Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

t shirt da blue din jeans iya gwiwa,

Tattarawa sukayi suka nufi part din mami lokacin tadawo tana zaune tana waya dasu Abdul wadanda zasu dawo wani satin,

Zama sukayi takawo masa abinci yaci sannan suka yiwa mami sallama suka fita,

Ac ya kunna musu acikin motar ya rufe gaba daya glasses din ya kunna wata waka ta turanci _you are my African queen..._,ahankali wakar take tashi yanabi yana makale da hannun hafsat guda daya acikin nashi yana driving da dayan,

Wata hamshakiyar unguwa tamasu fada aji taga yakaisu, wani tangamemen gida suka shiga mai manya manyan part har guda hudu sannan kowanne upstairs ne,kuma daga can gefe B/Q ne,

Nafarkon yabude suka shiga nan taga tangamemen falo da kitchen da store sai dining area, saman kuma bedrooms ne guda biyu masu dauke da bathroom acikin kowanne,

"Kinga gidan da na sai mana zamu dawo nan bada jimawa ba domin har nabada asiyo furniture's,nafi son ina dawowa daga Cairo insauka anan"

"Wai amma gidan ya hadu yaya, ga girma komai awadace.."

Murmushi yayi yariko hannunta suka fito, "kin dai k'i zancen ko?"

Murmushi tayi,

"To amma yanaga part din guda hudu?"

"Daya namu, daya na mami, daya nasu Abdul"

"To dayan fa?"

"Na amarenki"

Duka takai mishi,

"Allah kabari"

Dariya yayi yabude musu motar suka shiga batare da sun shiga sauran part dinba domin gaba daya parts din tsarin gininsu da komai iri dayane,

Saida suka gama yawonsu agari sannan suka koma gida.


Washe gari hafsat gidan umminta tatafi tawuni acan, misalin karfe 2 narana mami nazaune tana yin lunch taji sallama, har cikin falon mai sallamar tashiga sai faman budada kamshi take nan ta durkusa tagaida mami,

"A'a tashi ki zauna, sannu da zuwa"

Saida mami ta gabatar mata da abinci da abubuwan sha sannan ta dubeta da fara'a,

"Sai dai kuma ban ganeki ba" inji mami,

"Ehh ai momy baki sanni ba, sunana hafsat kuma ni yar gidan alh musa ce ubangidan ya yusleem"

Sake fadada fara'arta mami tayi ta dubeta....


_Fans kuyi min uzuri zakuji ni shiru kwana biyu saboda wani uzuri da ya taso min na gaggawa amma insha Allah nanda sati daya zaku cigaba da jina ina fata zaku yimin afuwa..._



*_Ummi Shatu_*πŸ‘ŒπŸ»
[6:28PM, 4/1/2018] ~Maman_twinsπŸ’žπŸ˜πŸŒΉ: Β© *HASKE WRITERS ASSO*
_(Home of expert & perfect writers)_




*ALWASHI...!*πŸ’
_(Labarin Hafsat)_




_*Na*_
*_UMMI A'ISHA_*



_DEDICATED TO MISS XOXO_



*Fans ina mai mutukar baku hakuri dangane da jina shiru da kukayi kwana da kwanaki hakan yafarune ba ason raina ba sai tarin hidimomin da suka shamin kai, ban san ta inda zan fara baku hakuriba, indeed i have no words to apologize you saboda nasan kuna mutukar ji da alwashi domin kun nuna min hakan kullum cikin amsa wayoyinku da karbar sakonninku nake dan haka ina mutukar godiya kuma ina mika gaisuwata agareku, insha Allah hakan bazata sake faruwaba, ina yimuku fatan alkhairi aduk inda kuke,duk wata masiyiyar alwashi tayi alfahari da page din yau domin mallakinta ne, i heart u all.*



*56*



***Sake fadada fara'arta mami tayi tadubeta cikin murmushi tace,

"Allah sarki ya kika baro mahaifiyar taki da yan uwanki, duk suna lafiya ko?"

"Lafiya lau suke..."

