Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kin gaji da yawa koh"
Tace"um um MK wlh nasa raina a fitar nn dan Allah muje"
Yace"ae tunda kina so za'a je d'in,tashi muje to muyi wanka sae mu shirya mu tafi"
Tare suka tashi zaune Ryynt ta rungumo sa tare da shafo cikin sa tace"cikin ka kmr kana jin yunwa"
Yace"wlh kuwa yunwa nakeji sosai kema nasan kina jin yunwar koh?
Tace"um um ba sosai ba kasan kafin mu koma bacci naci nmn kaza bari na kawo maka kaima kaci sae muyi wanka koh"
No kawo min fresh milk kawae nasha idan muka fito wanka sae muyi breakfast gabad'aya.
Nan ta tashi ta jawo bathrobe ta saka snn taje ta tsiyayo masa fresh milk a cup ta dawo ta same shi shima ya saka bathrobe d'in sa yana zaune akan bed yana duba missed calls d'in da ya gani a wayar sa don tun zasu koma bacci ya saka ta a silent.
Yana ganin ta dawo ya ajiyar wayar ,
ta zauna a kusa dashi ta bashi fresh milk d'in da kanta har sae da ya shanye snn suka je zuwa wanka basu wani jima sosai ba suka fito suka shirya snn sukayi break fast suka fita.

Da dare mohd ne zaune a falo kan doguwar kujera yana sanye da farar singlet n boxer yana kallon labarai yayinda Ryynt ke kwance kan qafafuwan sa tana sanye da farar rigar baccinta silk mae d'an siririn hannu da tsayinta ba zae wuce iya cinya ba ,wacce tuni tayi bacci sbd gajiya dmn yau yawo sukayi sosai a cikin garin mumbae wato gurare daban daban na bud'e ido da kuma gurin shaqatawa sukaje kuma duk inda sukaje sae da mohd yasa aka musu photo shida ita snn sukayi dasu Amir da matar sa da kuma d'an d'ansu sadiq dan duk tare suka fita shiyasa basu dawo ba sae yamma da kaya niqi niqi na en tsarabar da Ryynt ta siyo.
Da ya gama kallon labaran sa ne ya kashe TV ya d'auki Ryynt ya shiga ciki da ita.

Washe gari ne suka je Germany kwanan su biyu a can suka kammala abinda suka je yi suka tafi dubai sukayi kwana biyu dmn hutawa inda a germany har dubai sae da man yaja Ryynt suka zaga gari dmn ta bud'e ido.
Bayan sunyi kwana biyu a dubae ne washe gari suka kama hanyar dawowa Nigeria.

6anaren malika kuwa safiyar yau sae murna take tayi dan man ya kirata ya snr da ita yana hanya har ma ya snr da ita lokacinda jirgin nasu zae yi landing ai kuwa tasa aka shirya masa hadaddiyar liyafa wacce tana ganin lokacin saukar jirgin su ya kusa taje tayi wanka ta tsala ado taja motar ta sae Airpot dmn tarbon mohd wacce kwata kwata bata san cewa tare da Ryynt yake ba dan har yanzu bata da labarin komai asalima shaf ta shafe babin Ryynt a cikin rayuwar ta.




Billy giro??

```??BAZAN BARSHI BA!??```

????????
*page 78*
Da isar ta ne jirgin nasu ya sauko mutane suka fara firfitowa kan farin ciki bakin ta baya ko rufuwa sae rarraba ido take ta inda zata hango mohd.
Kai tsaye duk wani farin cikin nata a take ya tafi numfashinta ya nemi ya d'auke,
ganin mohd tafe cikin baqar suit maqale da Ryynt a jikin sa tana sanye da arabian gown baqa tayi rolling da black top kmr wata balarabia dan gabad'aya ta canza mata ta qara kyau da haske da ita har mohd d'in sae sheqi suke ga wani murmushi da suke da ya qara musu kyau suna tako cikin natsuwa.
Sam malika ta kasa gazgata abinda take gani musamman hannun mohd da ta hango ya zagayo dashi ta kunkunmin Ryynt yazo dashi har izuwa kan tulun cikinta da ya fito 6aro 6aro da cikin ne abinda yafi matuqar bata mamaki don har suka qaraso ta kasa gazgata abun wae kodai mafarki ne ba gske ba gashi ko qaramin yatsanta tama kasa motsawa sae dasqarewa da tayi a guri d'aya ta kafe su da ido tana kallo Nasir yaje ya tarbe su cike da murna.
