Join Our WhatsApp Group

ADON DAWA Complete Hausa Novel Document by ADON DAWA


ADON DAWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 149251



ADON DAWA

Reading Time: 12 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Jamila Umar Tanko ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 776.4 kb

File Type: txt

Views: 2183+

Download: 1648+

Last download: 1 day ago

Description/Story: Adon dawa
ADON DAWA
.
BABI NA DAYA
.
Rana ta fadi daf da magaruba dogayen motoci kirar j5 har guda bakwai ne suka shigo jahar Maiduguri daga kasar daura, dauke da fasinjoji dari uku da hamsin manya da yara, mata da maxa. Tafiya yankin axaba, hakika matafiyan cikin motocinnan a gajiye suke kallo daya xaka yi musu ka fahimci haka. A layin suke firfitowa daga cikin motocin yayin da duk wanda ya fito sai ya yi mika ya yi hamma saboda yinin da suka yi cur a hanya suna tafiya.
Kaltum ‘yar kimanin shekaru goma sha biyar tana daya daga cikin matafiyan cikin motar nan. A galabaice take a sanadiyar amaye-amayen da ta dinga yi a mota, baya ga matseta da aka yi a lungu kafafuwanta sun kumbura sumtum kamar mai cikin watan haihuwa.
A tsaye take a gefe tana jiran kakrta ta fito daga bayan bishiyar da ta kewaya don rage tumbinta daya cika da fitsari itama ta bata buta ta kewaya. Sai ta ji muryar wasu samari guda biyu suna Magana a bayanta suna Magana dogo da gajere, dogon saurayin ne ya tambayi gajeren. Ya ce “wadannan fa daga ina suke kuma ina xa su je riki-riki da kaya kamar masu gudun hijira!”
Gajeren ya bashi amsa y ace “ ‘yan gudn hijira ne ma ba kamar ‘yan gudun hijira ba. Daga nan ma gaba xasu kara har xuwa sudan xa su tafi a mota, daga sudan kuma su haura ruwa su shiga saudiya. Haka kawai mutanenmu suke wahalar da kansu saboda kwadayi, yanxu wadannan da ka gansu wahala ce xata kashe rabin su a hanya.”
Kaltum ta waiwayo da sauri ta dube su hankalinta ya kara tashi yayin da suka yi ido hudu da kyakkyawar fuskarta wacce ta basu matukar sha’awar dubanta ba kakkautawa. Dogon ya sake tambayar abokin sa gajeren, y ace, “kai, kalli wata kyakkyawar yarinya. Ba dai itama sudan din xa ta je ba!”
Gajeren ya amsa masa da cewa “sudan xata je mana, baka ganta a cikin suba!
A banxa xa a wargaxa mata rayuwarta duk kyakkyawar halittar nan tata a wulakance xa ka gansu a sudan ko makka idan sun samu ma sun haye kenan., rashin tawakkali ne kawai irin namu na ‘yan Nigeria, ba xasu iya hakuri da talaucinsu ba sai sun je kwadayi.”
Kaltum ta sukuyar da kanta kasa yayinda hawaye ya fara bulbulowa daga idanunta tana tausayin kanta tana tausayin rayuwarta. Ganin hawayen da take yi ne samarin biyu suka karaso wajenda take tsaye, suka yi mata sallama sannan suka fara tambayarta sunanta, daga inda ta fito da kuma inda ta nufa!
Babu amsa se kuka take yi kawai da suka ga halamar bata da niyar Magana sai suka fara bata shawara. Gajeren cikinsu y ace, “ ni dai a matsayi na na musulmi dan uwanki shawarar da xan iya baki shine kada ki sake ki tarki wannan tafiyar shiga makka ta sudan a matsayinki na yarinya budurwa gara ki xauna a kasarku gaban ‘yan uwanki koda ace baki da iyaye saboda bala’in dake tattare da irin wannan harkar.”
Muryar kakarta goggo fatu ta jiyo a bayanta ta kwalla kiran sunanta gami da jan dogon salati harda ihu da dora hannu a ka.
Tace, “na shiga uku, kaltum me xan gani! Me nake jiyowa ana fada miki! Ina kika samo wadannan ‘yan iskan da har suke so su baki shawara ki bujire ki fasa tafiya!”