"Madalla, ai kin kyauta da kika zo" inji mami,

"Ah babu komai wlhi ai an zama daya..."

Sun dan jima suna hira kafin hafsat tayiwa mami sallama tatafi, har waje mami ta rakata wurinda motarta take saida taga tafiyarta sannan takoma ciki.


K'arfe 6 yusleem yatashi daga aiki, Hafsat yakira daidai lokacin da yaje gaban motarshi,

"Ya yusleem..."

"Uhmmm, matata kina ina?"

Murmushi yaji tayi saboda sunan da ya kirata dashi,

"Da waye yace ba matarka bace?"

Cikeda alamun gajiya yabude motar yashiga ya zauna amma baiyi mata key ba,

"Nidai nasan matatace koda wanima zai ce ba tawa bace, dan Allah kina ina? Wallahi agajiye nake sosai"

"Ina gidan Ummi"

"Wai har yanzu dama baki koma gida ba?"

"Ai yau anan zan kwana"

Yar dariya taji yayi,

"Yanzu zanzo in daukoki ki shirya"

Yafadi yana daura sit belt ajikinshi,

"Ko baka zo ba ma ai zan dawo anjima"

"A'a ban yarda ba, gara inzo indauki abata intafi da ita ina jinta agefena"

Murmushi tayi tace "sai kazo" tareda katse wayar,

Mintuna ishirinne suka kaishi gidan, awaje ya tsaya ya kirata babu jimawa sai gata tafito rikeda jakarta da wata leda yar babba,

Bude mata kofar yayi tashiga ta zauna, mika hannu yayi ya rufo kofar yana kallonta, gaba daya wani kamshin dadine yaji ya cika cikin motar,

"Ummi tana gaisheka..."

"Ina amsawa, kefa? Bakya gaidani ko kina gaisheni?"

Murmushi tayi ta rike hannunshi wanda ke yawo acikin rigarta,

"Ina gaisheka, dan Allah kabari"

Murmushi yayi yatada motar yasoma tuki yana kallonta,

"Na fuskanci duk ranar da kikazo gidan Ummi bakya son komawa gida da wuri,meyasa?"

"Hirarce ke yin yawa bata karewa shiyasa" tafada tana murmushi,

Yan yatsunta taji ya kama,

"Me kike sha'awa yanzu mubi insiyo miki?"

Lumshe ido tayi, "Duk abinda kake kwadayi nima ina so"

Murmushi taji yayi kasa kasa yace,

"Ni ke naketa kwadayin samu kuma nagagara, kefa?"

Dauke kanta tayi ta mayar gefe saboda abinda taji yace, murmushi yayi ya dan kalleta,

"Yanaji madam tayi shiru?"

"Muje gida kawai basai mun tsaya ko inaba"

"Dama ai gidan zamuje"

Shiru tayi saboda yagama kashe mata bakinta, ita da zarar yayi mata magana makamanciyar wannan sai taji duk bata da bakin yimasa magana,

Juyawa yayi ya kalleta, "menene wannan haka mai kamshi ummi tabaki?"

"Turaren wutane da humra aka kawo mata daga Sudan shine tabani..."

"Ta kyauta kuwa dan naji kamshin irin wanda nake so ne"

Kawar da maganar tayi tahanyar cewa,

"Yaushe zaka je chairo dinne?"

"Zamuje dai, ai tare zamu tafi yanda muna dawowa mami zata fahimci cewar andace nagama warkewa".

Murmushi kawai tayi masa batare da tace komai ba saboda idan taci gaba da biye masa kunya zai ta sata tanaji,

Wurin wani mai sayarda balangu da tsire taga ya tsaya nan yafita yaje ya siyo yadawo, ledoji biyu yariko ya mika mata,

"Amshi wannan, na mami daya namu daya..."

"To angode, Allah yakara budi"

"Amin, me zaki bani tukwici?"

Shiru tayi masa takai hannu zata kunna radio, dora nasa hannun yayi akan nata yana lalubo mukunnar radio din,

"Ko babu abinda zaki bani? Naji bakice komai ba"

"Uhmm"

"Uhm fa kikace? Lallai, to ashe bazaki cimin balangu na ba tunda hakane"

Kallonshi tayi tasaki dan murmushi,

"Dama bada zuciya daya ka siyo ba kenan?"

