Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wajen girkin yan makarantar kwana da suke yi. Bazawara ce, Auren ta ya mutu. Yaran ta biyu suna wajen baban su. Bayan ta gaida gwaggo ta bude dakin ta da mukulli ta shiga tana hantse baccin da bata yi ba. Malam Bala ya sayo koko da kosai ya kai wa Gwaggo bayan ya gayshe ta. Gwaggo taci nata tana mai ajiyewa Maimunatu nata ita da Hadizalo.

Haj Maimunatu 鈥榶a ce awajen Gwaggo Haule. Domin tun tana kankanuwa iyayen ta suka rasu. Kuma ita kadai suka haifa. Sai rikon ta ya dawo wajen Gwaggo haulen. Gwaggo haulen kanwar mahaifiyar Maimunatu ce. Uwar su d鈥檃ya uban su d鈥檃ya. Da Gwaggo haulen itada su Maimunatu tun kafin su yiyyi aure har ya zuwa auren nasu kafin rasuwar mijin ta a tare suke da kishiyoyin ta guda biyu. Ita ta cikon ukun su. Sai amarya ta hudun su. Gwaggo Haule, Yayan ta biyu kacal da marigayi Aliyu mai faskaren ice, sauran gaba d鈥檃ya sun rasu. Sunyi zama na mutinci da girmamawa da kishiyoyin ta biyu. Hamdiyya da Zaitunah. Kafin a auro musu kubura. Shigowar kubura gidan itace ta tarwatsa zaman lapian da suke yi da kishiyoyin ta. Kawu na suka rabu. Daga baya ma suka hade kai aka ware gwaggo Haule. Abubuwa da dama sun faru lokacin da suke gida d鈥檃ya. Irin gidan nanne babba na da. Kowacce da dakin ta. Ga yaran Kowacce mata. Babu abunda ba鈥檃 sayarwa agidan nan. Gidan marigayi Aliyu mai faskaren ice shine gidan daya fara samun arzikin talabijin din kallo a kauyen, Tun daga kauyuka ake zuwa ganin abun kallon. Allah yayi masa arzikin kauye lokaci d鈥檃ya. Bai da鈥檇e da samuwar arzikinsa ba rai yayi halin sa. Aka raba gado kowacce tagama gaban ta. Shine Gwaggo Haule da yaranta biyu suka samu wannan gidan da suke ciki a matsayin rabon su.

***. ***. ***.

鈥淜u hito ki riko hannun ta. Kar muje mu tarar da layi. Wancen zuwan da mukai yace muzo da wuri Idan zamu dawo don yai mata gwaji.鈥� Cewar Malam Bala, Babban 鈥榙an Gwaggo Haule.

Hadizalo dake fente fuskar ta da hoda me ruwa (foundation) taja tsaki ahankali tana dadira jambaki a bakin ta. Sai kallon kanta take a mudubi tana mai yaba kyawunta.

鈥淕a ni nan fitowa, Gwaggo kin shirya ta ko?鈥�

鈥淢i? Yo wani shiri kuma banda wanda aka gama tun dazu.鈥�

鈥淲allahi Y鈥檃r 鈥榢urkurar har tazo.. 鈥�
Tsahare ta fada tana leka tagar dakin Hadizalo.

鈥淜eda kin cika minahinci Tsahare. Ina ganin ki ta wutsiyar idanu na.鈥�

Futowa tai daga dakin tana hararar Tsahare ta wasa. Ta shige dakin Gwaggo tana sake gaysheta.

鈥淭aso muje Addah Maimunatu! Allah ya baki lahia.鈥�

鈥淎llahumma Aamin鈥�
Gwaggo ta fada tana kallon Maimunatu.

