You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
nunan fifiko akan shi fisabilillahi mai nake wa Anwar da har Khalid zai hanani ganin shi?"
Khairat ce ta tintsire da dariya har tana bugewa da Kujera "Kema mama mai ya kaiki Ni wallahi ban ga amfanin baka son Mutum ba kuma ka dinga Nuna wa kana son shi a gaban idanun shi Tunda bakya Son Ya Anwar why note ba zaki Nuna masa zahirin Ƙiyayyar da kike masa ba seki dinga pretending Kina son shi a gaban idanun shi To ina zaton Sun gane ki"
Ihsan ma dariya take Yi jin maganar da Khairat tayi a daidai wannan Lokacin kuma Hanan ta fito daga Bedroom Ɗinta Babbar Yarinyar Mama ce tuni ta kammala degree ɗinta Hanan tana masifar Son Anwar duk da Mama bata son Anwar ko kaɗan Hanan agolar mama ce data zo da ita gidan su Anwar saɓanin Husna da Khairat da Ihsan da suke Ƴaƴan Mama acikin Gidan su Anwar dan mama bata da ɗa namiji matanta Uku a gidan har Hanan Huɗu kenan.
Husna tayi aure tana zaune a garin Abuja Mijinta ma'ikacin banki ne tana nan da ciki tsoho haihuwa ko yau ko gobe shirin dawowa gida take ta haihu kamar yadda mama ta buƙaci hakan, Husna ce babba acikin ƴaƴan mama A gidan su Anwar
Inkiya mama taiwa su Khairat akan suyi shuru gudun kada Hanan taji abin da ya sami Anwar ta ɗaga hankalinta bayan tarin wulaƙanci da take sha a wajan sa amman ita zuciyarta kamar kare ya cinye Komai zai mata bata ganin Laifin shi akan shi bata Kula kowa duk ta Kori maneman ta wannan dalilin ya ƙara hassasa ƙiyayyar mama da Anwar wadda bata yarda ta fito fili ta Nuna masa ba ta ƙaunar tashi.
Duk yadda mama a farko taso Taja hankalin Anwar akan Hanan tayi amman da yake kamar Dutse yake Ko gezau shi kuma Abba yaƙi ɗaukar mataki akan soyayyar Anwar da Hanan kasancewar Abba yace ba ze wa yaron shi Auren dole ba duk wadda yake so yana da ƴancin aura wannan kalamin na Abba ya tunzura mama dan taso yayi wa Anwar dole ya amshi auren Hanan ganin duk wata hanya tabi batai nasara ba yasa ta ƙara Jin wutar Ƙiyayyar Anwar acikin zuciyarta sedai Mama ƙarshen Makira ce bata yarda ko a fuska ta Nuna wa Anwar bata son shi wanda Tuni Khalid shi ya gama karantar wacece mama shima Anwar ɗin Ko ya karanceta Oho badai ya nuna mata yasan mai take ciki kasancewar shi Mutum marar son magana bare hayaniya.
Hanan tabi su Khairat da kallo tana Ƙoƙarin Yin magana ne Mai aikin su ta shigo da kayan Abinci a saman tray ta nufi dining maganar mai aikin ce tasa Hanan miƙewa da sauri inda mai aikin take tambayar mama ta gano Jikin Alhaji ƙaramin yaya Jikin nashi yake.
Zumbur Hanan ta Miƙe tana dafe Ƙirjinta.
"Mama Yaya ne babu lafiya amman baki gaya mini ba?"
Mama Yaƙe taiwa mai aikin tana cewa da sauƙi Mai aikin tana fita mama tace "To marar zuciya ubanki zaki masa yama Mutu mana wani nada asara ne" Hanan bata tsaya Jin ƙarashen maganar da mama take yiba ta fita daga Part Ɗin nasu Direct Hanyar part Ɗin Anwar ta nufa duk da yana yawan yi mata gargaɗin shigar masa part amman haka ta faɗa Cikin part Ɗin nashi direct Kuma bedroom ɗin sa ta shiga Duk Fuskarta ta Jiƙe da ruwan hawaye.............
