Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[10/14, 9:51 PM] Chopy: [9/6, 17:34] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣➖5⃣

Shaharrariyar kuma kyakkyawar matashiyar yar jaridar nace da take tashe ke gafatar da program a gidan television dinsu me suna PYRAMID TV, ba wata bace face AISHA AHAMAD TURAKI. Duk wasu masoyan pyramid TV , ayanzu haka suna bakin TV dunsu suna kallon program din da take bayani kamar haka " Assalamu alaikum jama'a masu kallo kamar yadda kuke gani muna kan titin zariya Road inda muke dauko muku wanan rahoto direct daga wajen bikin bode katafaren ginin nan me suna BAGAUDA HOUSE. Kamar yadda masana sukace sunyi bincike duk 9ja ba ginin daya kaishi tsaho, sboda yana dauke da 500 upstairs a ciki, kuma ba tsawon ginin ne kawai zai birge me kallo ba, shi kanshi design din ba irinsa a 9ja. Duk manyan bakin da aka gayyata har me girma San kano yazo yanzu zuwan me girma governor ake jira.

Faisal na ya kalli sagir abokina ina masifar son yarinyar nan sbd kwarewarta a aiki, tana da confidence ga Uwa uba kyau, dariya sagir yayi sanan yace yanzu kayi magana kace kana son fitinannan kyaunta, to ka fadamata mana. Kai! Ai bazan Iya ba kasan Dan banzan kwarjini ne da ita, Amma indai da gaske kana sonta to dole kayi mata magana idan ba haka ba zakayi son maso wani,,,,,,,,,,muryar tace ta katse musu zancen da suke da cewa jama'a kamar yadda kuke gani me girma governor yazo kuma anfara gabatar da abinda ya Tara mu. Na sami nasarar ganawa da managing director na BAGAUDA trading company limited wato wato the youngest multi billionaire KABEER MOHD BAGAUDA Wanda matasa yan uwanshi ke yiwa kirari da ADON GARI, yallabai gashi yau Allah ya cika maka burinka, har ana bikin bude katafaren gininka da ba irinsa kaf 9ja, so idan bazaka damu ba pyramid TV tanaso tasan duk 500 upstairs din kayi occupying ko kuwa zaka bayar da hayar wasu? Zan bayar da hayar wasu. OK to yallabai wane irin farin ciki kake ji, kuma me zaka ce da masoyanka Wanda suka zo, da kuma Wanda suna nan a bakin TV nsu suna kallon ka? Wani lallausan murmushi yayi farin cikina baxai fadu ba sabd na Dade ina burin zuwan wanan ranar, gashi kuma yau Allah ya nunamin sbd haka tsakanina da Allah sai godiya alhamdulilla. Masoyana kuma ina mika godiyata agareku, nagode da kulawar da kuke nunamin. Wani shu'umin murmushi nayi sanan nace pyramid TV tana maka murna Allah ya sanya alkairi, shima murmushin yayi sanan yace nagode. Jama'a kamar yadda kuke gani tattaunawar da mukayi ce Mr kabeer, dafatan masoyan adon gari da basu sami damar zuwaba suna tare da pyramid TV.

Zee ce ta saki wani ihu yehhh samira zo ki gani yau adon gari yayi smiling, dama yana murmushi? Allah ya mallaka min KB, Allah yasa shine mijina, mama ce tace a hakan kuna nade a gd kullum zaki aureshi? Kina ganin shegiyar yarinyar nan kamar wasa yanzu ba Wanda besan taba, duk wani me fada aji agarin nan sun santa, kamar yadda take gadara pyramid TV ta ubanta ce kuma haka, Amma don rashin zuciya kuna gd saidai kuci Ku kwanta, idan baki wasa ba ita ta aure Kabeer din ai, don naga alama ita yakewa murmushin. Don Allah mama dena fada kar zuciyata ta buga kinsan yadda nake son kabir kuwa?