Yayin da su saliha da mami dake tare dashi suka qanqame Ryynt cike da murnar ganin ta kafin suke zuwa gun matar Amir itama suka tarbe ta.

D'auke da murmushi mohd ke kallon malika dake qarasowa gurin su wacce tana isowa cikin tsananin 6acin rae ta damqo suit jacket d'in mohd da hannuwanta duka biyu ta jijjiga shi tace"gaya min shin mafarki nakeyi ko kuwa da gaske ne dae wnn abar ce nake gani a tare da kai!
Da qarfi mohd ya buge hannuwanta ya jawo Ryynt zuwa jikin sa yace"kin ganta gata ba mafarki kikeyi ba dagaske ne kuma wlh kar ki kuskura ki sake kiranta da wnn abar idan ba haka ba wlh zanyi mugun sa6a miki very stupid!
Nan kawae malika tayi kukan kura zata shaqo wuyan Ryynt man yayi saurin ture ta gefe
snn ya nuna ta da yatsa yace" Ryynt she is my wife n my life bazan ta6a yarda kici zarafinta ina tsaye ba and idan har kinsan tashin hankali ya kawo ki maza bar gurin nn in daina ganin ki ko kuma wlh na miki dukan tsiya a nn!
Tsaf tasan zae iya aikata abinda yace ta kalli Ryynt ta qyasta yatsunta tare da nuna ta tace"wlh wlh yau sae na zamo ajalinki"
Daga haka ta wuce fuuu a fusace.
Mohd dake kallonta ya buga tsaki dan shi a shirme ma ya d'auki zancen nata ya kalli Ryynt wacce still tana a jikin sa yace"Ryynt are u ok bata ta6a ki ba dae ko?
Ryynt ta girgiza kanta tana qoqarin maida hawayen da suka cika mata ido ba wae don ta tsorata da jin furucin malika ba sae don ko kad'an bata ji dad'in abinda ya faru ba har dae yanda gabad'aya gurin idon kowa ya tsaya a kansu har ma wasu na nuna su suna magana.
Nasir da Amir ne suka ce da mohd "wae me yake faruwa ne?
Mohd ya buga tsaki yace"da Allah ku fita batun mahaukaciya kuzo mu tafi"
Daga haka suka wuce ba wanda ya sake cewa komai.

Amir da matar sa da d'ansa motar su suka shiga da driven su yazo da ita yaja su zuwa family houshe.

Mohd da Ryynt kuwa motar Nasir suka shiga dasu har su saliha wanda basu zarce koina ba sae gidan inna wacce tana ganin Ryynt ta washe baki cikin tsananin murna suka rungume juna inna ta d'ago riqe da baki sae kallon Ryynt take cikin jin dad'i ganin yanda kallo da'ya zaka yiwa Ryynt kasan cewa tana samun matuqar kulawa da jin dad'i musamman yanda fatar ta tayi smooth da haske tayi fresh da laushi kmr ftr sabon jinjiri sae sheqi take tana qyalli.
Washe da baki inna ta qwalawa baaba hurera kira baaba hurare taxo da murna ta musu sannu da zuwa wacce itama ta kasa rufe baki sae kallon yanda Ryynt ta canza take.
Washe da baki inna tace"kema kinga yanda Rayyanah ta dawo ko awa wata balarabiyar saudia ai Alhamdulillahi ba abinda zance da kae Muhammadu sae nace Allah shiyi maka albarka dmn ba makawa Ryynt ta sami sauyi da kulawa a gurinka haqiqa naji dad'i wlh ubangiji Allah sarkin halitta shi qara yi maka albarka.
Mohd yace"Amin Amin inna"
yayinda yake kallon Ryynt dake murmushi tana fmn 6oyon tulun cikinta da take jin kunyar a gani.
Kai tsaye taga mohd ya d'aura hannun sa akan cikin nata yace"inna kalli d'an jikanki ki fa yanda ya taso"
Wata irin kunya Ryynt taji kmr ta nutse tayi saurin ture hannun sa zata bar gurin mohd ya janyota zuwa jikin sa yana dariya,a shagwa6e ta fashe masa da kuka ta qwace kanta ta koma jikin inna ta 6oye fuskarta a qirjinta tana ci gaba da kukan da ta soma maida shi da gaske don rugumar da ya mata yasa ta qara shiga wata kunyar.
