Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

727 9133: INSO CUTA NE....21

littafin na kudine ga masu bktr Cigabn littafin su nemi 090382757515.

normal grp2 ngd da adduarh.

Gabaki daya anty jannarht tafara tunanin koude HAMMAD din yafara shaye shayene..ji tayi jikinta yadauki wani irin chock.. tattaro dukkannin kuzarinta tayi hadi da tureshi daga jikinta ranta a matukar bace ..

Idanuwanshi sun kada sunyi jawur besan haka yakeba ..bemasan meya aikataba.. red eyes dinshi yazuba mata..

Se ynzu take nadamar sakewar datayi dashi din ashe hkn raini ze jawo mana..daman ummih tajima tana gaya mata illar hkn.

Kara kamo hannunta yyi rnta a matukar bace ta fisge hannunta yakara kai hannu yakamo hannayenta duka biyu ya matsesu cikinnashi Idanuwanshi na zubar da kwallah yace "pls anty kice wani abu..wlhy inasonki..ba laifina bane nima allahne, ya jarabceni."

jin abun takeyi kmr a mafarki yake faruwa .oh wai itace yau HAMMAD keta tattabawa kmr wanda ya biya sadaki.. "pls anty kice wani abu mna.. wallahi da gaske nakeyi inasonki.." mgnr ykeyi kmr wani zautacce.. fisge hannayenta tayi cikeda bacin rai ta wanka mishi wani irin mahaukacin mari ita knta tji zafin marin a hannunta...

A bangaren gogan kam kou gezau beji zafin marin datayi, mishiba wlhy ji yakeyi kmr yazama mahaukaci me bin bola inhar zesamu sassauci a game da sonta zeso yazama cikakken mahaukaci..

Cikeda kulewa tace "wato sakewar danakeyi dakai ita takawo rainin da har kakeda karfin halin rungumeni after that kabude bakinka kacewai kna sona..inkana shaye shayenka sekazo ka saukemin haukanka a kaina..bnason iskanci niba yar iska bace knajina kou! ..kuma wlhy jikina daka taba a matsayinka na ba muharraminaba allah ya isa tsakanina dakai...ashe ba ciwon kakeyiba da mummunan nufi a zuciyrka..ka gaggauta fitar mna a gida .."
tajuya da niyar barin falon..

Tinda tafara mgnr yke kallonta shi sam duk maganganunnata basuyi mishi zabiba hasalima sam bekai ko kwatn zafin dayake jiba a zuciyarshi.. binta yy ya kamo hannunta batare data juyoba ta fisge hnnunta rnta a matukar bace ta haye upstairs din bata tabbatr dacewar HAMMAD dan iska bane seyau..

Nan kasan ya tsugunna hannunshi dafe da kirjinshi yayinda wasu zafafan hawaye ke zirya a kn kuncinshi sam bemasan suna zubowaba.. waishin daman haka son yake.. wani irin ciwone me mugun radadi yake taso mishi a kirjinshi kuka ykeyi tmkr karamin yaro.. kusan 30mint yayi a wannnan halin..a daddafe ya mike hannunshi dafe da kirjinshi yana tafe yana tangal tangal hadi da dafe bango yabar falon. Fitowa yy harabar gidan still hannunshi dafe da bngo damn anwar yana tsaye bakin motar ganinshi yasa yy saurin karasowa ya kamoshi suka karasa yasashi a motar still tears na zirya a kunshinshi. Jan motar anwar yy sukabar gidan..sundanyi tafiyar 10mnt yayi parking Idanuwanshi na kn HAMMAD din daketa faman hawaye. Cikeda tausayawa yake kallonshi sauke ajiyar zuciya yayi yace "Blood don girman allah ka tsagaida da kukannan naka pls.. ka gaya matan kna sonta.."

Daga mishi kai yayi..

"Okay me tace.."

Hawayen kawai HAMMAD yacigaba dayi yace "muje gida pls.. kirjina.."

