Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels *GURBIN IDO*
_Ba ido bane_

*Mallakar*
*Safiyya Abdullahi huguma*
*Arewabooks username*
*HUGUMA*

©️®️ *ZAFAFABIYAR*

*ƊANƊANO*
*Page 01*



Faffada kuma yalwataccen daji ne iya ganinka,wanda ya wadatu da korayen tsirrai da kuma shukoki nau'i daban daban,masu tsaho da kuma gajeru,ciyawa tafasa da sauran tsirrai da ubangiji ya huwace musu su wanzu a wajen,wanda wasu ma dan adam bai san meye ba,wasunsu kuma magani ne da garkuwa ga jikkunan dan adam.

Yadda sararin yayi kore shar da nau'in tsirran da kuma yawaitarsu kadai xai bayyana maka cewa muna lokacine na yawaitar saukar ruwan sama wato lokaci na damina,duk da da cewa gurin waje ne mai cike da ni'ima da kuma albarka,albarka data sanya mawuyacine ka samu wajen a bushe ko kuma a qafe.....wannan dalili ya kawo wanzuwar fulani wajen a muhallin,suka kafa bukkokinsu suka kuma tashi gagarumar ruga a wajen....saboda waje ne daya dace da muradinsu da kuma buqatar dabbobinsu,wanda buqatar dabbobin nasu sama take da tasu buqatar.

Yammaci ne lis,wanda daqiqu kadanne ne zasu ratsa magariba ta shiga,lokacine da kowanne makiyayi yake qoqarin kada kan dabbobinsu zuwa gida inda zai turkesu saboda gabatowar dare,daga cikin wannan dajin mabanbantan tawagar shanu wani lokaci harda raguna da akuyoyi ke kutsowa cikin ainihin wajen da suke kira da gari a wajensu,kowanne tawaga na tafe ne da masu kula da ita,mutum biyu uku hudu har zuwa biyar idan sunyi yawa,yawancinsu maza ne,matan dake ciki daidaiku ne.

Da sannu sannu wadan nan dabbobi ke wucewa zuwa guraben da muhallinsu yake,kamar sun gama wucewa.....saiga wani garken na daban na bullowa a hankali.

Kyawawan shanu ne tunkiyoyi raguna da kuma awaki masu tarin yawa da daukar hankali,ba komaine ya kawo haka ba sai yanayin qoshi da kuma tsaft da garken keda yashi,kusan duk dabbar dake ciki fara ce.....sai wasu daga ciki dake da ratsin ruwan qasa......duka ba wannan ne abun mamakin ba,abu mafi daukar hankali shine Kyakkyawar matashiyar dake kara kaina daga hagu tsakiya xuwa daman dabbobin tana saita su,da fari zaka zaci ba ita daya ke wannan aikin ba,amma idan ka tsawaita dubanka a kanta zaka fahimci ita kadai dince,dauke da sanda guda daya tak.

Kyakkyawa kyau na musamman kuma na asali koda cikin fulanin,irin kyan da zaka tsammaci half case ce,maimunatu nada wani irin kyau na daban wanda ke sanya duk wanda yake baqon gani a gareta ke bata lokacinsa wajen binta da kallo,saidai kuma.....duk da wannan kyau nata babu mutum daya daya aboceta wajen tahowa gida,kusan kowa ya kado dabbobinsa ya barta,babu koda mutum daya ma cikin wadanda sukayi gaba dake waiwayota ko duba halin da take ciki bare yayi niyyar tayata ta samu ta iso gida da wuri.

Kusan itama hakan bai dameta ba,duk da tanashan wahala,amma ya zamar mata jiki,ta kuma saba da yanayin......sanye take da baqin saqi maimakon farin saqi da akasan mafi akasarin fulani na tu'ammali dashi,zaka iya hangen yadda kayan suka dangale mata sosai fiye da dangalewa ta al'ada da aka saba gani tattare da fulanin,don kuwa koda rigar maimunatu tayi dagewar da banda baqar rigar yadi data saka daga ciki,babu abinda zai hana mutum ya hango albarkatun qirjinta da suka fara tasawa,sai kuma yalolon baqin mayafin data sake rufe qirjin nata dashi,duk kuwa da cewa ba wani kauri ne dashi ba,bashi da maraba da abun tace koko,hakanan bashi da tsaho,don ko mazaunanta baikai ba,tun abun yana da girma da kuma kaurinsa take amfani dashi,amma har kwanan gobe ta kasa rabuwa dashi,saboda dumbin tarihin da mayanin yake dashi a gareta da kuma rayuwarta gaba daya.