Haj Maimunatu na gefen katifar Gwaggo, An shiryata cikin riga da zani na atamfa, Ga yalwataccen hijabi har kasa. Idanun ta sun sha kwallin da Gwaggo Haule ta rambada mata. Mikewa Gwaggon tayi. Ta mikar da ita. Har waje ta rakasu ta sakata a yar 鈥榢urkura (Adaidata sahu/Dan sahu/tricycle/velocipede)

鈥淭oh Allah ya dawo daku lahia, Allah ya bada nasara. Ku hidi masa likitan fa, tana yawan firgita ko taita wannan kukan da take. Amman babu fashe fashen da take a baya. Kuma wani lokacin bata fita ma, Yauwa ku hid鈥檌 ma shi takan kad鈥檃 kai ko girgiza shi wasu lokutan idan an tambayeta.鈥�

鈥淭oh Gwaggo! Sai mun dawo.鈥�

Dan kurkura yaja, Gwaggo na daga musu hannu, Hade da bin su da adduar dawowa lapia dama dacewar warkewar Haj Maimunatu. Cikin gida ta koma tana mai cigaba da adduoi. Tsahare na tsakar gida tana tular wanki. Data gama ta zuzzuba ruwa a mazubin sa. Ta share ko鈥檌na tas. Sannan ta koma dakin ta ta janyo littafin hausa tana karantawa.

鈥⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€�. 鈥⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€�. 鈥⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€⑩€�.

Suna zuwa asibiti, Likita ya fara tambayoyi yana duban Haj Maimunatu dake wasa da kasan hijabin ta. Sosai ya ga alamar samun saukin ta akan zuwan su na baya. Hadizalo ta sheda masa maganar Gwaggo. Likitan yayi rubuce rubucen sa a takarda. Ya dago ya dube su baki d鈥檃ya yana mai mi鈥檏awa Malam bala takardar.

鈥淎kwai sauran kudaden gwaje gwaje da basu kare ba, Mai gida ya sake aiko da wasu. Yanzu ku tashi ku je da takardar dakin gwaje gwaje ayiyyi mata seku dawo.鈥�

Mikewa sukayi, Suka fice. Hannun Haj Maimunatu na cikin na Hadizalo.

鈥淪hi dai baya gajiya?鈥滳ewar Malam Bala

鈥淢ai shariah ai baze gaji da hidimar Haj Maimunatu ba, K鈥檃una ce daga Allah. Allah dai ya bata lapia. Ya hada kawunan ta da iyalin ta.鈥� Hadizalo ta bashi amsa.

鈥淭oh Aamin ya rabbi..鈥�

K鈥檃rasawa cikin dakin gwaje gwajen suka yi. Cikin lokacin da bai wuce awa da rabi ba, aka kammala kowanne gwajin. Suka koma wajen likitan da sakamakon. Karba yai yana duddubawa fuskar sa k鈥檜nshe da fara鈥檃.

鈥淭oh Alhamdulillahi! Allah ya tabbatar mana da alkhairi.鈥�

鈥淎meen likita.鈥�

鈥淲ato cikin ikon Allah da qudirar sa. Babu wata sauran matsala akanta. Sauran gwaje gwajen ma komai ya nuna ba matsala.鈥�

鈥淢asha Allah! Alhamdulillah! Ana kuma hada mata da adduoi da tofi a gida. Duk asuba akwai makarantar almajiran dake sauke mata qur鈥檃ni.鈥�

鈥淒ama ai kai da kaga wannan sakamakon kasan bana na-saa-ra (turai)bane kadai. Allah yasa mu dace. Toh kowane irin lokaci. Ko da yaushe, Hankalin ta zai iya dawowa jikin ta. (Dementia/Alzheimer's disease) Sannan zata fara iya razana ko furgice idan tana bacci. Domin komai zai rika dawo mata ne daki daki. Ko kuma lokaci d鈥檃ya. Allah ya tashi kafad鈥檜n ta. Ya dawo mata da hankalin ta da nutsuwar ta. Idan hankalin ta ya dawo, Duk abunda yafi soyuwa agareta inma mutum ko abinci a temaka a kawo mata shi. Kar a dau lokaci mai tsawo.鈥�

鈥淚nsha Allahu likita. Allah ya saka da alkhairi鈥�

鈥淎amin! Ga wadannan magungunan a bayar a pharmacy na nan cikin asibitin zasu baku magungunan kamar ko yaushe. Idan akwai ragowar wasu a gida azubar kar ai amfani dasu.鈥�

鈥淢ungode likita Allah ya saka da alkhairi.鈥�

Malam Bala ya riko hannun Haj Maimunatu suka fita. Hadizalo na biye dasu a baya tana tafiya a hankali. Dan dagowa yai ya kalleta yana mai gyara zaman glasses din idanun sa.

