Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

taga Zaid ne.

Wani zafin gaske ne ya taso Mata daga qasan zuciya,
Duk lokacinda sunan zaid ya fado ranta Jin take tamkar Zata Kama da wuta sbd tsananin zafin kishi da baqin ciki.

Jefar da wayar tayi tareda nufar gaban madubu tafara shiryawarta.

Oil ta shafa tareda moisturizer kadan ta fesa su spray da body mist dinta ta nufi closet.

Sai after 9 tafito sanye cikin fitted long sleeve gown kalar blue sai qaramar scarf nade akanta.

Dakin umma yaganah take kokarin Isa Amma taji kaman muryan Abbinta a dining room Yana waya Dan haka ta juya ta nufi dining din.

Shi da umma yaganah ne zaune Dan haka itama ta qaraso tana cewa"

Tun yanzu anfara ware ni a gidan Nan.

Umma yaganah ce tayi Yar dariyar Jin Dadi ganin Inayar ta sake
Dama Allah Allah take MAJEED yafita gidan kafin ya dagosu su samu sugani idan zasu iya kashe zancen iya tsakaninsu.

Ita harga Allah babbar damuwarta irin fushi Mai tsanani da MAJEED din zaiyi idan yaji 'yarsa da duk arzikinsa da zamansa busy Bai hanasa tsayawa yana ture komaiba Dan ginarda tarbiyarta tun tana jinjira har zuwa yanzu yaji sunje gidan saurayi tasan wlh ranar ransa qarshen bacin Rai zaije,
Hakama Kuma qarin abin bacin ran da baqin cikin yaji Inayar da bakinta tana fadar hannun Zaid acikin riga Yana latsa nonuwan wata,su kansu sun San ranar sai yanda Allah dai yayi dasu daga ita umman har Inayar.

Ata wani bangaren tasan Sarai Inayah Zata iya fadar hakan gaban Abbin nata.

Dan hakan yanzu ba qaramin farin cikin ganin Inayah ta sakeba tayi har Saida kusan Abbin yagane Amma dai baice komaiba har lokacin.

Breakfast sukai suka Gama ya fice zuwa aikinsa.

Yana fita Inayah ta tattaro bacin ran da baqin cikin dataketa dawainiyar boyewa cikin ranta kaman zai kasheta.

Bata wani tsaya dogon zanceba tacewa umma yaganah Zata gidansu Neesah tadawo Dan tanason Jin komai dalla dalla daga gareta idan ba hakanba zuciyarta tashiga tunani kala kala da zasu iya hallakata.

Sanin irin tsananin zafin kishi da Allah yayiwa Inayah yasa umma yaganah barinta zuwa gidansu Neesah din.

Tana barin gida batabi ta hanyar da saita bi ta anguwarsu Zaid kafin ta Isa gidansu Neesah ba Dan Bata buqatan ganin gidan ko kadan,
Jin take ta tsana gidan da anguwar gabaki daya.

Tana Isa gidansu Neesah itama Neesar na kokarin fitowa da motarta Zata gurin Inayah din.

Komawa ciki Neesah tayi da tata motar INAYAH taqarasa shigowa da tata motar sukai parking tare suka fito kusan lokaci daya.

Kallonta Neesah keyi lokacinda ta fito mota fuskarta duk babu walwala.

Cikin kulawa tace"

Hey babes,
Yaya?
Are you okay?

Wani kallo Inayah tai Mata tana qarasa Kama hannunta data miqo Mata tana cewa"

Nai Miki Kama da wadda take okay?

Kina tunanin zan Zama daidai bayan abinda idona ya ganarmin jiyan?

Ciki suka qarasa suna magana ahankali sbd rashin walwalar Inayah.

Momy na gurin dadyn Neesah Dan hakan Kai tsaye dakin Neesah suka wucewarsu.

Zama sukai Inayah na wurgi da handbag dinta da car key dinta ta kalli Neesah dake miqo Mata bowl din Candies tace"

are you for real?
Me zanyi da candies bayan 'dacin da zuciyata take ciki.

