Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Haj balaraba tayi tana cewa"

Ai Dole zatayi kuka tun yanzu sbd auren nesa na gida Daman sai kaji kaman shikenan katafi.

Umma Hadiza kuwa Inayah data fito daga bedroom sanye cikin Riga da skirt na soft embroidery Swiss Mai kyau da tsada navy blue ta zuba Mata Ido gabaki daya tana kallonta.

Duk hotunan Inayah da vidcall dasuke ganinta idan Abdulsamad na gida basu bayyanar Mata da kamannin Inayah ba kaman yanzu datake ganinta a gabanta.

Da farko zuciyarta harbawa tayi da kyawun fuska Dana jikin Inayah hartana Jin Anya Abdulsamad bazai bartaba akan matarsa Inayah bayan auren
To Amma Kuma zuciyarta tarigada ta kamu da kaunar Inayah tun kafin auren sbd son da Abdulsamad ke Mata to yanzuma data ganta saitaji kaunarta Mai nutsuwa da tsafta takuma shigarta.

A natse Inayah ta qaraso Inda suke fuskarta duk yayi ja sbd har lokacin hawaye takeyi sosai Musamman ganinsu umma Hadiza sai taji kaman sunzo tafiya da itane gabaki daya zatabar gida.

Cikin farin ciki da kulawa tareda murmushi a fuska umma Hadiza ta kamo hannunta ta zaunar da ita a gefenta tana cewa"

Zo ki zauna 'yata Inayah kinji,
Ki daina kuka sbd inshallah bazamu taba Bari kiyi kewansu umma da Abbinki ba sosai Dan zamuyita tattalinki muma kaman yanda suke Inshallah.

Ba kunya Inayah ta dago ta kalli umma Hadiza alamar da gaske kike fada.

Da sauri umma da Anty Hafsat suka dungure Mata kan suna cewa"

Inayah wai bazakiyi hankaliba ko??

Su umma Hadiza da haj balaraba kuwa dariya suka sake atare harma dasu Neesah
Haj balaraba na cewa"

Eh Inayah Inshallah bazakiyi kukan shigowa zuriar muba da yardar Allah,
Barema wannan ja'irin Abdulsamad duk Wanda ya damar Masa Mata Inayah ai nasan zaburewa zaiyi da rashin arziki kala kala
Shima Kinga muna kaunarsa sosai Dan haka bazamu Bari matarsa ta Shiga damuwar dashima zai shigaba.

Washe Baki su umma yaganah suka hau Yi suna Jin dadin sirikan da Inayah tasamu masu kaunarta.

Murya a sanyaye Inayah ta bude Baki cikin girmamawa ta gaidasu tana Dan sake goge hawayenta.

Inayah daina kukan kinji Inshallah Baki rabu da gida ba duk lokacinda kikaso gida zakizo ki gansu
Kuma kin manta Anan Abdulsamad din yake aiki ne?
Bawani dadewa zakuyi a Adamawanba zaku dawo Lagos mune ma zamu ringa zuwa dubaku basaikunyi wahalar zuwanba.

Ahankali Inayah ta saki Dan siririn murmushi tana kallon su Anty Hafsat dake Mata dariya.

Da Raha Haj balaraba tasake cewa"

Inayah akwai sauran kuruciya kam,
Gaki 'yar fari shiyasa aketa shagwaba ko?
Nikam ma menene Ma'anar sunan Inayah Dan naji sunan shima na Yan shagwaba.

Dariya sukai saidai anty Hafsat ce tace"

Ma'anar sunan Inayah shine kyauta daga Allah,
Kaman ace kyautar datazo wadda bayan Allah Babu Mai iya baka ita.

Dukkaninsu murmushi sukai ana cigaba da Dan sake maganganu cikin Raha da mutuntawa har lokacin sallah yafara wucewa Dole suka tashi Dan gabatar da sallah.

A dakin umma yaganah aka Kai su umma Hadizan suyi sallah sai alokacin Inayah tasamu ta Isa Palo gurin Heart dinta.

