani da sa'a.

***

Alhaji Muhammadu Ubandoman Gombe shine kakanmu. Matarsa ta farko 'yaruwarsa ce wato Hajiya Fatima, sun kusan shekara takwas da aure amma bata taɓa haihuwa ba wannan yasa ya auri wata Fatimar wacce a yau kowa ke kiranta da Hajiya Kaka.
Sai da Hajiya Kaka ta haifi 'ya'ya biyar kafin uwargidanta Hajiya Fatima ta haifi Sulaiman sababin haihuwar Allah ya ɗau ranta. Macece kamila sosai, ga hakuri da ilimin addini wannan yasa suka samu zaman lafiya da Hajiya Kaka. Bayan rasuwan Hajiya Fatima Alhaji Muhammadu ya auro Hajiya Sadiyya, har ya bar duniya kuwa babu jituwa sam tsakanin matan nasa, wannan ya ja rarrabuwan kan 'ya'yan.

Hajiya Kaka ce ta raini Sulayman shiyasa ma bata banbance shi da nata 'ya'yan ba.

'Ya'yan Hajiya Kaka sune:

Fatima Bintu
Kabiru
Fatima Zahra'u
AbdulKarim
Umar
Ahmad
Maryam

'Ya'yan Hajiya Sadiyya kuma:

Abubakar
Fatima Batula
Isma'il
Ɗahiru
Shehu

Kabiru shine namiji babba kuma shi ya gaji sarautan mahaifinsu ta Ubandoma. Kowa da Alhaji yake kiransa.

Kafin na cigaba ya kamata ku san wani abu. Lokacin da Kakanmu ke raye yayi kokarin sakawa 'ya'yansa mata suna FATIMA kasancewar sunan mahaifiyarsa kenan sannan sunan matansa biyu. Sai dai duk FATIMAN da aka saka ba ta fin sati biyu ta ke komawa. Kafin Bintu sai da Hajiya Kaka ta rasa FATIMA guda uku a jere. Ta huɗun da aka kirata da Bintu sai ta tsaya. Da ya auri Hajiya Sadiyya ma 'yarta ta farko Fatima aka saka mata ai itama ba ta yi wata ɗaya ba ta koma, sai ta biyun da aka saka mata Batula sai ta tsaya. Wannan yasa Hajiya Kaka ta camfa da cewa in har aka saka sunan FATIMA kuma aka barshi ba a kira yarinyar da wani inkiya ba komawa za ta yi.
Wannan kuma ya zauna daram. Kuma kaman dole sai an saka sunan Fatima a gidan. Ina ji wanda aka raɗawa sunan Fatima a familynmu sun fi ishirin. Daga Fatima kaza sai Fatima kaza. Da ace an bar mana babban sunan da inaga sai dai a dinga cewa Fatima 1, Fatima 2, Fatima 3, har Fatima 30 ko 50.

Ance 'yar Alhaji ta farko ma Fatima aka saka mata kuma ba a ɓoye sunan ba. A kasar turai aka haifeta amma bata yi wata uku ba ta koma. Wannan yasa kowa ya saduda da kiran yaransa da sunan Fatima zalla ba tareda wani inkiya ba. Nima ɗin Fatima Sahla sunana.

Matar Alhaji ta farko Gimbiya Maryam ce 'yar Sarkin Gombe. Dake yana karatu a chan kasar waje dan haka a nan suka fara zama. Yaransu uku a chan kafin auren ya mutu lokacin da ya tada batun kara aure bayan ya gaji sarautar Ubandoma.

Gimbiya Maryam ita ta haifi:

Fatima (ta rasu)
Aliyu Faruq
Fatima Hasina
Fatima Sayyida.

Bayan rabuwarsu ya auri Hajiya Aishatu wacce kowa ke kiranta da Mama, yaran Mama sune:

Fatima Karima
Mustafa
Abdullahi
Yusuf
Amina
Fatima Firdausi
Abbas
Fatima Nasiba

Matarsa ta biyu ita ce Hajiya Zainab wacce muke kira Ummi, yaranta tara amma uku sun rasu.

Sulayman
Asiya
Abbas
Fatima Zuhriyya
Safiyya
Fatima Haniefa

Matarsa ta uku kuma ita ce Hajiya Bilkisu, bazawara ce, yaranta biyu a gidan:

Fatima Fadila
da Fatima Nabila

Matar Alhaji ta Huɗu ita ce Anty Rafee'ah wacce muke kira Anty Amarya. Itama 'yar gidan Sarauta ce, mahaifinta kanine ga Sarkin Gombe. Shekaransu tara da aure amma har yanzu ba ta haihu ba. Ita ɗin likita ce shiyasa ba ta shiga tsurkun cikin gidanmu.