Ajiyar zuciya Neesah tayi tana Zama cikin sautin Mai mahimmanci tace"

Maganar 'dacin Rai ko baqin ciki bashine abinda yakamata ki fuskantaba,

Zaid dai wallahi Neman mata yake,
Nasha ganinsa da Amal a yanayi marasa kyan gani,
Nayi bibiyarsa Dan tabbatarwa Kuma na tabbatar Dan haka bawai maganar kishi ake ananba
Maganace ta ki nutsu kisan wanda Zaki aura da halayensa,

Bansan yaushe ya sauya yakoma hakan ba Amma a zahirance ya dade a wannan rayuwar da Amal Dan hakan maganar sauyawarsa lokaci daya zaiyi wuya....

Kasa magana Inayah tayi ta zubawa Neesah idanuwanta dasukai jajir sbd tsananin baqin ciki da zafin zuciya.

Cikin takaici da masifa tace"

Shine Baki taba fadanba?
Da banganiba da kaina ahakan Zaki Bari ayi auren nagama haukacewa a sonsa shikuma Yana can Yana kwanciya da wata macen?

Cikin damuwa Neesah tace"

Inayah Kona fada ba ganewa zakiyiba sbd idonki ya rufe akan Zaid,
Tayaya Kai tsaye zance Miki Zaid is sleeping with another woman?
Zaki yarda ne idan nafada?

Kalman "sleeping with another woman" shine yafi komai gigita dukkaninta Dan hakan Batasan lokacinda hawayen baqin ciki Mai qarfi suka fara gangaro mataba.


Sanyi jikin Neesah yayi ta matso kusada ita cikin tausasa murya tace"

Inayah wannan shine Namiji,
Duka wannan kadan ne idan baka nutsu kasamu mijin dakakeson more rayuwan aure dashi,

Inason aure nima kinsani sosai Amma Kuma bazan iya auren Wanda nakewa so irin hakan dakikewa Zaid ba sbd disappointments na cikin irin wannan son..

Gudu hawayenta suka qara sbd ba itace ta sawa kanta son Zaid ba Allah ne ya jarabceta da irin wannan son datake Masa,
Uwa uba ga zafin kishi datakeji Kamar ta hadiye zuciyarta ta mutu.

Rarrashinta Neesah tafara yi Amma Sam takasa Jin sassauci Dan hakan ta miqe tareda daukan Jakarta da key dinta tana nufar kofa.

Binta Neesah tayi tana cewa"

Babes Ina Zaki?

Cikin qunci tace"

Zanje naji daga bakinsa meyesa zaimun hakan.

No Inayah please karki Kuma zuwa gidansa sbd kada komai ya qarasa lalacewa,
Qazantar da baka ganiba tsaftane.

Bata sauraretaba tayi gaba tana cewa"

Idan bazakiba please kibarshi a iya.

Bazan iya Bari kije ke kadaiba Kuma ai dole zanbiki,
Bani key din I will drive.

Miqa Mata key din tayi tareda budewa ta shiga kafin Neesah din tashiga mazaunin driver ta tada motar suka fice daga gidan.

Tafiya suke zuwa gidan Amma babu wadda zuciyarta Bata bugawa acikinsu,
Neesah tasan tabbas sai sun samu Amal a gidan.,

INAYAH Kuma fargaba da shakkar samun mace take agidan tareda zaid sbd wannan karon bazata iya daurewaba komai zai iya faruwa Dan kuwa zuciyarta Zata iya bugawa.

Kuma ganin Zaid da wata tamkar qarasa buga zuciyarta ne zatai.

A slow Neesah ke tafiyar itama tanata adduar Allah yasa kada su tadda Zaid a gidanma gabaki daya bare wata Amal.
#MAMUH#
#AA MAJEED
#AYSHATOUH INAYAH
#MARRIAGE
#LOVE/ROMANCE



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/18, 1:57 PM] Mariyamah: *_17_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Suna Isa kofar gidan dake cikin jerin irin tsarin gine ginen turawa da basada gate sai harabar gida.

Parking Neesah tayi tana kallon motar Zaid data tabbatar da Yana gidan,

Kallon Inayah da idanuwanta sukai jajir tayi duk saitaji ranta yasake dugunzuma itama,

Allah yasani tafi kowa sanin irin son da Inayah kewa Zaid tunda itace aminiyarta,
Mahaifinta yasan tana son Zaid shiyasa dole shima yake kaunar Zaid
Hakan yasa duk suma suke kaunar zaid sbd Inayah na sonsa.