鈥淜hadija...鈥�

Da sauri ta juya tana murmushi. Jin muryar sa daddada data kira ta.

鈥淣a鈥檃m Dr. Mahmood鈥�

鈥淶o mana... Mu gaysa.鈥�

Komawa tai ta zauna a kujerar ganin likita dake kallon sa. Ya zare gilashi idanun sa yana mai kare mata kallo. Yana k鈥檃unar ta tun sanda ya fara dora idanun sa akanta. Kyakkyawa ce domin suna yanayi da Haj Maimunatu. Ba zaka ce ta taba aure harda yara biyu ba. Saboda yadda take cin zawarcin ta da lasisi.

鈥淕a ni Doctor.鈥�

鈥淪amun number ki a wayata. Saboda idan na koma garin mu zan dinga kiran ki ina jin ya jikin yar uwar ku.鈥�

Karbar wayar tasa tayi a yangance tana rubuta masa.

鈥淕ashi..鈥�

鈥淕odia nake Khadija.. Ya yaran naki kuwa?鈥�

鈥淪una gidan su.鈥�

鈥淎llah ya raya mana su. Yauwa bari nayi saving number ki da kunya ace nayita kira ta wayar yayan ki.鈥�

鈥淶an iya tafiya?鈥�
Ta tambaye shi tana mai rausayar da kai.

鈥淓h... Khadijaaa na.鈥�

Rufe idanunta tayi da tafukan hannayen ta. Tayi masa sallama suka koma k鈥檃uyen su. Suna zuwa suka shedawa Gwaggo wannan daddadan labari. Shima Dr. ya kira attorney a sirrance ya gaya masa..... Kowane bangare ciki suke da farin cikin jin wannan daddadan labari na Haj Maimunatu. Kowa ya shiga adduar Allah ya tabbatar da alkhairin sa akanta.....


***DALAAL***

Tana gamawa da asibiti ta dauki hanyar gida. Ita ke driving da motar Ummy. Go slow ne a hanyar gidan. Ta zaro wayarta tana dubawa. Missed calls din Ummyn tagani har biyu. Da sauri ta kira ta. Ummyn ke sheda mata idan ta koma gida abinci na kitchen. Ita bata nan sunje dubiya da sauran matan. Jin haka yasanya Dalaal juya kan mota ta dauki hanyar ofishin su Habeeb. Yana zaune yaji knocking. Mikewa yai ya bude kofar yana mamakin ganin ta.

鈥淎h鈥檃hh! Gayu.. Shigo鈥�

鈥淵es! Esq (in U.K. it is used by anyone considered a gentleman; in the U.S. and Canada it is used by lawyers)鈥�

鈥淵es your honor.鈥�

Kujera ya nuna mata ta zauna tana kalle kallen ofishin.

鈥淵a akai kika gano office din?鈥�

鈥淲ani na tambaya.. Kaga kallo kamar ba mutane ba鈥�

Dariya Habeeb yai yana gyaggyara files din gaban sa.

鈥淢azan kano kenan, Da son farar mace.鈥�

鈥淟iterally yes! Naji wani cikin su na cewa wai fara ko mayyace ko aljana ce Allah ya bashi. So vexatious鈥�

Dariya Habeeb ya shiga yi yana rike cikin sa. Sai da yai mai isar sa kafin ya jijjiga kai.

鈥淗alin su sai su. Basu rokon Allah mai alkhairi. Allah ya kyauta, Me zaki ci? A kawo. Akwai Pizza Hut anan gaban mu. Da bobs restaurant.鈥�

鈥淣o.. I鈥檓 okay. Tafiya ma zan鈥�

鈥淜in tabbata?鈥�

鈥淎llah na koshi..!鈥�

鈥淭oh ai kuwa bara na hada takarduna mu tafi. Nima na tashi ai.鈥�

Mikewa tai tana jiran sa, Ya hada kayan sa suka sauka k鈥檃san. Anan ya bar motar sa. Kan cewar zai dawo anjima ya dauka. Ya shige motar dalaal suka koma gida tare... Sosai sun shaku da juna yanzu. Fiye da yadda alkalami zai rubuta...!!!!