Lamarinna dagulawa anwar hnkli jan motar yayi sukabar gun rabi hnklinshi na kn hammad rabi na kn tuki.. HAMMAD kam ji yy dama yasani dabe gaya mataba domin seya karajin damuwarshi ta ninku tafi da zuciyarshi tukuki ji ykeyi kmr zata fallo ta fito fili...

Tana hayewo saman a corridor sukayi kicibis da ummih .. bata ankaraba taji ummih ta daga hannu ta sharara mata lafiyayyun maruka guda biyu..dafe kuncinta, tyi ta mugunji shigar marin nan ta durkushe hanunta dafe da kunshinta tana hawaye tunanima takeyi me tayi.. domin ita batayi tunanin ummih ta gnsuba.. "ashe baki da hnkli bnsaniba seyau..kinga abin nke gya miki tin tini ya tabbata ko..nce miki ki dena sakarwa dan gidan zainab dinnan fuska amma kika ki..ashe dama tin tini yna tattabaki seyau asirinki ya tonu wato abun a office be ishekuba sekunzo har cikin gida kou.." cikeda bakin ciki ummih take mgnr.

Se ynzu ta fahimci me ummih ke nufi wato taga sadda HAMMAD ya rungumeta..cikin kuka tace "ummih wlhy be taba tabaniba se yau dakika gani.."

A kufle ummih tace "zaki rufamin baki kouse na hada miki wasu marukan..kina ganin kmr bnsan halin da kike cikiba ko keda yaron tou nasani bazaki wayance minba kallonki kawai nakeyi .. .. nafi tunanin abinda yasa innasa miki doka bakya bi kike fatali da lamarina saboda bani na tsugunnaba nakawoki duniya..amma bakomi komi kikayimin ba laifinki bne lefinane tinda harna fifitaki a kn yadda na tsugunna, nahaifa .." ta karashe mgnr cikeda takaici..

Tinda take bata tabajin maganganuba masu zafi daga bakin ummintaba se yau ..bakincin yatarun mata yazamar mata biyu.. cikin kuka tace "ummih dan allah kiyi hkr pls karkice haka ummihna.."

Juyawa ummih tayi da niyar barin gun.. cikin kuka tace "ummih pls tsaya kiji..ki fahimceni dan allah ummih ..."

Tsayawa, tayi batare data juyoba tace "ta yaya zan fahimceki byn na kamaki red hand dumu dumu..har yana furta miki kalmar so.."cikeda dacin zuciya takarashe mgnr. Kuka jannarht keyi riris .. ummih tacigaba dacewa "kuma duk lefinkine..tinda yau yayi kissn dinki kinga next time se hawanki zeyi..years kece kikabashi offer din hkn. "

Mgnrnan na ummih na karshe yafi komi batawa Jannarht rai..tsananta kuknta tayi..

"Kinga tin kafin hknya ksnce is bttr ace bana tare dake.." tana kaiwanan tacigaba da tafiya rnta a matukar bace datasan hknne ze kasance da duk magiyar dazatayi mata bazata barta ta tafitaba.. direct tanufa hnyar upstairs din saukowa tayi dakinta dake kasan ta nufa.. kwantawa tyi a kn bed dinta zuciyrta na tukuki "waishin ni rukayyah wace irin kaddarace ke bibiyata ina tunanin na yadda kwallon mangwaro nahuta da kuda ashe ba hk bne..." Nan da nan zuciyarta ta tsinke tabbas jikinta nabata wani abu bad na bibiyarya ... hajiya zainab gumel tana daya daga cikin mutanen data tsana a rayuwarta kwata kwata matar batada zuciyar musulunci amma abin bakin ciki wai yau danta shine ke furtawa Jannarht dinta kalmar so ...kai ji tyi duk tabi ta kara tsanar yaron da duk family din gumel din..

Sahura dake labe tanajin meke faruwa tanajin ummih tasauka kasa ta karaso ta kamo anty jannarht din dataketa kuka kmr rnta ze fita.. kamota tayi tace"kiyi hkri anty jannarht..komi yy zafi mgninshi allah.." tana kukan takamota takaita dakinta ta zaunarda ita a gefen gadon itama ta koma tazauna a kasa . Dukda bataji komi ke faruwaba amma ta tsinci wani abu a ciki.. kumata fahimta.