Wannan abin dayayiwa Inayah yasa taji duk ya fita ranta,

Takuma San tata tsanar Mai saukice akan wadda mahaifin Inayah zai Masa duk ranarda yasan abinda yayiwa 'yarsa.

Motar INAYAH ta bude Kai tsaye tareda nufar hanyar kofar gidan
Neesah ta fito da sauri tabi bayanta tana cewa"

Inayah give him a call atleast yasan da zuwanki,
Banason asake samun.......

Maganarsu ce ta katse daidai bude kofar da Zaid yayi zai fito Amal na bayansa riqeda hannunsa tana Masa magana Kamar wata karuwa.

Ba zato ba tsammani yagansu kofar,

Qwace hannunsa yayi da sauri daga na Amal Yana kallon Inayah dake kallonsa cikin Ido da jajayen idanuwanta.

Matsowa yayi gabanta zaiyi magana ta girgiza Masa Kai idanuwanta na kasa riqe Mata hawayen dataketa kokarin riqewa.

Cikin yanayi na tausasa harshe da damuwa yace"

Baby babu wani abinda yake faruwa anan,
She's just a friend.....

Cikin baqin cikin abinda yafada Amal ta matso gaban Inayah tana kallon kyakkyawar fuskarta datai jajir tace"

Banajin fa tana fahimtar abinda kake fada besides inaga ba illa bane idan friends sunje gidan juna hakama ke da qawarki ke kwana gidanku ya damu daya tambaya abinda ke tsakaninku ne......

Wani mahaukacin Mari Inayah ta saukewa Amal sbd baqin cikin abinda take nufin fada akanta da Neesah,
Sai alokacin ta juyo ta kalleta cikeda tsana tace"

Banajin nayi magana dake bare kiban amsa.

Kan Zaid din ta maida kallonta a tsananin qyamace take kallonsa zuciyarta na tafasa da wani irin baqin ciki tace"

Me take dashi daka zabi rayuwar shashanci da ita akaina?
Tafini kyau ne kokuwa?
Ita wacece?
Daga Ina ta fito?
Ina Zata?
Kudi tafimu ne?

Cikin Dan daga murya Zaid din ya katseta da cewa"

Inayah please duk ba wannan bane,
Qaddara ce...

Ahankali ta iya bude Baki ta furta"

Neesah muje.

Juyawa tayi ta wuce tabar gurin ko ganin gabanta batayi sosai.

Amal dataga ba'ayi balai da masifar dataso ayiba ta tafi da sauri Tasha gaban Inayah tana cewa"

Idan na fahimci maganarki ta qarshe da kyau kina nufin son kudi yasa Zaid da iyayensa suke son aurenki??

Kina tunanin mahaifinki fin nasa mahaifin yayi kome?

A wulaqance da zafin kishi da baqin ciki tace"

Mahaifina ba abun wasar dazaki iya hadawa da tarkacen haukarki bane so better watch out you bitch....

Da mamaki Zaid ya katseta da cewa"

Kece Zaki San abinda zakina fada Inayah sbd Alan haukar kishi ko zafin kanki karki zaga nawa mahaifin..

Murmushin Jin Dadi Amal tayi sbd dama tasan babu Wanda zai dauka zancen banza akan mahaifinsa Musamman Inayah dako Wasa ba'ayi da sunan mahaifinta Dan kuwa Bata dauka ko kadan.

Tsoki Mai zafi Inayah tasake batareda tasan ta sakeba zuciyarta na tsananta kuna tace"

Ba karuwarka kadaiba ko Kai na haramtawa fadar sunan mahaifina a bakinka bare hadasa da kowa.

Juyawa tayi a zafafe tabar gurin tareda nufar mota.

Neesah ce ta iya tsayawa qarasa musu da cewa"

Zaka iya jawa budurwarka kunnen daina shiga abinda Babu ruwanta.