"Wallahi da zuciya biyu nasiyo, kici balangu ki bani tukwici"

Rasa abinda zata fada masa tayi dan haka taja bakinta tayi shiru, shikuwa sai sake nanatawa yake yi dahaka har sukaje gida,

Part din da yake yawuce yayinda ita kuma tawuce part din mami, mamin nazaune tana lazimi da alama sallar magrib ta idar, ciki Hafsat tawuce taje ta dauro alwala tafito, saida ta idar da sallar sannan suka gaisa da mami ta fito da kayan da Ummi tabata da kuma naman da yusleem yasiyo,

Tuwo da miya tazubo musu ita da mami,sun fara ci kenan yusleem yashigo,

"Mami ni baza ajirani ba inzo shine kuka wareni"

Murmushi mami tayi,

"Kai ai kayi girma da yawa Yanzu babu mai wani riritaka"

Samun wuri yayi yazauna kusa da mami yana murmushin shagwaba,

"Gaskiya mami a'a"

"Basai kayiba kuma" inji mami,

Dariya Hafsat tayi ta dan kalleshi nan suka hada ido dama shidinma ita yake kallo,

"Am yawwa kafin namanta, dazu wannan yarinyar Hafsat tazo yar gidan alh musa..." Mami tayi maganar tana kallon yusleem,

Saida yaji gabanshi ya fadi saboda jin abinda mami tace,

"Mami lafiya? Meya kawota gidan nan? Tace miki wani abune?" Duk ya jerowa mamin wadannan tambayoyin lokaci guda,

"A'a ni babu abinda tace min, kawai dai zuwa tayi agaisa, akwai wani abune tsakaninka da ita da kake tambayar me tace?"

Kallon hafsat yayi amma ita bashi take kalloba tuwonta kawai take ci sai dai gaba daya tasauya ta danyi wani iri tana sauraronsu, ita dama bata sawa ranta cewar ita kadai zata zauna dashi ba tunda tasan watakila shima akan kansa nan gaba zai bukaci kara auren,daurewa tayi tai watsi da duk wata damuwa taci gaba da cin tuwonta batare data bari bacin rai ya ziyarci zuciyarta ba,


Kallon mami yusleem yayi bayan ya tsame hannunshi daga cikin kwanon tuwon da suke ci,

"Mami ni banida wata alaka da ita, kawai dai abinda nasani shine ina zuwa gidansu wurin mahaifinta kuma tana girmamani"

"To ai shikenan hakanma yanada kyau, Allah ya rufa asiri.."

Bai amsaba yasaci kallon Hafsat, balangun da yasiyo musu yaga tabude tafara ci,

"Baby nanah babu ko bisimilla?"

Murmushi yaga tayi tatura masa gabanshi,

"Haba ya yusleem taya zan hanaka bayan kaine ka siyo, gashi muci"

Tashi mami tayi tawuce domin wanko hannunta, ganin haka yasashi rage murya,

"Nidai sai dai kibani abaki..."

Tun kafin yarufe bakin nashi ta dauki naman tasaka mishi, murmushi yayi yarike hannunta,

"Yawwa matata..."

Dariya tasaki saboda jin abinda yace,

"Ni kana bani dariya idan naji kafadi haka, wai waye da yace ba matarka bace?"

"To laifine dan nasake jaddadawa?"

Hannunta tazare daga cikin nashi saboda jin tahowar mami,sake rage murya yayi,

"Ya kamata fa kitashi muje mu kwanta saboda yau jina nake asama sama..."