Yana ganinta ya taso a natse tareda miqa hannunsa ahankali ya kamo nata hannun suka Isa kujera suka zauna Yana kallon fuskarta datai ja cikin damuwa da kulawa sosai yace"

Baby sosai kikai kuka haka?
Oh my God,why baby?

Wasu hawayen takuma gangaro Masa tana sake narkar Masa da fuska tace"

Heart Dan Allah karmu dade Adamawa da yawa mudawo Lagos da wuri.

Numfashi ya sauke Yana goge mata hawayenta da tissue din dake palon cikin kulawa kaman ya janyota ya rungumo yace"

Baby ki daina hawaye da damuwa please,
Idan Dan zakibar gidane na miki alqawarin bazamu dauki lokaciba zamu dawo okay?

Gyada Masa Kai tayi tana tsayar da hawayenta.

Lallabata yayi takoma ciki Dan yin sallah shima ya fice zuwa qaramin masallacin dake gefen gidan yayo sallah Yana dawowa yace su umma su fito ya maidasu gida akwai baqinsa dasuka iso daga Adamawa yau Dan daurin aure zai samesu a hotels din dasuka sassauka su gaisa friends dinsane sosai.

Yana harabar gidan jikin motarsa Yana jiransu saiga motar Abbi tashigo yadawo shima.

Su umma Hadizan ne suka fito tareda su Anty Hafsat da Mimi dasuka rakosu harma da Inayah dake maqale gefen Haj balaraba tana sake rarrashinta cikin kauna da kulawa.

Cikin maroon luxury motar Bentley bentayga yadawo gidan Dan haka suna ganin motar duk suka tsaya Dan gaidashi dakuma su umma Hadizan ma su gaisa tunda yariga yadawo.

Cikin wani Sky blue tsadaddiyar soft Italian cashmere a jikinsa ya fito
Fuskarsa fresh a kamile.

Kyakkyawar fuskarsa ya juyo da ita ya kalli Inda suke gabaki dayansu sun tsaya suna jiran fitowarsa daga motar a girmame.

Hasken fatarsa da dogon hancin zuwa haiba da kwarjini Mai yawa da Allah yayi Masa yasa dukkaninsu Babu Mai iya Masa kallon quru quru saidai a gaisa kana Dan sauke Kai a mutunce.

Inayah ce tabar gefen Haj balaraba ta nufesa tana kallonsa cikin kulawa tace"

Abbi barka da dawowa.

Wani nutsatsen murmushi ya sakar Mata Yana amsawa Kai tsaye da kallon fuskarta datai ja sbd kuka a natse cikin lafazinsa masu nutsuwa yace"

Duk kukan da kikaita yine wannan?

Bata fuska tayi zatai magana anty have ta Dan qaraso kadan tana Masa sannu da zuwa cikin girmamawa tace"

Sirikan Inayah dinne wato mahaifiyar Abdulsamad sukazo tareda yayar mahaifinsa zasu tafi ko zaku gaisa.

Ok ba damuwa"
Ya furta tareda qarasa tahowa cikin nutsuwa Inayah din na gefensa kaman Zata maqale Masa.

Tunda suka doso su kowa ya sake Dan kame kansa suna rage kallonsu akansa sbd kam badai cika Ido da zallar haiba ba.

Umma Hadiza datai Masa kallo daya taga fuskar kaman wadda ta sani Dan haka ita bata dauke idonta akansaba taci gaba da bude idanuwanta dakyau akansa.

Dan juyawa kanta yayi kadan sbd toshewar Dan qwaqwalwanta ke Neman Yi gabaki daya da kamannin nasa.

Baya wani kallon Mata Musamman su din dayaga ba laifi dattijai ne Dan haka a mutunce ya gaisa dasu ya kalli Abdulsamad dake nuna umma Hadiza yace"

Sir wannan itace mahaifiyar tawa.

Dan sake fuska Abbin yayi kadan tareda kallon umma Hadizan a natse yace"

Barka da zuwa Haj,
Ya hanya?
Allah ya hutarda gajiya......

Tsit yayi bayan yasamu yakai qarshen gaisuwar a Dan rarrabe.

Kallon fuskarta yakeyi dakyau cikin Dan basarwa sbd danne duk wani Abu dayake yunquro Masa cikin Rai.

