Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce wa Hajiya?"
Shuru yayi mata sai da ta kuma nanatawa.
Sannan yace mata.
"Kice mata Anwar yace zai mayar dake Gidan ku, Ki basu kuɗin da suka baki"
Jimm tayi tare da sakin Ajiyar zuciya kafin ta fita daga Falon nashi.
Daran ranar Saadatu bata rintsa ba, Ta rasa ina maganganun sa suka dosa amman ta bawa zuciyar ta amsa da Taimakonta yake so yayi.
Washe gari Sabgarta ta shiga ganin bai mata magana ba.
Shima a nasa ɓarin Ayyuka ne suka taru akan shi a office, Ga Binciken daya tsaurara akan Fitar da kuɗin da akai bawai Biyan Kuɗin ne yayi Mishi ciwo ba A,a zafin Zargin da Abba ke masa shine ya ƙara tunzura shi akan dole ma sai ya Gano yaya akai Kuɗin suka fita wannan dalilin yasa a wannan rana ya dakatar da Alhaji Jamilu ya kuma dakatar da Chief Information Officer lamarin daya Girgiza zuƙatan mutane Biyun wato Alhaji jamilu yayan Mama matar Mahaifin Anwar da Amininshi wanda suke haɗa ka wajan cuta da handama acikin Kamfanin.
Anwar bai shigo gidan ba sai yamma Lis part Ɗin Innah ya wuce yaci abinci sannan ya fito zuwa nashi part Ɗin Lokacin daya shiga ana kiran sallar magariba alwala yayi ya fita masallaci sai da yayi sallah sannan ya Watsa ruwa Cikin shiga Black Jeans da white shirt ya fito yana ta baza ƙamshin turaren shi na Tom ford Oud wood, Babban falon su ya Nufa Baba kande tana ta hidimar haɗa Girki da sauri ta russuna tana gaishe dashi ya dakatar da ita.
Dan baya so babba kamarta tana rissuna mai.
"Baba kiramin wannan yarinyar mana"
Bata fahimta ba.
Yanayin yadda take yine ya nuna masa hakan.
"Wadda aka kawo sabuwar nan"
Da sauri baba kande ta juya ta shiga ɓarin su ta kirawo saadatu data ke zaune ta idar da sallah dan Lokacin ta sami tsarki sabida dama bata wani Jimawa.
Gaban sa'adah ya faɗi sanda Baba kande ke sanar da ita Alhaji ƙarami na kiranta.
Tashi tayi ta biyo bayan Baba kande zuwa falon.
Baba kande ta wuce Kitchen ita kuma ta Nufi inda yake tsaye ya harɗe hannayen shi a saman Ƙirjin shi.......
*YANKAN ƘAUNA...I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*


*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAƊANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ƊANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAƊIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAƊANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ƊAIƊAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAƊANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
        
         *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *18*

Tunda ta doso wajen shi yake binta da kallo ta ƙasan idanunshi wanda ba lallai itan ta gane irin kallon ƙurullar da yake yi mata ba.
A hankali ta ƙaraso gabanshi ta tsaya daga nesa dashi ta sunkuyar da kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.
"Wuce muje"
Ya faɗa mata a taƙaice.
Ɗago idanunta tayi tare da yin raurau da su kamar zatai kuka! kafin tai magana cikin sakarci kaɗan tace masa.
"Nifa ban gama shirya wa ba"
Tsira mata kaifin idanunshi yayi wanda yasa ta yi saurin Kauda kanta tana jin wata irin faɗuwar gaba.
Cikin ƙaramin sauti ya furta.
"Muje ko"
Ya faɗa lokacin daya juya domin fita daga falon bata da wani zaɓi face na bin bayan shi ko Kuɗin bata mayar wa da Husna ba haka zalika bata ɗauki kayanta ba, Bare tai wa Baba kande sallama.
Sai da ta ƙara da Gudu sannan ta cimmasa sabida saurine dashi ba ɗan kaɗan ba a bakin wata farar Mota ta tarar dashi sai da ta ƙaraso sannan ya shiga ɓangaren driver ya sa hannu ya buɗe mata kusa dashi sannu a hankali ta shiga cikin Motar ta zauna.