Hada kai tayi da guiwa tana cigaba da rero kukan kmr rnta ze fita..

"pls anty jannarht kiyi hkri kukanya isa hk.." cewar sahura..

Cikin kuka muryarta na sarkewa tace "pls.. kije.. kibawa.. ummih hkri..wlhy bazan..jure bacin rntaba.." takara fashewa da kuka tinda take bata taba tsintar kanta atsanar hammad ba se yau..

Tagumi sahura tayi itakam abun beyi mata dadihba gaskia domin a yadda tji ummih bata taba shiga bacin raiba kmr na yau.. sahurade hkri tashiga bata hadi da ban baki.

Kouda suka isa gidan seda anwar yakamashi yakaishi dakinshi bakowa a falon kowa na bngarenshi.

Kwantr dashi anwar yayi yakoma gefe yy tagumi hadi da zuba mishi ido .. hawayen ykeyi babu kakkautawa ya dafe hannunshi da kirjinshi idanuwanshi na fidda kwallah me mugun zafi.

"Pls HAMMAD kayi hkri..don allah ka kawo sassauci a lamarin pls.."

Lumshe ido HAMMAD din yayi a fili yace "wayyo anty jannarht dina.." yy mgnr yna wani irin Murmushi .. anwar de na binshi, da ido.. turo kofar dakin akayi aka shigo.. dago kai anwar yiyi dan ganin me shigowa..

Bance allah ya isaba😎
[10/30, 3:47 PM] +234 803 727 9133: INSO CUTA NE...23

littafin na kudine ga masu bktr Cigaban littafin su nemi 09038275715.08033368013.

Time din posting 5:pm and 11:am


Kyar ya tsayar da idanuwnshi a knta ynajin wani iri game da itan inza aje ya kiyasta yanda yakeji din sam baze iyaba..

Ganin ya tsaya kallonta nema yasa yace "Inbazaka fitaba ni zan fita inbar maka office din.." tyi mgnr rnta a matukar bace.

Cikin sanyin murya yace "naji zan fita..amma dan Allah ina rokonki abu daya a matsayinki na musulma kinga soyayyarkide allahne ya dauramin ina rokonki ki tayani rokon Allah ya ragemin sonki.." cikeda tausayawa yake mgnr.yna gma mgnr yajuya yabar office dinnata jiki babu kwari, bynshi tabi da kallo harya fice daga office din komawa tayi tazauna dafe da goshinta. Ita inma ta rasa miji kawai setayi soyayyah bama aureba da kanin bayanta ai sam bazama ta iya wannan abun kunyarba , gaskia allah ma ya tsareta da shiga bakin duniya Wlhy ganin abun takeyi kmr a mafarki..

dai dai ya fitou sukayi kicibis da anty salaha kallonshi kawai tayi tagane wani abu na damunshi daman ita tini tasha ganinshi da anty jannarht tana bashi abinci a baki tin a lokacin tafara karanto wani abu a fuskar HAMMAD din.

Binshi tayi da ido tace "honey.."

Sunkuyar da kanshi yayi kasa yace "anty gud afternoon.."

"Fine..honey ya akayine.." smiling kawai yayi kamo hannunshi tayi suka nufa office dinta dashi tazaunar dashi itama tazauna tana facing dinshi tace "honey meke faruwane duk kabi ka rame.." shiru yayi babu amsa zuciyarshi na deep deep..

Jimm tayi tace "baka da lafiyane.." daga mata kai yayi .. tasan kouda ynada ciwon ba ciwon bane yafi damunshi a ynzu .." okay swry..anty jannarht ta dubaka.."