*YANKAN ƘAUNA…I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*
*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*
*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*
_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAƊANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ƊANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAƊIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*
*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*
*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAƊANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ƊAIƊAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAƊANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO
*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*009*
Kwance yake samɓal a saman gadon Numfashin sa yana sauka a hankali, Idanunshi a rufe ruf duk Zara zaran gashin idanun shi sun rufe masa Idanu ruf, Ƙarasawa tai wajan Ac control ta ƙara mai ƙarfin AC'n kafin ta nufi gadon jikinta duk a sanyaye wani Irin tausayi rayuwar shi take bata wadda take Jin Ninkin soyayyar shi acikin Zuciyarta fiye da ƙima Fiye da zaton mai zato.
Guntun hawayen dake Zubo mata take sharewa a fili ta furta "Wai kai baka jin Yadda nake jine wai kai wace Irin zuciya gare ka ban taɓa Jin ka furta kalmar kana soba sedai naji kalmar ana son ka a bakin mata da yawa daga Ciki harda ƙawaye na Dan Allah ka cire tsanar soyayya a zuciyarka kazo ka tallafi wadda take maitar son ka" Hanan ta furta kalmar tana tsira masa ido shima kuma adaidai nan ya buɗe idanun shi da suka ɗan Kumbura kaɗan suka ƙara Girma Yawun tsoro ta haɗiye ga kuma wani irin fitsari daya ke Ƙoƙarin zubo mata a hankali take ja da baya tana Ƙoƙarin sauka daga saman gadon sedai hakan bai samu ba sakamakon hannunta da Anwar ya cafke yayi wa Riƙon tsauri wanda har ƴar ƙara ta saki sabida zafi.
Rintse idanu tayi ta buɗe su har lokacin kallonta yake ba ko Ƙiftawa yana so yasan yaya son ta zai shiga zuciyar shi Kodan nacin ta gare shi amman ya kasa Gaba ɗaya zuciyar shi a bushe take kamar Dutse Bai taɓa furta kalmar soba hasalima in aka ce ana son shi haushi yake Ji shiyasa yake mamakin Yadda yake Jin Khalid na waya da ƴammata shikam yayi ƙoƙarin gwada Saka soyayya aran shi amman hakan ya gagara sabida kallon mata yake duka halin su ɗaya wani abune yake taso masa tina wani mikin da yajima a zuciyar shi da sauri ya saki hannunta ya Jingine kanshi da Pillow wani irin hawaye mai zafi ya soma gudu a saman Fuskar Jarumin namiji kamar Anwar Da sauri Hanan ta Tashi har tana tuntuɓe garin saurin barin ɗakin dan tana hango Tashin hankaline a cikin Idanun shi wanda inta zauna kusa dashi Komai na iya samunta.
Karo aka ci tsakanin Khalid da Hanan wanda bata Kula shiba Inna tabi Hanan da kallo haka suka ɗunguma zuwa ɗakin Anwar wanda Jin alamun shigowar su yayi saurin share hawayen shi.
"Oh Ni ƴasu bawa dai ba abakin Komai yake ba Ni Baraka Jibi yadda Muhammadu ya koma Lokaci ɗaya sannu kaji Muhammad Anwar"
Inna ta faɗa tana zama a kusa da shi kansa ya ɗauka ya ɗora a saman kafaɗun Innah a jikinta ne yake Jin Ɗumi na uwa.
"Khalid bai gaya maka dalilin ciwon nashi ba ko?" cewar Inna Khalid daya ke ɓallo magani tare da ɗaukar Gorar ruwa ya nufo wajan su yace wa Inna "Wallahi innah ban sani ba Allah dai ya bashi lafiya kawai" daga haka ya ɗago kan Anwar ya damƙa masa maganin a tafin hannun shi.
Anwar ya ɓata Fuska kamar wani ƙaramin yaro sabida a rayuwa baya ƙaunar magani tun yana yaro haka yake kuma gashi har an girma bai daina ƙin maganin ba.