Ya kunna ya tashi Motar suka bar wajan a bakin gate ya danna Horn masu gadi suka Buɗe masa suna ɗaga mai hannu ya fita daga harabar Gidan gaba ɗaya saman kwalta ya cilla hancin Motar tashi.
Tafiya ce suke kamar ta Kurame yana sane daya zo layin yaɗan wuce da sauri tace.
"Ga layin namu fa"
Yaɗan kalleta yana cewa.
"Nina ɗauka Kurma ce ay"
Dariya ta saki kaɗan tana sa hannunta tana rufe fuskarta.
Cikin layin nasu ya shiga yana tafiya a hankali har yakai daidai inda ta Nuna masa ya kashe Motar ya ɗan kalleta.

"Ki shiga gida to sai da safe"
Magana take son yi masa amman kwarjinin shi ya hana ta furta abin da take son gaya masan.

"Ko na rakaki?"
Ya faɗa yana ɗage girar shi guda ɗaya.
Sunkuyar da kanta tayi tare da kama Murfin Motar zata buɗe ta fita.
Da sauri ya kamo hannunta.
Itama da sauri ta ɓamɓare hannun nata daga Cikin nashi.
"Ashhh kin fama min Ƙunata"
Ya faɗa mata a hankali.

Da ɗan ɓacin rai ta juyo gareshi zata yi masa magana, Yay saurin hanata furta maganar ta hanyar Rungumeta ta baya yana zuba mata dukkan Nauyin shi Kokawa suka shiga yi acikin Motar hankalin Saadatu yayi Mugun tashi.

Sai da tayi da gaske sannan ta iya Rabashi da Jikinta sai faman Nishin azaba take Ranta a tsananin ɓace ta kalle shi da Manyan idanunta waɗanda suka Sauya launin su zuwa jajir.
"Dama haka halin ka yake? mai yasa kayi min haka daman dan ka lalata min rayuwata ka rabo ni da Gidan dana ke sa ran samun halak ɗina?"
Sai hawaye! shaaa suka soma ambaliya a saman fuskarta.

Dafe kanshi yayi yana Ƙoƙarin saita Nutsuwar shi a hankali ya zira Hannu Cikin Aljihunshi ya ciro kuɗi masu yawa wanda bai ma san adadin suba ya kama hannunta ya damƙa mata gaba ɗaya ya kasa magana.
Watso mai da Kuɗin tayi Jikinsa.
"Allah ya kiyaye na amshi Kuɗin ka ko zan rasa komai bazan iya amsar Kuɗin kaba Kuma sai Allah ya saka Min abin da kayi Mini"
Daga haka ta fita daga cikin Motar tana wani irin Kuka mai tsuma rai da zuciya.

A guje ta faɗa Gidan ko sallama bata iya yiba

Da kuka ta shiga ɗakin su Ummi na sallah Ummi tana idar da sallar ko addu'a bata tsaya yiba ta Juyo tana tambayar sa'adatu.
"Lafiya kika shigo da kuka! menene mai ya faru?"
Ummi ta faɗi maganar a firgice ganin yadda saadatu take Gursheƙen Kuka!

Baffa yana bakin dakalin Ƙofar Gida yana kallon sanda motar ta sauke saadatu har zuwa sanda saadatu ta fito daga cikin Motar Murje idanunshi yayi yana kuma Buɗesu tabbas saadatu ce ta fito daga Motar Jikin Baffa har tsuma yake wajan takewa saadatu baya zuwa Cikin Gidan daga tsakar Gida ya soma ƙwala mata kira.