"Nop kisamin drib kou znji karfin jikina.." yy mgnr yana bending a kn kujerar. Cikeda tausayawa take kallonshi ..nan tayi mishi yan gwaje gwaje damande kou beceba dolene asa mishi drib. Drib din tasa mishi a office dinnata ba jimawa bacci ya kwasheshi. Takira anwar tasanardashi don tasan dolene ze nemeshi. Yna baccin anty nahnah tazo kawai tagnshi da drib tace "oh mmn ihsan ashe ciwon yayi tsanani har haka ni mommah ta gayamin amma tace yaki yarda a kaishi asibiti da yauma nakeso inje inga jikinnashi tindadeshi in an kirashima be dauka.." tyi mgnr tana zama a kn kujera.

"Aikuwade yau dinma danni na matsa mishi .."

"Au nasha shine yakawo knshi ai.."

"A'ah nazo zuwa office dinki naganshi yafito daga office din anty jannarht.."

Jinjina kai anty nahnah tayi dan ita sam batasan meke faruwaba. "Allah yakara lafia ai HAMMAD halinshi seshi ace kna ciwo amma kaki zuwa hospital inba shibama mommah ai bazata kula kowa ba.."

Murmushi anty Salaha tayi tace "ammen de..ai HAMMAD dan darune miskili kenan.." hk sukaci gaba da yan hirarrakinsu.
Kwananshi daya a asibitin aka sallameshi anwar ne ke jinyarshi duk family din waziri babu wanda bezo ya dubashiba har mama rabi da diyarta jawaheer yadan murmure anwar na bashi baki da bn haquri da bn baki. amma still tna rnshi be tabayin daidai da second ba batare daya tunataba. yadan sawa rnshi dangana amma kullum se yazo asibitin daidai lokacin tafiyarta ya tsaya ya zuba mata ido harta shiga car dinta tabar Asibitin inya gantan yana samun sassauci,a rnr yakan samu yadan ci abinci kou yayane. Anwar de kullum cikin lallashi yake.

Ganin yadan samu sassauci kwana biyu daman mama rabi takan dan zagayo dataga yasamu sauki tasamu mommah da mgnr.

Suna zaune a dakin mommah anty Safara'u na gefe nasreen na zaune kusa da ita a kn kushin. jawaheer na zaune kusa da mama rabi a kn bed mommah na zaune ita kuma a kn carpet a kasa ta gishin gida da katon trea a gabnta wanda yake cike da kyn marmari. Suma sauran dukkaninsu akwai trea din a gabansu.

Wani shu'umin Murmushi mama rabi tayi cikeda kissa tafara magana ." Zainab yarkifa ta matsamin.."

Tashi zaune mommah tayi tana smiling irinnasu na manya kuma jinin sarauta tace " Toufa jawaheer.."

"A wallahi.."

"Tou diyata taho ki gayamin menene ke damuwarki.."

Rufe fuska jawaheer tayi wai ita adole tanajin kunya.. mama rabi dake kallon yar tata tace "ai bazata iya gaya mikiba.."

"Tou mama rabi ki gayamin knsan banison dmwar diyarnan tawa.."

Anty Safara'u de suna sauraren koume suke cewa.

"Wai daman yar gida takeson ayi.." cewar mama rabi.

Cikeda rashin fahimta mommah tace "kmrya kenan kunsani a duhu.."

"Wai HAMMAD takeso nikuma nace wannan ai abune me sauki inde a gunkine.."

Anty Safara'u dake gefe ta rangada wata uwar guda..nasreen ce kadai bata waniji dadin hknba amma bata bayyanaba.

Mommah kam kmr dadih ze kasheta tace "ai wannan abun farin cikine..se ayi tuwona maina, haba ga abu a gida ai ba a kaiwa dawaba.. diyata wannanne kiketa kumbiya kumbiya."

Farin ciki fal ran mama rabi ganin yadda kowa yayi Naam da lamarin. "Aikuwa tin tini taketa fadimin nace A'ah.."

"Habade wani A'ah..mama rabi aiko suma nijer zasuji dadin labarin hadinnan. Kai abu yayi dadih yau kam zanyiwa daddy kyakyawan albishir...dmnni tin tini nkeso ayi hadinnan bnde furta bne."