Zanin jikinta shima a dage yake sasai,kanta na sanye da Hular kaba irin wadda fulani ke yawaita amfani da ita da suke kira da(malafare)sakamakon yawaitar zafin rana ko kuma tunanin saukar ruwan sama,wadda ta baiwa doguwar jelar gashin tsohon kitson dake kanta bayyana sosai,kitson DOKA inji hausawa,su kuma suce dashi(BIƊEJI)(mai tudu daga tsakiya)shine a kanta,don haka jelar ga sauko dama da hagu na fuskarta da kuma bayanta,abinda ya qarawa kyakkyawar fuskarta kyau da kuma bayyana asalin yarenta.

Kunnenta babu dan kunne,saboda bata dashi,bata ma ta'ammali dashi,amma hannayenta cike suke cankas da duwatsu kalar kore shar da kuma ja,irin shirin duwatsun da akasan fulani dashi,hagu da damanta gaba daya,masu yawan gaske,wasu daga ciki ma sun girme mata,amma dai wasu abubuwane da bata iya rabo dasu,tana jinsu ne tamkar fitar numfashinta.

Daga qugunta salkar ruwa ce ta duma da aka fafe daure tam,abu guda daya da take da damar tafiya dashi zuwa wajen kiwo,qafafunta kuwa wasu takalman roba ne rufaffu wanda baka rasa bafulatani dashi saboda yanayin shiga daji qayoyi da sauransu,shi kadaine fari a jikinta,duk da tsufar da yayi amma fes yake,da alama ya samu kulawa.

Cikin matuqar juriya da kuma jajircewa take wulga sandar tata tana maida dabbobin hanya,duk kuwa da cewa numfashinta baya sauka zuwa cikin cikinta saboda uwar yunwar dake sakadar hanjinta kamar zata tsinka mata su,cikin matuqar kulawa take kada sandar,saboda ko kadan batasan ta samu kowacce dabba a cikinsu,wannan kusan al'adarta ne,bata dukansu,saidai duk umarnin da zata basu suna ji suna kuma biye da ita,hakan ya haifar da shaquwa mai ban mamaki tsakaninsu,idan tana magana dasu wani lokaci,kai kace tana magana ne da mutane 'ya uwanta.

Har mantawa take cewa ba bil'adama bane kamarta,sau tari takanji sunfi mata mutanen dake kewaye da ita take kuma rayuwa a cikinsu,idan tana tare dasu,tana jin kamar bata da wata sauran damuwa,tana daukansu ne kamar wasu 'yan uwanta.

Sannu a hankali take ci gaba da kadasu cikin juriya da qarfin hali zuwa hayar da zata sadasu da gida.

Tafiya me matsakaicin nisa suka bayyana a rugar ummaru,faffadan riga mai dauke da bukkoki masu yawa,ga wadanda suka zaunu kuma sun fara gini na jar qasa da kara wanda suka tasheshi a matsayin katanga.

Ta bayan dakunan da suke mallakin wasu suka keta,jimawa kadan sai gasu a haggo(wajen daure dabbobi),ta waiwaya a hankali tana duban sararin gidan,babu matar daya zame mata wajibi duk sanda fa dawo ta shaida mata dawowarta,wannan qa'ida ce,wadda tsallaketa ko saba mata dai dai yake da saima kanta tashin hankali da rashin nutsuwa tsahon wasu kwanaki,idan ma batayi sa'a ba,cikin duka kwanakin da zasu biyo.....za'a yita kiranta da sunan da duk duniya babu sunan data tsana sama dashi

"Miwarti inna!" Ta bude dukka kaifi muryar da Allah ya bata tana qwalawa innar kira tare da shaida mata ta dawo,saidai yanayin zaqin da muryarta ke dashi,sam bata da amsa amo ko kuwwar da kiran xai isa inda takeso

"Inna miwarti!" Ta sake fadi,saidai da alama ko kusa da inda innar take basu jita ba.