Mummunan bugawa Mai qarfi zuciyarsa tayi wadda bayajin yataba samun wannan bugawar.

Sam Bai nuna halinda yashigaba saima juyawa da yayi ya wuce ciki Yana musu a sauka lafiya.

Mutuwar tsayece da daukewar hankali na daqiqu agurin ya Kama Hadiza Saida Haj balaraba ta Dan girgizata tana ambatar sunanta.

Kasa motsi tayi sai kawai sukaga tana neman zubewa sbd duhun dayake Neman rufe idonta da qyar ta iya bude Baki murya a hargitse ta furta"

BP Dina ya hau sosai please ku kaini gida Nasha magani bana gani sosai.

Hankali tashe Haj balaraba da Abdulsamad din suka kamata ta shiga mota dukkanin jikinta na rawa a rude sukabar gidan.

Da tausayin umma Hadizan su Inayah suka koma cikin gida Bata tsaya komaiba ta nufi sashen mahaifinta.

Zaune yake numfashinsa na Dan fita da sauri
Qananun zufa na tsatsafo Masa a goshi da alama Yana Jan numfashi ne dake Neman qwace Masa da qyar.

Da gudu tayo kansa tana Kiran sunansa hankali tashe da firgici Dan Bata taba ganinsa hakaba.

Bai dago ya kalletaba ya karba tissue din datake goge Masa zufa
Ya Dan kame kansa Yana kokarin basarwa a hankali yace"

Ya Isa haka, I'm okay kije
Kawai.

No Abbi bakada lfy
Kana gumi fa.

Ahankali ya furta"

I think my BP dropped.

Wat?" Tafada da sauri tana kallon yanayinsa.

Juyawa tayi da sauri tana cewa"

Bara naduba.

BP monitoring machine harma dasu sphygmomanometer ta dauko da sauri tadawo cikin damuwa sosai.

A tsaye ta taddasa kaman ba Wanda tabari Yana Dan hada gumi ba da jajayen Ido.

Da mamaki ta tsaya da Kaya a hannunta tana kallonsa cikin mamaki da kulawa tace"

Abbi?

Magana zatai ya Dan waiwayo ya kalleta a Dan kame yace"

Kibarshi kawai ya wuce
Zanyi baqi yanzu ki koma ciki.

Kallonsa tayi a marairaice da fuska Zata Kira sunansa da 'dan daga murya yace"

Nace kije Inayah.

Hawayen tashin hankali da tsoro taji suna Shirin gangaro Mata sbd yaune karon farko da Abbi yayi Mata tsawa tunda dai ta girma tasan kanta.
##MAMUH#
#AYSHATOUH MRS AA MAJEED
#LOVE/ROMANCE/MARRIAGE



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/26, 4:02 PM] +234 813 060 4664: *_27_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Kasa riqe hawayenta tayi suka gangaro Mata ta juya a sanyaye tana Satan kallonsa Zata fice ya sauke wani boyayyan numfashi tareda ajiyar zuciya Mai tafe da hucin zafin da Kai da kirjinsa suka dauka a natse Yana sake kame kansa da basar da yanayin dayake ciki ya bude Baki yakira sunanta a natse.

Da sauri ta juyo ta dawo Dan dama bason tafiyar takeyiba ta kallesa tana share hawayenta tace"

Na'am Abbi.

Sake sauke ajiyar zuciya yayi wannan karon kansa na qara daukan zafi Mai tsanani kawai dannewa yakeyi Yana basarwa kada hankalin 'yarsa ya tashi babban burinsa a yanzu ya karkata akan baya kauna ko kadan bare fatan wani illa yazo ya gifta a cikin auren Nan da zaa daura gobe dan kuwa wannan karon aka fasa auren 'yarsa Allah ne kawai zai Raya Masa ita sbd gargadin da likitanta yabasu akan sake shigarta tashin hankali.,

Komai zai iya faruwa da ita idan takuma shiga wani mummunan shock na tashin hankali,
Ganin wannan matar ya girgiza kansa da tun tsawon shekaru masu tsayi kan ya bushe,
Ganin mahaifiyar Abdulsamad babbar masiface tabbas Zata bayyana Dan kuwa idan itace mahaifiyar Abdulsamad akwai gagarumar matsala.

