Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da aka soya kadan.

Har qarfe Tara ta buga da mintuna Abbi Bai fitoba sbd baisan ta Yaya zaifara cewa su Inayah su shiryaba zasu bar qasar ayau datake ganin ranar Daurin aurentane.

Yarasa ta Ina zai fara,
Ta Ina zai tarbo wannan rikitaccen matsatsen yanayin.
Innalillahi wainnan ilaihrrjiun.

Gashi jama'a da dama manyan tunanensu sai kiransa akeyi ana tayasa Murna wainda bazasu samu damar zuwaba basa qasar dama wainda suna qasar uzuri bazai basu Daman halartaba.

Kansa Neman bugawa yakeyi,
Duk wannan masifar damuwarsa da tashin hankalinsa na Inayah ne da Zata shiga mummunan hali daga lokacinda aka Kuma fasa aurenta dakuma wannan mummunan labarin da har abada baya kaunar tajisa cewan bashine mahaifinta Wanda ya haifetaba,ko alaqan Jini basuda a taqaicema baisan mahaifinta da mahaifiyarta ba Dan zuciyarsama badan ya tattabar akansaba cewa uwa na iya yafe danta da bama zai yarda da cewan Hadiza ce ta Haifa Inayah ba Dan uwa Bata iya Yar da 'danta
To Amma hakan tafaru dashi sbd tasa uwar ta yafesa sbd zarginsa na aikata abinda Bai aikataba bayajin ma zai taba iya aikatawa.

Tayaya zai Bari Inayah tasan wannan 'datacciyar Gaskiar?
Baya fatan ko kadan ta 'dandana 'daci Mai kaifin gaske da ciwon uwa mahaifiyarka ta gujeka sbd wani dalilin banza Wanda Koda bakada uba tunda qaddara ta Samar da Kai baka cancanta hakanba.


****Hadiza Koda safiyar ta waye tagama fita nutsuwa da hayyacinta,
Bata ji Bata gani matuqar ba 'yarta Ayshatouh AA MAJEED yadawo Mata da itaba,
Tayi gangancin rabuwa da yarta shekarun baya Amma yanzu ko zaisa a daureta asibitin mahaukata sbd arzikinsa wlh bazata yardaba saiya Bata yarta tadawo hannunta ciki kuwa harda Koda Zata qaryata kanta agurinsa da cewa ba itace ta Haifa Abdulsamad ba idan yaso a daura auren su tafi da Inayah Adamawa suna zuwa can ta fada Gaskia a Raba auren 'yarta dai tadawo hannunta.

Wannan rubabben tunanin shedan ya qissima Mata ta tashi hankali tashe Musamman ganin lokaci na tafiya tasan rasai AA MAJEED din zai bar qasar da inayah kafin lokacin daurin aure Dan haka a rikice ta iya watsa ruwa ta kimtsa kanta sbd kada Wanda yagano halinda take ciki na firgici da tashin hankali.

Da mamaki su Haj balaraba suke kallonta lokacinda ta fito dakinta a shirye tsaf harda gilashin fuska sbd kada a gano tsananin kumburin da idanuwanta sukai
Gashi iyaye maza yanne da qannen mahaifinsu Abdulsamad din sun iso yanzu da safen daga Adamawa suna hanyar isowa gidan kafin lokacin daurin auren yaqarasa Amma ta fito tana cewa zataje karbo saqo tadawo.

Kafin Haj balaraba data saki bakin kallonta tayi mgn umma Hadizan ta wuce hannuwanta na rawa sosai keys din motar ma daqyar ta iya damqesu suka tsaya a hannunta ta Isa motar ta bude ta shige da gudu tabar gidan tana kallon agogo.

A daidai wannan lokacin Abbi yagama yanke shawarar tura Inayah da umma yaganah su fara wucewa qarfe goma Sha daya jirginsu zai tashi shikuma zai tsaya ya bawa mutanensa dasuka zozzo hakurin fashin auren batareda Inayah tasan fashin auren akaiba idan yaso Bayan kwana biyu zai samesu acan yasan yanda zai rarrasheta ya fahimtar da ita fashin auren ta wata hanyar.