Waiwaya tayi gefe guda,yarone dan kimanin shekara takwas,zaune yana wasa abinsa,yayi fututu,kai zaka ce daga sansanin gudun hijira aka tsamoshi,kai ta jinjina,tanason tace dashi wani abu amma tana tsoro kada cibi ya zama qari,bata da zabi illa ta aikeshi ya kira innar

"Laulo,yanoddanan inna" daga kai yayi ya dubeta yana yamutse fuskarsa dake harmutse da qasa

"Owalad'o(bata nan)" ya amsa mata a tsiwace yana maida kansa ga wasansa.

Kanta ta daga sama tana kallon sararin samaniya,hadari ne yake hadowa wanda bisa dukkan alamu ba zai dadeba zai bada ruwa daga yanzu zuwa kowanne lokaci,bata qaunar yanayi irin wannan,lokacin da take dawowa daga kiwo.....cike da gajiya qishi da yunwa,take fara ta turke dabbobin a muhallinsu....ta sanar da inna ta kuma shaida dawowar tata,ta wuce zuwa cikin gida,duk da cewa koda ta wuce din bata da tabbacin samun hutun da dukka jiki irin nata daya wuni yana kara kaina tsakanin jeji da jeji a tsakiyar dabbobi,ba shakka da biyu inna ke aikata hakan a gareta,sai taja da baya kadan ta jingina da wani turke tana ci gaba da duban sama,zuciyarta cike da addu'ar dawowar inna a wannan lokacin.

Cikin matuqar d'ar d'ar take a wajen,duk da ba karatu ne da ita ba mai yawa....amma ta sani xama a wannan lokacin cikin turakun dabbobi abune mai hatsari,bugu da qari ma,a al'adarsu tasan yadda suke taka tsantsan da wajen a lokaci irin wannan.

Sosai ta lula cikin duniyar tunani a dan zaman da tayi a waje,wanda har batasan laulo yabar wajen ba,hakanan batasan hadarin ya gama hade jikinsa ba waje guda,ya kuma fara busa iska dake hade da qura,saida qurar ta gifta ta gaban idanunta,daidai sanda ruwa ya fara sauka.....dai dai kuma lokacin da idanunta suka kai mata ga dabbobin da suka tarwatse a wajen.

Da sauri ta miqe cike da fargaba guda biyu,na farko ruwan saman da zai taba jikinta duk yadda taketa qoqarin kauce masa,na biyu kuma warwatsewar dabbobin data tabbatar da cewa saita sake wani aikin kan ta hade kansu.

Tana miqewa dai dai bullowar wata mata,doguwa ce sambal,farar bafulatana ta usul,sanye da fararen kayan saqi,ta yane kanta da babban mayafi kore shar da shi,a gurguje matar take,da alama itama tana gudun tabatan da ruwan saman zaiyi

"Maimunatu!"ta qwala mata kira bayan taja birki tana hangota tsakiyar dabbobin cikin dan ragowar hasken da duhun hadari dana dare ya fara hadiyeshi

"Na'am inna"

"Muguwa!......saboda bana nan ne shine kika barmana dabbobi su wulaqanta......seto me wanna nima ɓerde(sai na bata miki rai),ki kamasu ki kallaceminsu" daga haka ta sanya kai zuwa shiyyar da dakunansu suke ganin ruwan na sake qarfi.

Abinda ya daga hankalin maimunatu kenan,ta riga data saddaqar yau din mawuyacine ta samu barci matuqar ruwan yaci gaba da taba jikinta,wani irin jiki Allah yayi mata da baya qaunar ruwan sama,indai zai tabata to lallai zata kwana da zazzafan zazzabi,amma sai gashi innar ta wuce abinta ko a jikinta,nata burin dai kawai ta tattala mata dukiyarta.

Duk da yadda ruwan yake dukanta hakata dinga kamasu tana killacewa,ta daure wata saniya tana laluben danta da aka haifa wancan satin,santsin tabon dake wajen ya debeta,ta tafi suuuuu idanunta a rufe tana jiran ta jita a qasa,amma sai taji wani abu ya cake gaban qafafunta,abinda ya hanata faduwa kenan,ya kuma sanyata bude idanunta d asauri wanda tun kan ta bude din haske ya cika idanun nata.

Tarwai ta bude manyan idanun nata da ruwa ya jiqe gashin idanun nata,kamar yadda ya jiqe na girarta da kanta yasa suka hade gaba daya,fuskarta ta sake haske ta kumayi tarwai da wani irin kyau.