Sunkuyar da kanta tayi batare data tanka mishiba har mami takaraso cikin falon ta nemi wuri ta zauna,

Hira sukeyi kadan kadan shida mamin yayinda ita kuma hafsat ta tattare kayan da suka ci abinci tafita dasu bayan tagama cin naman dayake gabanta,

Dawowa falon tayi itama ta zauna tana kallo sannan tana dan sauraren hirarsu mami wadda yanzu akan dawowarsu Abdul ne,

Da ido yusleem yake yiwa Hafsat alamun ta tafi bedroom zai biyota,

Makale kafada tayi, kallonta yayi yadan jijjiga kai alamun zan kamaki ne, murmushi tayi gamida yimasa gwalo, hakan da tayine yabashi dariya,

Gani yayi sam bata da niyyar tashi domin lokacin har karfe 9:30 tayi gashi mami itama yau hirar takeji saboda tana nan zaune bata motsa ba,

Dan gyangyadin da taji yana fusgarta ne yasata tashi badan tasoba tawuce bedroom, binta da kallo yusleem yayi har ta shige,

Wanka ta shiga bata dauki lokaci ba tafito tana daure da towel din surayya wanda dakyar ya ritsata saboda dan jikin da tayi,

Humrar da ummi tabata yau ita tabude tasoma shafe jikinta babu bata lokaci dakin gaba dayanshi ya gauraye da daddadan kamshi,tana rufe kwalbar yusleem yaturo kofa yashigo, da sassarfa yakaraso gareta sakamakon kamshin da yakaiwa hancinsa ziyara ya ratsa har cikin kwakwalwarsa.......




_*Ummi Shatu*_πŸ‘ŒπŸ»
[5:24AM, 4/4/2018] ~Maman_twinsπŸ’žπŸ˜πŸŒΉ: Β© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_




*ALWASHI...!*πŸ’
_(Labarin Hafsat)_



_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*




_DEDICATED TO MISS XOXO_




*57*



***Wata lafiyayyiyar runguma yayi mata bayan yacusa fuskarsa awuyanta yana sinsinarta,

Towel din dake jikinta tarike gam yayinda shi kuma yasake tsananta rukon da yayi mata,

"Ya yusleem...."

Kasa amsawa yayi illa gyada mata kai da yayi alamun yana jinta,

"Ya yusleem kabarni inshirya...."

Sake kankameta yayi yana janta ahankali har suka dangano da gadon dake cikin tsakiyar dakin,

Makaleta yayi sosai ajikinsa ya shimfidar dasu nan yasake bada himma wurin isar mata da sakonnin da yafara bata tun suna tsaye, sosai yau taga ya fice daga hayyacinsa sakamakon yakai makura wurin bukatarta, wani zazzafan numfashi yake fitarwa yana sauka ajikinta,

Sun dauki lokaci mai tsawo cikin wannan yanayin wanda shi yusleem jinshi kawai yake yashiga wani wahalallen hali maimakon yasamu relief daga azabtuwar da gangar jikinshi da rushinsa ke ciki, badan yana jin tausayinta ba kuma yana tsoron kar ya cutar da itaba da ayau dinnan ba gobeba babu abinda zai hanashi zama cikakken ango,sake kankameta yayi yana faman jujjuya kanshi,

Shiru Hafsat tayi tana saurarensa cikeda jin tausayinsa, dakarfi da karfi take jin fitar numfashinsa har yasoma fita ahankali ahankali dahaka har yadawo fita normal sai lokacin ya iya barin jikinta ya matsa gefenta amma har lokacin yana makale da hannunta kamar wadda za adauke masa ita,

Jin yadan sassauta rikon da yayiwa hannuwanta yasata zaton cewa bacci ya daukeshi,tashi tayi ahankali tawuce bathroom, ruwa takama tadawo tadauko rigar baccinta tasaka takoma kusa dashi ta kwanta tana faman runruntse idanuwanta saboda irin dakumar da yayiwa kirjinta har wani irin radadi takeji yana damunta,

Dakyar ta iya yin bacci awannan dare, shikam yusleem tunda yasamu bacci ya daukeshi bashi ya farkaba saida asuba wannan dinma Hafsat ce ta tadashi, wata wawiyar mika yayi sannan yashiga bathroom din, yajima aciki kafin yafito domin saida yayi wanka,

Lokacin da yafito Hafsat tana zaune akan abun salla tana lazimi, kallonta yayi yai magana ahankali,

"Bari naje part din can..."

