Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»Ώ[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»

*Amincin Allah ya tabbata ga wad'anda zasu karanta wannan labari nawa dama Wad'anda basu samu damar karantawaba ina maku fatan Alkhairi akodayaushe*

~Note~
*Wannan labari 'kir'kirarane banyi dan wani ko wataba, ko satar fasahar wani saboda haka duk Wanda/wacce taga yazo dai-dai danata abune yazo d'aya sai ha'kuri*

*GARGA'DI*
```Ban yarda wani ko wata yayi amfani da wannan labari nawaba ta wata siga saida izinina idan kuma akayi bada iziniba, ban yafeba saboda haka akiyaye```


"Hassana waike bazakiyi sauri mutafiba ke kullum idan mutum yahad'a abu dake sai ranshi ya 6aci, yanzu dan Allah so kike daddy yadawo yahanamu fita, kuma sanin kankine muddin idan banje *Dinner* d'innan ba zuby bazataji dad'iba kinsanfa bikinnan na best friend d'inta ne, kuma ta gayyacemu ba dad'i mu'ki attending.

Cikin sanyin murya wacce aka kira Hassana take magana "Haba Hussaina nifa wlh banison wannan abun dakikeyi, ke shikenan koda yaushe da an gayyaceki ferty kin dinga 'kyarma kenan kamar wacce aka gayyata zuwa aikin hajji.

Magan-ganun Hassana suka 'kara harzu'ka Hussaina cikin bala'i da d'aga murya take cewa "dallah malama kada ki gayamin magana, ke dama duk wata harka ta wayewa baki santaba, idan bazakiba basai kin gayamin maganaba kawai ki zauna a gida, haka zaki 'kare, kullum kitchen.

Zama Hassana tayi bakin gado tare da cire mayafin data sanya, "nikam bazaniba kitafi kawai sai kindawo, ni dama wlh hankalina be kwanta da tafiya wannan *dinner* d'inba kiduba agogo yanzufa 'karfe bakwai da rabi na dare.

Jin Hassana tace bazataba yasa Hussaina zuwa kusa da ita ta du'ko dai-dai fuskarta har numfashinsu na gauraya dana juna, sannan tafara magana cikin sanyin murya.

"Haba my sweet sister, plz ayimin ha'kuri kinsan bazan iya tafiya batare dakeba......

Ringing d'in wayarta ya katseta da maganar datake, da sauri tasa hannu ta d'auko sunan Zuby tagani yana yawo kan screen d'in wayar da sauri ta danna OK tare da karawa a kunne.

"Hellow Zuby ya?
A d'aya 6angaren zuby ta amsa
"Haba 'kawata me kike har yanzu baki fitoba, halan wannan sister taki ce take maki kofsi.
Hussaina kallon Hassana tayi sannan tace "a'a yanzu zamu taho, tare da itama zamuzo.
"Dan Allah kuyi Sauri.
"Owk kawai Hussaina tafad'a tare da tsinke kiran.

A Falo suka tarad da momynsu tana kallon tashar sunnah TV, cikin ladabi sukaje gabanta Hassana tace "Momy zamu tafi.
Momy ta kalle yaran nata daga sama har 'kasa babu wata shiga ta aibu tattare dasu, atamface suka sanya d'inkin Riga da zani pieces, sai wadataccen gyalen da suka yafa.

"To amma kada Ku wuce 'karfe tara kunsan dai tara da rabi dadynku yake dawowa gida, Momy tafad'a tana 'karemasu kallo,
Hussaina ce tayi saurin cewa "kada kidamu Momy Tara a gida zatayi mamu.
Hassana tace "insha Allah Momy munyi maki wannan al'kawarin.
"To shikenan kuje Allah maku Albarka
Tare suka amsa da Ameen sannan suka fice daga gidan.




Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ»shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------2

Suna fita get sukayi 'yar tafiya kad'an sukasamu napep suka fad'a masa inda ze kaisu.