Idan har idanunta dai dai suka nuna mata mutum ne tsaye a gabanta,matashin saurayi dauke da lema da kuma fitilar torch light mai tsananin haske.

Da sauri taja da baya cike da tsananin tsoro,saboda tunda take kaf kafin rugarsu bata taba sanin wannan fuskar ba,abune kuma mawuyaci indai kaidin haifaffen rugarne ka tashi bakasan dan wani gidan ba"tsaya mana" ya fadi da dan qarfin murya amma a tausashe,abinda ya dan bata nutsuwar tsaiwar,yadda take dubansa ya tabbatar masa data gamsu dashi ba,don haka yace

"Me kike a ruwa a daidai wanna lokacin a haggo?" Qas tayi da kanta saboda wadatuwar hasken da walqiya ta bayar a lokacin ya haska mata fuskarshi sosai,ta kuma so ta ganeshi

"Ina daure dabbobi ne" kamar xaiyi magana sai kuma taji baice komai ba,ya ajjiye lemar kansa gefe,ha saqale fitilar a jikinsa,ya fara kama mata dabbobin yana tayata dauresu.

Tsai tayi tana dubansa,sai kuma ta taka a hankali itama ta fara kama wadanda zaa daure din tana tayashi sunayi tare,lokaci lokaci tana satar kallonsa,kamar yadda shima yake satar kallon nata lokaci bayan lokaci,ta gaza gasgata idanunta,wani yau a rugar yasa hannunsa yana taimakonta?,abinda ba zata iya tuna lokaci na qarshe da hakan ya faru ba,rashin sabo da ganin hakan ya sanyata dari dari dashi,har zuwa sanda suka gama tas,ya qarasa wajen lemar ya dauketa yana rufeta,saboda bata da wani sauran amfani a wajensa,saboda abinda zatayi masa rigakafi dashi ya riga daya faru.

*ZAFAFA BIYAR*

*_Kundi kuma dausayin zaqaqa kuma da d'ad'an litattafan hausa masu cike da nishadi soyayya darasin rayuwa dana zamantakewa,tsantsar ilimantarwa da kuma fadakarwa_*

*Wannan karon ma gasu tafe da wasu taskirar tsararrun litattafan guda biyar*

SANADIN LABARINA
Hafsat rano

BABU SO
Billyn abdul

GURBIN IDO
Huguma

FARHATUL K'ALB
Miss Xoxo

INAYAH
Mamuhghee

Dukka guda biyar din akan

1k

Guda hudu:::700
Guda uku:::500
Guda biyu:::400
Guda daya:::300

*_Garzaya ki biya naki a fara a kan idanunki ta wannan account din_*

Hafsat Kabir Umar
2270637070
Zenith bank

*Saiki tura shaidar biyanki*
07040727902

*MASU KATIN WAYA ZASU TURAWA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYA*

09134848107

*_KARKU MANTA.....HAR KULLUM,SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA NE_*

*GURBIN IDO*👀👀👀

*Free page 02*


"Migodake" ta fada a hankali tana sharce ruwan fuskarta,dubanta yayi,ya sakar mata murmushi,wani abu me suna nutsuwa da sanyin halin daya karanta tattare da ita na dan qaramin lokaci yana burgeshi

"Karki damu,ba komai" kai ta jinjina,saita juya tana nufar cikin gidan tana qudundune jikinta waje daya saboda yadda sanyi ya fara ratsata,da alama akwai damuwa kenan,yayin da shi kuma ya juya ya dauki torch dinsa ya fara gangrawa yana barin wajen,saidai sau kusan uku yana waiwayarta kafin ta qule masa yabar ganinta,ya sauke ajiyar zuciya yana maida hankalinsa sosai ga hanya,zuciyarsa na qissima masa ita,tsahon wanzuwarsa a rugar bau taba kula da ita ba,hakanan bai taba ganin macen da Allah ya zubawa kyau me sanyi da tsari irinta ba,ko wacece ita?,da wannan tunanin ya isa kofar wani gida,wanda shi dayane kaf kafin wajen dake dauke da ginin qasa da bulo.