Mama rabi ta kara rangada guda tace "kice yar taki ta kwantrda hnklinta.."

Mommah tace "kwaraima kuwa kmr tsumma a ruwa..aida ita da HAMMAD din duk dayane a gurina.."

Anty Safara'u ta kwashi wata uwar shewa tace "ai kuwa mude sede muce Allah yasa alkhairi wannan abun dadih hk..gaskia Mommah asa rnr bikinnan a kusa mu debo makida da mawaka..wannan dadih hk.."

Murmushi mommah tayi tace "aikuwade bri Safara'u nji ddh wlhy.. daman dukya sukurkuce ai kwara ayi mishi auren ko ze natsu.."

Mama rabi de baki har kunne itakuwa uwar gayya tinda aka fara zancen ta rufe ido wai ita adole kunya ammafa farin ciki fal rnta. Itakam Nasreen tanajinsu batace uffanba bataji dadihn hknba har rnta. Babu wanda besan cewa yarinyar bin maza takeyiba, tayi ciki yakai sau hudu wanima yayanta bilalne keyi mata kai daka gnta zakaga komi a sassake kmr na bazawara.

Da daddare mommah tasamu daddy a falonshi da mgnr abun mamaki tash ze bata matsala amma se taga akasin hkn yayi farin ciki shima danshi a tunaninshi ko yaran sun shirya kansune.

Shikam gogan bemasan meke gudanaba, abinda yake gabanshi kawai anty jannarht dinne.

**
Lokacin bikin nata matsowa a ynzu hk saura kwanaki 35. Ganin yar tata tashiga taitayinta yasa Ummih tadan fara saukowa don ynzu tana amsa gaisuwarta harma tana feeding dinta sosai tadan fara sakewa da ita amma ba kmr adaba.

Yau takasance sunday ne bata zuwa aiki. Wajajen 12:12pm kwance take a dakinta a kn makeken gadonta da wayrta a hannunta. Kasancewar yau ana rana me zafi dagani zakasan rnr ta ruwa ce, hknne yasa acn dakin a kunne yke. Ummih tashigo dakin da sallamah. Amsa sallamar tayi hadi da tashi zaune. "Sannu ummihnarh.."

"Yauwa mamana.." tazauna a gefen bed din idanuwanta na kan Jannarht din. "Ki shirya gobe me gyaran jiki zatazo daga chardi za a fara miki gyara."

"Ummih gyaran jiki kuma.."

"Eh mna kou kina nufin hk zaki kai mishi jikin babu gyara..ai dole se anyi miki gyara.." cewar ummih.

Murmushi tayi tace "tou ummih.. ta yaya kikasan me gyaran jikin a chard.."

"Eh makwabciyarmu dinnan maman Ibrahim ita kinsan yar chardi ce to itadincema ta dauko miki ita kuma ta biya kudin.." maman Ibrahim babbar macece kmr su ummihn take mijinta babban low ne Yaranta uku biyu maza daya mace suna mutumci da ummih.

"Allah sarki ai mmn Ibrahim akwaita da mutunci .aiko mungode allah yabar zaman tare.."

"Ameen..seki shirya ai gobe tana tafe.." cewar ummih.

"Tou ummih aikinfa nji ance in ana gyaran ba'a fita.."

"Zakije mna ai rana baya dukanki tinda kina mota ne. seta rinkayi miki dasafe da kuma yammah .."

Murmushi tayi tace "tou ummihnarh nagode..." itade har rnta da danta itane bawani gyaran dazatayi.

Washegarin matar ta iso dayake jirgi tabiyo zuwa 2:pm ta iso lokacin jannarht batanan tana office. mmn Ibrahim ta tura dreba ya daukota yakawota gidanta. Ta huta taci abinci. Sannan suka shiga gidannasu. Suka gaisa da ummih da hajiya fatima itama babbar macece amma seka natsu zaka gane hkn, taci gyara dan daganinta zaka gane tabbas itadin me gyarace and farace sol.