Maman Aysha
[9/6, 20:13] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
5⃣➖1⃣🔟

Bayan an watse daga wajen taron office muka koma, muka karasa kammala wani aiki sanan na tafi. A gajiye na shiga gdn a compound na sami zee tana waya ta kalleni ta tabe baki angama yawon karuwancin an dawo? Duk rahoton da kika dakko dazu na gani, kuma naga kallon da kk yiwa KB, sbd haka idan ma sonshi kike to wallahi ki daina KB nawa ne ni kadai insha Allah ni zan aureshi. Wani murmushi nayi nace nima zan tayaki da addua Allah ya baki KB Yaya zee. Na wuce part dinmu, INA shiga na sami mum a zaune kawai saina fada kanta nace wash wallahi yau na gaji mum, ai naga rahoton da kika dauko very interest Allah ya kara daukaka min ke, amin mum ina junior da basma suna ciki basusan kin dawo ba, anje nayi wanka to kafin suzo su dameni. Mikewa nayi na shiga toilet din dakina nayi wanka nasa wata doguwar riga na fesa turare, sanan na dawo falo naci abinci, sanan junior da basma suka dauko H/work dinsu na koya musu dad ne ya shigo aikuwa da gudu junior ya tafi ya dale shi oyoyo dad, sai kawai basma tasa kuka wai ya rigata kamota nayi haba basman aunty, rabi dashi bazan sayo mishi chocolate ba, idan da sabo mun saba da rigimarsu baka isa kayiwa daya Abu ba kaiwa daya ba. Karasowa Abba yayi ya zauna, sanan nace sannu da zuwa Abba yace yauwa Ummi na, naga aikin ki yana kyau iam proud of you Allah ya kara temakawa nace amin, sanan nayi musu saida safe na kwashi yan rigimar mum junior da basma muka shiga daki.

Washe gari , da wuri na tashi sbd dad a part dinmu yake suna can suna bacci da mum na tashi na hada break fast, na gyara gdn nasa turaren wuta, sanan nayiwa twins din mum wanka na shiryasu muna gama cin abinci nayi dropping dinsu a sch sanan na wuce office. Ina zuwa manaja ya kirani naje office dinsa, dama jama'a ne sun damemu akan sunaso suji matakan da Mr kabeer yabi yayi achieving goal dinsa akan ginin BAGAUDA house, shine nakeso kuje Ku same shi ya fada muku time din da zaku sami damar ganinsa, kinsan irin wanan manyan mutanen anashan wahalar ganinsu, Nace to, office dinsa zamu kenan? Eh, to bari muje. Elbash na samu yana wani aiki, nace idan ka karasa oga ya bamu aiki, wane aiki kuma? Zuwa office din adon gari, tab lalle ya hadamu da aiki kam wanan muskilin mutumin, danma dake zamu shine saukin abin, hammm in din wacece? Shifa wanan da kake gani mata basa gabanshi. Amma wallahi duk kin matansa idan ya ganki saiya jijjiga, sbd ke acikin mata daban kike, sai antara mata Dari kafin a sami guda daya irinki. Basar dashi nayi idan ka gama kayi min magana mu tafi ina office, yace is alright.

A motata muka tafi, saida muka hau lifter sbd a hawa na 200 office dinsa yake. Ba yanda bamuyi da sakatariyarsa ba akan ta barmu mushiga Amma taki, daga karshe muka nemi PA dinsa mukayi magana dashi, sanan yaje yayi masa bayani shine yace mu sameshi ranar Saturday a gd, mukayi godiya muka tafi.