"Saadatu! saadatu!! fito nan Munafukar Allah, yau Allah ya tona miki asiri dama na jima ina zargin ki yau dai Abin Ɓoye ya fito Fili"

Saadatu daga cikin ɗaki ta Matse Ummi jikinta sai rawa yake tana tsiyayar hawaye!
Ummi ta ɗago tana kallon Yadda saadatu take kuka! adaidai nan Baffa ya ƙaraso gaban Ƙofar ɗakin yana Bugawa da ƙarfi yana kuma nanata Kiran sunan saadatu.

"Idan baki Fito waje ba zan tona Miki asiri a cikin unguwa kowa yaji"
Da sauri Ummi ta kama hannun saadatu suka fito tsakar Gidan.

Suka zube a gaban Baffa.

"Dama ni na jima ina zarginku to yau na ga komai da idanuna saadatu ashe ba wanke wanke da shara kika jeba ashe yawon iskanci kika je uban waye ya sauke ki a mota?"
Ya faɗa cikin ƙaraji.

Wanda faɗin maganar tashi tayi daidai da sanda Abbati ya shigo gidan Umma dasu Jamila kuma suka fito daga cikin ɗaki.

Yowa kanta baffa yayi kamar zai daketa yana kuma tambayarta.
Toshe bakinta tayi tana wani irin kuka!
"Ba magana nake Miki ba uban waye ya sauke ki a mota? wato mu zaku mai da marasa tunani Kin tafi wajan namiji ya kwana dake, Shine zaki fake da tafiya wajan aiki"
Kuka saadah take sosai a wannan karon.
"Wallahi Allah Baffa Babu wani Iskanci dana je ɗan gidan ne yace na dawo Gida na cigaba da Kula da Hajiya wallahi Iya gaskiyata kenan Kuma shine ya kawo ni har nan"
Baffa yayi wata irin dariya.
"Bayan ya gama lalata dake Ko? babu wanda zaku rainawa hankali kawai kawaliya ce tai Miki Hanya kika je kikai kwana biyu kika dawo Gida To bari Kiji ba agidana wannan abun Kunyar ba wallahi bazan ɗauka ba sabida haka tun wuri Ku haɗa ina ku ina ku Kubar Min gidana danni ba zakuja Min zagi a cikin Unguwa ba"

Da sauri saadatu ta kama ƙafafun Baffa tana wani irin kuka!
"Baffa iya gaskiyata kenan Wallahi bai min komai ba in ƙarya nake kazo Muje Gidan ka tambaye shi"
Wani irin naushi abbati yakai mata babu ji babu gani yahau dukanta Ummi ta rungume saadatu wanda ya haɗe su gaba ɗaya yana duka har wata tsuma yake.

"Mu zaku wulaƙanta? dama ni Jikina ya bani ba alkairi ne ya fitar dake daga gidannan ba ashe yawon Iskancin ki kika tafi to yau saina Illataki na lalata duk wata Kafa da namiji zai gani ajikinki har yayi sha'awa" Cewar Abbati yana dukan su Umma dariya take Ɓoyewa tana furta.
"Abbati kai mata a hankali fa kar Cikin nata ya zube bafa a dukan mai Juna biyu"
Duk da saadatu tana cikin Jin raɗaɗin Dukan da yake mata sai da ta juyo ta dubi Umma saboda raɗaɗin Maganar Umma yafi Dukan yi mata zafi!

Babu irin Cin zarafin da Baffa bai Musu ba Kuma babu wanda ya ƙwace su daga dukan abbati har seda ya gaji dan kanshi sannan ya soma Kumfar baki yana balbalin bala'i Ummi ce ta janye sa'adatu suka shiga ɗaki Lokacin saadatu Ko hannunta bata iya ɗagawa Kuka kam tayi shi harta Godewa Allah taja wa Anwar Allah ya isa tafi Cikin Carbi ta la'ance shi har babu adadi don shine Silar Jefata Cikin wannan matsala a haka sum sum dashi kamar na Allah.

