Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

AURE KO BOKO Complete Hausa Novel Document by AURE KO BOKO


AURE KO BOKO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 43587



AURE KO BOKO

Reading Time: 3 Hours

Added On: 20, Jun 2024

Author: Sumayya Abdulkadir Takori ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07030137870

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 228.1 kb

File Type: txt

Views: 1287+

Download: 1169+

Last download: 2 days ago

Description/Story: 
AURE KO BOKO?
(Littafi Ga Matasa Maza da Mata)



















SUMAYYAH ABDULKADIR
[email protected]



GABATARWA
Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai.
Duba da halin da matasa ke shiga a kasarmu Nijeriya a yau, daga mazan har matan, akan rashin aikin yi ga wadanda suka samu damar yin ilmin zamani mai zurfi da matsalolin da hakan yake haifarwa, sannan da halin wasu daga cikin manyan 'yan bokon wannan zamani na baiwa boko fifiko akan addini, yasa na yanke shawarar rubuta littafin AURE KO BOKO? Ba don komai ba sai domin ya zamo hannun ka mai sanda ga irin wadannan 'yan boko da matasa masu zurfin ilmi marasa aikin yi. Tasirin furucin iyaye akan 'ya'yan su mai kyau ko maras kyau, hakika shi bakin iyaye kaifin sa da tasirin sa yafi na reza. Sannan 'ya'ya amana ne a hannun mu, kasancewar Ubangiji yayi musu umarnin su yi wa iyaye biyayya sai da yayi tagociya ga cewa banda akan umarnin Ubangiji.

Ina fatan wannan dan littafi ya zamo mai amfani ga al'umma, matasa maza da mata, ya zamo sadaqatul jariya ga iyaye na ya yafe min kurakuran da ke cikinsa.
- Sumayyah Abdulkadir (Takori)
3rd June, 2021

GARGADI
Ban yarda a karanta wannan littafi a kowanne gidan radiyo ko kafafen yada labarai ba tare da izni na ba, ko copying dinsa a kafafen sada zumunta, yin hakan karya doka ne kuma abin tuhuma daga Lauya na Barr. Sadiq Rufai Wali.


GODIYA
Ga dukkan members na Takori's online Forum, na gode da kaunar ku da goyon bayan ku.


FATAN ALKHAIRI
Ga duk makaranta littatafan TAKORI. Wadanda na sani da wadanda ban sani ba, ina godiya da yabo da fatan alkhairin da kuke yi mun, Allah ya barmu tare cikin alherin sa, har zuwa ranar da muka daina numfashi.







SHIMFIDA
BABI NA DAYA
A cikin babbar hedkwatar hukumar sadarwa ta kasa (Nigerian Communications Commission) da aka fi sani a takaice da (NCC) da ke kan titin Aguiyi Ironsi Street, Maitama, Abuja, motocin ma’aikatan su ke ta shigowa daya bayan daya harabar ma'aikatar suna fakawa a faffadar harabar ma'adanar motoci, wannan motar na wane waccan, duk da cewa ba ranar aiki ba ce, amma alamu sun nuna wani muhimmin taro ne za su yi na iya ma’aikatansu tare da (Board of Commissioners) din su a babban dakin taron su wanda ya fi kowanne girma cikin ma’aikatar. Duba da yadda suke ta shige da fice don ganin komai ya kammala ya yi yadda ake so kafin isowar Executive Chairman.
Kowannensu tsuke cikin suit mai kalar fari daga ciki, baki daga waje, wuyan ya sha tsuka da tie din bature, da takalma bakake sau ciki a kafafun su. Sai da duk suka gama hallara a dakin taron, suka nutsu wajen zaman su, kwamishinoni suka iso suka zazzauna, sannan suka ji daga wajen hall din dirin isowar jibgegiyar motar Executive Chairman wato PROF. ZUBAIR MOHD. NUMAN.
Farin dattijo mai kyakkyawar suffar fulanin usli da tsantsar ilmin boko. Inda ace ana kure boko to da mun ce Prof. Numan ya kure shi. Shi din fitacce ne, kuma sananne a kasarmu Najeriya akan harkar sadarwa, domin ya dade yana rike da manyan mukamai daban-daban a gwamanatin tarayyah tun kafin ya karbi ragamar (NCC), sannan tsohon malamin jami’ar Igbinedeon ne.

Prof. Zubair Muhammad bafullatanin garin Numan ne, don haka kallo daya za ka yi masa ka tabbatar an zuba kyau a zamanin kuruciya. An sha gwagwarmaya a ilmin boko da ma’aikatun gwamnati, sannan ana kan damawa da shi a shekarun girman sa, domin kuwa na hannun daman shugaban kasa ne, duk da ba ya siyasa, shi ne ya dora shi matsayin da yake kai a yanzu, wato Executive Chairman na Nigerian Communication Commission (NCC).

Prof. Zubair ya shigo hall din cikin kakkarfan takunsa, da ganin sa ka ga bakin bature, a gefensa hagu da dama wasu santala-santalan ‘yammata ne guda biyu; a ido daya ta girmi daya, sun yi shiga irin ta ‘yammatan zamani gogaggu, ‘ya’yan gata irin su, wato ‘ya’yan kusoshin gwamnatin Najeriya. Tafiyar su kadai abar kallo ce, yayin da suka maka bakin glass (prada) wanda ya cinye kusan rabin fuskar su. Mayafin jikinsu shi da babu duk daya. Har gara na babbar. Kallo daya za ka yi musu ka tabbatar ‘ya’yansa ne na cikinsa, sabida tsananin kamanninsu da mahaifin nasu, duk da cewa sun fi shi hasken fata kasancewar su mata.
Shigowar su hall din ke da wuya gabadaya ma’aikatan suka mike domin girmamawa ga shugabansu. Har sai da ya zauna a kujerar sa tare da ‘ya’yansa a dama da hagunsa a kujerar musamman da aka tanadar musu, sannan gabadaya ma’aikatan suka zauna a mazaunin su.
Bayan addu’ar bude taro daga limamin ma'aikatar mai gabatarwa ya yi bayanin makasudin taron, wato taron ba na komai ba ne, na taya murna ne ga ‘ya’yan shi Prof. Zubair ga kammala karatunsu daga jami'ar National Autonomous University, Mexico. Sannan Prof. Zubair ya mike ya yi jawabin godiya ga ma’aikatansa da kwamishinonin sa a kan hadin kan da suke ba shi wajen gudanar da ayyukan su na sadarwar Najeriya.
A karshen bayaninsa kuma ya ce, daga yau ya dora babbar ‘yar sa Engnr. Halimah Zubair Numan matsayin mataimakiyar sa wato (Executive Vice Chairman), ya kuma dora kanwar ta Hanan Zubair Numan a matsayin (Human Resource Manager), za su shiga ofis daga wannan satin mai kamawa.
Yana fatan za su ba su hadin kai wajen gudanar da ayyukan su tare da su, kamar yadda suka saba bashi. Su sani cewa ba ya hada komai da wadannan ‘ya’yan nasa guda biyu, dalilin sa ke nan na kawo su kusa da shi su yi aiki don ba zai iya barinsu su yi aiki a karkashin wani ba, balle a taka mishi su, shi ya sa ya kawo su karkashin sa.
Hanan sai gyada kai ta ke kamar jangwalagwada, tana taunar cingam kas-kas-kas, cikin jin dadin bayanan da mahaifinta ke yi. Ai gara duk su san matsayin su a gun Daddy tun yanzu, kada ma su kawo musu raini don sun gan su yara. Yayin da Haleemah ta sunkuyar da kai cike da jin kunyar wannan rashin kawaici na mahaifin ta. Me ya hada harkar ofis da kaunar da yake musu saboda Allah? (This is personal).
Daga nan shugaban bangaren daukar ma’aikata na baya (former Human Resource Manager) wanda yanzu ya koma karkashin Hanan ya mike cikin rashin jin dadi ya yi wa ‘ya’yan Prof. Zubair barka da zuwa ma'aikatar NCC, tare da alkawarta musu cewa, za su samu duk hadin kan da suke bukata tare da su. Ya yi bayanin ne cikin cijewa a madadin sauran ma’aikata, duk da kokarinsa na boye damuwar wannan ragin mukami da aka yi mishi da ‘yar cikin sa rana daya.
Daga nan aka fara ciye-ciye da shaye-shaye na alfarma, zukatan ma’aikata cike fal da magana wadda ba wanda ya isa ya furta. Don haka kowa ya hadiye abarsa. Taron da ya dauke su awanni biyu cif! Kafin a watse direba ya kwaso su Halima da Prof. Zubair zuwa gida.

Gidan Prof. Zubair na nan a unguwar Asokoro, wani tankareren gida mai ginin sama-da-kasa. Gabadaya ginin gidan an dauko samfur dinsa ne daga kasar Brunei. Sai dai abin da zai ba ka mamaki shi ne; daga shi sai ‘ya’yansa biyu suke rayuwa cikin wannan tafkeken tankareren gidan, sai tarin ma’aikata rututu maza da mata. Babu matar aure a cikin sa.

Asalin Prof. Zubair ya fito
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download AURE KO BOKO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album