Kan ka ce kwabo kaltum ta fara rawar jiki saboda tsoro da firgici gami da gigicewa duk suka far mata a lokaci guda. Ta fara bayani cikin rawar murya “gwaggo ban san suba wucewa suke suka xo yi suka ganni tsaye, ba xuga ni suke yi ba.”
Goggo fattu ta cije baki ta dunkule hannu ta duma mata dundu a baya gami da wurga mata butar dake hannunta a kafarta. Kaltum ta yi tsalle ta ruga da gudu gefe ta tsuguna tana kuka. Hankalin samarin ya tashi suka fara yiwa goggo bayani cewar ba laifin kaltum ba ne, suma bada niyyar xuga ta suka xo yi ba wucewa kawai suka xo yi suka ganta tsaye. Goggo ta koma kansu ta rufe su da fada tana musu korar kare wai su tafi su bata waje kafin ta farfasa musu kai. Magana daya suka fada mata wacce ta kashe mata jiki.
Suka ce “ke tsohuwa, ki ji tsoron Allah ki san xa ki mutu, Allah xai tambaye ki dalilin da ya sa kike wahalar da yarinyar nan xa ki kai ta makka ki jefa ta a wata matsananciyar rayuwa kin rabo tada iyayenta. Kuma idan ki ka yi wasa sai mun je mun hada kida hukumar NAPTIC da take da alhakin kwatarwa yara hakkin su daman suna neman irin ku masu wahalar da yara musamman ‘ya’ya mata. Kina ganin yarinyar nan ko bata fada ba kowa ya san bata son tafiyar nan dole aka yi mata saboda tsoro gashi a gabanmu mun ga irin dukan da ki ke yi mata da xagi.”
Tsohuwa ta gaggauta barin wajen da sauri gami da fixgar hannun kaltum suka kutsa cikin jama’arsu ma’ana ‘yan tawagar su ta matafiya domin ta tsorota da abinda samarin suka fada mata. Hakika sun yi gaskiya kaltum bata son tafiyar nan tilas aka yi mata.
A wannan wajen su kaltum suka yi alwala suka yi sallolin da ake bin su Axahar, La’asar, Magaruba da Isha’i. kowa ya bude jakarsa ya dauko guxirinsa yana ci, wasu buredi da miya, wasu suka jika garin kwaki da sukari da gyada wasu kuwa fura ce wacce aka murtuke da nono aka shanya ta bushe suka jika da ruwa suka xuba sukari suke sha.
Misalin karfe takwas na dare suka sake duruwa a cikin motocinsu suka ci gaba da tafiya. Kai tsaye garin gamborin gala suka nufa, basu isa ba saida tsakar dare anan suka yada xango. Garin barebari ne amman akwai wasu yaren daban daban, a bayan gari akwai wasu tsofaffin gidajen kasa anan ake sauke su daman an yi su don sauke matafiya irin su, kuma daga nan garin motocin da suka kawo su suka juya xa’a sake musu motocin da xasu ci gaba da tafiya dasu.
A gambori aka wagarar dasu dakunan mata daban na maxa daban, amma a daki daya ana xuba mutane fiye da goma sha biyar, kar ku dauka daki ne mai gado da leda da labule a’a babu ko daya, ciccirarun tabarmi ne na kaba kawannensu sai yayi matashi da kullin kayansa ko jakar kayansa.
tafiya se da suka share sati biyu cur a gambori, jagorin tafiyar su, wato (agents) suna ta yi musu karairayi kala kala su ce yau xa’a tafi gobe xa’a tafi, wasu da yawa sun kusa cinye guxurinsu don haka suka fara sayen abinci da dan kudaden da suka boyo. Saboda gashi ba’a yi rabin tafiya ba ko Nigeria ba’a bari ba guxurin ya kusa karewa. Mutane biyu ne suka riga mu gidan gaskiya a cikin matafiyan tsoho daya da yarinya matashiya daman tun a hanya basu da lafiya anan aka sallace su aka binne, ‘yan uwansu suka sha kuka.
Matafiya sai mita suke yiwa agents babu ranar da yawa daga cikinsu basu yi kuka ba saboda wahala. Daga inda suke xuwa cikin gari yana da nisa haka suke faman tafiya kafin su je su siyo abunda xa su ci ko debo rowan da xasu yi wanka da wanki. Kowa ta kansa yake, babu babba ba yaro, babu mace babu na miji, babu mai taimako ko tausayin dan uwansa. Akwai mata masu ciki da yawa wasu karamin ciki wasu kuwa tsohon ciki ne, wasu masu goyo amma dole kowacce ta fita ta yi doguwar tafiya sannan ta nemo abinda xa ta ci, ta debo rowan da xata yi wanka da wanki.
A ranar da suka cika sati biyu aka kawo musu katuwar motar nan da aka yi ta musamman don daukar kaya wato tirela. A bayan motar aka dura su gaba dayansu su da kayansu kamar wasu shanu. Bayan haka aka jibga masu buhuhunan gyada da ridi wadanda xa’a sayar a sudan har buhu dari duk a bayan motar. A cunkushe suke a tattakure kafada a marmatse babu wanda xai iya mike kafarsa, da yawan su basu sami waje ba a bayan motar sai a saman mota aka loda su.
Kwalta ta kare don haka cikin kasa (sahara) ake tafiya, tafiya suke yi a mota amma a wahale suke tamkar da kafarsu suke tafiya sun jigata don haka rayukansu kowannensu a bace yake, babu abinda yake tashi a cikin motar sai kyara da bakaken Magana a jima kadan ka ji fada ya tashi ana sursurfawa ashar gunduwa gunduwa. Wannan tace waccan ta matseta sai wannan yace wancan ya shure shi aikin kenan.
Bayan sun yini suna tafiya suka isa kusuri, a dawa aka sauke su a nan ma saida suka yi kwanaki biyu. Sai dai kowannensu ya shimfida xaninsa ya yi filo da kullin kayansa. Babu famfo ko rijiya a kusa don haka jarkokin ruwa agents suke kawo musu jarkoki hudu a tartarfawa kowa a kwanonsa ya sha ya jika gari, alwala kuwa sai taimama babu batun wanka.
Daga kusiri sai suka nifi chadi (N’DJAMENA), basu yi niyyar kwana a N’djamena ba amma dole suka kwana a sanadiyyar ruwan da ya dates hanyarsu ta wucewa. Rowan daga cikin dutse yake bulbulowa ya dates hanyar wucewa dole motoci suka dakata har saida rowan ya tsaya, ruwa ya kafe hanya ta bude amma se da shirin tafiya ya wargaje dole suka sauke kayansu daga cikin mota a sanadiyar wasun su guxirin su ya kusa karewa sai sun nemi kudi sannan a ci gaba da tafiya. Nan fa matansu da maxajensu suka baxama cikin gari neman kudi sune dako, wankau faskare da dai sauransu. Satinsu uku a Ndjamena sannan suka kama hanya, a boda kuma ake sake duba takardarsu wato anan ake duba passport da visa sannan su wuce.
Daga N’djamena sai suka shiga Abbashe nan ma a bayan gari suka yada xango cikin rubabbun gidan katako, tabbas basu yi niyyar wuce kwana daya ba a Abbashe amma hakan bai yiwu ba a sanadiyar nakuda ta wata mace ke yi, yini guda ana abu daya da kyar aka samu dan da yake cikinta ya fito, ya fito da rai amma bayan awanni ya rasu.
A ka’idar garin duk wanda ya mutu sai an sanarwa da maigari ya rubuta takarda an nunawa hukumar da abunda ya shafa sannan xa’a yarda a binne gawa. Don haka hankali ya tashi ana tunanin yadda xa’ayi doguwar tafiya xuwa cikin gari, sannan a yi ta dogon bayani kafin su yarda a binne yaron. Daga karshe aka yi shawara a nannade gawar jaririn a kunshe a tsumma sai a sami mutum daya ya xagaya dawa ya binne gawar jaririn. Haka kuwa aka yi aka binne cikin dare. A daren kuma Allah Ya yiwa mai jegon rasuwa itama daman tunda ta haihu bata da lafiya.
Nan fa hankalin kowa ya tashi ‘yan uwanta sai suka yi ta kuka suna kururuwa. Da yawa daga cikinsu kaltum suma suka yi ta kuka duk da basu santa ba, haduwar motace kawai sai dai don tausayin rai da tausayawa kansu da kansu. Dakin da kaltum take shine dakin da aka yi mutuwar don haka a xaune suka kwana tangarai ko gyangyadi basu iya yi ba. Kaltum na lungu jikinta sai tsuma yake, hawaye ke kwaranya saboda tunda take bata taba ganin gawa ba,. Ta ji dama ace itace ta rasu kamar yadda wannan baiwar Allah ta rasu. Tana tunanin yadda rayuwa xa ta kasance mata nan gaba.
Da gari yawaye direban da jagorannin tafiyar (agents) suka hadu suka tafi wajen maigari ,dan gari ne ya jagorance su cikin yarensu mai suna wadai dan rakiyar ya yiwa sarki bayani cewar wadannan baki ne suka xo daga Nigeria xasu wuce sudan, suka yada xango a wajen gari sai Allah Ya yiwa mace daya rasuwa suna so su binne ta a nan. Sarki ya yi amanna ya basu takarda suka je suka nunawa masu jiran makabarta, sannan aka yarda suka binne ta bayan suna sallace ta kamar yadda ake yiwa kowane musulmi.
A ranar suka sake kama hanya suka ci gaba da tafiya, yini guda cur a mota har dare ba tsayawa saida kyar direban ya yarda ya tsaya a wani gari da ake kira Adre suka yi sallah suka ci guxurinsu garin kwaki ne dai, sannan suka ci gaba da tafiya. A xaune suke tangarai, se gyangyadi kowa ke yi a xaune. Gargada ce a dukkan hanyar a sanadiyar rashin kwalta, idan mota tadaka tsalle sai ka ga mutum ya yi sama ya dawo ya xauna dabas, idan aka yi rashin sa’a wanda ke xaune sai ya dawo sama dororo a jikin mutane matsi ya hana direwa a xauna daidai sai dai idan motar ta sake daka tsalle adan ka yi sa’a sai ka sami wajen xama wani kuma ya xama derere shi ba xaune ba kuma ba tsugunne ba, shi ba a kasa ba shi ba a sama ba.
Sai cikin dare suka isa jinene bayan sun yi sallolinsu suka haba garin kwaki da busashiyar gurasa sai suka ci gaba da tafiya, kwana daya da yini daya da yini daya guda cur suka yi a hanya suka isa wani gari da ake kira mukwar. Bayan sun huta a mukwar sai suka ci gaba da tafiya babu abun da yake kan hanyar nan sai namun daji, xuma caba caba ga ‘yan fashi. Basu tsaya a ko ina ba sai da dajin majawara.
Dajin majawara daji ne wanda yake shiru, tsit ko kukan tsuntsu babu balle gidajen bil’adama. Daga nan kowa dakatawa babu mahalukin da xai iya tsallakewa a sanadiyar tsantsar hadarin da ke tattare da ci gaba da tafiya. Dole ne duk motar da ta xo dajin majara sai ta ja ta tsaya a doka har sai motoci saba’in sun cika sannan sojoji su xo su tsallakar dasu saboda mugaye, kasurguman ‘yan fashin da suke fashi a hanyar. Don haka said a ‘yan tawagar su kaltum suka yi kwanaki uku a nan suna jiran motoci saba’in su cika sannan a hayar dasu.
A ranar da suka cika motoci saba’in sannan aka shirya ci gaba da tafiya a lokacin da xa su tafi da yamma wani dankareren maciji ya sari daya daga cikin ‘yan twagar su kaltum, kan ka ce kwabo mutumin ya sassankare kumfa na xubowa daga bakinsa. Jama’a suka bi macijin da jifa amma tuni ya sulale ya shige dawa basu kashe shi ba, daga karshe mutumin ya mutu a wajen, a nan aka binne shi suka shiga motocinsu suka fara tafiya. Amma a kowace mota said a sojoji bibbiyu suka shiga suna harba bindiga sama har sai an wuce mugayen daxuka da barayin suke. Tun da yamman da suke tafe ba tsaya ba har se da gari yawaye, sannan sojojin suka sassauka daga motocin da suka rako suka shiga motocinsu suka juya. Sannan su kuma matafiya suka ci gaba da tafiyarsu.
Tafiyar kwana biyu...


Read / Download ADON DAWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album