"Saadatu Meye dalilin ki na baro Gidan aikin sannan na kasa Gasgata gaskiyar maganganun Baffa shin waye ya kawo ki acikin Mota?"
Cewar Ummi.

"Kema zargina kike kema ba zaki Min Uzirin ba shikenan Ni kawai gwara na mutu na huta"
Sai ta soma yin wani Irin tari wanda ya ɗagawa Ummi hankali Duk taurin zuciyar Ummi kuka take na ganin Halin da ƴar uwarta ta shiga Hajiya dake kwance itama kukan take ganin Saadatu bata yin Motsi yasa Ummi fita don neman ɗaukin mutan gidan nasu amman Duk ihun da take babu wanda ya Kulata Ganin wankin Hula na neman kaita dare yasa ta fita Gidan Aunty Murja Wadda ta biyo Ummi zuwa gidan babu yadda Saadatu take Haka suka ɗagata Mijin Aunty murja ya ɗauko Motar shi suka sakata aciki wani Ƙaramin asibiti dake kan titin Rijiyar zaki suka kaita Nurses suka amshe ta da gaggawa Suka shigar da ita ɗakin duba marasa lafiya.

Jingine kanshi yayi a jikin Sitiyarin Motar yakai Minti Goma a wajan kafin ya tayar da Motar tashi yabar Layin Cikin kasala yake Driving zuwa Gida gaba ɗaya kanshi ya Kulle Har ya ƙarasa Gida ya Fita daga Mota Ya shiga part Ɗin shi bai gama dawowa daidai ba wani Irin Yanayi ke Fisgarshi bai ɗauka zai kamu da wuri haka ba.

Tun ranar daya soma ganinta a part Ɗinshi da yamma Da alamun ɓatan kai tayi ta shigo masa, Yaji gabanshi ya faɗi bai son soba sabida bai taɓa Yiba amman yana Jin lamarin ta mai girma acikin zuciyar shi bai damu da ƙasƙancin taba shi dai yafi damuwa da tarbiya.

Babu laifi taci jarrabawar shi, sabida yana Gudun sharrin mata tunda akwai tabo acikin zuciyar shi bai ɗauka zai kamu cikin sauƙi ba sai dai Tun ranar daya ganta ya kasa sukuni ya kasa Nutsuwa ita kaɗai yake kalla acikin Idanunshi.

Yayi saurin kauda ita ne daga Cikin Gidansu sabida kar ayi amfani da ƙarfin Ta azuciyar shi a cutar da Shi sabida Yana jin baze Taɓa Jure kawaici akanta ba, ita ce mace ta biyu data ji tausayin shi bayan innah ita ce mace ta biyu data kare Lafiyar shi sanda za'a cutar dashi Tabbas Lamarinta mai girma ne a gare shi.

Lumshe ido yayi yana Neman yafiyar Allah na rungumar da yayi mata wanda ba don komai yayi mata hakan ba sai don ya ƙara gwadata akan wankin ido ko itan ta kasance acikin jeri ƴammata masu wankakken idanu sai dai kashh bai samu nasara akanta ba sai ma ƙarin Tashin hankali daya gani kwance a cikin ƙwayar Idanunta hakan ya bayyana masa tsantsar kamun kanta.

Kama lips ɗinshi yayi yana Tsotsa Jinshi yake a wata irin Duniya ta daban yana jinta a ranshi amman yana Jin nauyin furta mata kalmar da zata haɗa zuƙatansu waje ɗaya sabida yana ganin kamar har yanzu akwai sauran Lokaci.

Mirginawa yayi tare da matse ƙaramin Pillown dake gaban shi yana sakin sassanyan Numfashi da ƙyar ya tashi yayo sallar Isha'i wata irin kewa yake Ji acikin zuciyar shi da gangar Jikin shi kwanciya ya kuma yi babu Jimawa bacci mai daɗi wanda ya jima bai samu ba ya ɗauke shi.