Saturday 4pm
4:30 dot shine time din daya bamu, kuma PA dinsa ya fada mana baya son African time, sbd haka tun 4pm mukaje gdn muna jiran a kiramu shiru, gashi bamu karbi no PA din ba. Muna zaune har 5pm tayi nacewa elbash ko mutafi yace mu Dan kara hakuri dai, na duba naga bayan mu akwai mutane sunfi mutun goma suna jiransa. Kai gaskiya elbash na gaji mutaf.....ban karasa ba naga gate yana bude kanshi jerin gwanon motocinsa ne suka sako kai Wanda yawansu yakai guda 12 kuma duk cikinsu ba ta kasa da 3million, da gudu aka bude masa kofa ya fito, body guards dinsa suka Mara masa baya yana wata tafiya ta kasaita suka shiga ciki. Ya shiga befi da 10 minutes ba saiga PA dinsa ya fito jama'a don Allah kuyi hakuri yallabai yace ba Wanda zai Iya gani ayanzu, sabd ya dawo agajiye yana bukatar hutawa, sbd haka don Allah kuyi hakuri zan karayiwa kowa sbn schedule na ganinsa, wasu daga cikin Mutanen sukace ba matsala, cikin bacin rai nace elbash me yasa wasu masu kudin basu da adalci ne? Wanan ai rashiin sanin mutuncin Dan Adam ne, nidai tpy zanyi mayi waya, yace to shikenan.

2 days later
Yauce ranar daya kara bamu appointment, 11am mukayi dashi ko baccin kirki banyi ba muka tafi Amma Dan renin hankali sai yace muyi hakuri Tuesday mu dawo. Min taho akan hanya mukaga mutane a tare anata hayaniya daidai jikin wani katon kamfani muka tambayi me ya faru? Sukace gubataccen ruwa ake sakar musu daga kamfanin yake Shga musu rijiyoyi da gdajensu yana illatar da Mutanen yankin sosai kuma sun yiwa shugbn kamfanin magana beyi wani Abu akai ba, shine suke zangazanga. Aikuwa nan take na fito da kayan aiki na fara dauka, sanan nayi hira da wasu daga cikin Wanda abin ya shafa. Muna komawa office na watsa, cikin kankanin lokaci gari ya dauka har gwamnati suka shiga maganar sunsa anyi magana da shugaban kamfanin kuma ya bada hakuri yace zai gyara.

Maman aysha
[9/6, 23:06] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
🔟➖1⃣5⃣

9pm
Ina kwance a daki dad ya shigo ya kwala min kira rai abace da sauri naje nace gani, me ya hadaki da alhj danladi? me kamfanin maganin sauro, OK na kwashe lbrn abun daya faru na fadamasa, kirana yayi a waya yanata masifa wai anci masa zarafi a gdn TV na, Ashe shine marar gaskiya, is OK jeki Allah yayi miki albarka nace amin

4days later, 5:15pm
Muna kofar gdn Mr kabeer, yau shine zuwanmu na shida kenan. Muna zaune saiga PA yace bismilla mu shiga. Gidan ba karamin girma ne dashi ba, maganar kyau da tsaruwa kuwa abin baa magana saida mukaje bakin falon shiga gidan kawai saigashi ya fito da body guards dinsa oh Suleiman harka kirasu ne? Wallahi kaga wani important meeting ne ya taso min, saidai su dawo gb ya cigaba da tafiyarsa ko be ta kanmu beyi ba. Cikin bacin rai na tari gabanshi me yasa Ku masu kudi Baku da adalci be? Me yasa kuka dauki Dan Adam ba komai ba bayan kuma ko wane mutum da irin baiwar da Allah yayi masa, zuwanmu shida gidan nan bama samun ganinka wanan shi ya nuna cewa bakada cika alkawari bayan kuma cika alkawari yana daga cikin quality na salihan bayi......tasssss ya daukeni da mari ke wacece da zaki zo kina fadamin irin wanan maganar kuma har cikin gdn, yar iska kawai, ko angayamiki ni mata suna gabana, ko kuma angayamiki ina daukar nonsense? Ku fice min daga gd karna kara ganin kafarki a gdn nan. Harya fara tafiya na kara shiga gabansa karkayi tunanin don ka mareni shikenan kaci banza wallahi bashi ka dauka, ko bayanzu ba sainayi maka abinda ya bata maka rai fiye da yanda kayimin, kuma inaso ka Sani ni ba irin yan matan da kake mu'amala dasu bace, kuma dukiyarka ko wani kyaunka baya gabana harkar aiki CE ta kawoni gdnka, kuma don kana gadara kana da kuni baka isa ka wulakanta ni ba, zan kara repeating kaina Marin da kayimin bashi ka dauka kuma wallahi saina rama. Daya daga cikin body guards dinsa ne ya iyo kaina kawai sai naga ya daga masa hanu, sanan ya kalleni cikin bacin rai yace walk out from my house juyawa nayi na kalli elbash da yayi mutuwar tsaye nace zo mu tafi. Raina a bace na shiga gd wanka kawai nayi na gabatar da sallar magriba, nayi karatun kur'ani har akayi isha'i sanan na fito falo su basma sukazo suna tayimin surutu, ni kuwa yake kawai nake sbd duk lkcn dana tuno marin da adon gari yayi min sainji kmr nayi hauka Dan bakin ciki. Dad ne ya shigo da fara'arsa Ummi na, nace naam dad gobe idan Allah yakaimu zakiyi bako, kuma koda wasa ban yadda ki wulakantashi ba nace to yayi mana sallama ya tafi