Dan hakan Kai tsaye yakira umma yaganah a waya ya sanar da ita ta shirya itada Inayah akwai Inda zasu qarfe Sha daya kafin lokacin daurin aure.

Yana fadan hakan ya kashe wayarsa sbd kada tayi Masa tambayar komai.

Agogo ya kalla yaga qarfe goma da kusan rabi Dan haka ya miqe ya nufi toilet yayo wanka cikin nutsuwa.

Daure da Brown towel mai kauri a qugunsa ya fito farar fatarsa sai tsiyayar ruwan wanka takeyi so freaking fresh.

Gaban mirror ya nufa ya tsaya ahankali Dan baya Zama gaban mirror kaman mace saidai ya tsaya a tsaye yayi komai.

Lumin body moisture ya shafa tareda fesa spray din Paco Rabanne
Yayi brushing sumar kansa tareda sauran Shirin daya saba yagama ya wuce closet din tarin kayansa.
##MAMUH#
##MARRIAGE/INAYAH.


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/26, 4:02 PM] +234 813 060 4664: *_29_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Qarfe goma da minti arbain su Umma yaganah da Inayah suka fito tana shirye cikin Tsadadden red Australian lace mara nauyi dinkin fitted gown daya zauna jikinta da kyau
Shafaffen cikinta zuwa hips dinta dake Dan baje sun fito da kyau cikin kayan ta yafo 3D veil dinta kayan touches na lace din.

Zallan qamshi Mai sanyi da nutsuwa take fitarwa
Kyakkyawar fuskarta sai sheqin farin cikin dake ranta take fitarwa.

Suna fitowa harabar gidan Abbi ma na fitowa Sanye cikin wata fitinanniyar farar shadda Mai tsadar gaske da laushi.

Basu taba ganinsa da babbar rigaba sai yau shima sbd Inayah data nace abbin saiya saka Kaya masu babban Riga a aurenta sbd kada mutane da dangin mijinta su ringa cewa babanta Bai manyantaba sosai.

Qamshinsa ne ya gauraya iskar gurin suka zuba Masa Ido dukkaninsu Musamman Inayah dake washe bakin farin ciki tana cewa Abbinta na Musamman ne aduk Inda yaje.

Neesah kuwa dasu Safnah take kowaccensu taji da Abbi matsayin yayan Inayah ne ba mahaifiba Babu abinda zai hanasu aurensa.

Umma yaganah ma cikin kulawa da farin cikin ganinsa cikin Shiri da adon auren Inayah a hankali tace"

Masha Allah laquwata.
Allah yaqaro girma da 'daukaka
Yabaka tsari da kariya
Yayi maka albarka tareda kawo dawamammen farin ciki rayuwarka data zuriarka.

Amin"
Su Safnah dasuka jita suka amsa suna dauke idonsu daga kallonsa sbd grima da kwarjininsa.

Ahankali ya kalli fuskar Inayah ganin farin cikin dake tattareda kowane irin yanayinta,
Ta Bangare daya baisan tayaya zai Samar dasuba qasar zasu Bari yau.

A natse fuskarta daukeda murmushi tace"

Abbi you look handsome,
and...

Katseta yayi a nutse da cewa"

Inayah kuje karkuyi latti Inda zaa kaiku.

Kallonsa tayi a natse tana cewa

"Abbi Ina zamuje?

Dan rufe idonsa yayi ya bude tareda kallonta cikin tsananin kulawa yace,

"Idan kunje Zaki gani.

Da murmushi akan fuskarta tace"

Okay.

Umma yaganah ya kalla sukai gaisuwar safe d basuyiba tunda ba haduwa sukaiba.

Su Neesah ma da Safnah cikin girmamawa sosai suka Masa Ina kwana kafin ya kalli umma yagana a natse cikin Dan takaita magana yace"

Idan kunje komai na hannun Ahmed zai damqa miki komai
Zanzo daga baya.

Tsit suka Dan Yi da mamaki suna kallonsa duk da basu gane komaiba akan Inda zasuje sai jikin umma yagana yayi sanyi taji zuciyarta na Neman shiga wasi wasi.
Inayah ma jikin nata taji yafara sanyi take ta kalli abbin da rauni Amma batace komaiba.