Washe gari bai yarda sun haɗu da Abba ba sabida Tun jiya yake ganin Kiran abba amman yayi Buris sabida yasan baze wuce maganar Alhaji Jamilu bace.

Ayyukan shi ya cigaba dayi acikin Office koda ya kammala Komai da yamma ya fito daga Office yana driving yana sakin Murmushi wanda tunda ya tashi a safiyar yau Fuskarshi ke cike da Wannan Murmushi wanda ya nuna zahirin farin Cikin da yake Ciki.

Hanyar Gidansu Mami ya nufa sunan daya sa mata kenan Sanye yake Cikin farar shadda ƙal wadda Kallo ɗaya zaka yi wa shaddar ka gane zahirin tsadarta.

A ƙofar Gidan su yayi parking ya fito daga Cikin Motar ya jingina ajikinta yana neman yaron da zai aika ya kira masa ita.

Ummi da Aunty Murja a wajan saadatu suka kwana wadda zazzaɓi mai zafi ya rufeta fuskarta duk ta fashe Ba yadda Aunty Murja batai da Ummi akan ta tafi gida ba amman taƙi data takura mata ma sai ta saka mata Kuka dole mijin Aunty Murja yace to ta kwana da ummi.

Washe gari da Zazzaɓin saadatu ta kuma tashi, sai amai take ruwa aka saka mata bacci ya ɗebe ta wajan rana Aunty Murja ta koma gida ta Yo Musu Girki bayan ta dawo Ummi ta tafi sabida ta ɗauko kayan su ta kuma gyara Hajiya don har Lokacin Saadatu bata farka ba.
Sabida allurar baccin da aka zuba mata acikin ruwan.
Ummi ta kammala Komai ta gyara Hajiya sai da akai la'asar sannan ta fito daga Gida.
Wanda tana fitowa Anwar yaɗan zuba mata ido ganin yanayin su da saadah yasa ya ƙarasa Wajanta Ummi da Anwar ya cika mata ido da sauri ta Rissuna tana gaishe dashi ya amsa yana tambayarta Ina Saadatu Dan Allah kozata Kira masa Ita.

"Tun jiya muna asibiti yanzu ma kayanta nazo ɗauka"
Ummi ta faɗa masa cikin damuwa.
Yanayin yadda yaɗan Ruɗe abin ya bata mamaki.
Cikin sauri yace mata.
"Dan Allah in babu damuwa Muje naga Jikin nata"
Sai da tayi Jim kamar ba zata Bishi ba sai kuma ta bi bayan shi ta shiga Motar suka tafi.
Wanda duk abin da ya faru akan idanun Zubaida Ne babbar ƴar Umma wadda Ta dawo daga Unguwa tun tsaiwar Anwar ta kasa ƙarasowa wajan ta zuba mai ido tana kallon shi bata Firgita ba sai da ta ganshi tare da Ummi Ai suna barin wajan tai Gida aguje tana Kiran Ummah duk hankalinta a matiƙar tashe.............


Tafiya irin ta Kurame sukai Ummi tana ta mamakin wannan Haɗaɗɗan Mutumin ne yake neman saadah to a ina suka haɗu Ko shine ya kawota Jiya Sanin babu mai amsa mata yasa ta sunkuyar da kanta ƙasa domin gaba ɗaya kwarjinin sa ya hanata sukuni ita tsoro ma yanayin ɗaure Fuskarshi yake bata.

Tana nuna masa inda zai yi da yatsanta har suka ƙarasa bakin asibitin yayi parking Ɗin Motar tashi Ita ta soma fita sannan yabi bayanta a reciption suka haɗu da Aunty murja wadda take zaune Ummi ta tsaya a wajan Aunty Murja shi kuma ya wuce Cikin ɗakin data nuna masa wanda saadah ke kwance acikinsa.