2wks later
Naje BAGAUDA mall sayayya na fito kenan saiga jerin motocinsa sun danno kai cikin mall din tsayawa nayi INA kallonsa har aka bude masa kofa ya fito mar daga sama saiga wani mutun daga gani daya daga cikin staff din mall din ne, fada naga yanayi masa saidai bansan me yake CE masa camera ta na saita na fara daukarsa, kawai sainaga ya taskawa mutumin mari har guda biyu, bayan ya tafi na Kira mutumin muka koma gefe na tambaye shi me yayi masa yace sata yayi wa wani mutun ya bashi kaya yasa masa a mota ya boye wasu, shine mutumin yakai kararsa nace ni yar jarida ce, inaso ka juya lbrn ka da temako ka nema yayi maka shine ya mareka zanyi maka tambayoyi, idan kayi yanda nace zan baka 50k. Aikuwa ya amince

Maman aysha
[9/7, 11:39] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣5⃣➖2⃣0⃣

8:30pm
Jama'a barkanmu da warhaka, barkanmu da sake saduwa daku acikin wanan shiri namu me farin jini na ya take ne? Kamar yadda kuka Sani ya takene? Shiri ne da yake kawo muku abubuwan alajabi, ban mamaki, da kuma barkwanci. A yau shirin namu zai fara ne da abin mamaki, abin mamakinmu nayau akan shahararran matashin me kudin nan ne kabir M Bagauda, Wanda yan mata da samari suke kira da adon gari. Wata yar iskar dariya nayi sanan naci gaba"duk Wanda ya kalli video nan dana sako muku yanzu, zaiga Mr kabeer ne ya takarkare ya taskawa wani bawan Allah mari, abin mamakin anan shine, mutane da yawa suna daukar Mr kabeer a matsayin mutumin kirki, me tausayi, kuma me son talakawa. To idan har hasashen da mutane suke masa gaske ne, me ya jawo hankalinsa ya mari mutumin da na tabbata ya haifeshi? Kuma wane irin lefi wanan bawan Allah yayi masa? Masu kallo waka a bakin me ita tafi dadi bari na hadaku da baba dattijo" baba me zaka ce game da tambayar danayi yanzu? Wato abinda ya faru shine "naji mutane suna fadin temakonsa, shine naje wajensa nima ya temaka min, Amma sai aka sami akasin hakan Ina gama fada masa matsalata kawai saiya mareni yace na tafi na bashi waje. Waw idan har zan Iya tunawa ba wanan ne karo na farko da adon gari yayi mari ba, domin kuwa ya tabayi agabana. Abin mamakin anan shine me yasa adon gari ya mari baba? Kudin da baba dattijo ya nema ne bashi da shi komai? Ko kuwa adon gari ya canja raayi daga me temakon talakawa ya koma marar temako? Naso jin amsar tambayata daga wajen adon gari saidai kash ban sami ganawa dashi ba. So masoya adon gari Ku biyomu wani satin don jin yadda zata kasance, baba dattijo ya take ne? Baba yace hakan take, wata yar iskar dariya nayi nace jama'a nima nace hakan take a madadin gdn TV na pyramid TV ni Ayshat Ahamad TURAKI nake ce muku maassalam sai mun hadu a shiri na gaba.