Juyawa yayi yana kokarin Isa motarsa aka bude gate motar CM tashigo ko qarasa rufe gate baayiba motar Dr Abdul ta Sako Kai itama.

Umma Hadiza ce aciki Kuma tanayin parking idonta ya sauka kan Ayshatunta take taji wasu hawayen da tsananin kaunar yarta suna finciko Mata tako Ina,
Kaunace Mai tsananin gaske wadda uwa kewa 'danta Bayan tacire ran samu ko ganinsa har abada.

Hawaye takeyi sosai tana kallon Inayah din tanajin tamkar taje ta rungumota tayita kissing dinta tana fada Mata yanda take kaunarta da qaddarar datashiga akan cikinta.

Wani zafi da tirnikin bacin Rai da tashin hankali ne ya taso Mata ganin suna kokarin shiga mota tasan wlh qasar zasu Bari suna fita gidan yau bazata Kuma ganin 'yartaba Wanda haukar da Allah ya taqaita Mata lokacinda tayi danasani tashiga Neman yarta to haukar zatayi yanzu matuqar takuma rasa Ayshatouh.

Hankali tashe ta fito motar da gudu ta nufosu Inayah tana Kiran sunanta.

Dakatawa umma yaganah tafarayi tana kallon Hadizan kafin Inayah itama ta dakata suna kallonta cikeda mamaki.

Inayah kuma umman na isowa gabansu ta kalleta da kyau taga yanda idanuwanta da fuskarta sukai jajir tashin hankali bayyane kan fuskar umma Hadizan
Wani mummunan bugawa zuciyar Inayah tayi har Saida ta dafa Neesah dake gefenta.

Muryarta na rawa itada umma yagana ma data shiga zullumin abinda zasuji Dan dagani ba lafiyaba murya a hautsine sukace"

Umma Hadiza....

Kasa tambayar abinda ke faruwa sukai sbd tsoron abinda zasuji.

Kai tsaye Inayah taji wani jiri na Neman dibanta kafin tayi kokarin dafe kanta taji muryar Umma Hadiza a hargitse tana cewa"

Dan Allah kadaku tafi wlh qasar zaku Bari kuna fita,
Aurenki Inayah da Abdul bazai fas....

Inayah Bata gama jiba qafafuwanta suka yanke zuciyarta na neman bugawa ta tabbatar fasa aurenta yanzuma akai ko ake neman Yi.


Innalillahi wainnan ilaihrrjiun"
Mezan gani hakan Ni yaganah,
Innalillahi, innalillahi.

Hawayene ke kokarin gangarowa Inayah Amma tashin hankali yaqi Bari umma yaganah dasu Neesah da duk suka shiga tension din suka fara kokarin kamata sukoma ciki da ita

Umma Hadiza ma cikin tsananin tashin hankali da dimuwa ta ringa maimaita ba fasawa nace anyiba Dan Allah Inayah karki shiga wani hali,
Babu fashi aurenki da Abdulsamad,
Zaa daura zamu tafi dake adamwa zan Baki duk wata soyayyar uwa da Baki samuba,
Inayah, Inayah.

Sam Inayah Bata gane kalma daya da umman Abdul din take fada sbd zuciyarta bugawa takeyi sosai da tashin hankali da attack data samu take Dan hakan komai Bata ganewa sai rawa da jikinta keyi.

Su umma yaganah kuwa take ta fara tunanin daqyar idan umman Abdul nada lafiyar qwaqwalwa sbd duk tabi ta rude da Kiran Inayah da suna biyu.

Abbi da hankalinsa nakan CM dayazo daukansa su wuce daurin auren tare Bai lurada Hadiza ce tashigo a motar Dr Abdul ba Saida yaji salatin da umma yaganah ke qwalawa da qarfi hankalinsu duk yakoma Kai cikeda mamaki da zafin zuciya Mai qarfi ya kalli umma Hadiza Yana kallon 'yarsa dake Neman siqewa cikin tashin hankali numfashinta na neman gagararta.

Cikin bacin Rai Mai qarfi ya qaraso gurin tareda kallon umma yaganah yace"

Ku kaita ciki Dr farhat ta dubata da sauri.