Meyake Shirin faruwa da 'yarsa idan komai ya lalace a daidai wannan gabar?

Sake Kiran sunansa Inayah tayi cikin sanyin murya ganin yanda yayi shiru kaman Yana nazarin wani abun.

Waiwayowa yayi ya kalleta da fuskar kulawa yace"

Kukan barin gidan ya isa haka Inayah,
Idan kina wannan kukan zan daga auren zuwa nxt month saiki sake cire kewan gida da kyau.

Murmushi tayi tana share hawayenta tace"

Na Dena kukan Abbi.

Wani murmushin Dole ya saki Yana sake boye damuwarsa yayi maga Yan maganganun dasuka sanyata sakewa sai gata tana dariya Wanda shikuma hakan yasake caza kansa akan abinda zai iya zuwa ya komo.

Lokacin sallar ishai dayayine yasanta ficewa daga palon Abbin Takoma.

Tana fita ya sauke wata nutsatsiyar ajiyar zuciya idanuwansa na neman sauyawa.

Miqewa yayi ya fice zuwa masallacin gidansa sallar ishai.

Ana Gama sallar yadawo ya rufe sashensa ya zauna Dan tattara abinda yake yawo cikin kansa Yana Neman juyawa.

Dafe gashi yayi Yana Jin gaban kansa kaman zaiyi bindiga tsabar nauyi da zafin daya dauka.

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun,
Meyesa wannan matar da Baya fatan sake ganin fuskarta har abada Zata bayyana rayuwarsa da 'yarsa a daidai wannan lokacin Kuma ta bullo ta mabulla mafi firgici da tashin hankali.

Tun a shekarun baya tsanarta ta ginu cikin ransa tsanarda tasa ya rufe shafinta ruf daga rayuwarsa gabaki daya Dan ko a kamanni baya fatan sake ganin Mai kamarta,

Shin ita dince ma kuwa wadda yake tunani kokuwa?

Bazai taba manta kamannintaba sbd itace ta taka mahimmiyar rawa gurin ruguza rayuwarsa a karon farko,
Itace wadda ta wargaza buri da gatansa na zama cikin iyaye da 'yan uwansa tasakashi a matsatsen hali mafi matsuwa da Muni.

Kamanninta Zane suke da baqin alqalami a idanuwansa,
'yarsa Inayah da girman mahimmancinta da qauna Mai tsanani ta uba da 'ya dayake Mata yasa ya yafewa matar Nan Amma Kuma har abada bayajin zai iya cire tsanarta Mai girma a ransa bare kallonta da daraja ko qima.

Haduwarsu ta farko da ita Bata Zama Alkhairi ba Dan hakan ko yanzu yasan bayyanuwarta rayuwarsa ba Alkhairi bane a rayuwarsa data 'yarsa Dan haka Dole yanason Jin amsa biyu rak daga bakinta daga ya samu amsoshinsu bazata Kuma ganinsaba dagashi har 'yarsa har abada.


Shi idan Yana cikin damuwa ko tashin hankali Sam baa wani ganewa sbd alokacin nutsuwarsa da kamewarsa take fin yawa,
Shiru yakeyi Yana nazari batareda buqatan hayaniya ko katse Masa nazariba shiyasa su Inayah dasun gansa irin yanayin suke yin tsit gidan duk da dama ba hayaniya ce dasuba gidansu.


*******Qarfe goma da mintuna Ashirin ya fito harabar gidan sanye da black hoodie Thom Browne Riga da wando masu kauri ya nufa White jaguar motarsa ya bude ya shiga tareda tada motar ya nufi gate dama tuni Bosco yaga fitowarsa da sauri ya bude Masa gate ya fice.

Yana fitowa daga street din gidansa motar Abdulsamad Tasha hanasa tareda danno Masa full light.

Wani banzan numfashi ya saki tareda Dan juyar da kansa cikin takaici da baqin ciki ahankali yace"

Wannan matar tabbas zatasan waye AA MAJEED.

