Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sbd yanda Inayah duk tabi ta sukurkurce akaro na uku da fashin auren.

Alqawari tayi bazata qara kawo kowaba ya nema auren Inayah tun basu fara tsanartaba
Amma duk mijinta Inayah Zata aura alqawarine ta dauka itace Zata jajirce su tsaya sosai da umma yaganah suyiwa Inayah gyaran gaske da duk wainda sukaiwa kansu hasarar rashin aurenta sai sunyi kukan baqin ciki da Dana sani.

Yanzu sosai take tsoron kula mazama kwata kwata basa ranta sunma fice Mata Rai sbd a matsayin da raunin zuciyarta yakai aka Kuma samun matsalar rashin aurenta komai zai iya faruwa da ita Dan haka tayi nesa da duk wata alaqar dazata Kuma jefata soyayya.

Abbinta ma sosai yake data da taka tsantsan akan Wanda Zata Kuma samu yaanzu sbd kaucewa hadari da damuwa,
Duk aka Kuma samun irin wannan matsalar likita ya fada Masa zuciyarta ba lallai takuma daukan wani mummunan tashin hankalinba.

A yanayin weak heart irin na Inayah shi baimasan me zatayi da soyayya ba sbd duk wani disappointment Yana cikin soyayya yake gani.

Haka suketa lallabawa da tunanin ta Inda wani manemin auren zai bullo mata.,

Ita dai umma yaganah fargabarta da babbar damuwarta kada Inayah din itama auren yafita ranta kwata kwata kaman mahaifinta,

Shi namijine bazaiyi tsufa a aurenba Nan kusa barema kusan yanzu ne yake cikin shekarun da neman aure agurinsa abune Mai saukin gaske,

Ita Kuma yanzu tanada sauran kuruciya ayanzu ne auren ya kamaceta kaman yanda take buri da tsananin kaunar yin auren
Dan haka ta ninka roqonta gurin ubangiji Allah yakawo musu abokanan rayuwa masu albarka suyi auren.


***Familyn Dr Abdul hankalinsu yafara tashi akan yanda ya dauko hanyar tabarbarewa akan mace,

Duk Wanda yake Dan uwansa yasan INAYAH A MAJEED a rayuwar Dr wata babbar jarabawace,

Abin haushi da baqin cikin shine duk yabi ya lalace akanta Amma wai Bata saniba hakama iyayenta suna gani sunyi kaman basu ganiba,
Hakan yasa kusan duk wasu Yan uwansa sukaji basa kaunar Inayah din sbd Dan uwansu daya Zama gwanin tausayi baida zance sai nata.

Ana cikin hakan Inayah ta hadu da wani yayan abokin Safnah.

Mimi da gudu ta ringa Jin Dadi sbd yanzu mijin ta bangarensu ya bullo Dan haka ta zaqe tanata sake cusa zancen Ahmed din gurin Inayah da umma yaganah saidai Inayah Sam hankalinta Bai kwanta takuma sakewa sosai akan soyayyaba Dan har yanzu akwai sauran son faruk maqale acikin ranta.

A karon farko da zancen ya Isa kunnen Dr Abdul sanyi jikinsa yayi ya silale ya zaune Yana sauraren Inayah din dake fada Masa da kanta.

Bai iya ce Mata komaiba saima kasa kallonta da yayi sbd kada taga yanayinda yake ciki Dan kuwa Zata girgiza da ganin idanuwansa dasukai jajir.

Bai iya tsayawa yin aiki ba ranar sulalewa yayi ya koma gida sbd ciwon Kai Mai tsananin gaske daya taso Masa.

Itama haka Takoma gida jiki amace sbd yanayin Dr Abdul din daya sakata damuwa.

Baiyi bacci ba ranar haka ya kwana Yana juye juyen ciwon Kai Mai tsananin gaske da azaba,

Yasani matuqar Mai samu Inayah ba wlh zai iya haukacewa
Hauka tuburan ta gaske,
INAYAH tazamar Masa jarabawa Kuma qaddara.