Lokacin dasuka 'karaso had'addiyar Hotel d'in da'ake gudanar da *dinner* d'in kai tsaye suka nufi hall d'inda suka tabbatar da nanne ake farty saboda mutanen dasuka hango ciki.

Suna shiga lokacin Zuby na zaune suna labari itada wani boy friend d'inta wanda tadad'e da afkawa kogin 'kaunarsa tasha nuna masa haka amma ya'ki yagane dan kwata- kwata Zuby bata cikin tsarin kalar yan matan dayakeso kawai dai yabarta a matsayin Friend.

Cike da farinciki Zuby ta tarbo 'kawarta Hussaina, ko kallan Hassana batayiba, Hassana ma nunawa tayi batasan da zaman wata halitta wai ita zuby ba, dan ita dama tun can jininta be had'u dana zuby ba.

Guri suka samu suka zazzauna kan kujerun dake Jere a hall d'in.
Zuby ta kalli boy friend d'inta sannan takira sunansa "Hafiz, ga 'kawayena danake gayama 'yan biyu ne, wannan itace Hussaina wannan kuma itace Hassana tafad'a tana nuna Hassana yayinda itakuma ta kauda kanta gefe dan ko kad'an ita batason a had'ata da wani namiji barantana kuma har suyi wata magana, shiyasa kodayaushe Hussaina da Zubby suke kiranta bata wayeba.

Haka suka zauna zuby sai wani shishshigema Hafiz takeyi tanata mashi surutu, shikuma kwata- kwata hankalinsa be kanta, tunda su Hassana suka shigo idanunsa suke kan Hussaina, yariga yagama fad'awa kogin 'kaunarta, wanda zuby bata lura da hakanba, amma ita Hussainar ta dad'e da d'agowa dashi kodan yanda dasun had'a ido yake sakar mata wani tsadadden murmushi, dama gashi kyakkyawa ajin farko, take itama Hussaina taji takamu da sonshi.

Wani irin kid'ane ya tashi lokacin da Mr DJ ya kunna Speaker's d'insa, wayyo jikin zuby har 6ari yake, dama haka take mayyar rawace duk sun dad'e da sanin haka saboda haka basuyi mamakin hangonta tsakiyar fage ita kad'ai tana caskad'ewaba, ba kunya take rawar sai wani kaso shoki takeyi..... _Lol_

Lokacin Hafiz yasamu damar yima Hussina magana, "Ya kike 'yan mata, wayyo wani iri Hussina taji a jikinta lokacin da ta tsinkayi muryar Hafiz a kunnenta, a zuciyarta tace "Wow fantastic, nice voice, Ashe dai yanda yahad'u hakama murayarsa ta had'u gaskiya gayen yagama had'ewa.

Lokacin Hafiz yasake magana karo na biyu batare da Hussaina tabashi amsar ta farkoba, "idan bazaki damuba kisakamin numberki ko bayan kin koma gida sai muyi magana,
Ba musu ta amsa tasakamai numberta, sannan ta mikamar wayar dayake Hafiz gogaggen d'an duniyane gurin amsar wayar saida yahad'o da hannunta, suduka wani irin shock sukaji lokacin da tattausan hannuwansu suka had'u dana juna, kasa sakin hannunta Hafiz yayi sunkai kimanin minti biyu a haka sai itace tayi 'karfin halin zare hannunta daga nashi, kashe mata ido yayi tare da sakar mata wani 'kawataccen murmushi.

Duk abinda sukeyi Hassna batasaniba duk da guri d'aya suke zaune, hankalinta nakan wayartane tana chat a wani group na Zee Mmn khady me suna *Ciwon Ya mace* tanajin dad'in group d'in sosai yanda ake bada shawara me kyau da kuma yanayin abubuwan amfani da ake turowa, ba kamar kuma Had'in kai da 'yan group d'in suke dashi, duk da yanda takejin dad'in chat da *Mmn Ummi da Ameeno, Mmn Ramadan da rukky abdull* hakan behanta duba lokaciba dan kada suyi dare basu koma gidaba, dan yanzuma data duba 'karfe takwas da rabi, tasama ranta takwas da minti arba'in zasu koma gida.