鈥⑩€⑩€⑩€�

INSTAGRAM:YERWAINCENSE_AND_MORE馃憦馃徎FOLLOW/LIKE/AND REFER US TO YOUR LOVEDDD ONES.


*_鈽� AL-茦IBLA_*馃挊
_Na Safiyya Huguma_

*_鈽� MABU茒IN ZUCIYA_*馃挅
_Hafsat Rano_

*_鈽� DALAAL_*馃挐
_Na Miss xoxo_

*_鈽� UBAYD MALEEK_*馃挀
_Na Mamu gee_

*_鈽� MAKAUNIYAR 茦ADDARA_*馃挃
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nisha蓷i馃拑馃徎馃拑馃徎馃拑馃徎馃拑馃徎.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka馃憞馃徎馃拑馃徎

茒aya___300
Biyu____400
Uku_____450
Hu蓷u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki馃憞馃憞

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban ta whatsapp shedan biyanku(evidence of payment/Account name)馃憞馃憞

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU馃憞馃憞

聽 0903聽234聽5899

馃拑馃徎馃拑馃徎馃拑馃徎馃拑馃徎馃拑馃徎
TEAM----ZAFAFA BIYAR馃敟馃槝馃グ馃槏
10/17/21, 2:10 PM - Aisha Adam: *NH*


*00:17:00*

***SANDAMU***

**Hajiya Maimunatu na daga kwance tana bacci. Tafara shusshure k鈥檃fafunta saboda yadda wani tuna baya/mafarki dauke da rayuwar ta ta baya tun somawar komai lokacin tana yar budurwa ya shiga zayyano mata akai...

***WAIWAYE!!!***
(ADON TAFIYA)

鈥淢aimunatu... Maimunatu..Maimunatu!!鈥�
K鈥檃warta Hindu ta shiga kwala mata kira. Maimunatun na daga tsaye tana janyo ruwa a rijiyar tsakiyar gari.

鈥淣a鈥檃m Hindu..! Ya garin?鈥�

鈥淟ahia lou! Ke Musalle ne ya aiko ni.鈥�

Maimunatu ta buga zani tana mai murgud鈥檃 bakin ta tamkar Musan ne a gabanta.

鈥淜e na raba ki da gayan zancen sa. Haka kawai yar mitsila dani, Yaje ya nemo sa鈥檕in sa mana. Da an fara tadi. Yai ta hid鈥檌 maka zancen aure鈥�

Hindu ta sheke da dariya tana mai bubbuga kafafun ta akan simintin da aka shimfide bakin rijiyar da shi.

鈥淵arinya wazobia ya bani. Kuma mun isa aure dan kiji, Innata tace ba sai mun fara jini za鈥檃 mana aure ba. Ko yanzu aka aurar da mu babu komai.鈥�

Maimunatu ta sheke da dariya. Tana karasa nada gammon da zata dora ruwa akanta. Ta yafito Hindu da hannu tana mata rad鈥檃.

鈥淒an kiji.... Ina wannan bak鈥檌n da ke zuwa daga kano?鈥�

鈥淟alala yan gayun nan?鈥�

鈥淪u.. Toh dan kiji saurayin yace yana so na. Wai idan yai...鈥�

Bata karasa ba. Hadizalo ta shek鈥檕 da gudu tana kiran Maimunatu.

鈥淎ddah Maimunatu! Gwaggo na bidar ki.鈥�

Labarin da Maimunatu bata karasa bawa Hindu ba kenan. Suka tafi wajen kiran Gwaggo. Hindu ta ciji yatsa. Taso jin karashen labarin.

***. ***. ***

Duk hutu kafin rasuwar iyayen su sai sun ziyarci sandamu sunyi hutu acan. Marigayi Alhaji Ibrahim sandamu shine mahaifin saifuddeen da Ziyadah. Sai mahaifiyar su marigayiya Malama Indo Akilu. Su kadai ne awajen iyayen su su biyu. Daga Alhaji saifuddeen sai hajiya Ziyadah.

A hutun da suke zuwa sandamun ne Alhaji saifuddeen lokacin yana matashi yai tozali da Maimunatu. Kyakkywar bafulatar budurwar data sace zuciyar sa lokaci d鈥檃ya. Ya kasa nutsuwa. Sai daya samu lokaci ya tsare Maimunatu akan hanya ya gaya mata sakon zuciar sa. Tuni ta bada kai bori ya hau, Domin ita dinma ya burge ta. Domin yanada nutsuwa ga kyawun hali ba kamar matasan karkarar su ba.