Juyawa tayi itama tabi bayan Inayah dake Jan numfashi cikin mawuyacin hali tamkar Mai Asthma.
Da sauri ta tada motar ta nufi hanyar gidansu Inayah din tana adduar kada su sama Abbi a gida.

Suna Isa gida umma yaganah na ganinsu tasan ankuma kenan.

Dakin umman suka kwantar da ita suna faman kwantar Mata da hankali da kokarin ganin tadawo daidai.

Wata irin weak heart gareta da bakomai take iya dauka ba na tashin hankali ko quncin shiyasa tunda take duniya mahaifinta AA MAJEED Bai taba Wasa da duk abinda ya shafi 'yar tasaba,
Duk wani gata da walwalar rayuwa ya wadata Yar yasa dashi,

Sbd ita yayi gwagwarmaya da Fadi tashin rayuwa ba dare ba Rana Saida Allah yabasa arziki
Duk sbd wadatar da 'yartasane gashi lokaci 'daya wani qaton gardin banza zai lalata Masa rayuwar 'ya.

Daqyar suka samu ta iya dawowa daidai tayi shiru daga kwance hawayen baqin ciki na gangara daga idonta suna jiqa pillon datake kwance akai.

Tunda suka dawo Bata iya fadar kalma ko dayaba sai hawayen baqin cikin datake zubdawa zuciyarta na quntatuwa da rashin Zaid da zatai ta bangare daya Kuma gabaki daya neman fita ranta yakeyi sbd Sam lokaci daya take tsanar duk Wanda ya nuna rashin girmamawa ga mahaifinta.

Har Neesah ta wuce gida Inayah taqi cewa komai saidai kukanma ta daina saidai dukkanin fuskarta ta Gama yin ja da kumburar data bayyanarda zallar kukan datasha.

Bayan tafiyar Neesah umma yaganah tasata taje tayi wanka da sallah tayi kwanciyarta daki abincima taqi ci tace Bata buqatan komai.

Har dare Inayah din Bata fitoba har Abbinta yadawo baisan abinda yake faruwaba dayake latti yadawo gidan Dan hakan yasan sun Riga sunci abincinsu sun kwanta.

A cikin daren daqyar Inayah ta iya bacci sbd tsananin ciwon Kai na kuka da damuwar data cikata.

Gari na wayewa har 10 Abbin baigantaba Kuma baiga kirantaba Dan hakan Kai tsaye ya daga waya ya Kira wayarta amma yaji akashe.

Da Dan mamaki ya kalli wayar tareda ajiyewa ya miqe tsaye Kai
Tsaye ya nufi hanyar bedroom dinta.

A hanya ya hadu da umma yaganah zubbi na biyeda ita da tray a hannu jere da breakfast zaa kaiwa Inayah din.

Da mamaki ya kalli umman Yana sake maida kallonsa kan abincin da zaa kaiwa Inayar harda maganin da tunda safe umma yaganah tasa Dr farhat takawowa Inayah din Dan basuso ya sani.

A natse ya bude Baki yace"

Meyake faruwa anan?
Inayahn batada lafiya ne?
Meya sameta?

Ajiyar zuciya umman tasake sbd tasan yanzu kam Babu wani sauran boye boye Dan dama ciwon Inayah mahaifin natane yasan yanda yakeyi da ita Tasha magani.

Jiki amace tace"

Ciwon Kai ne taketa fama dashi Mai Dan tsanani,
Dr farhat takawo wannan maganin abata.

Manyan fararen idanuwansa ya zubawa umman batareda zallar mamakin dake ransa ya bayyanaba ko kadan sbd qwarewarsa gurin riqe emotions.

Kai tsaye dakin ya bude yashiga da nutsatsiyar sallama.

Jin muryar Abbinta yasata bude idanuwanta ahankali ta kallesa tanajin wata sabuwar karyewar zuciya da kuka na zuwar Mata.

Fuskarta da idanuwanta ya kalla take yasan Bata rintsaba kuka tayi Wanda Bai taba barin tayiba shida yake ubanta,
Uban waye yasaka 'yarsa a wannan halin ya furta a zuciyarsa data dauki 'daci da mamaki.

Maida kallonsa yayi kan umma data sake shiga kame kamen Inda Zata fara bayani.