Muryar Hussaina ta tsinkaya "Hassna dan Allah aromin wayarki zanyi kira, bansan credit d'ina yakareba, ba musu Hassana ta mi'kamata "amma gaskiya dakin gama wayar zamu tafi saboda tara takusa kuma kinsan Al'kawarin da muka d'aukoma momy,
"To kawai Hussaina tace, tawuce tanufi gunrinda akayi parking d'in motoci kamar tana wayar gaske.
Dai-dai motar da Hafiz yafad'amata nan ta tsaya, jingina tayi da motar idanunta akan wayarta.

Tashi Hafiz yayi yabi bayanta, Hassana na kallo amma bata kawo kome a rantaba, iatadai fatanta kawai idan Hussaina tagama wayar datadawo sutafi gida.




Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------3


Bud'e motar Hafiz yayi gidan baya suka shiga, kasancewar motar tanada ba'kin glass bazeba wanda ke waje damar ganin nacikiba dukda dama gurin akwai duhun dare,

Ac Hafiz ya kunna musu, take motar tad'au sanyi tare da wani daddad'an 'kamshi
Zaune suke gaf da juna har jikinsu na had'uwa dana junansu, Hafiz ne yafara magana cikin kwarewa da gogewa na yan duniya "Babyna ammafa kin had'u kinganki kuwa kamar matan hurul'ayni, wani 'kawataccen murmushi Hussaina tayi tare dasa hannunta tarufe fuskarta, duba Hafiz yakai kan shantala-shantalan yatsun hannunta wanda yake d'auke da awarwaraye da wani had'adden zobe na azurfa, hannu yasa Yakama hannun nata yamatse a hannunsa, sannan yafara wasa da zoben "kai amma ring d'innan yayimin kyau babyna, amma set ne tare da sarkarki koh?
Yafad'a tare dakai hannunsa kan wuyanta yana wasa da sarkarta, lokacin yagama kashema Hussaina jiki yanda yake shafar wuyanta, ko magana bata iyawa sai maida numfashi datake d'aya d'aya, hakan yabashi damar yin 'kasa da hannunsa zuwa cikin rigarta yafara wasa da breast d'inta, wani irin yarrrr taji ajikinta, saboda ba'kon Al'amarin daya risketa yau, domin Hafiz shine mutum na farko daya fara yimata irin wannan wasan, suna soyayya da Jabeer amma koda wasa beta6a kai hannunsa kan jikintaba, "hakan yana nufin jabeer be iya soyayyabane ko miye....

Tana cikin wannan tunanin taji Hafiz ya rungomota yahad'ata da jikishi, yana rad'amata kalmar "I love you a kunnenta, cikin kasalalliyar murya tace "mee too my Dear,
"Wow nice my Baby, Hafiz yafad'a tare da had'e bakinsa da nata yacigaba da kissing d'inta.

Dare yafara Hankalin Hassana ya masifar tashi dan tanemi Hussaina ko'ina a cikin hall d'in da wajen hall d'in amma bata gantaba, duk tabi tarud'e, gashi Zuby tunda tashiga fagen rawa batako wai-waiyesuba barantana ta tambayeta kotasan inda Hussainar take gashi tatafimata da waya barantana takirata.
Komawa tayi kan kujera ta zauna tayi tagumi hannu bibbiyu,

Can Hankalin Zuby yayo kan inda tabarsu Hussaina amma batagansuba sai Hassana wacce tahad'a hannuwa biyu ta tallabe kumatunta kwalla suncika idanunta, da sauri zuby takaraso inda take "Ke ina 'yar'uwarki? Hassana batajitaba dan tayi nisa cikin tunanin irin hukuncin da daddy ze yanke masu idan yadawo ya tarar da basunan, batakaran suba ranar momynsuma bazata fitaba dan dady mutumne me zafi tsaye yake kan tarbiyar iyalanshi.

Ta6ota zuby tayi "tambayarki nake ina Hussaina?