Sannu ahankali labarin kaunar da yake mata ta karad鈥檈 dangi da karkarar baki d鈥檃ya. Soyayya suke gabzawa sosai. Baya kyamatar a kauye take ko rashin zurfin karatu da bata yi ba. Domin iyaka cinta firamare. Kuma dududu alokacin shekarun ta basufi 13 ba, Shi kuma zeyi 20.

A shekarar ne su Hamdiyya da Zaituna kishiyoyin Gwaggo Haule suka kafa kahon zukar sai sun aurar da yaran su. Gashi ko jini basu fara ba. Haka marigayi Malam Aliyu alokacin ya nemi Gwaggo Haule kan ko za鈥檃 hada da Maimunatu? Gwaggo tace a鈥檃h, Sai ta kara tasawa. Sannan kuma manemin nata karatu yake a birni. Akayi bikin su Ummilo da Haire. A shekarar kowacce ta dawo gida da takardar shika uku. Mazajen sun sausu saboda matsalar yoyon fitsari da suka samu. Sakamakon auren wurin da aka musu basu fara jini ba.

A kwana a tashi ba wuya awajen Allah. saifuddeen ya karasa karatun sa. Aka d鈥檃ura auren sa da Maimunatu. Lokacin tana da shekaru sha takwas a duniya. Tasha suka da zunde a kauyen saboda ba tayi auren wuri ba. Sa鈥檕inta kowacce tayi 鈥榶aya da yawa. Ana auren su ba dadewa iyayen saifuddeen suka rasu. Bayan komai ya lafa. Ya dakko matar sa suka dawo kano. Wata tara da aure haihuwa ta taso. A daidai lokacin da tafiyar saifuddeen law school ta tabbata. Haka ya hada yan kudaden sa ya mayar da Maimunatu kauye wajen Gwaggo Haule...

Firgigit Haj Maimunatu ta farka daga baccin da take yi. Ta kasa gane kan mafarkin. Da yanayin data samu Kanta. Data zurfafa da tunani sai kanta ya shiga sara mata. Wata kara ta saki tana dafe kanta. Gwaggo Haule ta tashi da sauri tana tambayarta.

鈥淵a akai Maimunatu? Minene? Uhm?鈥�

Babu bakin magana, Sai hawaye da ke kwaranya daga idanun ta. Gwaggo tashiga tofa mata adduoi. Dak鈥檡ar maimunatun ta cigaba da bacci. Lokaci zuwa lokaci abubuwa da dama kan waiwayo mata kai. Cikin baccin ne tacigaba da tunano ranar da zata haihu. Lokacin suna babban gidan su mai jama鈥檃......

Tana daga zaune. Cikin ta turtse tse ya taso gaba, Alokacin Gwaggo Haule ta tafi cikin birnin katsina sawo wa Haule kayan aure dan an fara mata tari. Gida ya zama sai kishiyoyin Gwaggo Haule da yara fal. Maimunatu na gefen dakin su. Hadizalo na wanke wanke a bakin rijiya. Yan gidan kuma kowa yana hada-hadar sa. Maimunatu na zaune kan kujerar tsugunno anata labari. Da wannan ya 鈥榢are a saki wancen a dau wani. Anata labartawa kunsan gidan yawa ba鈥檃 rasa guntsi fetsi. Ko baka tanka ba kana tashi za鈥檃yi da kai. Cikin Maimunatun ya tsufa ainun. Kafafun ta sun kumbura sosai, ita dinma ta kara hawa kamar farashi. Anata hira da ita, Idan ciwon cikin ya motso ta dan cije lebe tayi shiru, Yana lafawa Za鈥檃 cigaba da hira da ita.

Gashi sun je asibiti ance ba haihuwa bace. Ta kara dakatawa. Can ana hira setaga duhu. Du鈥檇um tadena ganin haske. Dake tanada fara鈥檃 sosai. Gashi idanun a bude suke babu wanda zai ce bata gani. Tayi shiru tana jiran sarautar Allah.