Kan umma Hadiza dake kokarin binsu hankali tashe ya maida kallonsa idanuwansa na Neman sauyawa yace"

Ni Zaki sama da duk abinda kikazo dashi,
Me kika fadawa Inayah yasata cikin wannan halin?

Ganin su umma yaganah Basu qarasa shigewa da Inayah ba yasashi juyawa tabiyo bayansa tana cewa"

Dan girman Allah da manzansa kaban 'yata,
Ka sanar da ita nice mahaifiyarta,
Dan Allah kada ka cutatar da uwar dake cikin qunci tsawon shekaru ta hanyar Hana Mata 'yarta....

Babban palonsa suka shigo ta tsaya gabansa idanuwanta na zubda hawaye sosai cikin mawuyacin hali tafara rokonsa akan ya sanar da Inayah itace mahaifiyarta.

Mamakine ya Kama CM dake tareda A A MAJEED din tako Ina.

Idan ya fahimta Kuma yagane wannan matar Inayah take Kiran 'yartace.

Itace mahaifiyar Inayah?

MAJEED da idanuwansa ke bayyanarda tsananin bacin ransa da fushinsa ya kalla yasan yau kam ransa yakai kololuwar baci tunda ya bayyanarda fushinsa.

Bai iya cewa umma Hadiza komaiba sbd baimasan mezai fada mataba,
Da alama tanada ciwon Kai Dan hakan tako Ina lalata Masa Al'amura zatai.

Cikin kosawa da ganinta gabansa ya bude Baki a gundure yace.

"Me kika fadawa Inayah da har kika data cikin wancan halin datake ciki?
Idan kin sanar da itane matsayinki a gunta kinyi babban kuskuren da....

Cikin sauri da bayyanarda gaskiyarta ta katsesa da cewa,

"Banfada Mata komaiba
Maganar aurenta da Abdul kawai nake fada musu.

Wani irin rufe Ido yayi ya bude cikin baqin ciki da takaici yace"

Kinsan shima hakan matsalar da Zaki haifar mata?
Kinsan halinda Zata iya Shiga akan hakan?
Meysa zakiyi kutse acikin Al'amarin da bakisan Yaya yake tafiyaba?

Numfashi Mai zafi ya sauke tareda fitarda ajiyar zuciya Dan bazai iya wannan tashin hankalinba yanzu.
dauke kallonsa daga kanta yayi a natse yace"

Idan harkina kaunarta a matsayin uwa kaman yanda kika fada kibarta taci gaba da rayuwarta batareda kin dandana Mata 'dacin rashin karbuwa daga uwar data haifeta kokuma dacin hanyar da aka samar da ita.

Maganarsa ta qarshe tayi mummunan girgiza,
Kenan shima daukan yake ta hanyar banza ta samu Inayah tunda yaga ta gudu tabarta?

Wasu hawayen baqin ciki Mai tsanani ne suka gangaro Mata ta dago da jajayen idanuwanta ta kallesa zuciyarta na quna da bacin Rai tace"

Na tsaya rokonkane ka bayyanarwa 'yata nice na haifeta sbd nabaka haqqinka amatsayin Wanda ya reneta da Amana ba cutatarwa bawai Dan narasa damata ta uwa agaretaba.

Kanason nuna dukiya ka rabani da 'yata rabuwar har abada Amma hakan bazai taba karbuwaba gurina.

Wlh bazan yardaba Sharia Zata karbamun 'yata tadawo hannuna.

Mamaki tafara basa ta yanda take iya furta kalamai batareda taji kunyar kantaba na abinda ta aikatawa 'yar a baya harma dashi.

Idan tana maganar qarfin ikone
To zai nuna Mata qarfin iko akan Inayah.

Cikin sautin bayyanarda gajiya da lamarinta yace"

Wannan shine Karo na qarshe da Zaki iya zuwa gidana ko kusantar daya daga cikin iyalin gidana,
Zaki iya tafiya.