Gurin Inayar ya qarasa ya tsaya akanta Yana sake kallon yanda fuskarta ta kumbura.

Zama yayi bakin gadon tun kafin yace wani Abu ta fashe da kuka tana cewa"

Abbi zaid yaci Amanata....

Ahankali yasake ajiyar zuciya sbd yasan zaa Rina ganin yanda Inayah take tsananin sonsa tun farko.

Ahankali ya Kai hannu ya zari tissue dake gefen gadon yafara share Mata wahaye Yana sake sakin ajiyar zuciya kafin ya kalleta cikin kulawa da kwantar Mata da hankali yace"

Ya Isa haka,
Tashi ki wanke fuskarki kizo kici abinci da magani zamuyi maganar daga baya.

Bata musawa Abbinta Dan hakan ta miqe tsaye sanyeda Riga da wandon bacci masu santsi ta nufi toilet.

Sunanan zaune duka ta fito ta zauna gefen abbin Ta karba abincin tafara da tea Mai zafi da umma yaganah ta dafa Mata da kanta.

Tana cikin cin abincin aka Kira wayarsa yamiqe ya fice daga dakin yabarsu.

Kallonta umma yaganah tayi tana cewa"

Inaga Inayah ki hakura da Zaid tunda dai da alama na Jin nasiha ko magana zaiyiba,
Nifa da kaina tun ranarda abin Nan yafaru kullum saina kirasa na Masa nasihu da nuni kan hanya Mai kyau Amma shine Dan baida niyar daidaituwa kullum Ina Masa nasiha yanacan Yana cigaba da aikata alfasharsa,

Tsakani da Allah da saninka dai auren mazinaci baida wata riba ko kwanciyar hankali,

Tunda baijiba Kuma baida niyar dainawa ki hakura ki cirewa zuciyarki ki dangana Allah yakawo Miki wani mijin Wanda yafisa kyawawan halaye..

Qala Inayah Bata iya cewaba saima danne 'dacin dayake taso Mata takeyi tana jinjina kanta.

Duk abinda umma yaganah ta fada akan kunnuwansa Dan hakan take ya dauki hannun abinda yake faruwa.

Fasa juyowa yayi ya juya ya komawarsa.


Gabaki daya wunin qin Kunna wayarta tayi sbd ko sunan Kiran Zaid Bata qaunar yi akan wayarta,

Tabbas tasan yanzu kam Abbinta dole zaisan komai Kuma hakan na nufin aurenta da Zaid ya Gama wargajewa Dan hakan zuciyarta tagama raunana,
Wuni tayi tana danne hawaye da baqin ciki.

Haka takuma kwana batareda Zaid ya biyota bada hakuri ba hakama koda ta kunna wayarta bataga kiransa ba Dan hakan taqara himmar kokarin fiddasa cikin ranta.

Ga Abbinta shima baice musu komaiba sai umma yaganah dayayi magana da ita ta zayyane Masa komai da komawarda Inayah takuma Yi gidansa.

Kwana biyu shiru ba Zaid ba wayarsa hakama Abbinta baice Mata komaiba duk saitabi taqarasa shiga wani hali.

Ta bangare daya basu daina shirye shiryen tafiya Nigeria ba Dan hakan takejin ko maganar aurenta da Zaid din tana Nan shiyasa wani bangaren takejin kaman zasu shirya komai ya wuce,taqi fidda rai.
*_Arewabooks for more pages_*

https://arewa-one.vercel.app/chapter?id=634d93b4bf002b318122db87

##MAMUH#
#LOVE/AYSHATOUH INAYAH
#ROMANCE/AA MAJEED



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/19, 8:19 PM] Mariyamah: *_18_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Washe gari da safe tana zaune dakinta tana waya da Dr farhat kan itama Nigeria zataje saiga zubbi da soqo.

Sai data kammala wayar ta kalla zubbin tana cewa"

Yes zubbi?

Am Mr Zaid ne yazo Yana guestroom Yana buqatan ganinki.

Kallon bakin zubbin daya isar da sakon takuma Yi kafin ta Dan jinjina Kai ahankali tace"

Ok am coming.