鈥淛ama鈥檃 na dena gani...鈥�

Mutan gidan suka sa dariya, Kowa ya dauka wasan data saba yi ne.

鈥淜ai Maimunatu, Baki ganin ne idanun ki haka, Kina kallon mu da fara鈥檃?鈥� Cewar Kubura kishiyar Gwaggo Haule.

Saura suka sa baki. Maimunatu tayi shiru kawai tana girgiza kai.

鈥淎i shikenan tunda baku yadda ba.鈥�

Aka cigaba da hira. Takansa baki. Duk kuwa dai da bata ganin su. Can kamar an kawo wuta. Sai kuma taga tar. Bak鈥檌n ya yaye. Idanun sun dawo nuna mata hotunan komai.

鈥淣a dawo ina gani...鈥�

Sauran suka sa dariya. Kowa na tofa albarkacin bakin sa. Harda masu sharo karyar dama wani lokacin ganin ka kawai seya dauke ya dawo. Nan aka cigaba da hira. Can gari ya lullube da hadari. Kan kace me ruwa ya kece. Kowacce ta shige daki . Hadizalo ta tafi dakin yara suka cigaba da yar carafke. Maimunatu kuma ta koma daki tana ciccije leben ta. Wani azababben ciwon ciki ne ya turniketa. Tashiga salati. Kunsan babban gidan kauye. Tsakanin daki da daki akwai rata/tazara sosai. Ga karar zubar ruwan sama. Shi yasa kowa bai jiyo Maimunatu ba.

Cikin haka Gwaggo Haule ta dawo daga kasuwa tana shiga dakinta dauke da sallama ta hango Maimunatu a sankare. Kafafunta a sama. Idanun ta sun kafe. Tanata wata irin jijjiga. Ai da sauri ta callara ihu, Mutan gidan kowa yazo. Aka fara tambayar meya faru? Domin ba dadewa aka gama zantawa da ita. Har ake gayawa gwaggon duk abunda ya faru. Balan da Gwaggo zata saka ya kira saifuddeen baya nan ya tafi aikin wankin mota acikin gari.

Da sauri ta koma waje ta nemo dan kurkura aka kinkimi Maimunatu aka zura a adaidaita sahun, Suna zuwa asibiti aka rasa gado. Wai sai dai su jira. Gashi tanata jijjiga. Dak鈥檡ar Gwaggo ta zube akasa tana kuka, Likitocin suka kinkimi Maimunatu suka ajiyeta a wani daki na ajiyar kaya. Da sauri suka fara bata duk wani temako daya ce. Gaba d鈥檃ya a galabaice take. Gashi masu haihuwan na da yawa. Ta dau tsawon lokaci tana labour. Dak鈥檡ar aka samu wani likita ya tsaya akanta. Ya fara samata ruwan inducing. Nan ma ba wani cigaba sai ma tagayyara data sake shiga.

Sai ga Bala yazo da sauri, Ashe har ya sanar wa saifuddeen ana sanar masa shima ya dauki hanya ya taho. Suna shirin yi mata aiki a galabai ce ta sunkuto 鈥榙an ta kyakkyawa kamar Saiffuddeen yayi kaki ya tofar. Dai dai lokacin da saifuddeen ya iso. Duk su Gwaggo suka furmitsa cikin dakin suna mata sannu.

鈥淢e aka samu....鈥�
Ta tambaya a wahalce tana mai rintse idanun ta saboda yadda wani sabon ciwon kai ya lullube ta.

鈥淜in samu namiji... Maimunatu nahh! Mun samu albarkacin MUHAMMAD-HABEEB-HABEEBULLAH. Allah ya raya mana shi.. Allah ya baki Lapia Maimunatu nah!鈥�

Dak鈥檡ar ta iya daga kai ta dube su shi da jaririn. Yai masa addu鈥檃 da radin suna alokacin.

***Tana kai wa nan ta farka daga baccin da take, gumi gaba d鈥檃ya ya sharbe mata jiki.

鈥淕waggo..! Gwaggo ina Habeebullah?鈥�

Ta shiga nanatawa tana girgiza kanta.