Ya riqo hannunta yace"zo ni na 6oye ki a nawa qirjin tunda kunya kike ji.
Da sauri Ryynt ta fizge hannun ta yayinda inna ta girgiza kanta d'auke da murmushi tace"Allah ya shirye ka muhammadu snn ta shafo bayan Ryynt tace"qyalesa Ryynh yi shiru daina kuka ae yau ya jawa kansa don baza ki koma gidan sa ba
sae ya zo biko"
Mohd yayi saurin kama kunnen sa yace"Aa inna amin afuwa bazan sake ba na tuba"
Inna tace"kaja kunnen ka ma yafi na zomo tsayi bazan haqura ba sae kazo biko tunda har kasa min ita kuka.
Mohd ya shagwa6e fuska kmr qaramin yaro yace"inna nine fa"
Tace"kaiwa daga ina"
Mohd yace"mai gidan naki kuma inna Baaba hurera kinaji fa"
Baaba hurera dake kallon su ita da su Nasir suna murmushi ta girgiza kanta d'auke da murmushi taje da sauri dmn kawo musu abinci da lemu da ruwan sha kmr yanda inna ta umarce ta.

A nn tsakiyar falon aka shimfid'a qatuwar darduma Baaba hurare ta jera kulolin abinci akai da ruwa da lemu wanda dama musamman dan su aka had'a.

Zasu fara cin abinci knn wayar mohd ta shiga ring koda ya duba mae kula da harkokin gidan sa ne ya kirashi yake snr dashi irin 6arnar da malika ke aikatawa a gidan shi don sae farfasa abubuwa take.
A natse ya kalli Nasir yace"plz bani makullin motar ka"
Ba musu Nasir ya miqa masa makullin yace"lafiya dae ko"
Yace"ba wani abu bane yanzu zan dawo inshaa Allah"
Daga haka ya fita Ryynt ta bisa da ido sae ga inna ta fito daga ciki d'auke da fruits salad mai sanyi da ta ciro a cikin fridge taga bata ga mohd ba tace"Aa ina kuma muhamnadu ya tafi"
Tayi mgnr ne tana mai kallon Ryynt wacce bata iya cewa komai ba sae Nasir ne yace"an kira sa ne ya d'an fita ya dawo"
Inna tace"ayyo"
tare da ajiye fruit salad d'inda ke hannun ta.

Mohd kuwa yana isa gida yayi tsaye a cikin falo hannuwan sa cikin aljihu yana kallon yanda gun dining duk yayi kaca kaca malika duk ta watsar da liyafar da tasa aka shirya mae ta kuma farfasa duk sabbin kayan da yasa aka zuba a falon na gyaran gidan da yasa akayi gabad'aya duk wani abin fashewa bata bar shi ba har TV kuwa.
Yana tsaye sae gata ta fito kitchen riqe da wuqa sabuwa dal zir sae qyalli take.
Tayi kmr ma bata ganshi ba ga mamakin sa sae sauri take ta fita yayi hanzarin fizgota yace"ke ina kuma zaki je da wuqa"
Bata masa magana ba sae qwatar kanta da take qoqarin yi ya qara damqar ta had'e da daka mata tsawa yace"ina zaki tafi nace!
Ta fizge kanta tace"so kake kaji to gurin wnn abar zan tafi don wlh yau bazan barta da rai ba sae na hallaka ta na kuma hallaka abinda ke cikin cikin.....bata qarasa fad'a ba taji saukar wani irin gawurtaccen mari ya kuma ja hannun ta ya tafi da ita sae fizge fizge take har ya kaita d'akin ta ya jefar ya fito ya rufe d'akin ya xare key ya saka a aljihun sa ya fita yana mamakin hauka da baqin kishi irin nata.

Gidan inna ya koma Nasir ya kar6i makullin motor sa ya fita zuwa aiken da inna ta mai wacce tana bashi saqon ta koma daga ciki sbd wayar ta da taji tana ring.
Ya kasance falon ba kowa don mohd yana fita Ryynt taja su saliha suka tafi d'akinta da inna tasa aka share tun jiya da taji zasu dawo.
Ya nufi d'akin kai tsaye ya same su zaune su uku suna cin abinci a mazubi d'aya sae firar bayan rabuwa suke cike da nishad'i.
Ba tare da yace musu komai ba ya riqo hannun Ryynt ya fito da ita zuwa falo suka zauna kan darduma da abincin sa ke ajiye da aka sa d'ayan plate aka rufe ya bud'e abincin yace"muci wnn sae ki bar musu wancan suci gaba da ci"
Tace"meyasa abincin fa yana da yawa baza su iya cinye sa ba na mu uku ne muka d'iba"
Yace"eh ki bar musu kawae"
Ya fad'i hakane tare da d'ebo abinci a spoon zae kai bakinta tace"mk nifa ina jin kunyar inna tazo ta same mu muna cin abinci a tare"
Nan kawae ya tashi yaja hannun ta riqe da abinci suka tafi d'akinta da niyar suci a can ,
gashi ita ko a gaban su saliha d'in bata iya cin abinci a tare dashi,
tace"plz Mk tafi kawae kaci abinka ni sae na ci gaba da ci tare da su saliha kaji.
Man da har ya zauna kan sofa ya kalleta kawae bae ce mata komai ba ya tashi ya fita d'auke da alamar fushi a fuskar sa.
Jiki sanyaye Ryynt ta zauna dmn ci gaba da cin abinci tare da su saliha.
Saliha dake kallonta tace"is better ki tashi kije ki bashi haquri kici abincin dashi dmn ga dukkan alama fushi yayi"
Ryynt da qwallah suka taru a idon ta tace"Saliha kunya nakeji da dae mu kad'ai ne zan iya"
Saliha tace"olryt bari to mu koma falo nida mami sae ku dawo a nn kuci"
Saliha ba haka nake nufi ba ,saliha da ta fhmce ta tace"to ai sae ki zauna mijinki na fushi dake mala'ikun Allah na tsine maki"
Ryynt ta kalli saliha ,mami tace"kije mana Anti meye abin kunya dan kinci abinci da yaya nima fa da muna gidan sa a tare muke cin abinci kin sani"
Ryynt tayi d'an guntun murmushi tana kallon mami snn ta tashi taje falo ta samu mohd ya mayarda abincin ya rufe zae fita don har ma yakai bakin qofa.
Ryynt ta kira sunan sa a hnkli.
Ya tsaya kawae ba tare da ya juyo ba.

Taje ta riqo hannun sa ya juyo yana kallon ta tace"MK ina zuwa kuma baka ci abinci ba?
Yace"zanje inda za'a bani ba tare da na roqa ba"
A nn tayi saurin sadda kanta qasa d'auke da hawayen da suka cika mata ido don sae taji wani irin kishi duk da taga yanda suka kwashe shida malika a airpot.
Murya can ciki tace"yi haquri muje na baka"
Yace"tafi kawae kici inda kike son ci d'in ni ki barni na tafi abuna"
Hawayen da suka cika mata ido ne suka silalo a hnkli ta share hawayen jiki sanyaye ta juya zata bar gurin,
Jiki sanyaye mohd ya riqo ta yace"meye na kuka kuma Ryynt inace kinfi ra'ayin kici abincin a tare da su shiyasa nace ki tafi"
Ryynt tace"Allah ba wani nn fushi kayi "
Ya janyo ta zuwa jikin sa yace"to yi haquri kuma ni ba fushi nayi ba dama na gwada ki ne kawai inga ko kina son mijinki da gaske sae naga ashe ke dad'i miji ce da ba kya son ganin fushin sa.
Da wasa ta sha toka tace"me kake nufi?
Ya d'aura mata kiss kan lips yace"abinda kika fahimta shi nake nufi"
A shagwa6e ta maqale kafad'a tana doka qafafun ta qasa tace"wlh Aa ni ba dad'i miji bace"
Ya lakato hancinta tare da fad'in"ba wani nn na gano ki ae"
Kuka ta fashe dashi ta shiga kai masa duka irinta ta shagwa6a tana fad'in"wlh Aa ni ba dad'i miji bace"
A nn Mohd ya shiga kare dukan sae dariya yake ita kuma sae ci gaba da dukan sa take tana fad'in ita ba dad'i miji bace shidai ne haka ba ita ba nn ya kama yatsan ta ya gantsara mata d'an qaramin cizo ya gudu ya barta sae kukan shagwa6a take tana yarfi da hannu yaje kan darduma ya zauna tabi shi ta kama yatsan sa ta rama ya shiga yarfi da hannu sae dariya take masa dan da gaske ta cije shi, ganin zae kama hannun ta ya rama ta tashi da sauri ya biyota dai dai inna ta fito taje bayan inna ta la6e sae gwalo take masa tañà dariya.

Sorry 4 dis one

Billy giro??
????????????????????
```??BAZAN BARSHI BA!??

????????
*page 79*
Nan mohd ya shiga qoqarin ganin ya janyota inna bata barshi ba sae fad'in take wae muhammadu lafiyarka?
Yace"Inna cizo na fa tayi"
Ryynt tace"wlh inna shine ya fara ni kuma na rama"
Ta qarashe mgnr tare da yi masa gwalo bata ankara ba sae ganin tayi ya jawota tace"wayyo Allah yi haquri inna zae rama dan Allah ce yayi haquri bazan sake ba wlh"
Inna taje zuwa qwace ta mohd yace"inna wlh ba abinda zan mata abinci zamu ci"
Ryynt tace"inna ba wani nn ramawa zae yi"
Ta fad'i hkne yayin da take yunqurin komawa ga inna amma bata iya ba dan man sae d'aukar ta yayi cak tana wuntsil wuntsil da qafafu har yaje da ita kan darduma nn inna tayi murmushi had'e da girgiza kanta ta tafi ta basu guri dan ta fhmci mohd ba kunya ne da shi ba.
Ryynt kuwa cikin fushi ta kalle sa tace"wae meyasa kake min abubuwan da kake sa ina jin kunya dan Allah ban so ka daina"
Ta qarashe mgnr cikin muryar kuka mohd ya d'aura mata kiss kan lips yace"to naji yi hqr muci abinci"
Ta tashi tare da fad'in"banci"
Mohd ya riqo ta ta buge masa hannu yayi saurin kama hannun nasa had'e da fad'in "Ash!
ya yaye hannun rigar sa wata irin babbar yankuwa ta bayyana yayinda hannun farar rigar sa ta ciki duk ta lalace da jini.
Da sauri Ryynt ta koma ta zauna ta riqo hannun sa tana kallon gurin ta kalle sa idon ta tap da qwallah tace"mk me ya same ka haka?
Bae ce mata komai ba sae kallon yankuwar yake yana tuna lokacinda yaja malika zae kaita d'aki ne wuqar hannunta ta yanke sa garin fizge fizgen ta.
Ya kalli Ryynt wacce duk ta rud'e tana basa haquri had'e da tambayar me ya same shi .
ya shafo fuskarta yace"d'an wani tsautsayi ne ya same ni d'azun da na fita amma kar ki damu kinji"
Ryynt da hawaye suka silalo kan fuskarta ta kalle sa tace"wnn ne d'an jifa yanda yankuwar tayi babba sosai warkewar ta ma zae yi wuya"
Ta qarshe mgnr ne cike da son fashewa da kuka.
Mohd da saurin kukanta ke bashi mamaki gashi baya son ganin kukan nata ko kad'an ya janyo ta zuwa jikin sa yace"don't cry mana Ryynt jikina baya da matsala take naji sauqi kar ki damu kinji"
Ryynt ta d'ago tare da share hawayen ta ta tashi tare da fad'in "to ina zuwa"
Ya maida ta yace"no yi zamanki bana so inna ta sani"
Tace"ba gaya mata zanyi ba first aid case zan d'auko"
Yace"yi zamanki kawae idan na fita zanyi dressing d'in gurin don idan inna taga kin d'auko first aid kit d'in dole zata nemi dalili"
Ryynt ta gyad'a masa kai tana kallon yankuwar da ya maida hannun rigar sa ya rufe.
Ya sakar mata murmushi yace"to muci abinci koh"
Fuskar ta cikin damuwa ta bud'e plate suka fara cin abincin tana bashi yana bata har suka kammala cin abincin.
mohd ya tashi zuwa sllr magrib.
Ita kuma ryynt sharp sharp ta kwashe kwanikan abincin ta kai kitchen snn ta tafi d'akinta ta sami su saliha tuni sun kammala cin abincin su,
Saliha na bathroom gurin yin arwala mami kuwa sae fmn game take da game tap d'in ta.
Ryynt ta kar6e game tap d'in ta kashe tace"mami ana yin kirayen kirayen sallah kina yin game ki daina ba kyau kinji"
Mami ta washe baki tace"to Aunty na daina amma yaushe zamu koma gidan yaya"
Ryynt tace" idan kun koma gida ki gaya ma umma a had'a maki kayanki idan zan koma sae mu koma kinji"
Mami ta daka tsalle ta rungume Ryynt tace"da gaske Aunty?
Ryynt tayi murmushi tare da gyad'a mata kai.
Sae ga saliha ta fito daga bathroom Ryynt ta tashi ta shiga.

Sae da suka ida sllr magrib da d'an jimawa Nasir yazo ya kwashe su ya maida su gida.
Ryynt kuwa d'akin inna taje sae firar bayan rabuwa suke cike da nishad'i.

Mohd kuwa tunda ya fita sllr magrib ba shi ya dawo ba sae bayan isha'i.
Kai tsaye d'akin inna ya nufa ya gaida inna dake jikin wardrobe ta saka dardumar sallah ta amsa gaisuwar yayinda man ya saki baki yana kallon Ryynt wacce zata shiga bathroom sanye da zani d'aura gaba da hijabi har guiwa riqe da brush a hannunta
yace"keda nazo muje gida kuma wankan me zakiyi"
Tayi murmushi tace"nifa a nn zan kwana"
Yace"hm da wasa kike kema yi sauri je yi wankan ina jiranki kizo mu tafi"
Inna tace"kai dae keyin wasa muhammadu ae Ryynh ba inda zata je sae ta min kwana biyu tukun"
Mohd yace"dan Allah inna daina zancen nn"
Inna tace"yo muhammadu kmr ya na daina zancen nn ,kwanaki da yawa bana tare da Ryynt su en kwana biyun da zata min na rage kewar ta kuma kace a'a"
Inna ba haka bane indai Ryynt ce gobe sae na kawo maki ita,
Inna tace"to muhammdu nuna min ka fini iko da ita.
Fuskar sa d'auke da damuwa yace"ba haka bane inna ina laifin dae ko kwana d'aya"
Inna tace"Aifa sae ka d'auke ta ku tafi ban hanaka ba"
Ba yanda mohd ya iya yace"Aa inna yanda kike so haka za'ayi"
Nan ya tashi cikin damuwa had'e da kallon Ryynt wacce kanta ke qasa yace"idan kinyi wankan ki sameni falo muyi sallama"
Ta gyad'a masa kai snn ta bisa da kallo har ya fita taje cikin murna ta qanqame inna tace"inna na gode nsn da nice ma ba zae bar ni ba"
Inna tace"inafa koni ai dan nasha masa toka ne amma ke kuma Ryynh meyasa baza ki bisa ku tafi ba naga fa kmr ya shiga damuwa sosai"
Ryynt tayi shiru ita kanta tana son bin sa amma kuma tasan idan ta bishi zata kwana cikin quncin rashin sa a kusa da ita dmn in ga adalci gun malika ya kamata ace ya kwana,shiyasa take son ta kwana biyu tukun in yaso idan ta koma sae ta fara koyon sa ma kanta haquri.
Tace"inna ni nafi so kawae na kwana a nn"
Inna tace"to shike nn ae tunda yana da wata mtr ba matsala bane jeki abinki kiyi wanka amma fa kar ki jima kinsan fa yace yana jiranki"
Nan Ryynt ta wuce bathroom tayi wanka sharp sharp ta fito ta shirya cikin riga da wando na bacci ta saka hijab ta fito tayi tsaye jiki sanyaye ganin mohd baya falon knn ya gaji da jiranta ya tafi ko kad'an bata ji dad'i ba amma hakan ta juya zata koma ciki sae ga mohd ya shigo ta sauke ajiyar zuciya a hnkli tana kallon sa tare da sakar masa murmushi tace"ae na d'auka ko ka gaji da jirana ka tafi har banji dad'i ba"
Sae da mohd yaja hannunta suka zauna kan doguwar kujera snn ya kalle ta yace"dan na tafi ae ba damuwar ki bane farin cikin ki ne tunda har kika yarda zaki kwana biyu ba tare da ni ba"
Tace"yi haquri kwana biyu ae kmr yanzu ne in ga rae da lafiya da kuma yardar ubangiji"
Yace"a gurin ki ba amma ni a gurina tamkar shekaru biyu ne"
Tace"uhm bacci ne fa kawae baza mu riqa yi a tare ba dan nasan zaka shigo gobe ae ko?
Yace"um um

Please Login or Register in order to submit comment