Kallon baqin ciki da damuwa lokaci daya take Masa tace"

Zantafi Amma kasani nice uwa dana Rena cikin Inayah nakuma haifeta har abada babu wani ko sunan dazai sauya mun matsayi akanta,
Nice nafi kowa cikakkiyar dama da iko akanta,

Kaikuma damarka da ikonka akan Inayah ya tsayane a matsayin mariki Kuma zai tsaya ahakan ne har abada.

'ya mace ce duk iko da isar da zaka nuna akanta saitabarka har abada sbd aure zatayi take gidan wani Kuma a qarqashinsa Dan hakan idan kafi qarfin hukuma bazakafi na shari'a ba,

Sharia Zata dauke inayah daga hannunka tabani 'yata,

Idanma shariar kafita ikone zamuga wannan sbd duk ikonka akanta bazaka taba aurentaba Dan kuwa aurene kawai zai riqe 'ya mace aguri wani ikon ya kasa dauketa dauketa
Kuma da yardar Allah Inayah bazata rufa wata a hannunkaba saina karba Yana Koda ta hanyar kawo Mata wani mijin auren ne.

Rintse idanuwansa yayi cikin takaici da baqin cikin ganin Hadiza agabansa.

Duk shekarun mace hankalinta da tunaninta na banza ne lokuta da dama,
Sam kansu toshewa yakeyi hat basusan me suke fadaba.

Idan Hadiza na tunani haryanzu akan shari'a Zata karba Mata Inayah a hannunsa to zai sakata a spot dinda ko shariar bazata iya dauke inayah daga hannunsaba a gurin.

Bai iya kallontaba sbd siqewa kai tsaye yace.

Kije Ina jiran shariar.

A fusace da baqin ciki ta juya tana hawaye sbd ba haka tasoba son tayi ya amince ya hadata da 'yarta idan Tai Masa barazana da sharia sbd tasan bazai taba son duniya tasan Inayah ba 'yarsa bace.

CM da kansa yayi matuqar daurewa da daukan zafi kusan yagama gano kan zancen shine Inayah dai ba Amininsa neba ya haifeta Kuma wannan matar itace mahaifiyar tata.

Baisan ya zancen yafaruba Amma tabbas a wannan tsukakken yanayin yasan akwai matsala Babba matuqar wannan Al'amarin zai shafa daurin auren yau.

Agogo A MAJEED ya kalla yaga Sha daya da rabi harta fara wucwa.

Bai iya cewa Amininsa komaiba yace su tafi kawai.

Shima CM tunda ba qaramin yaro bane yasan yanzu ba lokacinda zai tsaya tambayar MAJEED din meyake faruwa bane saidai idan an natsa zafi da dacin ransa ya sauka.

Suna fitowa Kai tsaye yabawa Bosco odar kada akuma barin motar Abdulsamad tashigo gidansa matuqar bashineba aciki.

Kai tsaye babban masallacin dake kusada gidan iyayen CM suka nufa Inda anan ne zaai daurin auren dama.

Mutane ne tako Ina sun cika anguwar ga securities da jamiaan tsaro kusan tako Ina sbd akwai manyan mutanensu dasun iso tuni Dan mintuna goma Sha takwas suka rage ga daurin auren.

Wani irin zafi da 'dacin zuciya yakeji ganin tarin jama'ar dasukazo Dan sheda daurin auren ga dangin Abdul ma da dama sun iso shi kansa Abdulsamad din ya iso gurin cikin shigar alfarma ta angon dake cikin tsananin farin ciki.

Qarfe goma Sha biyu daidai aka nutsu aka fara daurin auren Wanda CM ne da kansa yayi wakilcin Amarya mahaifinsa Alhaji babbah yayi wakilcin Ango sauyin daya faru tsananinsu take agurin.

Kafin iyayen Abdulsamad su Ankara sukaji ana shelar an daura auren ABDULMAJEED ABDALLAH da INAYAH A MAJEED.
#MAMUH#
#AFADA ALKHAIRI KO AYI SHIRU/#MASU YI DANI A BAYANA.



*_ZAFAFA BIYAR_*

*_INAYAH_*
_Mamuhgee_

*_GURBIN IDO_*
_Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/26, 4:03 PM] +234 813 060 4664: *_30_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Kusan da yawan jama'ar gurin Basu fahimci wane ABDULMAJEED din ake nufiba sai Amin kawai suke amsawa da ita suna qarawa da adduar zaman lafiya da albarkar aure sbd sunan Abdul din da aka ambata cikin sunan basu wani bambamceba tunda dai kowa yasan sunan Ango Abdul.