Juyawa zubbin tayi ta fice tana cewa"

Ok Ma.

Zubbi na fita ta rintse idanuwanta tanajin yanayinta na sauyawa zuwa damuwar abinda yakawo Zaid din Kuma.

Bude idanuwan tayi tareda miqewa tsaye ta nufi gaban mirror takuma kallon kanta.

White Alexandra chiffon top ce ajikinta Mai tsada sai sky blue Levi's ripped jeans,
Kanta qaramin farin silky scarf ne a daure,

Ko turare Bata buqatan qarawa sbd Qamshin dake tashi jikinta ahankali already Dan haka juyawa kawai tayi ta fice daga dakin ta nufi hanyar palon tana jin gabanta na faduwa kaman yaune ranar farko da Zata fara haduwa da Zaid din.

Tun kafin ta Isa take Jin muryarsa qasa qasa Yana waya Dan haka saita dakata Jin abinda yake fada a wayar..

"Nafada Miki karki Kira idan nafita daganan din zan kiraki,
Meyesa bakya ganewa ne Amal?
Abbinta ne Allah kadai yasan abinda yayiwa dad dina da duk yabi ya rude yasani zuwa Bata hakuri dole,

Nafada Miki zan kiraki idan nafita Dan haka banason damuwa,
Karki qaramun pressure akan Wanda Abbin Inayah ya dorawa dad shikuma ya Dora mun okay??

Kashe wayar yayi Yana sakin qaramin tsoki Dan Amal dinma gabaki daya tagama fita ransa Dan kuwa tsakanin jiya zuwa yau dad dinsa duk yabi yagama haukace Masa akan abinda yayiwa Inayah,

Shi kansa yasan Yana Sonta Amma Kuma bayajin zai Dora soyayyar Tasu akan burika ko ra'ayin iyayensu Wanda ita Kuma gareta da mahaifinta ganin sukeyi komai suke zasu iya samunsa sbd dukiya kokuma wani ikon dasuke gani.

Bata taba Jin Zaid yafita ranta kwata kwata ba sai yanzu din dataji irin fassarar daya yiwa mahaifinta da ita,

Wani sanyayyan numfashi ta sauke ahankali tareda qarasowa cikin palon batareda ta iya kallon fuskarsaba Dan Zata iya Masa tsana Mai girma.

Kan Luxury sofa dake gefe ta zauna tana ajiye wayarta gefenta ta waiwayo ta kallesa Kai tsaye tace"

Yes?gani ance kanason ganina?

Zuba Mata idanuwa yayi yanajin Sonta na qara Masa yawa Amma Kuma yanda mahaifinta yayi amfani da dama ya rikita nasa mahaifin akanta yasa yaji son nata na komawa fushi Dan haka shima ya Dan kame fuska sosai zaiyi magana ta katsesa da cewa"

Please Zaid idan hakuri zaka bani banajin akwai buqatan hakan sbd na Riga na yarda da matar mutum kabarinsa ne so ba buqatan mu.....

Inayah kina tunanin ahakan zamuyi auren duk abinda ya hadamu Zaki kwasa ki fadawa mahaifinki shikuma Yana yiwa nawa mahaifin barazana kokuma nuna iko akan wani abin?

Kina tunanin abinda kike samu koyaushe da kina gidanku shi Zaki samu a rayuwar aure?

Look bazan yarda Kuma bazan dauka ba rashin girmamawa ga iyayena da mahaifinki keyi sbd koba komai nawa iyayen sun girma naki mahaifin ko yayane.....

Miqewa tsaye tayi tana kallonsa da mamaki akan fuskarta tace"

Zaid Dan Allah katafi bana buqatan ganinka,
Kaje kaji da kunyar dayake dawainiya dakai na abinda kamun....

Nace Miki inajin kunyar abinda nayi ne?
Kinga alaman kunyar hakan ataredani ne?
Sbd me zanji kunya?
Sbd Ina tareda wadda tasan damuwana shine zanji kunyarki?