Rike kafarshi tayi saboda bata son yafita domin zasu iya haduwa da mami afalo,

"Dan Allah ya yusleem karkaje kayi sallarka anan..."

Murmushi yayi yasake rage murya kamar wanda baya son wani yaji abinda zai fada,

"Wallahi kayana bazasu yi salla ba saboda gaba daya sun baci..."

Cikashi tayi batare da ta kalleshi ba, wucewa yayi yaje yabude kofa yafice, aranta tanata addu'ar Allah yasa kar mami tafito taganshi, kwanciya tasake yi bayan ta kammala addu'o'in da takeyi,

Baccine yasake daukarta saboda jiya bawani mai yawa tayiba, ba ita tatashiba sai karfe 8 nasafe, wanka tayi tashirya cikin doguwar riga tawani jan material, turarrukan jiya tafesa ta hade jikinta da kamshi mai dadi tafita.

Abangaren yusleem kuwa dakyar ya iya komawa bacci bayan ya idar da salla, juyi kawai yarinka yi akan gado daga karshe wani wahalallen bacci ya daukeshi, karar wayarshi ce ta tasheshi lokacin karfe 8 saura nasafe,

Hannu yamika yadauko wayar idanuwanshi arufe, muryar Hafsat mori yaji tana magana cikin kasalalliyar murya da alama ita dinma daga baccin ta tashi,

"Ranka yadade ina fata ban tasar dakai ba a bacci?"

Batare da yabude idanuwanshi ba yayi magana,

"Meya faru? Dama ina son yin magana dake.."

Shiru tayi, jin baiyi magana ba yasata fadin,

"Ina sauraronka"

"Meya kawoki gidanmu jiya? Hafsat nafada miki fa inada mata, bakya tunanin zuwanki yana iya haifar da matsala tsakanina da iyalina? Dan Allah na rokeki karki sake zuwa gidanmu..."

Bai jira abinda zata fadi ba yakashe wayar kittt, daga nan tashi kawai yayi yashiga toilet yayi wanka yafito yanaji Hafsat mori nata kiranshi awaya amma yayi fuska yaki kallon koda wayarne,

Farin wani lallausan yadi yasaka yasha turare yadauki wayarshi yafita da hularshi ahannu, a tsakiyar falo ya hango Hafsat tana shirya jaridun mami akan centre table ita kuma mamin tana kitchen ita da kuku, wucewa yayi bayan sun gaisa da mami yashiga cikin falon, da kafadarshi yadan bugeta, murmushi tayi batare data juyo ba saboda tagane cewar shine domin kamshinsa yasanar da ita,

"Morning Nana hafsat"

"Morning ya yusleem" ta amsa mishi bayan ta dago amma bata kalleshi ba,

"Kinga irin wahalar da nasha dazu da asuba bayan nabar dakinki? Acikin week dinnan gaskiya zan koma chairo, wallahi nagama kaiwa karshe atakura"

Shiru tayi masa acikin ranta tana hangowa fitinar da yusleem zaiyi duk ranar da yagama samun lafiya,

"Yanaji kinyi shiru? Ko bakya son nawarke ne?"

Murmushi tayi tadago tana kallonsa saboda jin abinda yafada,

Kafin tayi magana tajiyo mami na kwalla mata kira daga kitchen, gefenshi ta raba tawuce batare data sake kallonshi ba,

Kayan breakfast tadauko tazo ta ajiye ta zuba mishi, da kallo yake binta yana kurbar tea din dake hannunshi amma yana lura da ita sai wani dan yayyatsina fuska takeyi, saida ya kammala breakfast din sannan yaja hannunta zuwa bedroom,

"Nanah meyake damunki naga alamun damuwa atare dake?"

Shiru tayi tasunkuyar da kai,

"Fada min Mana"

"Babu komai"

Murmushi yayi yakai hannu jikinta dasauri tarikeshi,

"Ya yusleem dan Allah kayi hakuri.."