鈥淕waggo ina 鈥榙an dana haifa.?鈥�

Cikin bacci Gwaggo Haule tajiyo muryar Hajia Maimunatu. Ta tashi da sauri tana kara hasken wutar fitilar lagwani. Can sai ga nepa sun kawo wuta wal.

鈥淢aimunatu! Kin gane ni?鈥�

Haj Maimunatu ta daga kai tana gyara daurin dankwalin kanta.

鈥淣a gane ki mana Gwaggo.... Meya faru kike tambaya ta.鈥�

Gwaggo ta dubi gabas tayi sujjada tana hawaye.

鈥淎lhamdulillah Ya Allah kai ne abun godia, Babu komai Maimunatu, Koma kiyi addua ki cigaba da baccin ki, Habeebullah na birnin kano yana karatu. Kin manta kina gida na kinzo duba ni? Koma ki cigaba da kwanciyar ki.鈥�

Ba tayi musu ba ta koma ta cigaba da baccin ta bayan ta tofe jikin ta da adduoi. Gwaggo kuwa kasa baccin tayi saboda tsabar farin ciki. Ta fita bayi ta yo alwala ta dawo tashiga sallolin godia ga rabbus-samawati wal ardi da fara samun dawowar hankalin Haj Maimunatu. Bayan tarin shekarun da鈥檃ka dauka tana fama da matsalar hauka....


**** 鈥⑩€⑩€⑩€�****

Sannu ahankali duk tarin dukiyar Dalaal dake hannun Alhaji Sameer, Shari鈥檃h ta kwato mata shi. Gaba d鈥檃ya ko tsinke dayake a matsayin na mahaifin ta wanda yake na fili dana b鈥檕ye duk an kwakwushe. Har wanda ya sassayar duk an kwato. Aka bude mata sabon account aka narka mata dukiyar ta aciki. Sauran kadarorin duk aka maida komai da sunan ta.

Za鈥檃 yanke masa hukunci dauri agidan kaso, Ko biyan tarin kudi. Dalaal tace ta yafe. Saboda matsayin sa da yake na mahaifi agareta. Duniya tayiwa Alhaji sameer zafi. Saboda duk ya gama lissafa komai da zaiyi da dukiyar. 鈥榊ar tasan data rage kuma dole ya biya basukan mutane. Masu aikin gidan sa duk ya sallame su. Aunty Nani ma ta kwashe ya nata tayi yaji. Kuma tatafi da Hissa can gidan su zata nema mata mijin aure ko da wanda zai aureta sadaqah idan ta horata ta ladabtu.

Moh kuma Adeel ya kaishi gidan mari. Yace a ladabtar dashi. Shi kuma Adeel din ya nemi tallafin karatu na scholarship zuwa kasar Sweden (country in northern Europe on the eastern part of the Scandinavian Peninsula) Can ya tafi karo karatun matakin degree na biyu a fannin banking and finance. A ranar da zai tafi ya kira Dalaal sun jima suna waya. Ya kuma gaya mata zuciar sa. Matsayin son da yake mata. Kuma yace ko ta girmeshi bai damu ba. Shi namiji baya kad鈥檃n. Daya dawo zai aureta inde batai auren ba. Dole a dubi zumunci da kuma muhimmancin Kazn a bashi ita auren sa. Duk sanda ya fadi haka Dalaal kanyi dariya. Kwata kwata ma Adeel baya cikin irin sahun mazan data ke burin aura, Sai dai yanada abubuwa da zata iya duba ta aure shi. Akwai manyan ce, Gayu ga iya kalaman sace zuciyar mace....


**MADRID**

Yana tsaye jikin calendar yana zagaye date da marker. Can kasan karshen watan kuma ya zagaye shi da kalmar 鈥楧-day鈥�.. Murmushi yai yana jan kasan leben sa. So yake kawai ya ganshi a cikin jirgi zasu koma kasar Nigeria. Rufe marker din yayi da murfin ta ya koma kan kujera ya zauna yana daddanna wayar sa. Cikin haka kira ya shigo da sauri ya dauka yana sanyawa a speaker ganin me kiran nasa *Tb**

鈥淎ssalamu Alaikum!鈥�
Hafez ya fada a nutse yana wasa da marker hannun sa.