Hawayene suka gangaro Masa masu zafin gaske ya miqe zaune tareda nade jikinsa waje daya Yana fashewa da kuka Mai tausayin gaske.

Washe gari Bai iya fita aikiba sbd ciwo ya kwantar dashi
Haka Inayah tazo tareda Dr Emma ya dubasa.

Ciwon kansa Mai tsanani ne Dan haka yayi requesting suje asibiti ya dubasa acan Amma yace AA ba buqatan hakan Inshallah maganin ma zaiyi Masa.

INAYAH ce tasaka aka kawo maganin daga asibiti yasha ya shige ya kwanta itama Takoma gida jiki duk amace.


Kwanansa biyu a kwance kafin ya Dan warware yaci gaba da fita aiki.

Babban abinda ya bawa Inayah tsoro itada umma yaganah da Anty Hafsat shine tun ba'aje koinaba akan maganarta da Ahmed Al'amarin ya lalace ta hanyar Kama Ahmed a drugs case.

Haka kawai hankalin Inayah yaqara tashi sbd ta tabbatar yanzu kam koma menene yake lalata aurenta daga gareta ne sbd shaidu da komai sun nuna Ahmed gskia mutumin kirkine baya hulda da drugs tako Ina Dan haka akafi tunanin sharri akai Masa.

Kan kace me mutane suka fara canfa daga Inayah ne duk Wanda yazo aurenta to masifu kala kala na zuwa garesa.

Hankalinta ya tashi sosai da wannan mugun Al'amarin har abin yaso tabata,

Abbinta kuwa take yafara Dana sanin dawo dasu Nigeria,
Da suna can duk da kila Canfi da wasu abubuwan rashin wayewa basu faruba,

A qasar waje da qabilu daban daban anan dinma basu damu da auren Wanda aka Haifa bada aureba sbd idanma hakane shi ai ba laifinsa bane,
A taqaicema shi abin tausayi ne Musamman ga Wanda hakan ta kasance dashi Yana musulmi.

Amma duk Anbi an hargitsa Masa rayuwa da tunanin 'ya Bayan duk tattalinsa da kulawarsa sun qare akan 'yarsa tilo guda.

Fara tunanin maidasu Australia yayi Nan Kuma hankalin umma yaganah yafara tashi sbd har ga Allah tafison zaman Nigeria sbd kana cikin qasarka kafi nutsuwa da kwanciyar hankali idan ba su dasuke Yan boko ba sunfi son rayuwar turai din.

Dama shi Abbin yafi kaunar zamansu acan ne sbd nesanta Inayah da irin wainnan maganganun dayasan matuqar suna Nigeria yau da gobe sai Mutane sunfara maganganun dazasu saka Mata wasi wasin asalinsu akanta.

Ya zabi barinsu zaman wata qasar ne da nesantata da bude Baki wataran ta tambayesa mahaifiyarta kokuma asalinsu,kokuma labarin yanda mahaifiyarta ta tafi tabarsu.

Gashi tun ba'aje koinaba anfara rikita Masa kanta da wainnan fitintinun,

Auren data sakawa ranta ta nace gashinan Bata samu 'dan amanar dazai iya aurenta dan Allah ba,
Daga Wanda keson aurenta Dan dukiyar mahaifinta sai Mai son wani bangare na jikinta sai masu aibata zuwanta duniya.
Dan hakan yanke shawaran maidasu kawai su koma sai Kuma gaba idan Allah yakawo dalilin dawowar.


Labarin barinsu Nigeria shine ya fidda asalin ciwon dake damun Dr Abdul akan Inayah Dan kuwa har Saida yayi Dana sanin lalata aurenta da Ahmed tunda wuri.,

Kusan zaucewa yayi Dan kuwa baimasan lokacinda yakai kansa gurin Abbinta ba Yana kuka da idanuwansa akan yabasa aurenta shi zai aureta sbd Babu Wanda yakaisa sonta.