Murmushi yayi yajuya yafita saboda ya fahimci abinda ke damunta, cikin falon tabishi tasameshi tsaye rikeda hularshi, karbar hular tayi tasaka mishi yajuya yafita, tana jiyoshi yana yiwa mami sallama domin har lokacin tana cikin kitchen saboda tafara shirye shiryen tarbar yan makaranta wadanda zasu dawo.

Wurin mami taje suka cigaba da aiki tare bayan ta kammala yin breakfast, har azahar tayi suna cikin kitchen suna aikace aikace zuwan khadija ne yasa Hafsat barin kitchen din suka shiga falo,

Yar hira suke tabawa bayan hafsat ta gabatarwa da khadija abinci shinkafa da doya da miya,

"Amarya ta ango" khadija tace da hafsat cikin wasa,

"Yanzu ai kece amarya khadija" hafsat tafada tana murmushi,

"A'a kedin dai"

"Zancen kike so" inji hafsa, maganar yusleem tajiyo acikin kitchen yana cewa mami,

"Yunwa ce ta dameni shine nadawo inci abinci"

Murmushi hafsat tayi saboda tasan ba gaskiya bane abinda yafadawa mami shidai kawai fitinarsa ce tadawo dashi, cikin falon yashigo ganin khadija yawani hade rai sama sama ya amsa gaisuwarta yawuce cikin bedroom,

Tashi hafsat tayi tashiga kitchen, abinci tahado masa ta dauka ta nufi cikin bedroom din har lokacin khadija tana zaune tana cin abincinta,

Kwance taganshi agefen gado idanuwanshi alumshe, ajiye abincin tayi taje kusa dashi,

"Lafiya kuwa ya yusleem?"

Bai bata amsaba illa kamota da yayi ya sadata da jikinsa ya kwantar da ita, fuskarta zuwa wuyanta yake sinsina da fuskarshi,

"Ni dama nasani" tafada acikin ranta,

Cigaba da birkitata yayi har zuwa tsawon wani lokaci dakyar ya iya barinta ya tashi domin cin abincin da ta Kawo masa saboda zai koma office,

Zuba mishi tayi ya dauka yafara ci yana kallonta,

Sunkuyar da kanta tayi taki kallonshi, dan murmushi yarinka binta dashi har yagama,

Fitowa sukayi bayan ya gama cin abincin nan taga khadija bata nan da alama tafiya tayi, saida ta rakashi har wurin motarshi taga tafiyarshi sannan takoma ciki.

Cikin yan kwanakin gaba daya busy hafsat take itada mami saboda aikace aikacen da suke yi na karbar baki, ranar laraba da yamma su Abdul suka dawo shida khalifa,

Bakin mami kasa rufuwa yayi sai murna take tana fadin "saura yar autana surayya itama tana tafe"

Tunda su khalifa suka dawo sai hafsat ta dauke kafarta da zuwa part dinsu wurin yusleem duk da cewar har yanzu yana nan adakin Abdul sukuma samarin sunyi skwatin adakin khalifa kafin akoma sabon gida,

Duk da bata zuwa amma shi kowanne daren duniya adakinta yake kwana,

Dawowar su Abdul da sati biyu itama surayya tadawo, murna hafsa tashiga yi harda rungume surayya nan suka kafa dandalin hira har karfe 11 nadare,

Wasu hadaddun English wears surayya tadawo dasu akwati guda, kallonta hafsa tayi tana murmushi,

"Wai ke sury bakida kayane sai wadannan...?"

Dariya surayya tayi,

"Wallahi ban iya saka wasu kayan inba wadannan ba, ke nifa atamfa da sauran kayan gargajiya gumi suke sani, ga uban nauyi shiyasa ma bana iya sawa"

"Amma kuwa kin hadu da aiki" inji Hafsat,

"Babu wani aiki, kema ai nakawo miki tsarabarsu kisa ki kashe ya yusleem"

"Bakida kunya..."

Karar wayar hafsa ce ta katse musu hirarsu,

"Ya yusleem ya akayi?"