"Ka daure ka sha ana shan magani ne ba don daɗi ba se don A warke daga ciwo" cewar inna.
A wajanta yake samun irin wannan kula da tarairaya kwanciyar shi ya gyara a saman kafaɗunta seda Innah tai da gaske sannan yasha maganin yana ta ɓata Fuska yana yatsina baki kamar zai dawo da maganin.
A hankali Muryar shi a dashe kamar mai cutar Mura yace wa Innah.
"Ni dai zan bar kamfanin Abba Innah dama kece kike bani haƙuri a kullum idan nazo miki da ƙorafin barin kamfanin shi"
Innah da Khalid suka kalli Juna dama Khalid ya raya hakan aranshi yasan musabbabin ciwon Anwar baze rasa nasaba da Ɓacin ran daya ke fuskanta daga wajan Abban shi ba.
"A kuya ce a daji Ta haifi ƴaƴa goma se Kuraye da zakuna suka zagaye wannan akuyar suna farautar ta, to akuyar ta rasa yadda za tai sabida tana son ko wanne acikin ƴaƴanta Kuma tana son rayuwarta Kuma idan ta gudu tabar ƴaƴanta cinye su waɗannan kurayen da zaku nan zasuyi sannan In ta zauna Tace ƴaƴanta su tafi waɗannan Kurayen da zakunan ba zasu barta ba Kenan Ko wanne acikin akuya da ƴaƴanta suna da Buƙatar Junan su sabida haka kawai sai akuya ta Fara kokawa da waɗannan namun dajin Tana gazawa se ƴaƴanta suka soma taya ta har suka cimma nasarar Kuɓuta amman fa seda suka ci wahala"
Cewar inna tana Kallon cikin ƙwayar idanun Anwar wanda bai fahimci mai take Nufi da wannan maganganu nata ba Katse shirun nasu ta kuma yi tare da cewa "To ina nufin barin ka kamfanin Alhaji kamar ka bawa mugaye da azzalumai damar handama da babakere ne acikin Dukiyar mahaifin ka dama abin da suke so kenan shiyasa suka shirya maka wannan Tuggun"
Anwar ya ɗage kafaɗa tare da cewa.
"Innah su kwashe mana kowa da arziƙin sa yazo Nifa inna bada ban abba yana dakatar dani ba ga Khalid nan da tuni na jima da barin ƙasar nan nayi tafiya ta Duniya na jingine kaina tunda bani da kowa"
Inna taɗan harare shi.
"Kada ka kuma faɗin haka, kana da Allah da Manzon shi, Sannan kana da mahaifin ka wanda yake matiƙar Buƙatar ka a kusa dashi Anwar kana da Basira wadda take taimakon Dukiyar mahaifin ka, Ba komai bane yasa ake Shirya maka wannan gadar zaren face ganin kana da ƙwaƙwalwar gano dukkan macutan cikin kamfanin ku, Ka saka a ranka wannan Dukiya bata kowa bace se taka sabida Alhaji Kai kaɗai ya mallaka ɗa namiji a duniya don haka ka jajurce wajan Haɓɓaka dukiyar mahaifin ka Don Kaine nan gaba zaka moreta"
Anwar cikin rashin damuwa yace.
"Nifa innah Dukiyar Abbah bata gabana shiyasa da Iya selary ɗina nake rayuwata wallahi Inna ficikar Abba ban taɓa fitar wa ba ga Khalid nan Duk abin da nake da Kuɗina nake yadda kowane ma'aikaci yake masa Hidima ya biyashi nima haka ne amman by mistake aka samu matsala Abba yana rufe idanun shi ya nuna kamar bashi ya haife ni ba da bani da matsala dashi amman tunda ya ɗorani a kan dukiyar shi nake samun matsaloli da Abba yanzu har takai A gaban kowa ma faɗa yake mini Ni kuma bana son zargi a rayuwata"
Anwar ya faɗa cikin ɓacin rai.
"Ba'a fushi da mahaifi Anwar ka bishi dukkan abin da yace Ka yarda koda kai ɗinne zaka cutu gaba zaka ga amfanin hakan"
Cewar Innah.