Dama yasan za'ai hakan to Amma shi kam soyayyar Dr Abdul din shakku take sakasa,

Son yayi yawa,
Bai taba ganin irin hakan ba,
Basa Inayah din kaman yanada hadari sosai sbd irin wannan ya wuce so ya zama possession.

Amma Kuma ta wani bangaren tausayi Mai zurfi Abdulsamad din yake basa sbd mutum ne Mai nutsuwa da Kamala tareda ilimi sosai Amma sbd soyayya shima duk hakan na Neman gagararsa,
He is loosing everything slowly.

Ta wani bangaren yasan samun Inayah ce warakar Dr Abdul din haka zalika badan tabin kan son dake Neman yawaba yasan Dr Abdul zai Zama Miji nagari Mai kula da kauna ga Inayah.

Dan haka ko yanzu Bai cire ran Dr Abdul din zai kasa kula da Inayah ba,
Yana saka ran idan yasamu Inayah din bazai Bari haukarsa ya cutatar da itaba Dan haka yace yabasa dama ya nema Inayah din idan ta amince shikenan,
Amma da sharadin zai bisu can qasar zai Samar Masa aiki a one of the best hospitals dake qasar
Yaci gaba da aikinsa acan da matarsa.

Baiga abinda zai tsaya tunaniba matuqar zaa basa auren Inayah din Dan haka Kai tsaye ya amince,
Dan koba komai kusan qaruwarsa ce zuwa wata qasar aiki.

A natse abbin ya girgiza Masa Kai Yana cewa"

No Kar kayi rushing abubuwan
Zaje kayi shawara da iyayenka da mahaifiyarka dakace,
Sbd kaman abune da bazaka iya yankewa Kai dayaba Dole kana buqatan iyayenka aciki.

Shidai farin cikinsa ya hanama ya tsaya dogon zance ya amsa da cewa"

Inshallah zan tafi cikin satin Nan na sanar da ita komai Umman tawa.

Allah ya taimaka yasa hakan shine mafi Alkhairi.

Amin, thank you sir,
Ngd sosai Allah yaqara girma da rufa asiri.

Amin.



******Abbi ne da kansa ya sanarda umma yaganah da Inayah buqatan Dr Abdul na abasa damar neman auren Inayah din Kuma yabasa damar Amma sai idan ta amince.

Umma yaganah ba Bata lokaci ta bayyanarda farin cikinta sbd ta jima tana yiwa Inayah shaawar auren Dr Abdul din Dan nutsuwarsa da kamalarsa,
Gashi kyakkyawa shima da Dan arzikinsa ba laifi.

Shi kansa Abbi gskia Dr Abdul din ya kwanta Masa fiyeda duka maneman da Inayah din tayi a baya Amma Kuma yafison tayi zabi akan Dr Abdul din da kanta.

Wani iri taji Al'amarin a farko Dan haka batace komaiba.

Neesah tafara fadawa a waya
Aikuwa Neesah ta ringa tsallen Murna sbd tasan Dr Abdul tako Ina yayi gskia,
Ita da harta fara yiwa kanta sha'awar aurensa Amma ganin basa qasa daya yasa bata zurfafawa kantaba dakuma hango tsagwaron son Inayah a idonsa.

Safnah ma tsallen murna ta ringa Yi tana cewa"

Wlh dama nasan zaai hakan sbd Dr Abdul ya dade da mutuwa akan sonki Naga alama.

Anty Hafsat ma a nata bangaren hamdala da godewa Allah tayita yi sbd dukkaninsu sun yaba da mutuncin Dr Abdul dakuma shedar irin son dayake Mata bazai taba gudunta ba Dan duk wani abunda zaa fada.

Itadai Inayah tanajin 'yar shakkar Al'amarin sbd girman matsayin Dr Abdul a ranta idan sanadin auren Nan suka rabu tasan Zata shiga mummunan hali fiyeda lokutan baya sbd matsayin Dr Abdul a ranta jinsa take yafi Mata duk wata soyayyar datake abaya,

Kaunarsa takeyi sosai cikin ranta tana jinsa tamkar wani jininta,
Tasha gwada yimasa kallon wani bangare na rayuwarta sbd mahimmancin mutuncin dasuke da juna.