"Zo ina jiranki awaje"

Tashi hafsa tayi bayan ta dauki hijab, kallonta surayya tayi tana murmushin shakiyanci,

"Saida safe kenan"

"Ahh kin manta sai jibi" hafsat tafada tareda ficewa daga cikin dakin, hannunta yakama lokacin da tafita yanufi part dinsu khalifa,

"Ya yusleem..."

"Bana son gardama"

Shiru tayi har suka shiga falon, su Abdul din suna zaune kowannensu dauke da laptop dinshi suna danne danne, kunya ce ta kamata hafsat saboda ganinsu abdul amma shi ko ajikinsa, sakata yayi agaba suka wuce ciki yamaida kofa ya rufe harda sa key,

"Haba ya yusleem..."

Bai kulata ba yacire rigar jikinshi ya kwanta,

"Idan kin gama mitar sai kizo ki kwanta.."

Yace da ita bayan ya lumshe idanuwanshi, ta dan jima atsaye daga karshe dai taje gefenshi ta kwanta, dama kamar jira yake yajawota jikinshi ya kwantar.

Koda asuba hanata tafiya yayi bai barta tatafiba sai da gari yawaye,ai kuwa tasha tsokana awurin surayya dan tun tana mayar mata har dai tayi shiru ta rabuda ita daga karshe tace,

"Bari yayan naki yafito sai nafada masa"

Jin haka yasa surayya yin shiru tabar zancen, tun daga ranar kowanne dare sai yazo ya tisata agaba yatafi da ita baya barinta tadawo sai gari yawaye,

Yau kam takasance weekend suna zaune adaki ita da surayya, sury tana karatun novel a wattpad ita kuma tana gyara farcenta tana sanye da hijab ajikinta duk da acikin dakine domin wata yar karamar rigace ajikinta pink colour da yar karamar skirt iya cinya, kwata kwata bata saba irin shigar nanba surayya ce tasata dole saida tasa gashi bahaushe yace zama da madaukin kanwa shike kawo farin kai, knocking akayi sannan aka shigo yusleem ne yana sanye cikin kananan kaya,

"Zo Hafsat..." Yace da ita yana kallonta, kasancewar babban hijab ne ajikinta yasata tashi tabishi,
"taho min da ruwan zafi"

Acikin kitchen suka tsaya ta dauki ruwan zafin suka fita, part din su Abdul suka shiga, dukkansu suna falon suna kallo,

"Kai me kuke yi?" Yusleem ya tambayesu,

"Yaya kallo muke" inji khalifa,

"To ko ku koma daki ko kuma ku fice ku koma part din mami"

Yana kaiwa nan yawuce cikin daki Hafsat tana biye dashi tana ji kamar kasa ta tsage ta nutse dan tsananin kunya.......


_Fatan alkhairi ga aminiyar kwarai maryam qaumi (Mrs.......),the above page is urs dear...!_



*_Ummi Shatu_*πŸ‘ŒπŸ»
[7:24PM, 4/4/2018] ~Maman_twinsπŸ’žπŸ˜πŸŒΉ: Β© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_




*ALWASHI...!*πŸ’
_(Labarin Hafsat)_




*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*



_DEDICATED TO MISS XOXO_


*_Kina ina DEEJAH ABDUL? Ina miko sakon gaisuwata da fatan alkhairi agareki aduk inda kike....!_*




*58*



***Tsaye tayi a bayanshi batare da ta motsa daga wurinda take tsaye ba,

Juyowa yayi ya kalleta, ganin taki motsi yasashi karasawa gefen gado yazauna yasake juyowa ya kalleta,

"Bazaki bani tea din bane?..." Taji ya tambayeta,

Sai lokacin ta motsa ta nufeshi fuskarta adan daure ta mika mishi cup din ruwan zafin dake hannunta,

Hannu ya mika ya karba yahada da hannunta yazaunar da ita akan cinyarsa,

"Fushin na menene nanah? Uhmm?"

Yafadi yana kokarin zare hijabin dake jikinta,

Boye fuskarta tayi saboda ganin ya yaye hijabin,

"Wowwww....., baby nanah kinyi kyau"

Kallonta yaci gaba dayi yana murmushi,

"Insha Allah dai mun kusa tafiya chairo saboda idan naci gaba da zama anan haka kina iya zautar dani...., sury ne ta koya miki saka kananan kaya ko?"