Jikinsa a matiƙar sanyaye ya buɗe Ƙofar ɗakin ya shiga ɗan ƙaramin ɗakine mai ɗauke da gado guda ɗaya sai toilet.
Cikin Nutsuwa ya ƙarasa bakin gadon data ke kwance ruwan ma ya ƙare an cire mata bacci take sosai sai dai Ganin yadda Fuskarta ta kumbura ne yaɗan sosa ranshi a hankali ya tsaya akanta ya Jingina da bango wanda hakan yayi daidai da sanda ta Motsa tana Buɗe idanunta a hankali ta sauke su acikin nashi wata irin firgita tayi da sauri ta tashi ba shiri take Ƙoƙarin dira daga saman Gadon.........
*YANKAN ƘAUNA...I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*




*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAƊANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ƊANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAƊIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAƊANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ƊAIƊAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAƊANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*19*


Ya zuba mata ido yana kallonta na wani Lokaci, kafin ya kawar da idanun nashi daga kanta, Lokacin har ta sami damar sauka daga saman gadon tana Ƙoƙarin Fita daga cikin ɗakin ma.

"Zo nan ki zauna"

Ya faɗa mata cikin ƙaramin sauti kamar mai yi mata raɗa.

Maƙe ƙafaɗa tayi kamar wata ƙaramar yarinya idanunta na kawo ruwan hawaye! shaaaa.

"Subuhanallahi, To kukan na menene?"

Ya faɗa mata cikin ƙureta da mayen kallon shi.

Shuru tayi masa shima bai ƙara yi mata magana ba, haka suka kasance yana tsaye ajikin bango ita kuma tana tsaye a bakin Ƙofa ita bata fita ba ita bata shigo ɗakin ba, Ƙirjinta sai faman harbawa yake fat! fat! sabida tsananin Tsoro tambayar kanta take yaushe yazo waye ya kawo shi inda take.

Numfashinta ne ya tsaya na wucin gadi sanda taji ƙamshin turarenshi acikin hancinta a hankali take ɗago ƙwayar idanunta tana ƙare masa kallo yana tsaye akanta gab da ita sosai kamar zai Rungumeta.

Baya ta dinga ja harta kai Jikin Ƙofa ta maƙure tana Sauke Numfashi.

A hankali ya kuma ƙarasowa gabanta dab da ita kamar zasu haɗe, Maƙure kanta ta kuma yi ajikin Ƙofa tana ƙoƙawa da Numfashinta.

"Muje ki zauna"

Taji muryarshi acikin kunnenta, Turo baki tayi gaba kafin tace.
"Ni dai ka tafi"
Ya ɗan zaro ido kaɗan wanda hakan ya ƙarawa idanunshi Girma wani sahihin kyau ya bayyana a tare dashi.

"To zan tafi amman Muje kiji"
Ya wani ja kijin da ɗan tsayi.
Raɓe shi tayi ta Nufi bakin gadon ta zauna sai dai yadda tai zaman ne in ka kalleta sai kai dariya sabida kamar kace mata Ket! ne ta zura aguje.

Da sassarfa ya ƙarasa wajanta ya tsugunna a gabanta tare da kama Gefen gadon ya zuba mata ido Jin kaifin idanunshi na yawo a dukkan sassan Jikinta yasa ta ƙara shiga wani Irin yanayi na kasala da Mutuwar Jiki.

"Sai kallo kamar ƙuda"
Ta faɗa a hankali tana Ƙunƙuni.

"Ni ay nafi Ƙuda ma komai da Komai"
Ya faɗa ashe yaji, Toshe bakinta tayi da hannunta tana zare ido.

"Me yake damunki? Jiya naga lafiya lau Muka rabu"

Kamar Jira take yayi magana sai ta rushe da kuka! bai hanata Yin Kukan ba kuma bai daina kallonta ba, Kai jama'a Anwar ƙarshe ne wajan Miskilanci sai da tai Kukan mai isarta sannan ta tsagaita dan kanta.