Da yammaci jannarht din tadawo tasamesu a falon kasa sunata hira da ummih da hajiya rafi'ah mmn Ibrahim da hajiya fatima. Gaishesu tayi cikeda girmamawa tayima mmmn Ibrahim din godiya. "Haba bakomi jannarht ai anzama daya.." cewar mmn Ibrahim din.

Hajiya fatima da tinda jannarht tashigo taketa kallonta tace "wannance za ayiwa gyaran hajiya rafi'a.." tyi mgnr idanuwanta na kn mmn Ibrahim

"A itace jannarht ba.." cewar mmn Ibrahim.

"Kai tubarakallahu..yarinyar akwai kyau kou babu gyaran wannan ta hadu.." cewar Hajiya fatima dataketabin jannarht da ido wadda tajima da mikewa ta haye upstairs din tnajin me hajiya fatima ke fada.

"Eh hajiya ammande a gyare mna ita kinga tnada kishiya yadda de yallaban ze rikirkice..kmrde yadda kika gyara sadiya.." sadiya yartace ta biyu.

"Kwantrda hnklinki hajiya ai ina tabbatr miki se yaji inba ita ya kusantaba ba mace ya kusan taba.." cewar hajiya fatima.

"yauwa hajiyata.."suka tafa.. ummihde tana jinsu Murmushi kawai takeyi.
[10/30, 3:47 PM] +234 803 727 9133: INSO CUTA NE...24

littafin na kudine ga masu bktr Cigaban littafin su nemi 09038275715.08033368013.

Daki daya aka ware mata a gidan dakine me dauke da komi da komi nan hajiya ta baje kayan gyaranta, da de mmn ibrahim tace aje gidanta hjya fatima tace aah ga mijinta bazasu sakeba.

A daren rnr hajiya ta fara ma jannarht din gyaran jiki Itade jannarh se yadda akayi da ita. Na sanyi aka farayi mata kasancewar yanayin damuke ciki a ynzu babu mace dazatace batada sanyi sede na wata yafina wata.

**
Tini mama rabi ta rinka shigar da mgnr muradinnata itada yar tata cikeda kissa da kisisina take gudanarda lamarinta.. tou damande mama rabi se yadda tayi da mommah kou ango ba a sanar mawaba.. tou wani ankone batashi akeyiba.. ankai kudin gaisuwa dana sadaki da kudin sa rna akasa rnr biki nan da wata daya. Mama rabi kam ba hi tasoba ita in asan samuntane ace sati biyu domin bataso auren yakai wataba tindade kowa a shirye yake .tini mgnr bikin ya zagaye ko ina a Waziris family. Kaji bikin da ango be saniba.🤔

Anwar yaji labarin bikin amma be samu HAMMAD da mgnrba don ynada tabbacin bada izininshiba ze auri jawaheer don yasan inharda yawonshine ko kallo jawaheer bata isaba HAMMAD yayi mataba.

Shikam HAMMAD bema ta kowa a family din tunanin anty jannarht yazama komi na duniyrshi a ynzu. Ji ykeyi kissn dintanma da yayi kara mishi sonta yayi. Kullum HAMMAD na daki anwar na tare dashi sam be gajiya dayi mishi natsiha. Shikam gogan yafi kaunar zaman kadaici fiyeda komi a rayuwarshi ta ynzu.

Su jawaheer kam Anata shirye shiryen biki tini tafara amfani da maganin matsi da gyaran nono don duksun kwanta dmn gasu nonon har ciki daman suke.

Mama rabi kuwa duk wani wanda ze kawo mata cikas a bikin tini ta gama dashi tariga takai sunanshi gun madam na bakin rafi, in Mommah tace zata gayawa HAMMAD mgnr bikin se mama rabi ta fatattake ta rufe ido tahau matsifa tana cewa "ke zainab kwata kwata baki isa da yarankiba inbnda abunki yaronnanfa kece kika haifeshi harse kin gaya mishi kibari mna se ana gobe biki kya sanar dashi aike kika haifeshi bashiya haifekiba"

Mommah takance "Tou mama rabi wai damande abinda yasa nakeso a gaya mishi saboda gudun matsala.."