Nayi tunanin kece wadda yakamata tafara duba yanayin Dana shiga tun wancan lokacin Amma kika nunan Sam bazaki iya take doka ko sharadin Abbinki ba,
You can't do sex before marriage,
You can't do this sbd Abbi,
You can't do that sbd Abbi,
You can't,you can't, you can't,duk sbd Abbinki,
Abbinki Annabi ne shi da bazaa.....

Wani wawan Marin da batasan yaushe tasamu qarfin yinsaba ta sauke Masa tana Masa kallon zallar tsana Bata iya furta komaiba sai"

I hate you Zaid,
Na tsaneka sosai,
Ban tsaneka sbd kaci Amanata ba sai sbd kalamanka akan mahaifina,

Dan haka kaje dakai da wanda yaturoka ban hakuri ku daina wahalarda kanku akan Abbina sbd Abbina nada business daku ne kawai sbd Ni
Ayanzu Dana cirewa zuciyata Kai Abbi ko Inda kuke Kuma bazai sake kallaba,
So please Mr Zaid can you kindly see your self out..." Taqarasa fada tana nuna Masa hanyar kofa idanuwanta jajir.

Wani shegen murmushin takaici da baqin ciki ya sake kafin ya kalli kofar yakuma waiwayo ya kalleta yace"

Bakomai bane agurin 'ya Dan ta gada ubanta,
Mahaifinki ma ya gagara Zama da mace tayaya kema ake tunanin kiyi aure ki zauna da wani?...

Wata irin tsawa Mai qarfi umma yaganah ta sakar Masa tareda Kiran sunansa da qarfi cikin tsananin fushi da bacin rai.

Kofa ta nuna Masa tana cewa"

Zaka iya ficewa rashin 'da'an ya Isa haka.,

Juyawa yayi ya nufa kofa yanajin sautin kukan Inayah data sake na tsananin baqin ciki.

Wani sanyi da damuwa yaji aransa lokaci daya,
Shi mutum ne da Baya Bari idan anmasa saiya rama,
Dan hakan ramawace yayi akan rashin da'ar da akaiwa mahaifinsa,
Yanzu daya Rama yaji daidai Dan haka zuwa gobe yasan ta sauka zai kirata a waya ya lallabata su shirya Kuma yasan idan ta shirya dashi dole yaganah dama Abbinta su shirya dashi.

Wani irin kuka Inayah keyi tun daga qasan zuciyarta takejin zafi da ciwon abinda Zaid din yayi Mata.

Janta umma yaganah tayi sukai ciki saidai abinda basu saniba shine MAJEED na gidan yadawo sbd wasu baqinsa dazasu samesa gida yakuma ji duk abinda suke fada.

Sam har baqinsa sukazo suka tafi har dare Bai nuna musu yasan abinda yafaruba sai washe gari ya sanarda umma yaganah maganar auren Babu Dan hakan da ita da Inayah din zasu Nigeria hutu sbd Inayah ta sake karta shiga damuwa sosai.

Bayanda Abbinta ya sanar da ita da kansa ba maganar aurenta da Zaid tayi kuka sosai sbd Tasan yanzu batada ranar wani auren kuma Dan haka da akace Nigeria zasu Bata wani damuba saima matsuwa datai su tafi ko Zata samu sassaucin tsananin damuwar data shiga.

Neesah hankalinta ya tashi Jin tafiyarsu Inayah din Nigeria Dan batada qawa ko daya bare aminiya idanba Inayah ba,

Taso binsu Nigeria din Amma momynta tace ba yanzu sbd sunata kokarin ganin tafara aikine yanzu,

Itama Inayah sbd Nigeria da zasu koma yasa batai saurin fara aikinba saita dawo tukuna.

Cikin kwanaki qalilan aka Gama Shirin tafiyarsu Dan haka Abbi na wucewa Singapore suma suka wuto Nigeria itada Umma yaganah da zubbi.

Saukar dare sukai a Murtala Muhammed international airport dake Lagos.

CM Nuraddeen da kansa ne yazo daukansu daga airport cikin lafiyayyar Cclass dinsa.

Cikin kulawa sosai yake musu barka da sauka tareda gaida umma yaganah cikin girmamawa.

Inayah datake amatuqar gajiye ma cikin Dan yanayi na sanyin murya ta gaidasa kafin suka shiga mota suka Kama hanyar gidansu.