Babu tantama yasan itace a motar Abdulsamad din

Itama Babu tantama dama tasan yau komai dare saiya fito nemanta sbd dukkanin Susan amsar tambaya daddaya dake zukatansu kafin daurin auren gobe Dan kuwa amsoshin tambayar dake ran kowannensu itace future din yayansu da zaa daurawa aure gobe Dan haka a wahalce ta saci jiki ta fito bayan tasa Abdul yabar musu motarsa incase idan ciwonta zai tashi da dare su wuce asibiti ya samesu acan.

Batada lafiya sbd jininta yakai kololuwar hawa ko tsayuwa Bata iyawa sosai Amma bazata iya kwana ayauba batareda tayi magana da mahaifin Inayah ba,

Zuciyarta bugawa zatai da sake sake da fargaba harma da tashin hankali matuqar yau batai magana dashiba taji abinda takeson ji.

Da wani irin speed ya fizgi motarsa yabi ta gefen motarta ya wuce Yana Jin tsohon tabon baqin cikin daya dade Yana dannewa yana taso Masa.

Ribas tayi ta rufa Masa da gudu itama duk da qarfin haline kawai takeyi Dan sosai takejin kaman zuciyarta Zata fashe,
Tsohon famin baqin ciki da quncin da tarin Dana sanin gaske datake dannewa shekaru masu yawa ne suke birkito Mata tako Ina tanajin zuciyarta na azabar zafi da qunci.

Baisan tasan Lagos ba sosai Dan haka ya ringa ratsa manyan anguwannin dazai bacewa ganinta saidai sosai ta nace tana binsa idanuwanta ma tuni suka fara tsiyayar hawaye Dan kuwa hakan ya tabbatar Mata da tunaninta Gaskia ne akansa shine Wanda ta gudu tabarwa Jaririyarta AYSHATOUH.

A daidai gaban ma'aikatarsa ya faka motarsa tareda qin fitowa zuciyarsa na qara daukan wani irin zafi da bacin Rai da baqin ciki Mai zafin gaske.

Baya kaunar ganin fuskarta sbd ganin fuskarta na tunatar dashi kowace daqiqa na lokacinda ya rabu da gatansa da iyayensa harma da farin cikinsa akanta.

Jajir idanuwansa suka kada sosai sbd tsananin zafi da zuciyarsa ke dauka.

Bude motar tayi ya fito ya wuce zuwa ciki tabi bayansa da sauri itama hawayenta na tsananta gudu kaman yanda bugun zuciyarta da tashin hankalinta ke tsananta.

Cak suka tsaya a tsakiyar office dinsa koina tsit ba kowa sai securities din ma'aikatarsa.

Zubewa tayi agabansa tareda fashewa kawai da kuka Mai tsanani da taba zuciya sbd Batasan me Zata fara fadaba ko tambaya.

Kukanta sake zafafa ransa yakeyi Musamman wannan sautin kukan shine ta ringa Yi Masa a wancan lokacin batareda da duba girmewar datai masaba ta lalata rayuwar 'dan matashin dake tsakiyar karatunsa cikin kwanciyar hankali da kulawar iyaye.

Wani mummunan 'daci da qunci Mai nauyi ya hadiye ta wuyansa tareda juyowa ya kalleta da idanuwansa dasukai jajir Kai tsaye Yana danne fushinsa da nutsuwa yace"

Bansankiba ko wancan lokacin hakama bansakinba a yanzu,
Banda alaqa kowace iri dake bayan wadda zamu qulla a goben ta auren 'yayanmu Kuma itama zan bar 'danki ne kawai ya auri 'yata sbd farin cikinta dakuma kaucewa abinda zai sameta idan akai fashin auren Dan haka ki amsa mun tambaya daya rak itama sbd kaucewa Mummunan Al'amari.

Kuka takeyi sosai sbd tasan Babu abinda daga ita harshi sukewa tsoro kaman alaqar 'yayansu
Saidai kafin komai yabiyo baya na abinda ya faru a baya shine susan makomar alaqar dake Shirin qulluwa goben wadda tuna abinda zai biyo batama tashin hankali ne da wata babbar masifar.