Iyayen Abdulsamad Wakilansa sune suka saki Ido da Baki cikin zallar mamaki da firgici Jin andaura da wani Abdul din daba nasuba Dan Babu Wanda ya tsaya kawo wani rubabben tunanin AA MAJEED mahaifinta ake nufi.

Shi kansa Abdulsamad kasa tantance meyake faruwa yayi saiyafara tunanin ko matsalar fadan sunan aka samu Mai fadar be kila ya rude ya fada sunan mahaifin Inayah a matsayin uba Kuma yadawo ya fada amatsayin Miki Wanda aka daura auren dashi.

Jin zuciyarsa dai takasa yarda sai tsinkewa data farayi yasashi kokarin baro Inda yake Dan zuwa gaban wakilan daurin auren yaji wane rudadden ne Mai sanarwar dazai saka kansa kuncewa da zancensa.

Kusan dai jama'a tsakani da Allah duk Basu ganeba idan ba wainda suke Yan uwan Abdulsamad ba sbd suka Sarai sunji ba sunan angonsu aka fadaba
Sauran jama'a da Basu ganeba tunda ba hankali mutane ke badawa sosaiba gurin daurin aure sai an daura zu amsa da Amin da fatan Alkhairi su tafi Dan haka aka ringa gaggaisawa ana Allah sanya Alkhairi ana neman fara watsewa.

Ciki mamaki Mai tsanani da kokarin danne bacin Rai yayan Marigayi salisu ya kalli CM da Alhaji babbah kafin ya maida kallonsa kan AA yace"

Alhaji MAJEED mufa bamu gane abinda yake faruwaba anan,
Auren da zaa daura biyu ne Daman kokuwa dai Wanda zamu daura dinne aka daura da wani 'dan ba namuba?
Dan idan naji daidai sunan yarinyar dai shine wadda zaa daurawa danmu da ita.

Duk Inda damuwa da 'dacin Rai Dana zuciya suke sune a dabaibaye da A MAJEED,
Bai taba samun kansa a yanayi Mai 'daci da qaqa nikayiba irin wannan Rana,
Ko a wancan lokacin daya hadu da qaddarar samun Inayah baishiga damuwa da quncin dayake cikiba yanzu.

Me zaiyi da auren 'yarsa ta kansa?
Wace mummunar masifa Hadiza ta sakasa daya qare qarshe a auren Inayah 'yarsa??

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun,
Yau shima yahadu da qaddarar Sharrin shedan Dana zafi da yanke hukunci cikin fushi.

Duniyama idan taji shine ya aura 'yarsa zai anyi Allah wadai da tunaninsa.

Gashi garin yanke hukunci kada Hadiza ta ra'bi Inayah har Inayah tasan bashine mahaifinta ba yaje cikin fushi da bacin Rai yayi abinda ba iya Inayah kadaiba da bayason ta taba sanin bashine ya haifetaba duniyama kowa zai sani yanzu Wanda harga Allah yaso riqeta amatsayin ya har abada batareda kowane Dan Adam yasan bashine ya haifetaba sbd daga lokacinda mahaifiyarsa datafi kowa saninsa da tarbiyarsa ta tuhumesa tareda yarda da zai iya aikata Zina harma ya Haihu a hanyar Zina yasaka a ransa ya karbi Inayah amatsayin 'ya dabazai taba barin wani yasan bashine ya haifetaba ciki kuwa harda mahaifiyarsa saigashi Rana tsaka Hadiza ta sakasa a mummunan tarko.

Hadiza itace masifar rayuwarsa yau ya tabbatarda hakan sbd akaro na biyu takuma sakasa masifar da kusan tafi ta baya yaqare da rataya igiyoyinsa na aure a wuyan 'yarsa baisan wane mummunan Al'amarin Zata Kuma kawo masaba a gaba Dan yasa zaifi wainnan zauta Kai da qwaqwalwa.

CM ne yayi saurin kallonsu Alhaji buhari ganin ransu yafara baci sosai sunason Jin bayanin abinda yake faruwa Dan haryanzu sunkasa yarda da auren matar 'dansu aka daura da wani sbd har lokacin Babu Wanda yakawo da AA MAJEED aka daura auren tunda ba abune Mai yiyuwaba uba ya aura 'yarsa Dan hakan kaf gurin Babu Wanda yakawo ABDULMAJEED mahaifinta ake nufi suma su CM da Alhaji babbah sunqi barinma agane wane ABDULMAJEED Dadi da qari kusan duniya da AA MAJEED tasansa bada cikakken sunansaba ABDULMAJEED ABDALLAH.

Cikin qarfin hali Abbin yataso Yana sallama da mutanensa dake wucewa suna Masa Allah ya sanyawa auren 'yarsa albarka Yana amsawa da amin.

Kaurewa da gurin yayi da jiniyar motocin 'yan sanda da civil defense ga yawan jama'a kowa nata kokarin miqa barkarsa ya wuce shiya taimakawa su CM gurin Jan su Alhaji buhari zuwa cikin gida palon Alhaji babbah Wanda shine da kansa ya iya fara tankwafarsu sbd fadan tozarci dasukagani qarara dasuka fara yi.

Alhaji buhari ne mai iya dan danne tsananin bacin ran dasuke ciki su Alhaji kabiru 'yan Nan Hadiza kuwa kasa dannewa sukai suka fara zuba masifar tashin hankali Dan duk Inda ake wulaqantawa an wulaqantasu ankuma tozartasu sun debo jiki tun daga adamawa sunzo Lagos daurin aure ace suna zaune suna kallo kaman wasu gumaka andaurawa amaryar aure da wani koma Dan uban waye ai Basu cancanta wannan tozarcinba.

Abdulsamad a rikice cikin tashin hankalin daya zaburo Masa tako Ina ya ringa kutsa jama'a Yana neman iyayensa maza dasune wakilan Amma Bai gansuba Dan haka ba Shiri ya zare hular kansa Yana Jin akwai gagarumar matsala Mai tsananin girman gaske kuwa.

Saida mutane suka rake sosai aka fara Ankara da abinda yafaru ganin rudewa da tashin hankali da Abdulsamad yake ciki da yawa wainda suka dauka sune basuji sunan daidaiba suka fahimci cewan daidai sukaji Ashe auren ne dai bada Dr Abdulsamad aka dauraba.

Take kurar hayaniya tafara kaurewa daga gurin
Ganin Abdulsamad na Neman zarewa yasa Abbi daya Gama sallamar baqinsa ya Kama hannunsa sukai cikin babban gidan na Alhaji babbah.

Qanin CM Professor Ibrahim shine ya tsaya yaqarasa sallamar sauran jama'ar aka watse wasu nata sake sawa auren albarka wasu Kuma na shiga mamaki da son Jin yanda wannan mugun Al'amarin yafaru hakama wasu take suka ringa maimaitawa wainda basujiba cewan sunan fa AA MAJEED ne aka daura dashi.
Mamaki da firgici wasu suka Kuma shiga Jin sunan Wanda aka daura dashi din aikuwa take tun anan suka fara shigar da gulmar Internet.

An watse tsaf ba kowa Dan hakan Alhaji babbah ya kalli su Alhaji buhari dake cikin mummunan yanayi na bacin Rai da fushi.

Cikin sanyi da taushin murya ga Wanda baa kyautawaba yace"

Alhaji buhari kuyi hakuri nasan baa kyauta mukuba tako Ina Musamman da baa sanar daku komaiba ko fahimtar daku komaiba Saida kukazo cikin baynar jama'a hakan tafaru.

Dr Abdulsamad dake tsiyayar wasu ruwan zufan tashin hankali da fita hayyaci ya kalla duk saiyaji jikinsa yayi sanyi da tausayin Abdulsamad din sbd duk Wanda ya kallesa yasan yana tsananin son Inayah so Mai tsanani,

Tayaya Za'a kallesa ace Masa uwarsu daya,
Uban ne kawai Basu saniba ko dayane tunda A MAJEED cewa yayi uwar kawai yasani itama a bisaga qaddara.