Mai bima Alhaji shine AbdulKarim wanda muke kira da Abba. Shi da matarsa da 'ya'yansa suna zaune a Egypt sai dai su kan zo sau ɗaya duk shekara. Yaransu huɗu ne:

Affan
Fatima Amal
Fatima Amra da
Sulayman (Boy)

Sulayman Muhammad Ubandoma shine mahaifina. Kamar yadda mahaifiyarsa ba ta yi tsawon rai ba haka shima bai yi tsawon rai ba. Kamar ma dai shi da mahaifiyata an halicce sune dan kawai su haifo Sahla sannan su bar duniya. Ance mahaifiyata ko sakani a ido ba ta yi ba har ta rasu. Awa ɗaya bayan ta haifeni ta koma ga mahaliccinta. Babana kuma ina shekara biyu ya rasu a hatsarin mota.

Yanzu Alhaji Kabiru shine mahaifina, Hajiya Kaka kuwa take zaman Kakata kuma Uwa. Amma a wannan gida duk gatana sai da a ka kirani da ɓarauniyar nama. Har yanzu zancen nan yaki mutuwa, in dai ana suyan nama ko a sallah ko a biki sai dai ban shigo ba amma yanzu za a maido zancen. Ni dai Allah ya isana tunda fiffiken kaza kawai na je ɗauka...

Ya kuka gani. Ni ɓarauniyar nama ce???

***

002...Sahla Dear...

Gidanmu yana da ɓangarori dayawa. Gini ne na da amma Alhaji ya gyara, an zamanantar da shi. Matan Alhaji kowacce da ɓangarenta, falo, kitchen da ɗakuna biyu, store da kuma banɗaki.
Ita Mama akwai son girma da shegen son nuna kai. Lokacin da aka aurota Kaka tana yawan mata gori da tsohuwar matar Alhaji wato Gimbiya Maryam. Wannan yasa ta ki jinin ka haɗata da duk abinda ya shafi Maryam ɗin, 'ya'yanta ma da suke kasar waje ko sun zo gidan ba ta yi da su. To ba ma zuwan su ke ba. Dan ni dai hana karya tun dana taso sau biyu na taɓa saka Anty Hasina da Anty Sayyidah a ido. Dan ko bikin Anty Hasina da aka yi shekara biyu da suka wuce a fadar Maimartaba akayi komai. Shi kuma Uncle Faruqu a hotunan biki kawai na ganshi.
To kamar yadda na ke baku labari. Mama dai kullum fitinarta mi za ta saka a ɗakinta da zai fi na sauran kishiyoyinta. In kuwa sutura ce ko bashi sai ta ciwo ta siya dan kawai ta saka ta fi sauran matan.

Ummi kuma ga kwaɗayi, roko da kuma rowa. Har yau tana zaran abinci a store ɗinta ta siyar ta kashe kuɗin. Kullum cikin rikici ake da ita akan kayan abincinta baya taɓa kaiwa karshen wata. Bayan waɗannan halayen indai wajen gulma ne to sai dai a shafa mata Fatiha. Radiyo ce mai jini. Wallahi duk gulmar Hajiya Kaka ta sallame mata. Tana da kazanta gaskiya dan da zaka duba karkashin gadonta za ka iya samun ruɓaɓɓen Albasa da aka ɓoye tun shekara biyu da suka wuce. Bara da ta haihu ɗan bai zo da rai ba wata Babarta ta zo yi mata wanka ta sharo mushen kyankyasai sun fi hamsin a kasan gado, inaga maganin sauron da ta ke sawa ne ya ke kashe su. Ga su ledar taliya su macaroni su ledar maggi da ta ɓoye ɓeraye sun ci na ci sun bar na bari. Gaskiya ranan girkinta anfi jin jiki. Ba zata taɓa girki tsakani da Allah ba, duk irin cefanen da za a bata ba zata taɓa amfani da shi duka ba. Gara Mama takan yi girki mai kyau sai dai ba zaku koshi ba, amma yaranta zasu koshi. Ita Ummi har a yaranta mugunta take musu. Duk wannan halayen nata fa tafi kowa zuwa Islamiyya a cikin matan Alhaji. Sai ka rasa mima ta ke koyowa idan taje chan dan sama da shekaru goma tana zuwa Islamiyya amma babu wani abu daya gyaru cikin halayenta. Da lokacin Azumi ma ita ce gaba-gaba wajen zuwa sallar taraweeh da tahajjud.