"A zahiri yake Nuna yafi yarda dasu Alhaji Jamilu fiye dani Inna mai zanyi da Kuɗin shi ban da Albashina Ina Parsonal Business ɗina wanda yake kawo Mini Kuɗi ga Khalid nan Ban damu da arziƙin da mahaifina keda shiba nawa na kaina nake alfahari dashi wanda na nema da gumina haɗin gwiwa Muke nida wani Babban Mutum acikin kwari Muke kawo Duk wani samfur na lagos lace da Dogayen Riguna daga India muke rabawa Ƴan kasuwa akan sari Tun Muna haɗaka da Mutumin yanzu takai ta kawo Nike bashi ya raba Innah iya waɗannan kaɗai nasan na riƙe zan dogara da kaina bare ma ina da shagunan dogayen Riguna dana zuba yara suke siyar Min acikin kasuwa Nifa wannan Matsayin da Abba ya bani ba ƙaramin takurani yayi ba"
"Ka dai yi haƙuri Muhammadu Kabi mahaifin ka in sha Allah gaba kaine zaka ci riba"
Da ire iren waɗannan maganganu Inna ta samu har ya sauka daga fushin nashi Ta shi yayi ya shiga toilet sabida akwai salloli akan shi Innah ta kaɗe masa gadon ta fita don ta sama mai abin da zai ci dan tasan tunda dare yayi ba lallai bane yaci dambu sani baya son cin abu mai nauyi idan Dare yayi Khalid shikuma zama yayi a saman sopa yana charting da wayar shi.
Wanka Yayi kafin ya gama ya ɗauro alwala ya fito Daga cikin Toilet Ɗin.
*YANKAN ƘAUNA…I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*
*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*
*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*
_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAƊANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ƊANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAƊIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*
*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*
*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAƊANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ƊAIƊAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAƊANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO
*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*10*
Hannunshi riƙe da ɗan ƙaramin tawul yana goge ruwan dake ɗigo masa daga saman kanshi, Cikin nutsuwa kuma a hankali ya ƙarasa gaban dressing mirrow yaja stol ya zauna Body spray ya ɗauka yana fesawa ajikin shi bayan ya kammala ya ɗauki Cream yaɗan shafa sama sama saboda yanayin garin na sanyi dake Busawa Gaban Closet yaje ya ɗauki Ash Jallabiya mai yankakken hannu da sauran tarkace yaɗan kalli Khalid da hankalin shi gaba ɗaya yana kan waya se wani tsadaddan Murmushi yake wanda ze nuna zahirin Nishaɗin da yake samu acikin wayar shi, Anwar Yaja tsaki! mai sauti yana ganin Khalid bai da aikin yi shikam soyayya yana ɗaukar tane a rashin aikin yi Fita yayi Falon shi ya shirya Sannan ya ɗauki sallaya duk yana jin ba daɗi na Missing jam'i da yayi Shinfiɗa ta yayi yana Mai tayar da sallah.
Cikin Nutsuwa da nuna ƙasƙanta kai wajan Allah maɗaukakin sarki Anwar yake addu'a cikin Sujjadar shi Ya jima Yana addu'ar kafin ya ɗago ya yi sallama Bayan kammala dukkan sallolin daya tara sakamakon rashin lafiyar data ɗan kwantar dashi har ta hana shi yabi sallar a kan Lokacin ta Istigfari ya dinga yi kafin ya soma karanto azkar daka ya kammala ya tashi ya Naɗe abin sallar yana mai zama saman One seater yana serching Channel dan ya kamo Mayyar tashi wato tashar kallon ƙwallon Ƙafa Tsaki yaja ganin basu fara wasan ba Khalid ne ya fito daga Bedroom Ɗin Anwar har Lokacin wayar shi na hannun shi Kuma gaba ɗaya hankalin shi yana kan wayar.
"Allah ya baka lafiya amman ni dai ina baka shawara wannan duk ba daidai bane ka zauna kana ɓatawa ƴaƴan Mutane Lokaci Danna san ba Budurwa ɗaya kake kulawa ba, This is not right, stop it"
Anwar ya faɗa mashi hakan, Khalid yayi Murmushi tare da cewa Anwar.