Ya ciro Hanky ya miƙa mata Ƙin amsa tayi tare da juya masa baya ta turo mai Ƙeyarta.

Murmushi yayi mai sauti yana hango tarin Ƙuruciyarta.
"Please accept and wipe away your tears" ya faɗa yana kuma miƙa mata.

Ƙin amsa tayi ta cigaba da yin ƙaramin Kuka wanda sautin shi ke tashi a hankali.
"Mami so kike nima nayi kukan?"
Taji sautin Muryarshi cikin wani irin yanayi.
Mamaki furucin nashi ya bata.
"Wannan kukan naki yana damuna Dan Allah ki bari"
Ta kuma jin furucin sa.
Ajiyar zuciya ta sauke jin tayi shurun yasan shi tashi ya dawo Kusa da ita ya zauna ƙafaɗun su na jeruwa dana Juna.
Da sauri ta matsa a hankali sautin Muryarshi ke tashi.
"Bana jin zan tsaya yi Miki Ɓoye Ɓoye sabida iya ƙwayar idanuna kaɗai Kika kalla kinsan yadda nake ji game dake, Bazan takura miki akan sai naji dalilin kwanciyar ki anan ba amman ina roƙon ki da Ki daina Kuka wannan Kukan naki yana ƙara Kiɗimani Please zaki Aure Ni?"

Gabanta ne yayi wata Mummunar faɗuwa wani irin kuka mai ƙarfi ya tawo mata Furucinsa na ƙarshe ya tsorata ta ya Kiɗimata.

A wahalce ta ɗago tana Binshi da kallo still hawaye na kwarara acikin Idanunta Shima idanunshi yana kanta sai dai bai Kuma ce mata komai ba.

"Bayan abin da kayi Min Jiya yau ma Biyoni kayi ka Ƙara tarwatsa Min sauran Farin cikina? yaudarar taka ta Koma aure na domin ka cimma Burinka Mummuna akaina?"
Tsira mata ido yayi tunda ya ganta bata taɓa yin doguwar magana dashi kamar haka ba zaƙin Muryarta ne ya ƙara Jefa shi Cikin wani yanayi bai san me zece mata ba sai ya zuba mata ido ya wani rafka tagumi yana cigaba da kallonta.

"Nidai zan aure ki sabida Allah After this I don't know what to say"
Ya faɗi har Lokacin idanunshi yana Kanta wayar shi ta shiga Ringing! a hankali ya ɗauka yana magana wadda ba zata ce ga abin da yake faɗa ba.

Lokacin Nurse ta shigo ɗakin ya tashi ya fita yana cigaba da wayar Bayan ya gama wayar ya shiga wajan Likita suka ɗanyi abun da zasu yi ya Biya Kuɗin komai aka basu sallama da tarkacen magunguna ɗakin ya koma Lokacin su Ummi sun shiga wajanta yaɗan Dubi Aunty Murja wadda take gaishe dashi ya amsa a taƙaice yana ce wa zasu iya tashi ya aje su agida sabida an basu sallama yana faɗin haka ya fita wajan Mota.

Sai da Aunty murja tai wa saadah jan ido sannan ta saka hijabi dan da cewa tayi babu inda zata Bishi.

"Meye haka saadah ni banga wani aibu a tare da bawan Allah'n nan ba yana da Nutsuwa kuma ba yaro bane daga gani"
Cewar Aunty Murja.
Ummi tai dariya kaɗan tana cewa.
"Ko shine ya kawo ki Jiya ne? ni a ƙofar Gida na ganshi yace Ina mami na kasa ganewa sai da ya kwatanta Min ke sannan na gano ki"

Hararar Ummi saadatu tayi tana cewa.
"To in ba shi ba waye ne ni ya wani takura ni tunda naje Gidansu

Please Login or Register in order to submit comment