Sai lokacin tadawo daga tunanin datake "nima wlh ita nake nema dan Allah ki kiramin ita da wayarki danni tatafi da tawa wayar.
"To ina Hafiz? Zuby ta'kara jeho mata wannan tamabayar
"Kinga ni dukansu bansan inda sukeba, nidai dan Allah ki taimaka ki kiramin Hussaina mutafi gida.

Take zuciyar Zuby tabata akwai wata kulalliya tsakanin Hafiz da Hussaina, idan kau hakane lallai Hussaina tad'auko ruwan dafa kanta.

Wayarta ta fiddo daga cikin poss tafara lalubar number Hussaina, kusan kira takwas zuby tayima Hussaina no answer, hakan ba 'karamin 'kular da ita yayiba, batako kalli Hassanaba tabar gurin tana cika tana batsewa.

Ganin dare na'karyi yasa Hassana tambayar wata budurwa kusa da ita "dan Allah 'karfe nawa?
Duba wayar tayi "karfe tara da Monti takwas tabata amsa a ta'kaice.


Cike da rud'ewa Hassana tatashi tafita harabar hotel d'in Allah ya taimaketa lokacin wani me napep ya sauke wasu, tagayamshi inda ze kaita, saida suka d'au hanya tafara tunanin inda 'yar'uwar tata tashiga "Toni yanzu mezanfad'ama Momy idan aka tambayeni Hussaina, wasu hawaye suka gangaro kan kumatunta.
"Allah sa dai tana lafiya duk inda take.
Tana cikin wannan tunanin har suka iso 'kofar gidansu batamasan sunzoba saida me napep yace "hajiya mun isofa sannan ta sallameshi tafita daga napep d'in.

Jiki a sanyaye tanufi gidansu, ahankali ta kwankwasa megadi yabud'emata bayan yatambayeta tagayamashi itace.

Ahankali tashiga gidan da sallama Momy tagani zaune tayi tagumi koba tambaya tasan jiran dawowarsu takeyi, ganin Hassana yasa Momy sauke wata ajiyar zuciya, "Alhmdlh ina 'yar'uwar taki take?

Hawaye yacigaba da zuba daga idon Hassana batare databa Momy amsar tambayar datayimataba, cikin tashin hankali Momy ta'karaso inda Hassana take takama kafad'unta "ina take nace? Ko wani abu ya sameta? Kifad'amin......

Ganin hankalin Momy yatashi yasa Hassana goge hawayenta "bawani abu yasametaba kawai na nemeta bangantaba, kuma gashi dare yayi...

"Subhannallah Momy tafad'a Allah sa dai lafiya, kin kira wayarta? "Nima wayata tana hannunta.

Hankali tashe Momy tasa wayarta takira Hussaina itama no answer aka gayamata kamar yanda duk wanda yakira ake gayamai, saida tayi kira kusan na goma sannan Hussaina ta d'auka cikin kasalalliyar murya tafara magana dan lokacin tana jikin Hafiz yagama rabata da rigarta yana 'ko'karin ciremata breziya,

Cikin fad'a Momy tace "dan Ubanki kiyi maza ki dawo gidan tun kafin dadynku yadawo, batajira me Hussaina zatafad'aba Momy takashe wayar

Lokacin sukajiyo horn d'in motar Alamar dawowar me gidan, cikin tsananin tashin hankali Hassana tafara magana "Momy dadyne yadawo nashiga ukku tafad'a tana yarfe hannu.

Da sauri Momy tace "maza ki shige d'akinku kada yazo yaga batanan, Dan batakaran itadayi laifinba mu kanmu sai rayukanmu sun 6aci.

Da sauri Hassana tashige d'aki, zama tayi bakin gado tayi tagumi hannu bibbiyu tana tunanin 'yar'uwarta.





Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------5


Jitayi an sha'kota ta baya a firgice ta juyo, ido biyu sukayi da daddy beyi wata-wataba yafara zabga mata cable wayar dake hannunsa nan tafasa 'kara tana ihu, amma daddy be sauraramataba, tsulamata wayar yakeyi iya 'karfinshi, mommy da Hassana suna daga falo sukajiyo ihunta, wani sabon kuka ya kwacema Hassana cewa take "Momy dan Allah ki taimaki Hussaina kiba daddy ha'kuri kada yajimata ciwo, kallonta Momy tayi cikin nuna rashin halin damuwa tace "koma miye ita tajama kanta 'kara yadaketa gobe bazata 'karaba.

Da gudu tashigo falon kamar wacce aka jeho, bayan Momy tanufa tana kuka ta 'kan'kameta "wayyo Momy dan Allah ki taimakeni wlh bazan 'karaba,
6an6areta Momy tayi daga jikinta tare da barin gurin tana cewa "lokacin dakikayi rashin jin naki kinyi shawara dani, dan haka kada ki nemi taimakona can ki 'karata jiki magayi, shigewarta tayi d'aki ta maida 'kofarta tarufe, wani irin kuka Hassana tafashe dashi ganin momy batada niyyar baiwa dady ha'kuri shikuma beda niyyar hakura, rugowa tayi tari'ke hannun daddy tanamashi magiya "dan Allah daddy kayimata ha'kuri bazata 'karaba, a harzu'ke daddy ya hankad'ar da Hassana gefe guda yacigaba da suburbud'ar Hussaina, suduka suke kuka suna bashi ha'kuri amma beko sauraresuba saida ya tabbatar Hussaina ta daku sannan ya rabu da ita yanufi d'akinshi yana huci yana cewa "gobema ki kara tafiya ki wuce magrib baki dawo gidaba wannan kad'an nayima shashasha kawai.

Kama hannunta Hassana tayi suka nufi d'akinsu, da kyar Husaina take tafiya saboda ba 'karamin duka tasha hannun daddynsu ba,

Zaunar da ita Hassana tayi bakin gado tana sharar kwallah, tace "kinga abinda nake gujemaki koh, ba irin neman dabanyimaki gurin *dinner* d'innan ba amma ban gankiba, wai ina kikajene?

Cikin dasashshiyar murya Hussaina tace "uhm yanzu banida lokacin dazanbaki wannan amsar,
Toilet Hassana tanufa batare data 'karama Hussaina wata maganaba ruwan d'umi tahad'amata tarakata har toilet sannan tajawo mata 'kofar, haka tayi wanka ta gargasa jikinta bayan tafito Hassana tasa Robb ta shafemata jikinta sannan sukabi lafiyar gado, kowace tayi shiru kamar me bacci a zahiri amma kowace da tunanin datake cikin zuciyarta, Hussaina tunanin Hafiz ne fall cukushe a zuciyarta, "lallai Hafiz ya iya soyayya, yanzu nagane jabeer ba kome ya iyaba a fanni soyayya sai dai kullum idan yazo yakamayimani nasiha da sauransu, nikam nafison namiji d'an life Wanda yasan takan love, gaskiya akwai sakal kan maganaraurean da jabeer dan ni yanzu babu namijin danake muradi a rayuwa kamar Hafiz, dan Abinda ya faru tsakaninmu yau yasa naji bana bukatar kowane namiji sai shi.

Hassana kuwa tunani take shin ina 'yar'uwarta tashiga har takai wannan daren bata dawo gidaba, Allah sa dai Hussaina bata biyema samarin shahoba, mayaudara "Hmm tafad'a shiyasa niko Alama bana harkar samari.
Da haka ta gyara kwanciyarta bacci yayi awon gaba da ita.

6angaren dady kuwa bacci gagaran idanunsa yayi tashi yayi ya zauna gefen gado ya zabga uban tagumi, zuwa can kuma yami'ke tsaye yafara safa da marwa cikin d'aki, "lallai dole inyi saurin yima tufkar hanci, saina tashi tsaye kan tarbiyar yaranan, saboda zamaninnan yanzu saika haifi d'a baka haifi halinsaba. Kusan raba dare daddy yayi yana tunani.