No matter how much I tell you how love is, you will not understand it sabida kai har yanzu baka san rayuwa yadda take ba ai soyayya dar ce nake gaya ma in mace ta gaya maka wata maganar ji zakai kana yawo a cikin gajimare dama zaka samu kai wuf da Hanan yadda take mai tar son ka malam ai da ka huta"
Tsaki Anwar yaja yaɗan taɓe baki Kamar baze yi magana ba can Kuma sai ya ce.
"She is not at all the type of woman I love, Sabida bana son siririyar mace In ma zan yi auren kenan, zan auro mace mai Ƙiba yadda nake Bani da jiki ɗinnan ta dinga tare Mini faɗa"
Ya faɗa yana Murmushi.
Khalid ya bishi da kallo Anwar bai da magana amman idan ya yanko maka wata maganar se ka cika da mamakin shi.
"To Mijin ƴar lukuta Allah ya ba ka"
Ɗage gira yayi bai cewa Khalid komai ba yabar wajan Direct part Ɗinsu ya nufa Ya nemi Guri a saman dining ya zauna Yana ƙoƙarin haɗa Coffee Wayar shi ta hau Ringing Innah Ce sanar dashi tayi ta masa faten dankali Da sauri ya tashi yabar Coffee ɗin yana Ƙoƙarin Fita Mama ta fito daga Ɓangaren Bedroom ɗinta da alamun Part Ɗin Abba zata shiga sanin Ya dawo ɗazu da yamma kano.
"A,a Yaya ina zaka kuma baka shafa coffee ba naga kamar shi ka haɗa?" cewar mama, ba tare daya kalli direction na wajan da take ba yace "Ehh na haɗa kuma inna tamin tayin fate" daga haka ya Nufi fita daga part Ɗin ta bishi da wani Mugun kallo tama kasa magana tai ƙwafa! ta nufi Part Ɗin Abbah.
Zaune ta tarar da Abba yana kallon Sunna tv a hankali ta ƙarasa wajan shi ta zauna a kusa dashi.
"Barka da zuwa Ranka ya daɗe yaya hanya?" Abba ya kamo hannunta wanda ya sha jan lalle yana murzawa.
"Hajiya shafa'atu Mowar mata yaya hidima da yarana da fatan na same ku lafiya amman wannan Ƙunshi yayi wa Farar fatar ki kyau" Ya faɗa still yana matsa hannun ta wanda yake a cikin nasa.
"Dan kai nayi Alhaji Allah dai ya barmu tare" ta faɗa tana kwanciya a saman kafaɗun sa wanda in ka kalle su sai kace matasa ne ƴan shekaru ƙalilan Cikin kwanto da iya kirsa tace.
"Nayi maka maganar zuwan Husna har yanzu baka bani amsa ba Ya kamata kace wani abu mana sabida ta shiga watan haihuwa ko yanzu aka ce mana ta haihu ba zamu yi Musu ba ta yaya zata haihu a dawa babu kowa nata"
Mama ta faɗa cikin Nutsuwa.
"Shafa'atu ba komai yasa kika ji nayi shuru ba ya kamata abar wannan yarinyar ta haihu a ɗakin Mijinta duka duka yaushe akai mata auren ma amman Mijinta ya kawon ƙararta na ƙazanta yafi sau Goma sabida haka kawo ta gida ma wata sangartar ce gaskiya abarta a ɗakin ta kawai"
Mama ta ɓata fuska.
"A,a nida nasa aka gyara ɗakin dake kusa da nawa hatta kayan baby na siyi komai Dan Allah Alhaji karka hana zuwan nan Please"
Ta wani haɗe hannu waje ɗaya tana roƙon shi.
Yayi murmushi"wato rigimarki tana da yawa Shafa tunda kina son hakan Allah ya kawo ta lafiya" Yana faɗar haka kuma ya ɗauki wayar shi.