Umma yaganah, Neesah,anty Hafsat da Safnah ne suka taru suka ringa azalzala Mata soyayyarsa da nacin nusar da ita irin yanda yake Sonta.

Tun tana jin Al'amarin wani iri sbd Bata taba tunani ko kawo kwatancin soyayya harda aure zai shiga tsakaninta da Dr Abdul dinba har tazo nacinsu da kulawarsa daya soyayyarsa da yanzu yagama bayyanar Mata suka sauya matsayi da kaunarsa cikin ranta zuwa tsaftatacciyar soyayya Mai nutsuwa.
##MAMUH#
#RIBA BIYU
#AA MAJEED ABBI/AYSHATOUH INAYAH




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/25, 5:26 PM] +234 813 060 4664: *_25_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ganin hankalinta ya kwanta akan auran Dr Abdul din sai kowa yaqara bada himma gurin qarfafa Mata gwiwa da sake kwantar Mata da Al'amarin cikin zuciyarta,

Bata sake sakankancewa ta budewa Dr Abdulsamad zuciyarta ba Saida Abbinta ya nuna Mata goyan bayansa akan auren Abdulsamad
Dan haka ta budewa Dr Abdul dukkanin zuciyarta ta karba soyayyarsa.


Abdulsamad tamkar a mafarki yakejin rayuwarsa yanzu dazai mallaki Inayah amatsayin matarsa halak malak batareda shamakin kowaba.,

Sosai kowa ke mamakin yanda duk yabi ya kasa sukuni ya rude Yana bayyanarda farin cikinsa koina.

Tamkar wani zautacce yakomawa Inayah soyayya yake nuna Mata kamar ba Dr Abdul din data saniba tuntuni.

Ita tausayinsama takeji Mai qarfi dayake qarawa soyayyarsa girma cikin ranta sbd Batasan haka yake tsananin sontaba da bazata taba tsayawa kula kowaba da tuni ta amince dashi anyi aurensu.

Mahaifiyar Abdulsamad kam sosai take qaunar Inayah sbd yanda 'danta ke tsananin sonta,
Da farko hankalinta yaso tashi sbd tunanin Bazaa bawa Abdul dinta auren Inayah ba duba da matsayinsu na wainda sukafi na Abdulsamad din kudi sosai sai gashi anyi halin girma anbasa aurenta Dan haka take kaunar Inayah har ranta duk da iyakacinsu waya haryanzu Allah Bai saka sun hadu a zahiri ba wata kila sai lokacin bikin Auren.


***Ansaka lokacin bikin Wata biyu masu zuwa Dan haka ko wannan karon su umma yaganah da Anty Hafsat da wuri suka fara shirya 'yarsu Inayah tako wane fanni.

Gyaranta akeyi sosai Dan kuwa Abbi ya sakar musu kudi suna yanda suke so dasu gurin harkar shirye shiryen bikin.

Wannan karon baiyi wani gayyataba sosai sbd kaucewa hayaniya albarka auren akeso ba taronba,
CM ne ma dai dayafi A MAJEED din shiga mutane sosai ya dauka nauyin gayyatar ta hanyar aikawa manyan mutanen dasuke taredasu special invitations na auren.

Anty Hafsat ta haukace tsima Inayah kawai takeyi tako Ina da abubuwa masu kyau da inganci nasu na manyan mata.

Umma yaganah Kuma masu gyaran jiki takuma sakawa aka kawo matasu daga maiduguri harma da 'yan uwanta biyu dasuka zo bikin auren Dan haka tako Ina families din guda uku nasu na A MAJEEDs,da iyalan gidan CM saina dangin ango dasuke Adamwa hidimar biki akeyi gadan gadan ta kowane bangare.

Inayah tana cikin wani irin farin ciki Mara misali sbd jikinta da dukkanin imaninta yabata wannan karon Zata auru Inshallah bazaa fasa aurentaba Dan haka taketa Jin farin cikin igiyoyin auren Abdulsamad dintane zasu hau kanta bana kowaba.