Cikeda baqin ciki yakuma kallonta Jin batada niyar amsawa sai kukan datake Yi kaman zata shide.,

Zafi da quna ransa ke qarawa Dan haka ya juya yanajin kansa na sake yamutsewa da babban tashin hankalin da Inayah Zata iya Shiga akan wannan matar...

Yanada zafin zuciyan gaske Mai tsanani Amma tunda rayuwarsa ta sauya ya iya boyewa da dannewa Babu Mai gane yanayinsa duk kafiyarka Amma yau zafin zuciyan tasa ya gagara dannuwa a zafafe ya buga glass table din dake gefensa take ya tarwatse da qara Mai tsanani
Saida Hadizan ta firgita tana dagowa da jajayen idanuwanta dasuka rine take sbd tashin hankali Mai tsanani da kuka.

Miqewa tsaye tayi hawayenta har lokakacin basu tsayaba Dan ba tsayawar zasuyiba muryarta na rawa tace"

Ina AYSHATOUH???

Wani matsiyacin kallon baqin ciki da takaici yayi Mata yanajin duk duniya Babu Wanda yakai Hadiza sonkai
Ya dauke Kai Yana kokarin danne kansa daga zafin fushin dake taso Masa Kai tsaye yace"

Idan kece kika haifi Abdulsamad menene alaqarki da 'yar da kika Yar????

Gangaro Mata hawayen daci da danasani sukai muryarta a dashe tace"

'yatace nice na haifeta da ita da Abdulsamad duk nice na haifesu Kuma mahaifinsu daya idan Inayah itace AYSHATOUH to uwarsu daya ubansu daya da Abdulsamad.......""da kuka ta qarasa zancen Dan kuwa babbar masifa ta diro ta sameta a zazzafan tabon ciwon qunci..

Idan Abdul Mai samu Inayah ba haukacewa zaiyi"" innalillahi wainnan ilaihrrjiun
Na shiga uku Ni Hadiza rayuwata tasake shiga wata babbar jarabawar Mai nauyi...


Mutuwar tsayece ta samu AA MAJEED Dan kuwa yayi fargabar Jin hakan Amma Bai yarda da zaiji tabbatar hakan daga bakintaba.

Qarasa rikidewa idanuwansa sukai jajir yanajin wani gumin zafi da babban tashin hankali na shigarsa.

Abinda yakeson tabbatarwa kenan daga bakinta dan shakku da fargaban daya shigesa na iya yiyiwar hakan Kuma ta tabbatar Masa Dan haka baida sauran buqata da ganinta kona second daya Dan a Karo na biyu ta sake wargaza rayuwar 'yarsa.

Juyawa yayi Yanayinsa na ninkuwa ada sauti Mai 'dacin gaske yace"

Zaki iya komawa ki sanar da danki dagani har 'yata yanzu bamuda alaqa daku Auren anfasa.

Juyawa yayi zai fice Dan hankalinsa gabaki daya yagama yamutsewa qarshe kaman kansa zai buga
Inayah yakejin tashin hankalin yanda Zata karba kaddarar rashin auren Abdulsamad sbd bazai taba fada Mata dalilinba Dan kuwa bazai taba barin Hadiza ta kusantar Masa 'ya ba.

Da saurin Hadiza Tasha gabansa tana rokonsa cikeda tarin nadama tace"

Dan Allah kafadamun idan Inayah ce Ayshatouh na,
Har abada nasan bazan taba samun yafita a zuciyarkaba Amma Dan Allah kada ka hanani Ayshatouh Inayah,
Wlh nayi Dana sani nayi nadama.....

Sauraronta tafasashi sukeyi tako Ina Dan shi kansa komai ya kunce Masa a yanzu.

Wucewa yayi Yana daga wayarsa zuciyarsa a quntace ya saka kirana Mr Al-amen Yana dauka Kai tsaye yace"

Ai Mana booking tickets da komai na tafiya nida familyna gobe kafin 12 zamu bar qasar....
##MAMUH
##MARRIAGE/LOVE
##AYSHATOUH INAYAH AA MAJEED


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/26, 4:02 PM] +234 813 060 4664: *_28_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Tashin hankali Hadiza tashiga Jin abinda ya fada a firgice Tasha gabansa tana rokonsa cikin mummunan hali na kuka tana rokon ya hadata da 'yarta Ayshatouh Inayah.