"Mtwss banaga matsalaba a bikin yataba nide..inde an daura auren ko bayaso ai dolenshi ya zauna da ita.. hba sekuyiyata bin yaya a memakonsu su biyu .."

"Tou mama rabi aibakomi yadda kikacedin hkn za ayi..."

"Yauwa ko kefa zainab...ynzude yakamata ki bada kudin gyaran amarya knsanfa tinynzu za a fara ynzu kimtsa kintse.. " cewar mama rabi tana washe uban hakora.

"Tou mama rabi..nawane.."

"A'ah ke kuwa ai anzama daya kide kamanta ki bada ..gashi kuma tanason tayi yn siye siye" cewar mama rabi cikeda kisisina.

"Okay 4millions yayi.."

Cikeda jin ddh ta Zaro ido mna tayi yar dariya tace "eh bkm yayi kinga ai ykmata a gyare mishi ita sosai da sosai.." cewar mama rabi ..Murmushi kawai mommah tayi.

Sam Mommah bata gayawa anty nahnah ba dayakema tayi tafiya zuwa dubai ita da mijinta. Seda ta dawo Nasreen ta kirata a waya dagawa tyi bynsun gaisa tace "anty inata kirnki baya zuwa.."

"Eh knsan munje dubai da bbnsu noor walhy tafiyarne unexpected mommah da daddy kawai nasanar mawa.."

"Okay.. mommah tagaya miki wani mummunan labari kuwa.." cewar nasreen

Cikeda rashin fahimta tace "menene yafaru.."

"Au ba a gaya mikiba.."

"A mna ki sanar dani mna ke bnason rainifa kinsani niba wasa nakeyiba dake.." cewar anty nahnah dayake tasan halin nasreen da raini.

"Nifa tsiyata dake kenan..Na kiraki zan gaya miki abu zaki hauni da matsifa.."cewar Nasreen.

"Ina jinki tou gyamin mna.."

"Hmmm wai yaya HAMMAD ne ze auri jawaheer.."

tsabar firgice seda boot takusan faduwa a hannunta tace "Wace jawaheer kenan..fahimtar dani mna .wacece jawaheer kuma.." cewar anty nahnah cikeda dimauta adduarh takeyi allah yasa bawai jawaheer din data sani bane..

"uhm Wace jawaheer kika sani kemade anty.." cewar nasreen.

"Kada kicemin jawaheer din mama rabi.."

"Munada watane byn ita.."

"What! Habade jawaheer din da kowa yasanta da bin maza ciki yafi a kirga datayi..!" kmr zatayi hauka take mgnr.

"Eh mna itadin de.." cewar nasreen ita knta haushin abunya isheta.

"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un Ni hafsah..menene yashiga kan mommah.."cewar anty nahnah cikeda mamaki.

"Hmm kinsan Mommah de mama rabi ce ke controlling dinta ita kuma mommah se yadda tayi da daddy .."

"Eh hkne kam abunde allah ya kyauta..Kai bnji dadin lamarinba wlhy ynzu blood dinne za a hadashi da sauran mazan..abunda manaki." cewar nahnah daga yadda take mgna zaka gane abunna cinta inside.

"Ai babu mamaki tinda mama rabi na garinnan..nifa kinsan ba shiri nakeyiba da ita jawaheer din ... se yadawa takeyi a social media zata auri jika ga waziris family...Wlhy kmr na kashe kaina tsabar bakin ciki dana gani ..."

"Tab..ammakou abu beyi kyauba..shi HAMMAD din ya, ya amshi batun.."

"Hmm bngaya mikiba ai mama rabi tace kada a gaya mishi se ana gobe bikin..tin ynzu se tatike mommah takeyi daga rnr da akasa ranar bikin zuwa ynzu mommah tabata kudi yafi 10millions.."