Shikan oga Dr Abdulsamad fadar irin farin cikin dayake cikima wasane Dan kuwa jin yake Kamar zai take kan jariri dama uwar jaririn ya wuce sbd zumudi da farin ciki.


Lafiyayyan lefen aure dangin Abdulsamad din suka kawo ana Saura kwana biyar afara bikin Wanda su umma yaganah sun yaba sosai da irin kokari dakuma uwar dukiyar dasu Abdul din suka kashe.

Neesah sai a ranarda aka kawo lefen itama tasamu isowa daga Australia tareda Dr farhat wadda ita ta sauka a gidan Mahaifiyarta dake aure a Lagos din Dan haka tana zuwa suka sake hautsinewa da Murna.

Safnah ma tuni tadawo gidan da kwana sai angama biki so gabaki daya gidan dai a kacame yake da jama'ar biki duk da ba wasu masu irin yawa dinnan bane.


Inayah gabaki daya ta sauya Takoma tamkar wata jaririyar da aka Haifa acikin watan sbd tsananin kyau da taushi da fatarta tayi,

Gyara da rashin fita tareda tsananin hutu da kwanciyar hankalin datake ciki a watannin yasa tayi wani irin zallar fresh sai sheqin fata takeyi.

Tunda Dr Abdul yazo yaga irin kyau data qara da sheqin amarci datake tun yanzu yasa yaqarasa rikicewa akanta duk da soyayyarsa Bata shaawa bace Amma tuni kyanta ya qarasa rikita Dan sauran nutsuwar dayake da ita akan Sonta daya zaburesa.

Ganin yanda yabi ya rude hakuri na Neman gagararsa yasa Anty Hafsat ta hanasu haduwa sosai tace sai lokacin bikin Dan haka yanzu a waya suke koyaushe ba sakat Kamar wasu hanta sa jini.

Abbi kam sosai Al'amarin nasu ke Dan basa mamaki da dariya kawai sbd yanda Inayah tasan ta iya soyayya sosai irin haka Dan shi haryanzu a jaririyar 'yarsa yake kallonta gashi zatai aure takoma qarqashin ikon wani.

Yau sosai take amatuqar gajiye sbd saka lalle da akai ayau din can gidan CM Dan haka sosai take amatuqar gajiya Koda suka dawo gida zare tsadadden lace din dake jikinta tayi Mara nauyi ko kadan ta nufi toilet tashige.

Gaban mirror ta tsaya tafara goge fuskarta tas da Neutrogena makeup remover wipes.

Wanka tayo da ruwan dumi kafin tafito daureda towel tana kallon Neesah ma dake jiran ta fito wankan itama tashiga tayo Dan duk makeup din fuskokinsu damunsu yakeyi sbd basa wani makeup dama can
Iyakacinsu Liner da mascara sai lipstick masu tsadan gaske dake zaunawa da kyau abakinsu idan sun saka.

Sama sama ta shafa Mai tareda spray dasu khumrahs masu sanyin qamshi da akayo Musamman masu tsada daga maiduguri.

Riga da wango tasaka masu kauri sbd sanyi sanyi datake ji.

Sallolin dake kanta tafara Yi kafin ta miqe ta fito tana waya da Dr Abdul dinta ta nufi dining tana cewa"

Heart yunwa fa nakeji sosai yau banwani ci abinci ba
Zaa ramar maka Ni da yunwar biki.

Cikin kulawa sa so Mai tsanani ya karyar da murya yana cewa"

Ni zasu illata gskia bazan dauka ba,
Kyakkyawar amaryar tawa ce zaa Bari da yunwa
Gskia bazan yardaba
Laifin anty Hafsat ne data hanamu haduwa yanda muka saba kewanki is driving me crazy
Gobe da safe zanzo na ganki kafin su Umma su iso sbd itama tana zuwa Zata qarawa anty Hafsat qwarin gwuwar hanamu ganin juna sai ranar Daurin auren.