Numfashi ya sauke a hankali tareda ajiyar zuciya Mai dumi kafin ya Dan dago ya kalleta kadan cikin nutsuwa kaman Wanda zuciyarsa ba tsananin quna takeba da 'daci takeba yace"

Babban taimakon da zakiyiwa kanki da Abdulsamad shine ki cirewa ranki da kanki tunanin sanin mahaifin Inayah bare ita Inayah din,

Inayah 'yatace Kuma Babu Wanda zaizo Rana tsaka yacemun shine ya haifeta,
Bansankiba Baku nada alaqan komai dake..

Ki nema yarki a Inda kikasan son zuciya yasa kin barta.

Zafi maganganunsa suka farai Mata sbd duk yanda tayi aikin son zuciya abaya Inayah dai yartace Kuma tayi danasani daga ranar data gudu ta barta.

Wlh bazata yardaba taga yarta sannan ya dauketa su bar qasar tasan bazata Kuma ganintaba har abada Dan haka cikin rashin tunani da tauna zancen abinda yafada matan tace"

Har abada saidai ka Kira kanka matsayin mariqinta uban daya raineta Amma bazaka taba sauyata daga nice wadda na dauka cikintaba na haifeta.

Bai tsaya saurarentaba ya fito Kai tsaye yashiga motarsa Yana cewa security a rufe Masa koina.

Cikin zafi ga figi motarsa da matsiyacin speed yabar gurin batareda yajira ganin fitowartaba.

Ikon Allah ne kawai da nutsuwa dayayita kokarin sakawa kansa sbd kada su Inayah su gano halinda yake ciki yakaisa gida lfy.

Yana parking ya fito ya nufi kofar dazata kaisa palonsa na farko direct batareda yabi kofar dazata bi dashi ta palon su Inayah ba kafin ya Isa nasa palon.

Yana Shiga palonsa Kai tsaye hanyar bedroom dinsa ya nufa ya shige tareda Zama kan luxury italian sofa dake dakin ya rintse idanuwansa dasukai jajir.

Ajiyar zuciya yafara jerowa da numfashi Mai zafi yanajin damuwa da tashin hankali Mai tsananin wannan auren da Allah yasa baa dauraba da tako Ina masifun da tashin hankalin bullowa zaiyi,

To Amma babban tashin hankalin da damuwar shine ta yanda Inayah Zata karbi fashin aurenta akaro kusan na hudu.
Tayaya zai iya taro matsalar da Zata iya samunta?
Innalillahi wainnan ilaihrrjiun.

Miqewa yayi ya nufa toilet ya sakarwa kansa daya dauki tsananin zafi ruwa yanajin zafin kan na tsananta.

Da ruwan dumi yayi wanka ya fito ya saka blue pyjamas sai sanyayyan Chanel na jiki ya kashe wayarsa tareda jefarwa gefe ya hau gado zauna Dan yasan yau koda qyaftawar Ido bazai rintsaba sbd fitina da tashin hankalin dayake jiransu da safe.

Umma Hadiza ma cikin masifaffen tashin hankali da tsoron AA MAJEED yabar qasar da inayah ta iso gida jikinta Babu Inda baya kakkarwa ta silale tashige dakinta batareda kowa yasan fitarta da dawowartaba ta rufe daki tareda zubewa qasa tafara kuka Mara sauti tana cewa"

Ya Allah kagani rashin mafita da madafa da Sharrin shedan ya hanani tawakkali na gudu nabar 'yata badan bana tsananin sontaba ya Allah nayi shekaru cikin qunci da damuwa da tawakkali ya Allah kada kabari wannan bawa naka ya tafi da 'yata wata qasarda bazan Kuma jinsu ko ganinsu.,,ya Allah ka duba maraicina ka hadani da 'yata,
Allah ka kawo Mana sassaucin wannan masifar data kunne Kai da tashin hankalin dazai biyo goben sanadin fashin auren yaran Nan.

Kuka takeyi sosai tana rokon Allah sassauci da mafita.