Umma Bilki. Hmm. Umma Bilki. Allah ya yafemu dai kawai amma ni kam gara Ummi sau dubu akan Umma Bilki. Ita Ummi duk halayenta a fili su ke sai dai kai ka sha maganin zama da ita, amma Umma Bilki hawainiya ce, yau kalarta fari gobe ja jibi kuma shuɗi. Munafuka ce mai lasisi. Tsabar iya munafurcinta har haɗa Alhaji take da Hajiya Kaka faɗa. Tsaf za ta shirya tuggu mai wuyar warwarewa. Kafin ka kamo bakin zaren ta riga ta cire hannunta a ciki. In dai za a yi faɗa biyu uku tsakanin Mama da Ummi to idan ka bi silsilan maganan za ka ga Umma Bilki ce ta haɗa su. Shiyasa sam bana shiga safgarta. Tun sau ɗaya da ta haɗa min wani sharri a wajen Alhaji na ja baya da ita. Gashi idan ka zo gidan ta maka wani tarba mai kyau sai ka ɗauka tafi kowa kirki amma...a bar kaza a gashinta.

Anty Amarya dai babu ruwanta da kowa. Bata shiga sabgar da ba nata ba. Duk da bata taɓa haihuwa ba bata irin nuna son yaran nan kamar yadda masu son haihuwa ke yi. Idan yaro ya shiga sashinta ya mata shirme zane yaro take sosai. Tana da tsabta har dana Allah ya isa. Idan ka shiga falonta ka ɗan jima. Kana fita za ta fara mopping. Duk wacce za ta kawo saurayinta na musamman to sashen Anty Amarya za ta sauke shi dan kuwa ba za ka ji kunya ba.

Ina ta muku gulman matan Alhaji ko. Idan ban muku gulman ba ba zaku gane abubuwan da zasu biyo baya ba. Ni da yake 'yar gaban goshin Hajiya Kaka ce duk wani abinda yake gudana a gidan ina sani. Dan idan aka je aka dawo duk a ɗakinta ake jibgewa.
Hajiya Kaka tana son Anty Amarya amma kullum korafinta wai bata girmamata yadda ya kamata. Wai itama halinsu ɗaya da Gimbiya Maryam wato jiji da kai.
Amma sauran matan 'yan ayi daɗi ayi faɗa ne.

***

Yau ina kwance a cikin ɗaki ina karanta wani littafin hausa mai suna 'Maraici' na ji muryan Alhaji yana sallama. Kaka ta shiga wanka dan haka ni kaɗai ne a ɗakin.
Na yi saurin jefar da littafin na jawo bargo na rufe fiskata amma ban gama rufuwa ba na jiyo muryansa a cikin ɗakin yana faɗin "Sahla taso nan"

Na san dubuna ne ya cika dan yadda yai maganar babu wasa a tattare da shi.
Na yaye bargon na sauko daga kan gado na biyo bayanshi. Ina ganin mun nufi zaure na kama salati a cikin raina, kar dai, kar dai.

Ina ganin Malam Buba Maitsire na fara rarraba ido.

Alhaji yace " Malam Buba ga ta nan ta biyaka kuɗin tsirenka"

"Alhaji Allah na tuba ba zan sake ba. Wallahi na tuba"

"Miye na tuba a nan Sahla. Ba kin ce karshen wata ya zo gida ya karɓi kuɗinsa ba"

"Ba haka na faɗa masa ba fa. Cewa na yi ya dinga lissafin kuɗin tsirensa idan ya taru dayawa sai ya samu Alhajinmu. Ko ba haka muka yi ba?"

Malam Buba yace haka ne.

"To dana ce ka samu Alhajinmu cewa na yi ka tambayeshi kuɗi ne?"

"Ikon Allah!. Yallaɓai..."

"Dakata Malam Buba, ka ga ni masallaci zan wuce. Ga Sahla nan za ta ba ka kuɗin ka"

"Dan Allah ka yafe mun. Wallahi ba zan sake ba. Tsiren ɗari huɗu da hamsin kawai na ci"

"Ɗari biyar da hamsin dai"

"To ba ranan gyara ka saka min ba"

Alhaji ya tsaya kallonmu muna ta lissafin kwanakin da na yi ina karɓan tsire. Dama rumfarsa a kan layinmu na zuwa Islamiyya yake shine idan na ɗan ji kwaɗayi sai na tsaya na ce ya yanka min tsiren hamsin a-haka-a-haka har ya taru yai yawa.

Da wata ce ba ni ba a gidan nan da kashinta ya bushe a wajen Alhaji. Amma Allah ya so ni, Alhaji baya dukana.

Inaga ma gajiya yai da lissafin da mu ke yi da Malam Buba Maitsire kawai dai na ga ya ciro kuɗi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On SAHLA A PARIS
avatar
mahamane-noura

6 months ago

Reply

Ya sanyi don ?aukar novel dan Allah

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to mahamane-noura

Domin downloading novel na mu dole fa sai kayi subs da mu

Please Login or Register in order to submit comment