Shiru tayi sai rufe fuskarta da tayi da tafukan hannunta, cigaba da zuzuta kyawun da tayi yayi yana faman sinsinarta.

Daren ranar lokacin da tayi shirin bacci kashe wayarta tayi domin tasan yusleem zai iya kiranta yace sai taje sun kwana tare,

Tana nan kwance suna yar hira itada surayya suka ji bugun kofarshi, saurin rufe ido hafsat tayi tace,

"Surayya dan Allah kice nayi bacci"

Tun kafin surayya tayi magana yabude kofar yashigo,

"Yaya tayi bacci fa"

Harararta yayi,

"Zata tashi yanzu ko kuma indauketa"

Dariya sury tayi tabishi da ido, wurin hafsat yaje yakamo hannunta,

"Tashi ko indaukeki..."

Jin abinda yace yasa Hafsat tashi tana faman zumburo baki, bai kulataba yaja hannunta suka fice.

Kasancewar angama hada komai na bukata agidan da zasu koma yasa suka fara tattara kayayyakinsu domin komawa sabon gida, duk wannan hidimar da khadija akeyi kullum sai tazo ta tayasu tattara kayan,

Shikam yusleem yanzu fafutukar samun visa yakeyi domin zuwa kasar chairo saboda yana cikin matsanancin hali na bukatuwa amma kuma visa din samunta yayi wahala,

Kusan kullum sai yaje gidan alh musa mori domin yagama zama cikakken dan gida yanzu danma wani lokacin baya son zuwa saboda Hafsat yar gidan alh musan domin tagama takura masa ita adole shi takeso ta aura duk da yayi mata bayanin baida burin kara aure amma taki hakura koda yaushe cikin yimasa waya take, gaba daya jinta take tagama tsanar Hafsat dinshi saboda tasan saboda itane yaki amsar soyayyarta wannan dalilinne yasa bata son Hafsat ko kadan duk da cewar basu taba ganin juna ba.

Ranar juma'a suka gama kwashe kayansu suka koma sabon gida wanda ya cancanci da akirashi da aljannar duniya saboda yanda aka kawatashi kuma aka zuba masa dukiya wacce bazata kididdugu ba, ba karamin kudi yusleem ya kashewa gidanba,

Sai daf da magrib Hafsat da sury suka gama gyarawa mami dakinta,agajiye Hafsat ta nufi part dinsu itada yusleem wanda ya hadu karshen haduwa, zama tayi afalon kasa tana bin falon da kallo yanda ya shiryu kamar aciki za a dawwama baza a mutuba, dan murmushi tayi saboda tunawar da tayi wai harfa agidan haya sun zauna itada yusleem,

Ganin zaman bazai kaita ko inaba yasata tashi ta nufi cikin bedroom dinta tayi wanka da ruwan dumi tafito ta shirya cikin wata doguwar riga yar kanti roba mai hannun shimi bayan ta shafe jikinta da turarurruka da humra masu dadin kamshi,

Sallar magrib tayi daga nan tasauka kasa tana rikeda wayarta sanye cikin hijab,

Yusleem tagani zaune afalon yana latsa wayarshi, sakon da Hafsat musa taturo masa yake karantawa wanda kusan kullum ne sai taturo masa,

Zama Hafsat tayi akusa dashi, mayar da wayar tashi cikin aljihu yayi yamika hannunshi ya kamo nata yajata jikinshi,

"Da abinci kibani? Yunwa nakeji..."

Murmushi tayi ta kalleshi,

"Da akwai, zakaci tuwo?"

"Zanci indai kece kika bani" yaceda ita yana faman shakar kamshinta,

Da dabara tasamu ta

2 Comments On ALWASHI
avatar
aliyu-1-5-2

1 year ago

Reply

I appreciate it

avatar
aliyu-1-5-2

1 year ago

Reply

I appreciate it

Please Login or Register in order to submit comment