Babban tsakar gidane daya kasance wayam babu kowa saboda ruwan daketa sauka,yakai dubansa ga dakunan dake jere a tsakar gidan,har ya nufi wani daki daga ciki,sai kuma ya dakata ya juya akalarsa zuwa wani daki dake daura dashi,muqullin ya taba,a rufe dakin yake dole dai ya karbo muqullin,abinda yasa ya juya da dan sassarfa ya nufi daya dakin,yasa hannu ya dage asabarin da aka saukema qofar dakin saboda kaucema shigar ruwa.

Dumine ya fara dukan fuskarsa kafin hasken fitilar aci bal bal dake dakin ya cika masa idanu,matasan mata ne guda biyu da yaro namiji guda daya zagaye da fitilar,kowannensu d kwanon tuwo a gabansa yana ci,sai babbar mace guda daya da alamu suka nuna mahaifiyarsu ce zaune gefe daya tana dubansu,jikinta nannade da mayafi me kauri,da alama sanyi takeji

"noi saare daada"

"Jam....alhamdulillahi,ina ka tsaya?,inata taraddadi ruwan nan sai daya dakeka" murmushi ya saki

"Zan canza kaya daada,a bani maqulli" hannu ta miqa wata qwarya dake kusa da ita da alama a nan take ajjiye ajjiyenta ta dauko,ta miqawa daya daga cikin yaran

"Nabugol(karbi)" ta fadi,sai yasa hannu ya karba din,sannan ya miqe zuwa inda yayan nasa ke tsaye

Cikin girmama ya miqa masa muqullin yana cewa

"Hamma....." Dakatar dashi yayi

"Micanjato kayaa sadam,ina zuwa"

"To" ya amsa yana murmushi,saboda ya qagu ya bashi labarin dake bakinsa,a nutse ya juya ya fice daga dakin ya sake nufar dakin da yayi nufin shiga dazu.

Batayi wani hanzari ba wajen isa dakinsu,saboda ta riga data jiqe,kuma koda ta isa dinma tasan bata da wani wajen zama daya wuce bakin qofa,dakinsu ne su biyu,amma kuma ya zama gaba daya kamar mallakin mutum guda,wato 'yar uwarta gaaje.

Cikin kula da takatsantsan ta dage assabarin dakin,hasken fitilar dake dakin ya bayyana,motsin shigowarta ya sanya matashiyar dake amsa sunan gaje din daga kanta tana dubanta,gabanta akushi ne madaidaici cike da dambu tana ci,wanda shine yawa yawan cimarsu,tuwo ko dambu,ba kasafai zaka gansu da shinkafa ba

Wani kallo ta watsa mata kamar wadda taga qullin kashi

"Dirdutu malama(matsa malama)" tasan neman bala'i ne kawai irin na gaje,amma inda take tsaye ma sam bashi da alaqa da wajen da gajen ke zaune,sai ta matsa gefan don kawai a zauna lpy,ta miqa hannunta zuwa ga wata tsohuwar baqar jakar bacco dake saqale jikin bango,darajarta wajen maimunatu dai dai yake da akwati a wajen kowa,duk kuwa da cewa duba daya zaka yimata kasan cewa ta sha duniya ta kuma ji jiki,a nan din take ajjiyar duk wani abu nata,duk da dewa ba komai ta mallaka ba face kayan saqinta kala daya da take boyansa saboda sallah ko wani sha'ani idan ya tashi,duk da cewar ita din ba shiga jama'a take ba,rayuwarta na maqale da wani tabo da ya hanata duk wani 'yanci da walwala da kowanne dan adam kan samu,laifin da bata da masaniya a kansa,bata kuma san sanda aka aikatashi ba.

Kayan jikinta ta zame ta matsesu da kyau daga bakin bukkar tasu,sannan ta dawo ta daura wani fallen zani guda daya da take rufa dashi,ta tara hannu a ruwa bunun dake sauka ta dora alwala,sannan ta dawo ciki ta tada sallah.

Sallar magrib ce kawai a kanta,saboda koda wajen kiwo bata wasa da sallarta sam,duk da ba ilimin addini gareta ba mai wani zurfi,amma tun kafin takai haka,zamanin da take rayuwa da mahaifiyarta ta koyar da ita yin salla da zarar lokacinta yayi,abu guda daya da ba zata manta da shi ba,ta kuma riqeshi har yau da kyau,kasancewarta mutum da bata da yawan mantuwa da kuma qwaqwalwa mai yawan riqe abu.