鈥淲a鈥檃laykm salam. Ah鈥檃h na Morocco sarkin gayu, Hafezullahi hafizin alqur鈥檃ni.鈥�

Dariya Hafez yai tamkar ana ganin sa.

鈥淕odia nake masoyin Allah! Ya gida da komi?鈥�

鈥淟apia kalau...! Kai ai fushi nake da kai..鈥�

Shiru Hafez yai yana mai jinginar da kansa ajikin kujera. Sai da ya sake tambayar sa karo na biyu sannan Hafez ya amsa masa ahankali.

鈥淢eya...Faru?鈥�

鈥淜a fini sani ai, Kai ai halin ka sai kai wallahi, Anyways ya jikin naka?鈥�

鈥淒a sauki...鈥�

鈥淵aushe zaku taho?鈥�

鈥淪oon Insha Allahu..鈥�
Hafez ya bashi amsa yana mai juya kansa yana kallo calendar din dayai marking da D-day.

鈥淪anda zaku taho lemme knw..鈥�

鈥淥kay鈥�

鈥淢eye Labari?鈥�

鈥淒ry...鈥�

鈥淜o yaushe dai zancen kenan. Kayi budurwar kuwa ko haryan zu bakai ba?鈥�

鈥淣ayi, Ban yi ba.鈥�

鈥淏angane ba..? Sannu mystery man.鈥�

鈥淎llah I鈥檓 serious, sau d鈥檃ya na ganta. Ban kara ganin taba. So Mysterious (secret of life, life's unexplainable quality)鈥�

鈥淏angane ba. Bro!鈥�

鈥淎llah banyi wata budurwa ba. Wadda na gani sau na d鈥檃ya na ganta ban kara ganinta ba. Na kamu da son ta...If it鈥檚 meant to be. It will ba. Idan da rabo, Zan nemo ta鈥�

鈥淚nsha Allah it shall be well. Kai da ka rike alqur鈥檃ni. Tun kana k鈥檃rami kake hakura da komai sai zab鈥檌n Allah, Insha Allah idan rabon kace zaku sake haduwa. Kai da baka taba soyayyah ba. Rabon kace da yardar Allah鈥�

鈥淎llah yasa, So ya naka?鈥�

鈥淭oh gani nan dai, Kasan na taba gaya maka mun rabu da wata first love dina, Tayi aure. So Ummah, Ta kara hadani da wata yar k鈥檃war ta abun bai working ba, Yarinyar idanta ya bude. Amma akwai Wadda nake addu鈥檃r samu yanzu da komai ya dai-daita zan sanar maka.鈥�

鈥淥kay... Allah ya tabbatar da alkhairi.鈥�

鈥淎amin鈥� na dame ka ko da surutu? Nasan danma ni ne ka iya sakewa kana magana. Shikenan sai na sake kiran ka.鈥�

鈥淲ill call you back Insha Allah! Thank you soo much. Agayda kowa鈥� Hafez ya bashi amsa, Don dagsken ya gaji da wayar. Hannun sa d鈥檃ya nakan kirjin sa saitin wajen zuciar sa.

鈥淭oh Allah ya kara sau鈥檏i, Ka gayda su Aunty.鈥�

鈥淶a suji Insha Allah.鈥�

Katse kiran yayi. Ya koma kan gado ya kwanta yana rintse idanun sa. Zuciar sa ce ke masa ciwo sosai, Maganin sa ya dakko da ruwa ya balla ya sha yana sauke numfashi. Don dakyar ya karasa wayar bayaso ya fahimci halin da yake ciki. Yana shanye maganin lokaci kalilan bacci yai awun gaba dashi.


***KANO STATE***


Attorney ne zaune a bangaren sa, Shi da Habeeb, Dake gefe a kasa yana sauraron mahaifin nasa, Fuskokin su dukka hawaye ne ke tsiyaya kamar ruwan famfo. Attorney ya goge hawayen fuskar sa yana mai cigaba da yi wa Habeeb maganar da suke.

鈥淪aboda haka, Shi Malam Balan daya sanarmun yace mu dakata tukun. Hankalin nata bai gama dawowa duka ba, Da jin haka sai na nemi Dr. Mahmood, Saboda nasan yamin bayani kan cewar da wuya masu irin matsalar (Ad/D) su warke. Sai yake

Please Login or Register in order to submit comment