Murmushi tasake Mai kyau tana cewa"

Dan Allah kazo goben da wuri Nima nayi kewanka fa sosai.

Zama tayi a dining daidai lokacinda Abbi ke isowa dining room din a kasalance ta ajiye wayar sbd bataso Gama waya da Heart dinta ba Amma Kuma girman Abbinta na daban ne akan komai.

Kallon abbin tayi Yana sanye da Fararen hoodie graffiti print sweatset.

Sanyin qamshinsa ne yake neman danne na Lafiyayyan abincin dake jere kan dining din yayi fresh Kamar ba baban amaryar ba Batasan lokacinda ta sake qaramar dariyaba tana cewa"

Abbi barka da fitowa.

Da Dan silent murmushi ya kalleta yana amsawa da cewa"

Barka Amaryan Dr Abdulsamad.

Dariya tasake tana kallonsa tace"

Abbi Naga kamanma ka matsu natafi nabar gida,
Kullum saikace mun amaryar,
Nidai kunya nakeji Gaskia.

Wani qayataccen murmushi ya sake daidai lokacinda Neesah da umma yaganah suka iso dining din cin abinci yace"

Inayah kinsan kunya dama?
Inace you don't know the name kunya,
Kin manta a gabana kike zuwa kina kukan soyayya da Kiran sunan zayyan ne sunan koma fahat ne I can't recall
And now kinata tsalle da murnan zakiyi aure shine kike fadamun kunya
Rashin kunya plus lie ko??

Dariya umma da Neesah sukai umma na saka musu Baki da cewa"

Inayah kam ai indai anan cikin gidane Babu Wanda take kunya saidai mutane waje take kunya.

Kai umma yaganah please karki sake batan suna gurin Abbi Kinga zaifi kowa kewata fa idan natafi ko Abbi?

Abincin data Gama zuba Masa yafara ci yana Dan gyada Mata Kai ahankali.

Bayan sun Gama cin abincin bin Abbinta tayi palonsa suka cigaba da maganganunsu na tsakanin uba da 'ya sai kusan after 9 tafito ta nufi daki ta kwanta bayan tasake goge fuskarta da face cleanser.

Washe gari shine zaai Mata lalle Kuma tasan heart dinta yace zaizo Dan haka da wuri ta tashi tayi wanka ta shirya cikin Riga da skirt na maroon super exclusive wax da qaramin Marron veil ta fito a sace sbd yaca Mata ya iso Yana palon Abbi.

Tana shiga palon Abbin Yana zaune tareda Abbi suna magana cikin nutsuwa.

Bude kofar tareda sallamarta a sirance tasaka su waiwayowa kallon kofar atare take zuciyar Abdul yakusa bugawa.

Ya salam ya furta a fili batareda yasan ya furta hakan agaban Abbin ba.

Qamshintane ya doshi hanyar mamaye palon gabaki daya sbd wasu irin qamshine kala kala na designer turarukanta masu tsada da turarukan khumrahs da akai Mata masu tsananin sanyin qamshi da shiga zuciya.

Kallo daya Abbi yayi Mata yaga yanda daga ita har Abdul din suke kallon juna yaji mamakin gaske yana kamasa ta yanda Inayah duk ta lalace har haka baida sani.

Ahankali ya dauke Kai daga kallonsu tareda gyara murya yana Kiran sunan Inayah din a natse.

Cikin nutsuwa da girmamawa tace"

Yes,
Good morning Abbi.

Qarasowa tayi tareda dauke kallonta daga kan heart din tana Zama kusada Abbinta tasake gaidasa.

Amsawa yayi tareda Dan kallonta yace"

Hafsat tasan kinzo Nan?

Murmushi tayi tana girgiza Kai da cewa"

Abbi Bata saniba banaso ta sani please.

Da mamaki ya Dan kalleta sbd yasan hakan bai kamataba Musamman yanzu irin yanda yaga suna maitar kallon juna bayason ko kadan shedan ya Shiga zukatansu Koda rungumace suyi kafin aurensu tunda daga yau ne sai gobe jibi zaa daura auren Dan haka ya Dan kame fuska a kame yace"

Ok ku gaisa ki koma ciki zanyi magana dashi.