Da kyar takai sallar da takeyi din saboda tsananin yunwa,takai dubanta ga kwanon da gaje ke cin abinci,tuni ta hallakeshi,dan abinda yayi saura a ciki bazai wuce loma biyu ba,ya tabbata bata da abincin dare kenan duk da dan karen yunwan da take ji?,ta rasa wanne irin azanci ne wannan....tare inna ke hada musu abinci ita da gaje,bayan bambancinsu da gajen kwatankwacin bambacin sama da qasa ne,saboda gaje irin mutanen nan ne masu shegen cin abinci,kamar ci suka kawo duniya,duk yawan abinci sai sun tasheshi....yayin da maimunatu ta kasance wata irin mace,duk yawan yunwar da takeji dan abinda zata ci maka bai taka kara ya karya ba,har wani lokacin ma idan kawai nono tafi ganewa tasha shi ko ajiyayyar madara idan tana da sauranta,kusan duk sanda aka hada musu abinci da gaje sai gaje ta kusan cinyewa ko ta cinye ma sannan take tunawa da ita,duk da cewa a yawancin lokuta bar mata take yi,amma duk lokacin data ratso da tsautsayi irin haka tana jin yunwa tofa saidai ta lashi walqiya ko ta nemi ma duk abinda zata ci din,gajen duka duka sa'anni suke da maimunatu,har maimunatun ma ta bata tazarar kwanaki masu dan dama a duniyar.

"Gaje ya baki ragemin ba?"

"Idan kina da wani ma ki qaro min" ta bata amsa tana sude hannu tare da ture kwanon da qafa ta gicciye anan wajen tana sakin gyatsa.

Fararen idanunta masu sheqi ta dauke daga kan gajen,dan qaramin bakinta mai dauke da jajayen labba yana motsawa kamar zata ce wani abun,saidai ba komai zata fada din ba,zallar bacin rai ne qasan ranta,wanda bata isa ta furta ba,bata jun a daren zata iya runtsawa matuqat bata sanyawa cikinta wani abun ba,ga gajiya da takeji tana nuqurqusar qashinta tare da qaramin zazzabi da taji ya fara lasarta,wanda dama tana tsammanin zuwan nasa.

Tsam ta miqe tana leqen waje ta qaramin window din cikin ginin bukkar,ruwan yadan sassauta,amma yana sauka kadan kadan da dan qarfinsa,saita dage qofar ta sanyo kai zuwa waje.

Gabanta na faduwa amma ta daure ta qarasa qofar dakin inna,sallama tayi,shuru ba'a amsa ta ba,ta sake sallama,a sannan aka amsa daga ciki a tsawace

"Wai waye!?"
"N.....nice inna?" Kamar ba za'a fito ba sai kuma ta jiyo motsinta,ta dage labulen ta fito tana mata wani duba daga sama zuwa qasa

"Menene kuma?" Sunkui da kanta maimunatu tayi

"Yunwa nakeji inna"

"Shine kika zo ki cinyeni?" Amsar data sanya maimunatu daga kanta da sauri tana duban innar hadi da girgiza mata kai

"A'ah inna"

"To meye?,bayan kinsan na hada muku abinci da gaje?"

"Ta cinye inna"

"Kina kallonta ta cinye?,to babu wani sauran abinci cikin gidan,saiki kwanta haka,kyaci gobe"

"A'ah,ba za'ayi haka ba" sukaji an fada daga bayansu,rabewa maimunatu tayi gefe daya,ko bata juya ba tasan waye,mutumin da shi kadai yayi saura wanda yake dubanta da idanun rahama,ya qaraso garesu yana sanye da rigar ruwa,da alama dawowarsa gidan kenan.

Da sauri maimunatu ta karbi kayan hannunsa tana tayashi saukewa hade dayi masa sannu da zuwa,inna na daga tsaye tana zabga mata harara amma bata kulaa da lamarinta,don ba zata iya ganinsa da kayan bata karba masa ba

"Yaya mutum zai kwana da yunwa......ki debar mata cikin nawa mana" tuni ta cika dama tayi fam da yadda yake nuna kulawarsa akan maimunatun,uwa uba kuma ya buda ledar hannunsa ya bata bread cikin tsarabar da yayo

"Wallahi ba

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

11 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment