Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*LADIDIN KAUYE*



_funny & love story._




*Labari mai ban dariya haɗi da faɗa karwa*


*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*_


*AND NOW*


*LADIDIN K'AUYE*


~MALLAKAR~ ZAINAB HABIB (mom Islam ).

*GODIYA* ina ƙara miƙa godiya ta ga Allah maɗaukakin sarki Wanda yabani ikon sake rubuto muku wanan ƙayatacen labarin cikin hikimar sa da iyawarsa Allah nagode maka.


*GARGƊi*_wanan labarin ƙir ƙirane ban yishi dan wani ko wata ba nayi shine dan ni shaɗii da ban dariya in yazo dai dai da rayuwarki /ratuwarka to hasa shene kawai._



🤏ban yarda wani ko wata su juyamin labari ba duk Wanda yayi yinkurin yin hakan to shida rabil izzati🤙.

08141799224

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




*EPISODE 1&2.*


📖____Yarinya ce ƴar kimanin shekara goma sha biyu da aihuwa sanye take da rigar atamfa da wandon yadi.

Tafiya takeyi tana waƙa da zabgegiyar bulala a hannun ta me rake ta hango da gudu ta ƙarasa gurinshi yana ganin ta ya washe jajayen haƙoransa kana yace "LADIDI daga ina kika fito haka"¿. Ɗaukar rake ƴan hamsin tayi kana ta ce "daga gida mana".

Ganin LADIDI ta kusa shanye rakeb hannunta tana shirin ɗaukar wani ido ya zare mata kana yace "ke baki da hankali ne kin ɗauki raken hamsin banyi miki magana ba yanzu kuma zaki kuma ɗaukar wani". LADIDI dake ta shan raken ta yawu nazuba a bakinta tace "wlh ko kabani raken in daɗa ko kuwa yanzu kaci najaki".
mai raken da aƙalla yayi sa,an baban ta dubanta yayi kana yace "yarinya ki wuce kitafi sabgar ki , LADIDI daketa juya bulala tana dariya tana kallonsa.

mai rake ne yace "yarinya ni natafi kiyimun addu,a yau inyi ciniki LADIDI ce tadubi mai rake tace "karka damu".

Mai rake ya juya zeja baron rakenshi yaji saukar bulala dur ƙusawa yayi yana ihu yana sosawa juyawa yayi yaga babu LADIDI babu samatan ta .


Gudu takeyi har ta isa gidansu , gidane ma dai daici kewaye yake da katangar kara.
YADIKKO na surfen dawa ko sallama batayi ba tashige ɗakin data ke kwana tarufe ƙofa YADIKKO tarasa abinda zatace ta girgiza kai ta ɗaga hanu tana rokon Allah yashir yamata LADIDI.

Kayan wasanta ta ɗibo kai tsaye gurin bishiyar kukar data mamayi filin tsakar gidan tanufa YADIKKO tana wanke dawar data surfa ta dubi Ladidi kana tace "bana ce ki dena zuwa gurin bishiyar nan ba¿.
LADIDI ce ta turo baki tana ƙananun maganganu YADIKKO ce ta riƙe haɓa kana tace "to kodai kin kwaso aljanu ne tunda kin nace da zuwa gindin kuka ita dai LADIDI bata kula YADIKKON ba taci gaba da wasanta .





YADIKKO ce take ta ƙwalawa Ladidi kira tasowa tayi tana bubuga kafa nera goma ta miƙawa LADIDI kana tace "ki ɗauki waccan dawar ki kai ingin Shafi,u kice ya miki yanzu .

Ɗauko mayafinta tayi ta ɗaure a kwan kwasonta kana ta ɗora markaɗen a kai .


Tana cikin tafiya taci karo da me awara ajiye nikan tayi kana ta kirashi tunda yaron ya tabbatar LADIDI ce me kiran har ze kwasa da gudu ta riƙoshi kana tace "ina zaka dan uwarka kasanni kuwa¿".



Dur ƙusawa yaron yayi kana yace "LADIDI kiyi hakuri talle mai ƙeya tayi kana tace "nawa nawa awaran¿

"Biyu biyar yaron yace saboda a tsorace yake Ladidi ce ta haɗa guda huɗu a guri ɗaya tacewa yaron naci biyu ƙara ɗibo huɗu takumayi tace naci na kuɗina saura ala koro nan yaron yadu beta yace "wlh LADIDI goggo na ta hanani LADIDI ce ta buge mai baki ta ɗiibi biyu.

Seda yaron yayi nisa sanan yace LADIDI bogaza Allah ya isa LADIDI tayi ƙwafa tasan ko ba komai taci awarar goma a talatin.

Nikan ta ɗauka tana zuwa dai dai ingin ɗin Shafi,u tace nakawo niƙa Shafi,u daketa nikan shi be kulata ba magana taƙarayi amma yaƙi kulata ramin cinnaka tagani kusada ƙafar shi ɗaya ta ɗauka tasamai a takalmin ƙafarshi takuma ɗaukar ɗaya tasamai a gefen rigarshi ragowar ɗayan tasa mai gurin da taga ya yage a rigar komawa gefe tayi kana tahau waƙe waƙenta .

Shafi,u ne yafara jin cizo ta kafa ze sosa yaji cizo ta kanshi yakai hannu ze Sosa kan yakuma ji ta jikinshi a she cinnaka har cikin wandon shi ya shige da gudu ya fice a ɗakin niƙan yana ihu LADIDI babu abin da takeyi in banda dariya shafi,u ne yayi hanyar gidansu yaje tsallaka murhun girkin gidan yataka tsakiyar murhun a she da wuta kwanciya yayi yana birgima an rasa meke damunshi sedai yasosa nan ya Sosa can LADIDI kuwa tunda Shafi,u yafice take gurin ingin niƙan dama ta iya tana gama niƙan ta daura a kanta tana tafiya tana dariya tana faɗin "dama nakashe goman YADIKKO gashi nasami niƙa a sabill.


Tana tafiya taci karo da wani me rogo dafaffe tsareshi tayi kana tasauke nikan ta dubeshi tace "mai rogo akwai ala koro¿." mai rogon nne ya galla mata harara yace "dan uwarki wanne kora dazan baki ala koro LADIDI ce tazaro ido kana tace "uwata fa kazaga mai rogo ne yace me kika isa kiyi jibeki kamar buhun alabo .

Be Ankara ba LADIDI ta ɓarar da tiran rogon kasa takwashi wanda zata kwasa tazo guduwa mai rogo ya riƙota faɗawa tayi kanshi tahau ruwan cikin shi tadinga kai mai duka baji ba gan.


Hakuri yashiga bata ɗagashi tayi kana ta ce "baka ganni yar ƙarama ba shine kakeson cin uwata a banza me rogo ne ya miƙowa LADIDI na ashirin ya zura da gudu .


Cigaba tayi da tafiyar ta har ta isa gida YADIKKO ce tace "LADIDI baky ajin faɗan da nake yi miki ko ¿.

sauke nikan tayi kana tace "YADIKKO zansha ruwa.

YADIKKO dake ɓarar gyaɗa tace "wlh ke da yar kishi yace kin shiga uku LADIDI ce kamar an tsikareta ta zabura a guje tafice waje.


Ƙarar mota ,
taji gurin masu motar tanufa ɗaya daga cikin su ne yadubi Ladidi kana yace "baiwar Allah tambaya muke yi" Murguɗa musu baki tayi kana tace "nifa banason kinin bibi zakayi magana kana wani tsari ɗaya daga cikin motar ne yace kiyi hakuri yammata dama muna neman mallam Adamu ne.

ta6e baki tayi kana tace "nasan gidan amma saidai inzaku sani acikin wanan akori kurar.

Wani daga cikin motar da tunda ɗayan yafara magana shi beyi ba leƙowa yayi ta cikin motar kana ya ce "ubanwa kika gani a akori kura¿.


Murguɗa mai baki tayi kana tace "karka ƙara zagina na kusa da shine yace Humaid mu lallaɓata ta raka mu .


Buɗe mata murfin motar Humaid ɗin yayi shigowarta keda wuya sukaji motar ta game da wari kamar anyi tusa Jalal ne yace "Humaid bakaji wani wari ba dede lokacin da warin ya iso hancin Humaid sun rasa meke wari a motar LADIDI ce ta dube su tace sewani toshe toshen hanci kukeyi sekace wasu malaman.

Duban tsafta Humaid ne ya ce wlh ga meyin warin nan hatta bakin ta wari yakeyi LADIDI data tabbatar da ita akeyi ciro alurar ɗinkin hannu tayi kana ta waiga taga Humaid ɗin yadena kallonta murmushi tayi kana tayi gefe da hannun ta sokawa Humaid alurar ihu Humaid yakeyi ba k'a kau tawa Jalal ne yafaka motar kana yazo gurin Humaid ɗin dake faman ihu LADIDI ce ta dubeshi kana tace "meyasa meka ne ɗan gayu¿

cikin su babu wanda ya kulata bare su waigo ta Humaid ne yace ja motar Jalal muyi sauri mu isa gidan .


Sun zo dai dai k'ofar gidan LADIDI tace "to munzo seku fito Humaid dake ɗin gisa ƙafarsa yace "to ai seki koma tun da kin rako mu. Zaro ido waje tayi kana a zuciyarta tace lallai wannan besan ko wacece LADIDI ba .


Duban ƙafar Humaid ɗin LADIDI tayi kana ta fashe da dariya Humaid da babu halin gudu ya dura mata zagi Jalal ne yace "tunda ta nuna mana ƙofar gidan to muje ka kyale yarinyar nan .


Hango wata zabge giyar sanda tayi ta ɗauka kana ta gyara bakinta seda tabari Humaid yazo dede saitin shiga gidan ta zula mai a kafar da tayimai allura zubewa yayi a ƙasa yana ihu da gudu ta ƙasa...

Malam adamu ne yaj ihu kuma na babban mutum da sauri ya ƙaraso Jalal ne yace "barka malam , malam adamu ne yace a,a wana ke gani kamar yan birni¿

Jalal ne yace "malam mune wata yarinya ce tara komu gidanka gashi ta bugawa Humaid sanda a ƙafa ta gudu ,malam yajin jina zancen kana yace "nasan ba wata bace illa LADIDI wannan aikin seita .


Humaid ne yayi ƙarfin halin magana yace "Jalal kaje kane momin yarin yar nan senaga waye ubananta.
Malam adamu ne yace "wlh gara ka hakura saboda wanan yarinyar ana tunanin tana da aljanu ......✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽.





*_~MOM ISLAM CE✍🏽.~_*

*LADIDIN ƘAUYE.*



_funny & love story._

*Labari mai ban dariya haɗi da faɗa karwa*


*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:ZAINABU ABU*


*_AND NOW *_

*LADIDIN ƘAUYE.*



*BIMILLAHEER RAHMANIR RAHEEM.*


*EPISODE 3&4.*


___malam adamu ne yayi musu nuni dasu ƙarasa cikin gidan inna Hauwa matar malam Adamu ta na ganin su ta shiga yi musu sanu da zuwa d'akin malam Adamu suka wuce kai tsaye Humaid ne yayi rau rau da ido kamar me shirin yin kuka yace "Jalal please help me jalal da shima hanka linshi ya fara tashi yace "sorry brother anjima ka d'an zakaji jikin naka ya koma normal Humaid ne a ts,wace ,ya dubi Jalal kana yace "baka san azabar da nake ji bane shi yasa .

Jalal ne ya mik'e jiki babu k'wari yanufi gurin da inna hauwa take tambayar ta yashiga yi akwai asibiti anan kusa¿ inna hauwa dake dama fura da nono ta ce "eh akwai amma fa akwai tafiya sosai Jalal ne yace indai akwai barin yiwa Humaid magana mutafi inna hauwa ce ta kwala wa malam adamu kira shigowa yayi d'auke da ledar lemu da ayaba da kankana ajiye ledar yayi ganin yanayin Jalal malam Adamu ne ya ce har yazu jikin humidun ne eh Jalal ya ce asibiti nakeso mu kaishi ko aliura ayi mai .

Shiga d'akin sukayi suka temaka mai ya mike suka sa shi a mota seda suka yi tafiya me nisa kana suka shiga asbitin .

Wani likita ne yazo gurin malam Adamu hannu ya mik'awa malam Adamu suka gaisa kana likitan yace "baba waye babu lpy ¿.
malam Adamu ne ya nuna Humaid da zazza6i yarufeshi ri rik'eshi sukayi yanuna musu d'akin kwantar da marasa lpy ruwa aka fara samai kana aka yimai allurori bacci ne ya d'auke shi me nauyi Jalal ne yaji cikin shi na kukan yunwa mik'ewa tsaye ,yayi kana yace mala barin d'an fita yanzu zan dawo.

Malam Adamu ne yace ina kuma zaka¿ Jalal ne ya ce wlh am feeling Hungary malam Adamu ne ya zaro ido kana yace naji kamar kace kwan giri Jalal ne ya tun tsure da ,dariya kana yace .

"Cewa nayi ina jin yunwa malam Adamu ne ya ce au to ko in koma gida ne in taho muku da fura da nono ¿".

Jalal ne yace a,a ai dazamu taho naga masu saida abinci malam Adamu ne yayi mai Allah ya tsare Humaid ne ya farka d'auke da salati a bakin shi.

Malam Adamu ne yace sanu Humaidu,, humai ne ya dubi malam Adamu kana "yace yauwa sannu ina Jalal yayi ?".

Malam Adamu ne yace Jalal yaje siyo abinci yanzu ze dawo .

Likitan d'azu ne yashi go d'auke ta ,takaddar salama mik'awa malam Adamu yayi kana ya tambayi Humaid ya,,ya kejin jikin nashi Humaid ne ya ce wlh yanzu babu inda yake ciwo hamdala malam Adamu yayi .

Jalal ne yashigo da ba bbar leda a hannun shi kifi yasiyo soyayye da kuma kaza guda biyu gasassu malam Adamu ne yace duk wanan kayan ina za,a kai su lemun kewalba ya mik'awa Humaid da kifi domin Humaid d'in ma,abocin son kifi ne jalal ne ya d'auke kaza guda daya ,ya mik'awa malam Adamu .


Malam Adamu ne ya e a a ni bazan ci ba ,dole dai seda ya kar6a tukun ya d'an sha lemun ya barsu a gurin ya nufi masalaci.

Suma bayan sun gama sallah sukayi kana suka biya likita kud'in shi ,suka hau mota suna cikin tafiya suka hango Ladidi tana jifan mangoro abishiya Humaid ne ya dubi jalal yace tsaya ga mahau kaciyar ,yarin yar nan .


Malam adamu ne yace kufa kiyayi Ladidi kotayi lefi babu me d'aukar mataki Humaid ne a zuciye ,yace wai malam wanan yar gidan waye ¿malam adamu ne ya ce yar gidan amini na ne malam musa.


Humaid ne ya ce dan Allah malam kabari ,inkoya mata hankali malam adamu ne ya ce jalal kawuce mutafi na gaya maka kar katsaya .

Humaid ne ya lek'a ta window yace ke Ladidi wlh kinci bashi zanga uban daya tsaya miki a fad'in a kurkin k'auyen nan .

Ladidi ,da kamar jira takeyi ta sami abokin fad'a dagudu tayi ,yo gurin motar amma ina jalal ya k'ara gudun motar duwatsu tasamu tanata kai jifa amma babu sa,a jifan data kai na k'arshe se a bayan wani bafula tani yana tsugune a wata gona yana kashi yaji ,jifa a bayan sa dasauri yaja wandon sa ya rik'e yana ihu Ladidi data lura tayi mugunta tazo guduwa bafula tani yace yau k'aryar ki takare kamota yayi kana ya dunga dukan ta .


Yana saketa ,ta mul mulo zagi shikuwa bafula tani dayaga Ladidi tafi k'ar fin shi ya shemeta da sanda ko motsi bata yi .




*_FARKON LABARI*_
Malam musa shine ma haifin Ladidi ita kad'ai Allah ya basu tun tana k'arama bata ji ko,kad'an bare duka shima be dame taba abota ce me k'arfi ta shiga tsakanin malam musa da malam adamu mutanen kirki .


Malam Adamu shine k'anin mahaifin su Humaid da jalal ma haifin su Humaid wato alhaji abdullahi tun bayan rasuwar mahai finsu wato kakan su Humaid kenan da mahai fiyar shi. ya had'a kayan shi yatafi neman ilimi shi kuwa malam adamu be bi d'an uwan ,nasa ba ya zauna ,yana koyar da almajirai .


Shigar dadyn su Humaid garin jos ya had'u da wani bawon Allah ya d'aukeshi zaman shagon atamfofi suna samun alkairi sosai saboda alhaji abdullahi akwai amana baya cin kayan da bana shiba shiyasa yake zaune lpy da mutane.

K'watsam wata rana uban gidan shi yabashi kyautar wani katafaren shagon da yagina had'i da bashi kaya masu yawa acikin lokaci k'alilan kud'i suka bunk'asa uban gidan nashi ne ya cire kud'in shi kana yabawa alhaji abdullahi ribar halak d'inshi ne yana juyawa yana karatun boko kan kace me arziki ya hau hawa .


Daga nan yafara neman aure Alhajin da ya bud'e mai shago shine yazama uba a garezhi yabashi kyautar gida a ranar alhaji abdullahi yayi ,kuka sosai ,yana fad'in inama iyayenshi na raye da sunga gatan da wadatar dayake ciki .

Bayan auran, ne malam adamu ya zo jos ganin ,gidan alhaji abdullahi gidane.

Gidane me kyan gaske sedai ba shida girma sosai amaryar tashi me suna Aisha tayiwa malam adamu tar ba me kyau.

Bayan y'an watanni Allah ya albar kace su ,da samun cikin Humaid cikin Aisha yasami gata sosai bayan wata ,tara da kwana goma Allah ya albar kacesu da samun k'aruwa kya'kyawan yaro me farin jini ya taso cikin gata da nuna kulawa ,kwatsam tana yaye Humaid se cikin jalal Allah yara bata da cikin lpy anyi hidima sosai tundaga lokacin aihuwa ta,tsaya mata .


*_BACK TO STORY*_
Bafula tanin ne ya d'auko jar, kar ,ruwan shi ya shek'a mata duka a jiki ware idanu tayi kana tace ,wai shin idan mutum ya mutu yana dawowa ne bafula tanin ne ya dube ta kana yace tunda kinga yanzu kindawo ba.

Shirin muguntar da zata yiwa bafula tanin takeyi sandar ,da ya buga mata ,ta d'auke ta ruga a guje .

Shikuwa bafula tani basan gidan su Ladidi ba yaro ne yazo wu cewa kiran shi yayi kana yace kasan gidan su Ladidi¿" yaron ,ne ya d'aga kai ,kana yace babu nisa ai bafula cewa ya yi to don Allah zoka ,rakani .


Barin shanun yayi suka nufi gidan su Ldidi yaron,ne ya shige cikin gidan ya diko ya samu tana shara gai sheta yayi kana yace ana sallama da Ladidi yadiko saboda jin dad'in yar tata zata fara zuwa hira ta ce kace gatanan fitowa .

Yaron ,ne Yakoma ya gayawa bafula tanin wai gatanan zuwa .

Ladidi ce ta fito daga d'akin yadiko tasha kwaliya in kagan,ta kace sabuwar aljana washe hak'ora tayi kana tace yadiko nayi kyau ¿"

Yadiko ce ta jin ,jina mata ,kana tafara yimata kira ,ri.


Kaga yar gidan yadiko ,washe bakin ta kumayi tana dariya.

Lek'awa tayi dan taga me sallamar hango shi tayi ,yana ta dunk'ule hannu kamar me shirin kai naushi .


K'ara mai da hanka linta tayi gurin sauraran abin dayake cewa jitayi ya na fad'in wlh tana fitowa zan ,zuba mata naushi .

Itako Ladidi jin haka yasa ta koma gida yadiko ce ,tace har kin dawo ¿".

A, a Ladidi tace kana ta shige d'an k'aramin d'akin ta ,,ta d'auko sandar bafula tanin ta dawo ta la6e kusa da inda yake zaune seda ta dede,ci ya juya baya ai kuwa ta d'aga sandar ta sheme shi fad'uwa k'asa yayi ita kwa Ladidi gaba ta k'ara ta barshi ,shida sandar shi a gurin yakasa tashi yana ta ihu.

Tana cikin tafiya ta ci karo da wasu samari su biyu .

Tana ganin su ta ,tuno inda ta, ta6a ganin su Humaid ne shi,da Jalal sun fito kewaye .
*LADIDIN ƘAUYE.*


_funny & love story._


*_Labari mai ban dariya haɗi da faɗa karwa_*


*NA*


*ZAINAB HABIB*
_{MOM ISLAM}._



*MARUBUCIYAR*


*ZAINABU ABU*


*AND NOW*


*LADIDIN K'AUYE*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*



*Episode: 5_6.*


____Humaid yasa shadda fara shi kuma jalal k'ana nan kaya ne a jikin shi Ladidi ce ta rik'e baki shagon da take kusa dashi ta shiga kana tace "dan Allah me manja samin a hannuna me manja ne ya dubeta kana yace "ke baki da hankali ko¿ LADIDI ce ta dubi me manjan kana tace "zaka ga aikin masu hankali roba ta hango a can waje zuwa ta yi ta d'auko robar shidai me manja yana kallon ta be ankara ba ta dumbula robar cikin manja .


Me manja da yaga barnar da LADIDI tayi mai mik'ewa yai kana ya nufo ta da niyar kai mata mari.


Ya d'aga hanu ze mare ta yaji an wanke mai fuska da manja sakinta yai kana ya nemi gurin zama .

LADIDI kuwa ganin haka ta kuma dum bular manjan tayi gaba .


Hango su Humaid tayi a gindin wata bishiyar mangoro suna hutawa .

A hankali ta tako kana ta zagaya ta bayan su inda bazasu ganta ba saboda bishiyar k'atuwa ce .


Juye manjan tayi a rigar Humaid ta baya sunata hira basusan abinda ke faruwa ba a jiye robar tayi a gefe .

Hango cinnaku tayi da yawa d'auko biyu tayi tasawa Humaid a dede gurin zaman shi kuma d'auko biyu tayi kana tasawa Jalal a daidai saitin da ya zauna.

Tashi tayi taje wani shagon da ake siyarda yar bebi jitayi anata ihu Humaid ta hango yanata tsalle shima jallal d'in tsalle yakeyi a tak'ai ce dai babu me temakon d'an uwansa.

Sun rasa inda za suyi aikuwa suka zuba a guje .

Kamar mahaukata Jalal ne yace "Humaid wlh bayanka manja .


Zaro ido Humaid yayi kana yace "kai k'yaleni bata manja nakeyi ba.


Mutane sa kallon su suke ta famanyi, ita kuwa LADIDI barin gurin tayi dan karsu ganeta da k'yar suka gane hanyar gidan malam Adamu saboda zuwansu na biyu kenan .


Da gudu su ka shige cikin gidan inna hauwa tanajin an shigo gidan da gudu bata tsaya ganin kosu waye ba itama ta ruga d'akinta da gudu.


Su Humaid ne suka shige d'akin da malam ya basu wanan na ihu wancan na ihu se zuwa can anjima ya lafa musu .


Humaid ne ya hau tattaro kayansu yana had'awa guri d'aya jalal ne yace "Humaid me zakayi da kayannan .


Humaid ne ya kalli jalal kana yace "insha Allah gobe zamu bar wanan k'auyen .

Jalal ne ya tuna da gudu da suka dinga kwasa ya kyalkyle da dariya .


LADIDI ce ta fito d'auke da tiren tuwo da miya malam adamu ne da malam musa suna zaune suna hira kasa kunne tayi taji suna cewa ai bak'in gidana gobe zasu tafi .

Tsalle LADIDI ta buga kana ta je gurin kayan wasan ta kusa da bishiyar kuka .

Dakin YADIKKO ta nufa samun YADIKKON tayi tana sallahr isha I .

Fitilar d'akin ta d'auko kana ta koma gurin kayan wasan .

Farar k'asa ta d'auko taje kan dutse ta dan dak'ashi seda yayi laushi.

Ta kwashe shi a leda d'akinta ta nufa mudubi ta samu .


Ta lakato mai me yawa ta shafa a fuskarta ta d'auko farar k'asar da tadaka shima ta goga a fuskarta, tunawa tayi ai batasa kwallin ba d'auko kwalkin tayi ta zana baki a bakinta takuma zazzana a duka fuskarta kayanta da suka yayyage ta d'auko .


Riga tasa me yagaggen hannu se wandon atamfa shima ta gwuiwa ya yage .

Dan k'aramin gyalenta ta d'auko ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment