Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta juya ta koma Amma takasa motsin Arziki, daurewa tayi ta k'ara Saka idonta Cikin Nashi still takasa mgn, durkusar da kai kasa tayi tafara motse da dankaramin bakinta, Kai Anamaka Kallon mai tausayi Ashe Kai mugu ne! Yusuf ne ya karaso wajen yace Ahh feenah yazeed fa mai tausayi ne tsoronta yake Ji kawai, Amma idan kin isa ki kalli Cikin idonshi kifada mai bashida tausayi mana. kallon Yusuf Feenah tayi ta yatsina fuska tace, Kan mai Xan kasa?? Toh idan Zaki iya Kiyimana. d'aga kanta tayi tasaka idonta Cikin Na yazeed yayin data daga Dan yatsanta tana nunashi kai yazeed Sam bakada..... ai da Sauri Yusuf yabar wajen yana fadin Wlh itace matarshi. Feenah itakam mgn take mai bako iftawa bare inda inda,,,,,Kai dama duk wannan fadin Ran naka barinshi kayi domin Sam baya maka kyau, yanzu kazo kana ma mage mugunta katuna itama Hallitace kamar ka! kuma Sai Allah ya muku hisabi kan muguntar dakai mata, kana ganin kaidin kamar kafi kowa ne Toh kasan wa'inda Zaka rinka mawa mugunta,kada Abun ya kasance Har kan bayin Allah. daga Haka feenah ta bar wajen....da Sauri Su inno dasu Leemah dake lekensu Suka koma Ciki ganin ta tawo, Ashe Yusuf daya koma yace musu Suzo Suga su feenah na Soyayya, bayan Sunma Nazir bayani kuma Sunci Shima kada yamusu magana Shine Suka Leko Suna kallonsu Amma Sam basajin Abinda Suke cewa, Leemah har picture ta daukesu Dan ba karamin kyau Sukayi Ayanda Suka tsaya ba.....yazeed a inda tabarshi ya daskare pic din bakinta kawai yake kallo lokacin da take motsashi da irin yanda take nunashi da Hannu Sam babu tsoro ko fargaba Atare da ita lokacin da take maganar.....Yusuf ne ya karaso yadan bangaji kafadar yazeed firgitgit yayi yadawo Cikin Hankalinshi, Janshi Yusuf yayi Zasubar wajen Saiga feenah ta fito da Ruwa A wani Cup na plastic ta Aje gaban magen ko kallonsu bataiba ta kara komawa Ciki. daki Yusuf yaja Yazeed Kan bed Suka Zauna, yusuf Ya kalleshi ya daga mai gira yaaa tayi ko? Ajiyar Zuciya yazeed yayi ya yatsina face wace? Yusuf ne ya kalleshi yace wace kake tambayana, yarinyar nan mana. Aini koda Nace maka nasaka gasa tsakanina dakai bance maka harda yarinyar nan Ackiba, wannan yarinyar Abinda yafi hakama Zata iya, Dan dama batada kunya yazeed ya fada yana kara kauda kai. gyara Xama Yusuf yayi yace Wlh Malan baka isaba Ai Kaine Kace Mun koma wacece, Kuma Ai Wannan tacika kowani Sharadi dakace kafison mace ta kasance tana dasu. Yusuf Sharuddana Uku ne dan tayi daya Ai batai Sauran biyunba. Karya kake duka tacika yazeed. Na1. kace wacce kakeson ka Aura ta kasance mai tausayi! Agabanka yanzu ta dibo Ruwa taba mage, Kuma kana gani magen tasha Ruwan Sosai Sannan tabar wajen Kenan dama k'ishi take ji yasa tazo kofarka. Na2. Kace ta Kasance mai kuzari tahaka Xata iya kula da gidanka da kai kanka da kuma yaranka! So Ayanda feenah tamaka mgn tana Nuna maka yatsa bakinta na furta Abinda takeso ya'isa kaa gane cewa ita din Mai kuzari ce. Sai Abu na3. Kace wacce Xata iya kallon Cikin idonka tayi magana, Naga feenah tunda tafara magana bata kifta ido ba, gashi ta Sumar dakai Atsaye Sabida Xakin muryarta. Toh me kuma kakeso ka fadamun yazeed??? Numfashi yazeed ya Saukar Ahankali yace Abinda nakeso yanzu ka kyaleni Yusuf tunda kai kacika naci kabari Zanyi Shawara. "Alright" Yusuf yafada yace kasan gobe Xani Zaria ko Zaka Rakani? Allah ya kyauta na raka ka wajen Mace yazeed ya fada yayi Hanyar Cikin gida. Tashi Yusuf yayi yabi bayanshi Suka Shiga parlon Atare. Yanzu hatta Mamy da Abba Suna parlon fira kawai Suke Suna dariya. Inno Naganin yazeed Sun Shigo tafara waka....."Namiji kuchaki Ahadashi da kuchaka Kamarshi, Na miji miskilalle Ahadashi da Miskila Kamarshi" gaba daya parlon Suka Saka dariya Abba yace Inno keda waye haka? Kallon gefen idon yazeed tayi tace Amadi wakar mu muna yara na tuna kawai...tabe baki feenah tayi Aranta tace tshohuwar Nan bazata Rasa Aljanu ba bakinta Sam baya Shiru. Shima yazeed Cikin Xuciyarshi Cewa yayi ai gara dai goben tazo kitafi muhuta. Inno kamar tasan mai suke fada cikin Zuciyarsu tace Wanda ya Zageni Cikin Ranshi Allah ya hadashi da daidai Shi. dariya Suka kara kwashewa dashi. yayinda yusuf yatashi yace nidai Zan tafi Saida Safenku. Inno tace yusufa Agaida gida, Abba da mamy ma Sukamai Saida Safe. tashi Nazir Shima yayi ya Kalli Twins kutashi mutafi, tashi Sukai gaba dayansu harda feenah...Abba ne yace Nafisatu Kibari ki Kwana Anan mana.durkusar da kai tayi kasa tace toh Abba. Saida Safe Nazir yamusu, Yana kashe ma Leemah ido Sukafita da Twins dake ta rigima su Abarsu. Cemusu yayi gobe zasuzo tare da Mum, tukun Suka yarda. bayan Sunci Abinci Su Mamy Suka nufa Sama,inno ma tashi tayi tace bari naje nahada kayana tun yau. dariya Leemah tayi tace toh inno Saida Safe. Yarage parlon Saura Leemah da feenah besty tashi Muma muje mu Kwanta, tashi feenah tayi suka Haura Sama Atare. Cikin dare yazeed kasa bacci yayi daya rufe Ido pink lips din feenah yake gani Yayin da take motsa Small Mouth dinta, ga manyan idanunta lokacin da take magana wani irin Haske dasuke Kamar mai Shirin yin kuka, kara Mirginawa yayi tunowa da Yanda Kumatunta Suke lotsawa Ga Cool Voice dinta dake fita Ahankali wai Nan Ahakama bude murya tayi. Murmushi ya Saki tunowa da yanda take Nunashi da yatsa tana k'aradashi irin Alamar honing din nan. OMG yafada da karfi Cikin Ranshi kuma yace "Tabbas irin matar danakeson Aure kenan, duk Sharuddana ta Cika Su, Sannan gata da Kyau da ilimi" Noooo yafadi da karfi yayinda ya dunkule hanunshi ya buga Cikin dayan, Ni bazan Auri yarinyar Nan ba Sabida Abu daya, Abunda Naji Sunayi lastym, har Sai Nasan menene Sukayi Aranar. Sannan ma Ai Twins Sun fadamun Cewa tana da yawa kuka, ni banason mace lyk dat, don bansaniba ko Aljanu gareta, gata daji dakai, bama Hakaba Ai Sunce Aure Za'a Mata da yaron Uncle dinsu.tsaki yaja yacigaba da mirgine mirginanshi, da ker dai bacci barawo yayi gaba dashi Aranar. bangaren feenah itama kasa bacci tayi tana tunanin Anya mutum ne kuwa wannan brother din na Leemah? Shi Sam baya ganin darajar kowa, wannan Shi dama Sojane Sai ace Sun Saba da bakar Xuciya but ko yaya Nazir da yake Soja Ai baya irin haka. Kai Wannan matar dazata aureshi tashiga uku, Ni misali ko dauramun irin mazan nan Akai A kafa inajin da gudu Xan kwance Wlh. Tsaki taja tunowa da muguntar dayayi ma magen nan, take takara jin tsanar yazeed Acikin Ranta. bude Ido Leemah tayi jin karar wayarta dama ita Tuni bacci yayi gaba da'ita. ganin feenah batai bacciba Sai juyi take yasata waro ido besty baki bacciba kinaji Aka kirani har 5miscall baki peeking ba kuma yaya Nazir ne fa! gani tayi bata kalletaba yasa ta d'aka mata duka ina mgn kinyi Shiru feenah. Arazane Feenah ta tashi Xaune tace banfa jiba. daga gira Leemah tayi tasaki Murmushi lokaci daya tace da kyau,tunowa datayi lokacin da take irin haka A Skul. Menene feenah ta wurga ma leemah tambaya? Aa ba komai ki Kwanta kiyi bacci nace. Ok feenah tafada yayin da taja blanket ta rufa. Murmushi Leemah takara Saki yayin data d'aga wayarta dake famaan Ruri.....

da Sassafe Inno yau tariga kowa tashi,daret kuma kitchen tashiga Acewarta bari ta hada musu karin kumallo Yanda dasun taso Sukaci Abba ya maidata katsina. Aiko waina tayi da miyar taushe wanda yaji tantankwashe.feenah ce tafara Sakkowa jin kamshi kamshi tanufa kitchen inno ta gani ta gama hada wainar tashirya tsaff. Inno ina Kwana, Saida Aka dan kwashi lokaci tace Lfy a takaice wai itama miskilanci tafara irin na yazeed da feenahπŸ˜‚ tabe Baki Feenah tayi tace toh dame Xa'aci wainar? Kular data Zuba wainar inno ta dauka takai kan table saida tadawo tace, da Ruwan Lipton...tsayawa feenah tayi tana kallon Inno ganin Yanda take bata Amsa, daga bisani ta daura Ruwan Zafi a huta tana Shirin yin kunun gyada. Kasa daurewa inno tayi tace Nafisatu Ki kira hafsat tazo da iyalinta dan naga tanason waina kinga Saisu karya Anan ko? daga mata kai feenah tayi kawai.Inno takara Cewa Zaki kirata ne koni na kira ta? Kirata feenah tace A takaice, Inno ta karkada Kai Alamar mema yasa take kula wannan yar? daidai Sanda Feenah tagama hada kunun gyadar inno takara juyowa Nafisatu Mutan gidan har yanzu basu tashi ba? "Eh" feenah tace tafita da place din hanunta, kwafa Inno tayi tace Zakuyi nadama. Karfe 8 daidai duk yan gidan Suka tashi Kowa nashirin wanka. Inno taba Leemat waya takira mata Mum mahaifiyar Feenah wai suzo su Karya tayi waina.Amsan phone din Leemah tayi Sanin fitina irin ta Inno. Aikuwa ba'afi Minti 30 ba Su mum Suka karaso gabaki dayansu Har dad, Nan Akayita Murna aka wuce danyin breakfast.
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Fitowar Yazeed daga Wanka Kenan Yana Shirin Shafa mai yasa Kaya,tura kofarshi Akai Ahankali Aka Shiga, Innalillahi ya fadi da karfi ganin Mufeeda ce! Murmushi tayi takarasa shiga Ciki tace yadai? Kofa ya nuna mata yace tashi kifita kamin na karyaki Acikin gidan nan.Murmushi ta kara yi tace duk Abinda kace daidaine Zanfita Amma kasani Ayau Saina dandana Yanda yazeed yake! Ido yafiddo waje yace bakida hankali ne?kitashi kifita nace, kona Zaneki Cikin gidan nan kuma Naga Uban da Zai tsaya miki. dariya Mufeeda tayi Sosai tace babu wanda Zai tsaya mun kuwa Sabida Kana takama da kyau da dukiya, Amma Kasani yau Saika biyamun bukatata Zanbar gidan nan,kokuma wlh yanzu Nafita Nashiga gidanku nace Raping dina Kayi Kuma Kake guduna kaki ka aureni, kuma kasan tsaff Zasu yarda domin ran Nan kakar ka taga Sanda Nafita Inaga tarufamaka Asirine kawai. dafe kai yazeed yayi ya Zauna kan bed yana kara dayasanin Sanin mufeeda Cikin Rayuwarshi....karasowa tayi gaff dashi Honey Kayi hakuri Sonka nake da yawa Sha'awarka ta Hanani Sukuni ka daure muji dadin Juna wata kila kaima kasaba da irin haka. Runtse Ido yayi wani irin takaici yakeji Aranshi, tashi Yayi Xaidau jallabiyarshi yasa, mufeeda takara Xaunar dashi pls honey ka kulani mana...hannu takai kan kirjinshi tana Shafa gashin tana honey wanann yana burgeni, Yazeed duk jikinshi yayi Sanyi yafara fita hayyacinshi domin shidin mai Saurin Sha'awa ne. Ganin haka Mufeeda tafara zarcewa! gaba daya tafara wasa da Sasan jikinshi, Shima gaba daya yafita hayyacinshi bakinta ya kamo yasaka nashi yana kissing dinta sosai tana mayar mai da martani. dad ne yace munata cin dadi banga dana ba. da Sauri Inno tace Halan yana chan yana cika yana batsewa,dad yace yakamata Akirashi Shima yazo yayi breakfast. Mum tace Mubeen jeka kira mai kyau kace yazo. da Sauri inno tace ai tunda Nafisatu na kusa Kawai taje takirashi, kallonta Feenah tayi ta galla mata harara, dad yace Ummina kirashi mana tashi tayi tanajin Haushin inno ta nufi part din yazeed. Su yazeed an Lula gaba daya bema san awaci duniya yake ba. Knocking take iya karfinta ba'a budeba. Mufeeda da tunda aka fara taji, murmushi tayi domi burinta yacika, dama So take Wani yagansu tasan dole za'ace ya aureta ta hakane Xata cika burinta na mallakarshi. tura kofar Feenah tayi da karfi dantana ganin kamar wulakanci yayi mata.....Ido ta fiddo waje yayin da take maimaita innalillah. Mufeeda Aranta tace yawwa kanwarshi ce Afili kashe mata Ido Mufeeda tayi tana cigaba da Shafa Jikin yazeed duk dacewa da kaya Ajikinta Shikuma towel ne kawai amma ya rufe.....Saman kirjinshine kawai Abude. fita feenah tayi jiki ba kwari har wani duhu take gani tace yace yana Zuwa daga haka tayi sama Abinta. Shikuwa gogan bema San me akeba kokarin cire ma Mufeeda kaya yake tayi Sauri ta Tashi daga jikinshi, domin dama ita har ga Allah tana tsoronshi irin yanda yake juya mace baya ko gajiya. jakarta ta dauka da gyalenta tace honey Anzo Ana knocking inaganin nemanka Ake, kaje kada Akara zuwa ni natafi, Karka damu zanfita lfy. daga haka tayi Hanyar waje. tashi yayi rike da mara yashiga toilet.


πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–
YAR LESBIAN CE
πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–
By
Nadeeya mohd Ahmad
(πŸ’–NadseerπŸ’‹)

dedicated to
Xaynab Ummu mahbub

Page....31

Bayan ya fito daga wanka Shiryawa yayi Cikin wata Shadda Sky blue ya feshe jikinshi da turare yayi Hanyar Cikin gida, Sai Asan nan yadamu dasanin waye yaje kiranshi daxun? D'an tsayawa yayi yana tunanin gashi kofar ba'a Rufe take ba..Toh Amma banajin wani ya ganmu domin naji Mufeeda tace knocking Akayi! Jikinshi dai yana bashi wani irin Alamu Ahaka yashiga Ciki. Zaune Suke Suna fira mum, mamy, dad nd Abba, Zuwa yayi gefensu yana gaidasu Cikin Sakin fuska duk Suka Amsa. dad yace my Son Anje kiranka kayi breakfast bakazoba kuma bayan Kace kana Xuwa. "Cikin Ranshi yace waye yace Haka Oho, bayan ko Shiga ba'ai ba" Afili cewa yayi daddy na tsaya Shiryawane. Allah ya muku Albarka. Amn yazeed yafada yace Ina Nazir? Mum ce tace yanzufa yake Nan wajen da! dad ne ya Dan tabo ta ya nuna mata Nazir da Leemah dake daga wajen parlon Suna Zaune da Alama fira mai dadi Suke. Murmushi mum tayi itama ta nuna ma Mamy dake kusa da ita...Cikin mamaki Mamy ke kallonsu take kuma Suka bata Sha'Awa dan ba karamin dacewa Sukai ba. Itama Abba ta nuna mawa Su, Shima dadi yaji har Cikin Ranshi ya kalli yazeed yace ka gansu Chan. Juyawa yayi ya kallesu Sun bala'in yin Kyau Ayanda Suke Azaune gashi Sai wani Murmushi Suke Sakar ma junansu, Cikin Ranshi yace Bakuda matsala. Inno ce ta Sakko rike da katuwar jakarta tsakiyarsu ta tsaya tana kallon Abba. Ya baka Shiryaba Amadi? Inno tafiya Zaki da gaske Mamy ta jefa mata tambaya? Tafiya Zanyi mana nagaji da Abunda Akemun Acikin gidan Nan. dad din feenah ne ya kalleta yace Inno kiyi hakuri kizauna ki fada mana me Ake Miki Sai A gyara insha Allah. Zama tayi tace ni banaso ma a gyara yau din Nan Saina bar gidan Nan. Hayaniyar inno ta juyo dasu Leemah dake Soyewarsu, tasowa Sukayi Ajere Suka nufo wajenta. Inno Ya naganki da jaka haka? Naziru yaron Albarka tafiya Zanyi Inda Ake ganin mutumcinta. Shidai Yazeed bece komaiba wayarshi kawai yake dannawa ko kallonta beyi ba. Inno Ki fadamana ko nice ke miki laifi ban Saniba Mamy ta fada cikin Sanyin Murya. Kallonta Inno tayi tace Ni Fatima bakimun komai ba kedin macen kwaraice ina Alfahari dake, kuma kaima Amadi bakaimun komaiba, laifinku daya dakuka kasa tankwarar da danku kan bakar Zuciyarshi. Mum ce tace inno ba bakar Zuciya gareshi ba bayason Raini ne. Oho mai d'a dan bayason Raini Sai Akace nima Rainashi nayi ko inno ta fada tana duban mum din feenah. dad ne yayima mum Alamar tayi Shiru, ya kalli inno yace Inno Hakane Anyi kuskure Amma kiyi hakuri. da Sauri tace nifa baniyin hakuri tafiyata Zanyi. Cikin Zuciyarta So take Yazeed yabata hakuri Amma Ya nuna kamar baisan tanayiba. Abba ne yace toh Shikenan Inno Xan kaiki katsina Amma kibari Zuwa gobe da Safe. da Sauri Yazeed yace Abba koni Saina kaita Ayau Idan kana da Wani Abunne. Galala Inno ta tsaya tana kallonshi ganin Shi Murna ma yake ta tafi...toh yazeed Ashirye kake Yanzu ko? Abba ya tamabayi yazeed.Abba Ashirye nake kallon Inno yayi yace tashi muje. Wani irin kallo tamishi tace Wlh naga Alama yazeedu murna ma kakeyi! Me kikeso nayi Toh? Me makon Kace nayi hakuri da hawayenka yazeedu. Chaff yazeed yafada kitashi muje dare nayi fa. Ai Wlh babu Inda Zanje tunda naga Alama bakin cikin Zamana a gidan Dana kake. Tashi tayi ta dau jakarta tayi Sama da ita. dariya Su Leemah Suka Saka gaba dayansu. komawa yazeed yayi ya Zauna inda ya tashi, Shi bahaka yasoba yaso ta tafi Ko tabari ya Sarara, Amma bazan kara mgn ba yazeed y fada Aranshi gudun Kada ta tonamishi Asiri yaji jiya Mufeeda tace wancen Xuwan nata inno ta ganta. Abba daya fara mgn ne y dawo da yazeed daga tunaninshi. Yazeed banason Inno takara kawo karanka wajena nagaya maka. durkusar da kai yayi k'asa yace insha Allah Abba. Dad dake gefe yaji Son yazeed yakara Shiga Ranshi sabida yanayin tarbiyyar yaron, cewa yayi Ahmad Ai jika da kaka Haka Suke ba'a hanashi ba kawai inno kishi take da yarinyar daya kawo kwanaki bakuga Abu Kadan maganar yarinyar take ba. dariya Sukai Gaba daya.Abba ya kalli mamy yace waini Fatima yarinyar batai bane? Tabe baki Mamy tayi tace ai inaga kwanaki yazeed hauka ya fara, yarinyar fa Kamar yanda Inno take Cewa kamar yar kafurai, Sam batada tarbiyya irin ta ya'yan hausawa. Gaisuwa ma Saida Shi Uban gayyar yasakata tukun ta gaisheni. Ahhh Lallai dole inno Ta kushe yar mum ta fada. Leemat ce tace Abba inada picture din matar barifa kagani. Phone dinta ta ciro tashiga nuna musu pic din mufeeda wanda kausar tamata sending kwanaki. kallonta yazeed yayi ya wurga mata harara ta kauda kanta tana mai gwalo. mamaki Suke yayinda mum tace ai wannan kusanma ta girmeka Son. durkusar da kai yayi yace mum Yanzu bama tare Ai. Yawwa yarona Sam bata dace da rayuwarka ba. Abba ne ya kalleshi Yanzu waka tsayar Toh? Sosa kai yayi yace Abba inadai nema. toh ka kokarta ka samo kamin ni nasama maka. toh yazeed yace.Leemah jitake Kamar tace Suna Soyayya da feenah, Saikuma tayi Shiru tonuwa da Inno da yusuf sunce Abari su bayyanar da kansu tukun. Kiran Sunan Nazir da Abba yayi yasa ta dawo daga tunaninta. Nazir kaifa kanada wacce kakesone Ko kaima Saina nema maka? Inda inda Nazir ya fara Abba..inadashi Amma Karatu take Yanzu. Kallonshi Abba Yayi da murmushi yace toh kasanar da iyayen yarinyar kanason ta? Sosa kai yayi yace bansanar dasuba Abba nabari Saita karasa. Abba cewa yayi yakamata kasanar dasu Yanda data karasa Saimuje neman Aure Ayi Abun Nan kusa. toh Abba insha Allah Nazir yafada. Kallon Leemah Abba yayi yace ke Halimatu. Saida gaban Leemah ya fadi Sosai.tace Na'am Abba! Ina feenat ne? Abba tana Sama tace kanta ke ciwo. Yazeed dake Zaune Cikin Ranshi yace "Ayya Shiyasa banganta ba, Nayi tunanin ma ko'itace taje kirana danaji Ance wai nace Ina Zuwa,Nasan babu memun Rainin Nan sai Ita, Ashe ba ita bace. Marairace fuska yayi lokaci guda Kuma Kamar bashi yayi maganar ba ya hade rai Yana ni ina ruwanama da ita" maganar Abba ta katse shi. toh Halimatu dake da Ita Kuma Zan dawo kanku Amma Saikun karasa karatun naku. toh Abba Leemat ta fada kanta a kasa. Kallon dad yayi yace Umar ko kanada magana dasu? Aa Ahmad Ai duk Abinda Xan fada ka rigani, Yanzu Kawai maganar Feenah ce, Zamuzo neman aurenta wajenka d'ana Ke bukata. Kallonshi Abba Yayi yace Umar Wani d'a gareka bayan Nasir da yazeed? d'ana d'an wajen Nasir yayana. Oho Abba ya fada yace mutan yola Zakace, Nayi farin Ciki dajin Wannan Abun,kahada Zumunci Allah ya biyaka. Amin. Dad yace Ya kalli Leemah yace, halimatu taso kawar taki kice tazo mutafi. Toh tace Tayi hanyar Sama. Feenah na kwance Gaba daya tarasa kanta, bakin Cikin halin dataga Yazeed da mufeeda Suke Kawai take. Maganganu barkatai take Cikin Ranta! Ashe Haka mum taji Ranar data ganni ina Aikata lesbian? Tabbas dole ta Suma adaidai lokacin Nan. hawayene ya fara zubo mata Yayin da take fadin nakara nadama da tsanar Kaina Akan Abunda na Aikata a baya, gashi Yanzu Na nashiga damuwa da bakin ciki kan Abun da brother din Leemah yayi, wai Nan ma Dan ba yaya Nazir bane, narokeka ya Ubangijina Ka gafartamun Abinda na Aikata Abaya,ya Allah kabani ikon danne Sha'awata harxuwa Sanda Zanyi Aure, Na Amince Kuma Xan Auri Kabeer kodan na kare mutumcin kaina. Yanzu Shi yayan Leemat ya rasa dawa zeyi Zina sai wannan kazamar yarinyar, Allah kadai yasan Sau Nawa Suka aikata wannan badalar. toshe bakinta tayi Sabida kukan daya tawo Mata! ya Allah karka tsayar dani Sheda Tunda ni banga Suna aikatawa gaban idona ba, Abinda nagani kiss. toh kodai maganar Su kausar gaskiyace dasukace yarinyar Zata lalatashi? Kai "Aa" bayanda mace Zata lalata namiji damachan Halinshi ne Shiyasa yake ma Mutane Wani gani gani. Numfashi ta Sauke Ahankali Allah kaciremun tunanin wannan Abun,Sukuma Allah kashiryesu. Tashi take kokarinyi Leemah ta tura kofar, da Sauri Feenah ta goge hawayen fuskarta. Karasowa Leemah tayi tace besty ya kan? Yayi Sauki besty yanzuma nake Shirin fitowa. Ji face dinki yanda duk ta kumbura kuka kikai ko? Aa bacci nadanyi Leemah. bacci Kuma idonki yayi jaaa haka, kodai bro yamiki Wani abune dakikaje kiranshi? dan tsaki feenah taja tace Kinfi kowa Sanin banason tambaya irin haka, yayan naki menene hadina dashi dazaimun wani Abu. Murmushi Leemah tayi tace Kuma hakane fa, kitashi dad nakiranki Xaku tafi. Toh Feenah tace tashirya ta sauka Kasa. Yazeed na ganinta gabanshi Yafadi Dan tayi Wani fiyaut,Kamar ba'itace jiya tagama mishi Rashin Kunya ba! Jiyayi Yanason Sanin Meke damunta gashi ba dama.karasawa tayi parlon tana gaida su Mamy, Amsawa Sukayi Suna mata ya jiki. Hada ido tayi da Yazeed ta wurga mishi harara Cikin Ranta tace jishi Kamar bashi yagama iskanciba! ai dama mubeen dinne yaje kiranka daya tona. Shima Magana yake Cikin Ranshi "mema yasa nake damuwa da yarinyar Nan? Wama yasani ko kallon iskancinta ta gama idonta ya koma haka jarababba kawai" dad ne yace kutashi mutafi ko. Tashi sukai gaba dayansu har nazir Sukai hanyar waje daidai Sanda Yazeed yakara kallon Feenah itama Akai Sa'a tajuyo Atare suka Sakarma junansu Wata harara Sai a idon Mamy. Tabe baki Mamy tayi tace Sukuma wa'inan ko lafiyarsu Oho. Fita sukai suka Shiga katuwar jeep din dad Nazir yashiga tukasu yayin da Feenah ke gaba kusa dashi, Su mum Na baya tare da Twins.

Yusuf A birnin Zariya! besha wahalar kai kanshi gidan Su Kausar ba, Tunda dama location ta tura mishi. Kiranta yayi Ya Sanar da'Ita ya karaso. Me gadi tasaka ya Shiga dashi part din da'aka tanada dan Saukar baki, ba karamin kayata wajen Akai ba dan Yusuf tsayawa Kawai yayi yana kare ma babban parlon kallo. bama Sai angaya maka gidan Sara dubai kazoba. Zama yayi adaya daga kujerun da'aka Zagaye parlon dashi gabanshi fruits ne makil. Wata yar matashiyace tashigo Sanye da uniform da Alama Aiki take Agidan, daret wajenshi ta nufa ta mai Sannu da zuwa amsawa Yayi, Kausar din tace tanazuwa.toh yace. Tafara yayyanka mishi fruits din daga bisani ta fita. Ba'afi mintina10 ba tsakani Saiga Kausar tashigo face dinta dauke da Murmushi, Sanyi take cikin wata doguwar riga Arabic gown ce mai launin Brown, red din mayafi tasaka ta Zagaye Saman kanta dashi yayinda takalmin kafarta ya kasance Jane, dankunne da Sarkar wuyanta zuwa Abin hanunta suma duk jane.ga Wata kwalliya data

2 Comments On YAR LESBIAN CE Book 2
avatar
umar-6-7

1 year ago

Reply

Nice book

avatar
abubakar-ibrahim-7

7 months ago

Reply

Yes

Please Login or Register in order to submit comment