Zaune yake ya kurawa TV din ido xuciyarsa band tafarfasa ba abinda da take, nan take wayoyinsa suka hau kuka friends dinsa ne suke kira Amma yaki dauka sbd yasan zancan zasu yi mishi, wani kiran ne ya kara shigowa saiyaga mum dinsa ce da sauri ya dauka hlo mum kabir me yake faruwa ne? Ya akayi a matsayinka na babban mutun a gari sukai maka wanan tozarcin? Ita yarinyar waye ubanta a gari da zatayi maka haka eye? Kodai wasu ne suka biyata tayi maka haka? Wallahi mum ni kaina banida amsar wanan tambayoyin naki, abinda na sani shine da gaske na mari tsohon, Kuma zamba cikin aminci yayi, kuma kinsan ba mutumin dana tsana a duniya irin me cin amana, shi yasa na mareshi. Amma karki damu mum insha Allah zan dsuki mataki akai. Mikewa yayi ya kalli Sulaiman da jajayen idanuwansa tunda uwata ta haifeni baa taba bata min rai irin Wanda yarinyar nan tayimin ba, wallahi saita raina kanta, kuma saita gane dukiya ba karya bace, duk Wanda yake da kodi yafi karfin wulakanci. Ka fadawa Barr Bashir gobe inason mgn dashi, to shikenan ranka yallabai saida safe.

Zuciyata tayi fari tas don na tabbata duk inda adon gari yake yanzu yana nan acikin bacin rai, wayata na dauko na kira baba dattijo nace baba kana ina? Yayi min kwatancen inda yake nace to ka jirani INA zuwa yanzu. Baba abinda nakeso dakai shine ka tattara kayanka kabar garin nan sbd zaka Iya shiga matsala, a wane gari kake? Yace Adamawa, OK to zan kara maka yawan kudin ya zama 150k don Allah baba ka tsarkake zuciyarka kaje kaja jari dasu, kaji tsoron Allah, kayi Sana'a ka nemi na kanka. To nagode Allah ya zaka miki da alkairi, dama talauci ne yasani, Amma insha Allah zanje naci gaba da sanaata ta saida gwanjo. Saida na saukeshi a tasha ya shiga mota sanan na tafi gida cike da farin ciki

Maman Aysha
[9/7, 15:32] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣0⃣➖2⃣5⃣

Wacece Aisha Ahamad Turaki?

Yace ga Alhj Ahamd TURAKI, Dan kwangila Wanda yayi suna duk area Kano ba Wanda be San da zamansa ba, haifaffan garin bichi ne, kuma hamshakin me kudi ne daya mallaki kamfanoni da gidaje, kuma shine mamallakin gdn TV na pyramid TV. Matanshi biyu ne, Haj bilkisu itace uwr gd yayan ta biyu Zainab da samira, ita kuma amaryar sunanta Haj Jidda yayan ta uku aysha ce babba saida aka haifeta da shekara goma sanan aka haifi yan biyu wato basma da Ahamad, alhaj sbd tsananin murna yasawa Ahamad sunansa shine ake kiransa da junior. Alhaji yana tsananin son amaryarsa sbd tanada kirki gata da son addini. Idan yana tare da ita mantawa yake yanada wata matar, kuma yanda yake tsananin sonta haka yake son yayanta, duk Wanda ya shiga gdn alhaj Ahamad a kankanin lkc zai gane alhaji yafi son Haj Jidda da yayan ta. Gabady yayan nasa sunyi degree idan ka dauke yan biyu. Zainab political science ta karnta, public admin ita kuma aysha mass communication. Da Haj bilkisu da yayanta a bichi suke da zama, ita kuma Haj Jidda a Kano da alhaj ya gama ginin damfareren gdnsa saiya debosu ya hadasu waje daya Amma kowa da part dinsa. A yanzu haka Zainab shekararta 24, samira 22 aysha kuma 18yrs.