Bata fuska take Neman yi ta marairaicewa abbin Amma ganin ba wannan damar yasata kallon Abdul daya Gama mutuwar zaune gurin satar kallonta ta gaishesa a gutsure.

Amsawa yayi batareda ya kalleta sosaiba tunda Abbi na gurin
Badan sun soba su duka haka ta juya Takoma Inda ta fito.

Shima Bai wani gane sauran zantukansa da Abbin ba sama sama ya gane yayi Masa sallama ya wuce.


Jiki mace akai Mata zanen kunshin sbd rashin ganawa dakyau da heart dinta.

Sai kusan yamma daya kirata yasamu yasaka zuciyarta da ranta ya sake suka Dan zanta a wayar kafin ta aje tashiga wanka sbd anmata dilkan yamma again.

Washe gari Koda ta tashi da murnar sauran kwana daya ta tashi hakama da damuwar rabuwa da Abbinta Dan haka ta ringa samun sauyin yanayi aranar,
Tayi farin ciki tashiga damuwa ahaka dai yamma tayi duk saitaji tashiga damuwar tunda gobene Zata bar gidan gashi har yamma tayi Babu abinda ya rage a wunin yawuce sai kawai ta fashe musu da kuka.

Bata taba tunanin halinda Zata shigana ranarda Zata rabu da mahaifinta sai yau Musamman idan ta tuna da Heart dinta Dan Adamawa ne can zasu tafi da ita bazata sake Zama gurin Abbinta ba
Tsorone Mai girma ke Neman cika zuciyarta sbd duk Inda Zata tafi jinta safe cikin nutsuwa da kwanciyar hankali agurin mahaifinta.

Tun su anty Hafsat na Mata dariya hardai suka fuskanci da gaske takeyi hankalinta ya tashi matuqa a tsorace take.

Umma yaganah ma jikinta duk yayi sanyi Musamman itama datai wata irin sabo da shaquwa da Inayah din tun jarinta.

Heart dinta hankalinsa ya tashi da kukan nata sbd kowa yayi yayi taqiyin shiru shiyasa anty Hafsat tafada Masa kozai iya zuwa ya lallashi Inayah din
Itama umma yaganah takira Abbi tafada Masa Inayah fa tana nan tana zabga kukan bazata iya zuwa Inda Batasan kowaba ta rabu da mahaifinta.

Cewa yayi idan yagama magana da baqinsa dasuka iso Lagos domin daurin auren goben zai iso gidan.

Dr Abdulsamad Yana tareda mahaifiyarsa da qannan babansa biyu Mata sai 'yayan yayyun mahaifiyar tasa biyu suma Koda anty Hafsat me Masa wannan bayanin.

Kallon umman yayi yace"

Umma Bari naje gidan Inayah ce tanata kuka wai bazata iya zuwa garinda batasan kowaba.

Murmushi umman tayi cikeda mamakin shirme irin na Inayah
Gata ta girma dai Amma gata yasa yarinyar kasa nuna ta girma.

Wayarta dake gefenta ta dauka tana cewa"

Kaga bara natashi muje tare sbd dama yakamata da muka iso munje gidan an gaisa kafin goben ranar biki muje gidan,
Kaga dama abinda yasa nazo da kaina kenan sbd Inayah din tasake tasan muna kaunarta sosai
Nice zan karbeta da hannuna Inshallah cikin Amana bazamu Bari tayi kukan baro gidaba.

Gaba yayi Yana cewa"

Okay umma saikin fito to.

Bayan fitarsa tsadadden mayafinta dake ajiye ta dauka tareda LV handbag dinta ta nufi kofa tana cewa"

Nafisat zo muje Naga kece a shirye da alama su Asmau akwai sauran gajiya atare dasu kaman wainda sukai tafiyar mota bayan jirgi kuka biyo.