****Daga AA MAJEED har umma Hadizan Babu Wanda ya rintsa yanda sukaga Rana haka sukaga dare da safiya.

A gidan A MAJEED da zallar farin ciki iyalan gidan suka tashi Dan ko su Anty Hafsat duk a gidan takwana da yaranta gasu Safnah da Neesah dasu Daman tuni suka tare sai Yan uwan umma yaganah guda biyu dasuka zo bikin Dan tayata Murna dakuma samun abun arziki.

Dr farhat dasu Mimi ma tunda safe suka iso gidan kaman dasu aka kwana.

Kowa farin cikinsa bayyananne ne sbd duka aurarrakinta da ake fasawa Babu Wanda yazo ranar Daurin auren  sai wannan yau gashi Allah yayi anzo daurin auren a wanni kadan ne suka rage tazamata cikakkiyar matar Heart dinta Abdulsamad salees halak malak.

Cikin kayan baccin data kwana dasu Riga sa wando masu santsi tafito da hula akanta fuskarta da dukkanin fatar jikinta sunyi fresh sai sheqin kyau da gyara sukeyi gashi yanayin data fito din kaman wata qaramar yarinya.

Kai tsaye dining ta nufa tana cewa"

Yunwa nakeji zubbi kawon tea nafara sha.

Tea da doughnuts masu laushi guda uku zubbi takawo Mata tana cewa"

Mint tea din Sir is ready
Zaa shirya Masa ne a dining kokuwa?

Tana Shan tea dinta tace"

No ki shirya zan Kai Masa palonsa yau da mutane a gidan bazai shigo ciki ba,
Harda dessert din kin kammala hada Masa?

Yes Ma.

Ok kije ki hado zan Kai Masa.

Ok Ma.
Juyawa tayi ta koma kitchen din Dan hadowa takawo Mata.

Wayarta ta daga tana kokarin Nemo numbern Heart sai gashi kiransa yashigo wayarta da farin ciki bayyane kan fuskar ta dauka da Yar muryarta Mai shagwaba tace"

Good morning Heart.

Wani sanyin farin cikine yakuma cika ransa sbd ranar yau din daqyar yaga garin ya waye
Cikin wani irin girmammen farin ciki yake Mai nutsuwa,
Allah yau yacika Masa burinsa na mallakar Inayah amatsayin matarsa dazata Zama uwar yayansa.
Ji yayima farin cikin yasaka jikinsa sanyi Musamman data Kuma kiran sunansa da HEART.

Muryarsa a sanyaye yace"

Morning baby,
Kin tashi lfy?
Yaya shirye shiryen da hayaniyar su Anty Hafsat?

Murmushi kawai tayi Tana cewa"

Idan anty Hafsat tajika Zata sa a 'daga tafiyan Amarya yau sai wani satin.

Wat? aikuwa Dana tare a gidan Abbi Nima.

Dariya tayi tana cewa"

Zan kaiwa Abbi breakfast zankiraka idan nafito
Kisses.

Murmushi kawai yayi Yana kashe wayar gabaki daya muryarta ta kashe Masa jiki yayi sanyi sosai,
Jin yayi har zuciyarsa na yin sanyi.


Daukeda tray ta nufi hanyar palon Abbi tana murmushin wayar data Gama da Heart.

Knocking kofar tayi ahankali tareda budewa ta shigo da sallama tana kallon palon da Babu kowa sai Sanyin AC dake aiki da Qamshin turarensa daya Gama Kama koina na palon.

Hanyar bedroom dinsa ta kalla tana ajiye tray din kan table.

Tabaro wayarta bare takirasa ta sanar Masa tana Palo Dan haka tana ajiyewa  ta juya ta fice.

Breakfast ta tadda duka kowa nayi wasu a dining wasu a dakin umma yaganah Dan haka tayi joining Dinsu itama tana cin Doyan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On INAYAH
avatar
amira-3-1

9 months ago

Reply

Mashallah

avatar
rilwan

8 months ago

Reply

Masha Allah

avatar
zainab-aliyu-rabiu-dal

4 months ago

Reply

mashaAllah

Please Login or Register in order to submit comment