Orchid Est Ikeja GRA suka iso Lafiyayyan qaton gidansu Wanda suna can abbin ya mallakesa.

Akwai Mai aiki daya sai securities dasuka sama a gidan Dan haka CM na ajesu ya wuce gidansa Dan dare yayi sosai.

Suna tareda gajiya dan haka basu wani tsaya komaiba kowannensu ya nufi Inda ya tabbatar Nan ne dakinsa sbd yanayin gyaransa.

Bedrooms hudu ne a qasa kowanne da toilet na Inayah ne kawai keda closet room na musamman sbd sanin yanda tsarin dakinta na Australia yake.

Dakin umma yagana ma babba ne da toilet dinsa aciki Babu abinda babu na Jin Dadi da kwanciyar hankali acikinsa.

Dakinsu zubbi Yana daga baya ta hanyar backdoor na kitchen.

Shi Abbi hanyar shigowarsama daban take saidai daga palonsa zuwa nasu akwai kofar wadda ta Nan zai ringa shigowa cin abinci a dining room dake babban palon gidan.

Babu Wanda yayi yunqurin komai bayan wanka da sallah dakuma bacci dayake cin Inayah Dan Sam acan Bata doguwar tafiya irin wannan.


Wanka tayo tafito daga toilet daure da blue towel tana gyara qaramin towel dake daure akanta ta nufi gaban maduba tana goge jikinta ahankali Amma da Dan sauri sbd sallolin dake kanta.

Body mist kawai ta shafa tabar gaban madubin ta janyo daya daga jerin akwatinan datazo dasu ta bude ta dauka Riga da wando na bacci masu Dan kauri ta saka tareda jallabiyanta na sallah ta saka.

Fitowa tayi tana tafiya Kaman qaramar baby ta qwalawa zubbi Kira.

Allah yasa Salimat na kitchen tana musu warming abincin data girka musu tun dazu
Itace taji Kiran ta fito tana cewa"

Ma, zubbi na daki wanka takeyi.

A kasalance Inayah ta kalleta tace,

Dama ke zance ta kirawo,
Inane gabas??
I mean alkiblah.

Nuna Mata tayi tana cewa"

Nan Zaki kallah Ma.

Gyada Kai kawai tayi tareda juyawa ta koma tana Jan qafa.

Sallolin dake kanta tayi duka
Tana idarwa Bata tsaya adhzkar sosaiba ta miqe ta cire abayar ta fada dan bubbuga gadon alamar kakkabawa kafin ta fada tashige bargo take bacci Mai qarfi ya dauketa.

Dama kusan koina na gidan gyare yake fes daga qamshi sai sanyin AC ke tashi koina.

Umma yaganah ce dai data Gama salloli da wanka ta Dan huta kafin tasa suka Kai Mata abinci a dakinta taci Salimat ta tattara gurin kafin takuma brush ta kwanta.

Inayah kam Salimat na zuwa dakinta so daya ta dakatar da ita akan kada su sake zuwa tadata su dameta sai gobe Babu abincin da Zata ci a daren.


Washe gari qarfe goma na safe ta fito a shirye tsaf cikin Riga da wando marasa nauyi na zaman gida fuskarta fresh sbd isashen baccin data samu Mai nutsuwa.

Wayarta ce a hannunta wadda take kashe tun ranarda Zaid yayi Mata Kiran farko bayan rashin mutuncin dayazo yayi Mata har gida.

Tun a daki ta zare layin sbd Baida amfani anan.

Palon take kalla koina tana Yana tsarin gidan da komai na gidan da yayi Mata daidai da can data baro,

Salimat ce datake bin kyakkyawar surarta data Gama bayyana a shape na yanayin kayan jikinta
Cikin girmamawa da sakewa tace"

Barka da fitowa Ma.

Sai alokacin Inayah ta juyo tayi Mata kallon tsaf fuskarta a sake
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On INAYAH
avatar
amira-3-1

9 months ago

Reply

Mashallah

avatar
rilwan

8 months ago

Reply

Masha Allah

avatar
zainab-aliyu-rabiu-dal

4 months ago

Reply

mashaAllah

Please Login or Register in order to submit comment