"Kazo ina son ganin ka inda hali ma kazo mini da shaidar dawo mini da kuɗaɗe na daka Fitar"
Daga haka ya katse wayar.
Mama ta wani marairai ce tana kallon Abba "Haba Alhaji Abin da kake wa Anwar Baya dace wa kamar ba mahaifin shiba, Nifa karka jamini zargi ace nike shiga tsakanin ka da ɗanka dama naga take taken matar Gidan can dan ɗazu ma da bai da lafiya dana je wallahi Khalid hanani yayi na ganshi yanzu ma kamar abin arziƙi yazo nan zai ci abinci Baraka tai Kiran shi ya fasa ya tafi can" mama a siyasance ta kawowa Abba ƙarar su Innah Murmushi Abbah yayi.
"Rabu da Shi dasu Baraka Kinji Ya riga ya saba dasu ne Kinsan ita ta yaye shi"
Mama bata so Abba yace haka ba se tai dariyar yaƙe ta kuma lanƙwasa kanta.
"Ina nemar wa ɗana afuwar ka dan Allah karka tuhume shi akan wannan Kuɗi'
Abba ya kalleta "Idan ban tuhumi Muhammad ba Jamilu zan tuhuma wanda shi nake tare da shi tun kafin Muhammad yayi ƙwari?"
Mama taɗan sosa kai.
"Ni ba nufi na haka ba sabida bawai Yaya Jamilu dan yaya na bane Nina san baze taɓa cin amanar kaba Allah ya huci zuciyarka ai yaranne se Addu'a damma shi Anwar Komai nasa yana Ɓoyewa wasu kuwa da zaka ga In suka ƙi yin auren suna aje matan banza a waje ai yawanci Kuɗin su a wajan mata yake tafiya" ta faɗa tana Murmushi wanda ta faɗi hakanne Don ta ƙara jefawa Abba zargin yaron nashi aran shi Amman ba zaka taɓa gane da wace siga ta faɗi maganar ba sabida tsantsar Kirsar ta.
Adaidai nan Kuma Anwar ya shigo falon sabida Lokacin Abinci ma zeci yaga wayar Abba ya rufe ya tawo.
Ko zama Anwar bai kai dayi ba yaji Muryar Abbah.
"Ka dawo Mini da kuɗina daga nan zuwa gobe, Sabida ni ban yarda dakai ba Ƙila ma matan banza Kake bi ace shekararka Kusan arba'in a duniya amman bakai aure ba Duk sanda nai maka maganar aure kamar na haɗaka da ajalinka To Ni kuɗina bada ga kwance na same suba seda na tashi nai gogayya da mutane kala kala na tara su ta hanyar halak wallahi seka dawo Mini dasu Mutumin banza daga kai har Khalid Ɗin kunƙi Aure saboda Kunsa shashanci acikin ranku"
Innalillahi wa'innah Ilaihirraju'un itace kalmar da Anwar yake ta nanatawa dan yaji sassauci a zuciyar shi na maganganun da Abban shi ya gaya masa a wannan Lokacin kafin a hankali ya.........*YANKAN ƘAUNA…i littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*
*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*
*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*
_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAƊANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ƊANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAƊIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*
*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*
*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAƊANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ƊAIƊAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAƊANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO
*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*11*
Ya Ɗago shanyayyun idanun shi waɗan da suka rine da zallar ɓacin rai ya dire su A saman fuskar Abbah wata irin damƙa yakai wa center carpet Hannunshi gaba ɗaya ya jiƙe da zufa Shi kan shi Abba yanayin ANWAR ya ɗan firgita shi sabida bai taɓa ganin Yaron nashi a haka ba.
Magana yake son yayi Amman ya kasa Muryar shi ta dashe.
Tashi yayi da sauri Kuma a gaggauce yabar falon.
"Alhaji karka fa.......
"Dakata shafa'atu wannan ba hurimin ki bane koma mai zai same shi ya same shi" da sauri Abbah ya faɗa kuma da sauri ya tashi yabar mata falon ya shige bedroom gaba ɗaya ya rufe kanshi