Waye kabeer M Baugauda?
Dane ga marigayi senator muhd Tahir BAGAUDA, mahaifinsa mutumin kirki ne kuma adali Dan asalin BAGAUDA ne shekararsa 12 yanayin senator a Kano, ya kawo cigaba a jahar Wanda tunda suke samun Dan siyasa baa taba samun me kirki da temakonsa ba, wanan shine dalilin da yasa sukai ta zabarshi har saida yace ya gaji, ba a siyasa kawai ya tsaya ba idan akazo harkar business ma shahararran Dan kasuwa ne ya mallaki kamfanoni da yawansu zai kai 40, banda sauran kadorori. Matarsa daya Haj asma'u da yayanta biyu wato Salma itace babba barrister ce, tana auran wani house reps a abuja take da zama, sai kaninta kabeer shi kuma civil engineer ne he very handsome, so kind, intelligent and very respectful. Mahaifinsu ya rasu ne a hatsarin mota akan haryarsa daga abj zuwa Kano, ba Iya iyalansa ne sukayi rashin sa ba, gabadaya Mutanen 9ja ne sbd alhaji mohd dattijon arziki ne. Bayan an raba gado sai kabeer yaci gaba da kula musu da dukiyar, kuma yana samun kwangila sosai sbd governor me ci a yanzu aminin babansa ne, babansa ne ya fara sashi a siyasa, kuma ba lefi ya rike alkawari sosai. Tun rasuwar mahaifinsa ya maye gurbinsa wajen temako da kaunar talakawa, har yaso yafi mahaifinsa ma, mata basa gabanshi kuma bayasan reni. Mutane ba karamin mamaki sukayi ba da sukaga program ya take ne? Da aysha ta nuna sbd kowa yasan ba halinsa bane

Cigaban labari

Maman aysha
[9/8, 09:50] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣5⃣➖3⃣0⃣

Cigaban labari

Daga tashar gd na wuce naje nayi wanka nayi sallah, sanan na fito falo ina cin abinci muna hira da mum, su basma kuma sun Dora Kansu akan cinyata. Abba ne ya shigo yayi dariya kaga mummyn yara me kuke tattaunawa ne da yaran naki? Murmushi mum tayi sanan tace hirar duniya muke, mikewa nayi zan koma naki don naga alama yau dad acikin soyayya yake😀, kawai sainaji yace zauna ummina magna nake so muyi dake, kinsan alhaji Lawan mati? Eh Abba, deputy governor ko? Yawwa yar gari, tare muke dashi yanzu haka yana guest Palo, shine bakon danace zakiyi last WK kuma be sami damar zuwa ba sai yau, inaso kiyi sauri ki shirya kije karki bata masa lkc, sauran bayani idan kin dawo kyaji. Jiki ba kwari na tashi na koma daki, dama gown ce ajikina rolling kawai nayi na fita. Har kasa na durkusa na gaishe shi sanan ya kalli securities dinsa yace Ku bamu GU, da rawar jiki suka fice sanan ya dawo da hanklnsa wajena ba saina yi introducing kaina ba, nasan kinsan koni waye. Ina daya daga cikin masoya kallon program din da kike na Ya Take Ne? Kullum bana missing dinsa, idan ina kallo har wani nishadi nake,da ina ganin kamar program din ne yake birgeni daga karshe saina gane ke nakeso, na kamu da sonki alokacin da bansan lokacn daya shiga ba, ina tsananin sonki Aysha, kuma bazan boye miki ba matana biyu da Yaya goma. Ya salam haba baba don Allah, sona fa kace kanayi? Ba Kaine Baban su nazifi Lawan ba? Yes nazifi Dana ne, Amma kuma kace kanason karamar yarinya kamar ni, iam just 18yrs fa, don Allah ka rifamin asiri ka janye wanan maganar pliss. Bazan Iya ba Aysha da zan Iya janyewa da ban tari mahaifinki da mgnr ba, nayi kokari naga nayi ignoring abin Amma na kasa, don Allah ki temaka min
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KABEER
avatar
abubakar-adam

2 months ago

Reply

Nice one

Please Login or Register in order to submit comment