"Kan ubannan..seriously sis ..kai matarnan tashiga uku wlhy...zanzo gobe gidan ai.."

"Hmmm ko kinzo mommah bazata saurarekiba.."

"Hakanande zanzo goben in Allah yakaimu.."

"Tou shikenan sekinzo a gaidamin cuties dina.." "zasuji.." A tare kowannensu ya ajiye waya. Cikeda alhinin abun rnr anty nahnah ta wuni.

Washegari da safiya kafin taje office ta biya gidannasu mommah. Mommahn ma bata tashiba ita ta tasheta. Bude idanuwanta tayi a hnkli taga mutum tsaye a knta ..tace "kinsan in ina bacci ba tashina lafiya.." cewar mommah.

Zaunawa tayi a gefen bed din bbynta noor na. hannunta tace "mommah wani labari naji..shine bn tabbatrba nazo inji daga bakinki.."

Mommah tace "inajinki.."

Gyara zama anty nahnah tayi tace "wai mommah HAMMAD jawaheer ze aura fisabillahi.."

"A se akayi yaya.." cewar mommah.

kallonta nahnah tayi taga babu alamar wasa a fuskarta tace "amma mommah shine ba a nemi shawarata ba.."

"Yi hkri uwata amina bnyi shawara dakeba.." cewar mommah.

" ba zancen hkba mommah..kinsande hadinnan beyiba harga Allah ..haba mommah waye besan halin yarinyarnanba dabin maza ..gaskia mommah dasake.."

Zaune mommah ta tashi da sleeping gown a jikinta tace "look uwata bnason mgnr bnza daman a kn wannan mgnrne zaki tasheni ina baccina...ki kiyayeni da mgnrnan yadda kika dawo kikaga anata hidumar bikin kiyi inzaki iya inbazaki iyaba zuba ido kawai...."

"Amma mommah kinyi tunani kuwa a kn mgnrnan yarinyarfa batafa da tarbiya.."

cikin hnzari mommah ta katseta "tinda ba abun arziki bne yakawoki..tashi ki fitarmin a daki..mara nutumci kawai..shiyasa ake cewa kun rainani a familyna tindade ni bn isaba daku dukknku.."

Mikewa anty nahnah tayi jiki babu katabus tafita still tana mitar mgnr kicibus sukayi itada nasreen gaisheta tyi ta amsa bby noor tace "yaushe kikazo.."

"Yanzunnan nazo..Mommah ma bata tashiba seynzu na tasheta.."

"Tabb ashe kinsha matsifar mommah yau dinnan..kinyi mata mgnr.."

"Hmmm eh..wlhy da gyara a lamarin mommah..nide kawai znsawa tsarautar allah ido cutanede an cuci HAMMAD..."ta karashe mgnr tana amsar diyarta daga hannun nasreen din ."allah ya kyauta..ainide shiyasa kika ganni bnce ko uffan ba..din ainace kada kiyi mgna gashinan knjawa knki bacin rai."

"Eh aide nide nafadi gaskia."

"Amma ai gaskiar beyi amfaniba.."cewar Nasreen.

"EH ayanzuba wata rana ai gaskiar dana fada ze bayyana.." cewar Anty nahnah.

"hmmm.. "kawai nasreen tace.

"Ni zanje office..ngama nayi latti" cewar anty nahnah tna kallon agogon hannunta . "tou sis bye.." juyawa anty nahnah tyi da yarta a hannunta tabar gidan.

Ashe duk maganganun dasukeyi mommah na labe tana jinsu aikou anty nahnah na fita ta fara zazzagawa nasreen matsifa wato ita tagayawa anty nahnah... Itade nasreen bata tanka mataba..Mommah ta karaci fadace fadacenta tabar gun. Itade nasreen ko a jikinta wai an yakusa kakkausa.


8:30pm Alhaji mansurne zaune a sitting room din yna jiranta sanye yake da mnyan kaya wani danyen yadine kalar bleu ya amshi jikinshi kyn.. da

Please Login or Register in order to submit comment