Shi kansa Dr Abdul idanuwansa duka da hankalinsa suna kan Alhaji babbah sbd ya fahimci agurinsa zasuji abinda suke buqatan ji Wanda zuciyarsa ayau harbawar datake yasan ta wuce kowane irin tsari da akeson zuciyar Dan Adam ta buga.

Babu wani yaren dazai gane ayanzu idanba na maganar aurensa da Inayah bane.

Dan jinjina maganar dake bakinsa Alhaji babbah yiyi tareda dauke idanuwansa daga Abdul ya maida kan su Alhaji buhari dasuke manya zasu fahimtarsa a natse yace"

Ita wannan yarinya Inayah wadda mahaifiyar Abdulsamad ke Kira da Ayshatouh 'yar mahaifiyar Abdulsamad ce wadda ta jima da Bata tun jarinta Wanda A jiyan bayan haduwar mahaifin Inayah Wanda yanzu zance mijinta da ita mahaifiyar tasa suka tabbatarda Dr Abdulsamad da Inayah uwa dayace ta haifesu,

Dr Abdulsamad da Inayah uwarsu daya Kuma kaman yanda duk muka sani Babu aure tsakaninsu,

Sauyin Wanda aka daura dashi Kuma wannan nine Nan na tayasa yanke wannan hukuncin sbd kaman barazana da ita mahaifiyar yarinyar takeson tayiwa MAJEED Dan hakan muka yanke hukuncin ya aureta.

Dan haka a taqaice ABDULMAJEED shine ya aura AYSHATOUH INAYAH,
Shine mijinta ayanzu,
Sauran bayanin Inda ita mahaifiyar Dr ta samo yarinyar har suka Zama uwa daya da Dr wannan saidai aji daga gareta.

Wani mummunan shock da matsiyacin zufane ya fesowa Alhaji kabiru zuciyarsa na harbawa da mamaki ya juya ya kalli malam Umar Dan uwansa Wanda harya fisa jiqewa jagab da zufa.

Alhaji buhari daya Gama samun qullewar Kai da mamaki da Yar rudewa yace'

Inayah kuma Yar Hadiza?
Tayaya?
Garin Yaya?
Yaushe?

Shaqewa muryar Alhaji kabiru tayi a Rikice murya na yankewa yace"

Inayah itace AYSHATOUH????
'yar da Hadiza ta Haifa ranarda mahaifiyarmu ta rasu??

Da tashin hankali malam Umar ya karba da cewa"

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun
Tabbas Hadiza ta haifi 'ya takuma saka Mata Ayshatouh.,
Idan har ya tabbatarda Hadiza ce dimun wadda tabar Masa 'ya to tabbas kuwa wannan 'yar ta Hadiza ce halak malak sbd ranarda ta haifeta ranar tabar gida.

Sai alokacin zufa ta karyowa Alhaji buhari Jin dai ta tabbata Hadiza haihuwa tayi ba aure bayan rasuwar salisu.

Da sauri malam Umar daya fahimci tunanin dake zuciyar Alhaji buharin yace"

'yar Hadiza 'yar halak ce
'yar sunna Dan kuwa cikinda salisu yabarta dashine muma sai daga baya muka Ankara da hakan Dan haka 'ya 'yar halak ce
Uwarsu daya ubansu daya da Abdulsamad gashinan zaun....." Ya qarasa fada Yana waiwayawa Inda Abdulsamad ke zaune sai kawai sukagansa zube baya numfashi da alama ya jima da sumewa Basu saniba sbd tashin hankalin da kowa yake ciki.

Arikice Alhaji buhari yayi kansa shida malam Umar suna Kiran sunansa Amma da alama ba sumar kadai yayiba kaman harda attack yasamu.

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun""Alhaji buhari yake fada Yana kamo Abdulsamad din da qarfinsa
Ba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On INAYAH
avatar
amira-3-1

9 months ago

Reply

Mashallah

avatar
rilwan

8 months ago

Reply

Masha Allah

avatar
zainab-aliyu-rabiu-dal

4 months ago

Reply

mashaAllah

Please Login or Register in order to submit comment