Ficewa suke kokarin Yi yayar mahaifin Dr Abdul dake sallah tana idarwa cikin Dan daga murya tace"

HADIZAH.

cak umman ta tsaya tareda waiwayo tace"

Na'am.

###MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/26, 4:02 PM] +234 813 060 4664: *_26_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ku jirani a motar Bara na sauya Kaya muje Nima zan gaisa da iyayen na Inayah tunda dai kaman yanda kikace din yakamata muje a gaisa basai gobe bayan daurin aurenba muje.

Ok Tom muna jiranki a motar.

Juyawa tayi ta fice daga babban dakin ta ratsa palon zuwa babban palon gidan na mijinta Wanda Sam basa Zama anan tunda aikinsa na soja ya maidasa Abuja ita saita koma Adamawa sbd uwar gidantace a Abuja ita Kuma a Lagos to ana Masa transfer zuwa Abuja tabar Lagos Takoma babban gidansa dake adamawa.

Tana Isa motar Haj balaraba na isowa Dan haka sai kawai suka shiga suka wuce zuwa gidansu Inayah din.

Tafiyar mintuna sukayi suka iso lafiyayyar anguwar ta masu abun duniya.

Kai tsaye security ya budewa Abdulsamad din gate Yana daga murya da cewa"

Welcome Sir.

Yauwa thank you Bosco.

Parking yayi tareda kashe motar suka firfito su umman na sake yaba arzikinsu Inayah din Dan kuwa gidan irin tsarin ginin turai ne komai ma kusan yanda Inayah takeso akayisa.

Kai tsaye hanyar kofar palon cikin gida ya nufa dasu
Sbd su din Bai kamata yabi ta hanyar palon Abbi dasuba.

Suna Isa kofa Safnah na fitowa da waya a hannunta tanayi ganinsu yasata katse wayar Dan nuna girmamawa gasu umman Abdul din dasuke manyan Mata sosai.

Cikin sakewar fuska da girmamawa tafara musu sannu da zuwa tana gaidasu.

Juyawa tayi tai musu jagora zuwa can qurya palonda kowa yake Anata fama da Inayah din.

Tsokar Abdulsamad tayi da cewa"

Yanzu sbd heart din taka ka tado su umma da magribar fari Dan azo a rarrasheta.

Dariya yayi yana cewa"

Safnah harda ku kuka sake rudar mun da ita gskia
Amma haka kawai baby bazata fara kukan Nan ba.

Shi a palo ya zauna Yana amsa waya sukuma su umma palon ciki tayi dasu.

Su umma yaganah dasu Mimi na ganinsu cikeda farin ciki da mutuntawa suka tarbesu suna musu sannu da zuwa a waye.

Mahaifiyar Abdulsamad hadiza babbar mace ce Mai tattare da Kamala da mutunci sosai Kuma a bayyane ta nuna kaunarta da kulawarta ga Inayah.

Drinks da snacks zubbi da Salimat suketa aikin kawo musu Anata sake musu sannu da zuwa.

Cikin Jin Dadi da farin cikin yanda aka karbesu hannu bibbiyu da mutuntawa suketa amsawa suna sake yaba gatan da Inayah take dashi Dan duk Wanda is kalla yanayinsa a gidan zaka tabbatarda yanda yake kaunarta tunda kusan duk albarkacinta kowa keci acikinsu adai cikin gidan da rayuwar AA MAJEED.

Da 'yar Raha umma yaganah tace"

Kuna fama da gajiyar tafiya Rigimar Inayah ta fiddoku,
Shima Abdul din dabai daukokuba ai yabari Kun huta shegantaka ne kawai irin na Inayah Zata fara kukan barin gida tun yanzu
Ai tabari har zuwa goben idan andaura aure.

Yar dariya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On INAYAH
avatar
amira-3-1

9 months ago

Reply

Mashallah

avatar
rilwan

8 months ago

Reply

Masha Allah

avatar
zainab-aliyu-rabiu-dal

4 months ago

Reply

mashaAllah

Please Login or Register in order to submit comment