** ** ** **

Washe gari zaune suke kan dining suna breakfast bakajin motsin kome sai 'karar plate da cokulla, kowane ka kallah cikinsu rai a dagule dakuma tunanin abinda yafaru jiya.

Bayan sun kammala daddy yayi gyaran murya "kunajina? Suduka suka jiyo suka kalleshi, "tunda abin naku yazama lalata inaso insanar daku na soke maganar makarntar dazakuje *AMUSLIM COMMUNITY SCIENCE &TECHNOLOGY FUTUA* daga yau kucireta a ranku kuduka aure zanyimaku, ke Hassana inaso kifito da miji nanda wata d'aya, ke Kuma Hussaina ya watsamata wani matsiyacin kallo "kigayama jabeer inason ganinshi, wani irin Fad'uwar gaba Hussaina taji dajin dady yace yana neman jabeer, sadda kai tayi 'kasa "daddy nifa mundad'e da 6atawa da jabeer.

Shiru daddy yayi yana kallonta, toki fiddo miji nanda wata d'aya, idan kika wuce iya adadin kwanakin dana ebar miki zand'au duk matakin danaga ya dace.

Mi'kewa yayi tare da d'aukar jakarsa ta zuwa office sannan ya kalli Momy "maganar fita kuma daga yau nakasheta idan sunbar gidannan a tabbatar islamiyya zasu, yana gama fad'a yasa kai yafice.






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» Shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------4


Hassana na daga d'akinsu taji shigowar daddy wani mummunan fad'uwar gaba taji, tanajin lokacin da Momy kemasa sannu da zuwa, yana zama ba abinda yafara tambaya sai "Ina yarannan suke? Cikin inda-inda Momy tabashi amsa "uhm am suna d'akinsu ko Alh....

Kwalamasu kira yashigayi "Hassana....Hussaina....
Hassana naji tayi saurin Amsawa "na'am...
"Kuzo nan ina nemanku "to ta amsa jiki na kyarma tasako d'an karamin hijab d'inta ta fito, durkusawa tayi gaban daddy "gani daddy tafad'a tare da sunkuyar da kanta 'kasa gabanta sai dukan tara-tara yake.

"Ina 'yar'uwar taki? Daddy ya tambaya, "im ahm....uhmmm tafara inda-inda tarasa wace amsa zata bayar domin kare 'yar'uwarta shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta.

Tsawa daddy ya kwatsa mata "ke.... Ba magana nike dakeba ina 'yar'uwarki nace? Jiki na 'kyarma tafara magana tana d'an ja da baya dan taga yanda daddyn nasu ya zuciya a lokacin ze iya mazgeta, "daddy munje walimar bikin wata 'kawarmune shine dazan taho nayita nemanta bangantaba shine nikuma nataho,
"Owk good hakan yayi kyau, shine ita ta zauna dan bata tsoron fushina, aiko ranta inyayi dubu a gidannan yau sai ya 6aci, kallon Momy yayi "kekuma kinsan bata dawoba amma ko ajikinki saboda baki damu da tarbiyar yarankiba ko "haba Alhj ya zakace bandamu da tarbiyarsuba, wlh tun d'azu nake faman kiran wayarta sai tacemun gatanan to ya kakeso inyi? Ko zuwa zanyi intaho da ita,
"A'a ba tahowa zakiyi da itaba, idan bakije kika taho da itaba nizan taho da ita dakaina, yafad'a yana nuni da 'kirjinshi da hannu.

Bejira abinda zatafad'aba ya zari cable d'in jikin tv yafita zuwa harabar gidan,
Me gadi na hangoshi tafe yataso da sauri "Sannu da fitowa Alhj, "yauwa mal bala, abinda kawai ya furta kenan sannan yafita daga wajen get d'in gidan ya tsaya ya maida hannuwanshi duka baya, yafara safa da marwa yana jiran yaga ta ina Hussaina zata 6ullo, tsawon kimanin minti goma sha biyar yana zarya gurin Amma bako Alamarta,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment