Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da lafiya yanzu zan kama hanyar Kano

Mum tace maike damunta?

Dad yace wlh ban sani ba, Tadai fad'i ne kuma ance Dr bai fito ba

Mum tace amma daka bari gobe saimu tafi gaba d'aya koh??

Yace a'a yau zani ku saiku tawo gobe

Nan Zarah tace zata bishi

Yace Toh kiyi sauri muje kin San ban son jira

Zarah tashi tayi da gudu taje ta zuba kayanta a akwati tare da abun bukata sannan ta fito suka Kama hanya ita da Dad, mum dai tace ita da najeeb gobe zasu tawo

Bayan fitan su Dad saiga najeeb nan ya fito ya tashi Daga bacci.

Mum tace harka tashi

Yace eh mum Ina Dad ya fita ne??

Tace ya tafi Kano yanzu

Yace yanzu da yamma haka? Lafiya kuwa??

Mum tace granny ce aka kwantar a asibiti, shine ya tafi shida Zarah Nima gobe zamu tafi

Yace Subhanallah maike damunta?? Kai ni bamma taba ji ance tana ciwo ba sai yau

Mum tace Wlh bata ciki ciwo ba, gashi wanda bai ciwo inya tashi yi bai iyaba

Najeeb yace Allah ya Sawake, nima da Ina nan Aida nabi Dad munje tare

Mum tace gobe saimu tafi da safe ai, kaci abinci ko saina zuba maka ne??

Dariya yayi tare da fad'in tunda y'ar autarki bata nan yau nine autan sai a zuba min din kawai

Mum tayi dariya tare da zuba mai, nan suka zauna suna ta fira Inda NAJEEB yace Mum yanzu nasan ina rayuwa wanda da gaba d'aya ba rayuwa nake ba

Mum tace kaman ya??..

Yace Nasan addini na, Mum da gaba d'aya Ina amsa sunan ni musulmi ne amma ban San miye addini ba, amma a yanzu Alhmdlh Nasan abubuwa da dama kuma ina kan koya

Mum cikin mamaki tace najeeb a Ina ka koya??..

Murmushi yayi tare da bata labarin abubuwan daya faru Bayan tafiyar shi

Mum wani hawaye ne ya zubo mata tare da tashi ta rungumeshi ta baya tana kuka tare da fad'in Alhmdlh Alhmdlh Alhmdlh yau nafi kowa murna yau Ina cike da farin ciki d'ana ya fara neman ilimin addini, najeeb Wlh baka ga yanda naji dad'i ba, abunda yake ranmu kenan akan muyi maka magana sai gashi kaida kanka ka Fara koya Wlh ji nake yau kamun anyi min kyauta Mafi girma a duniya

Najeeb yayi murmushi tare da fad'in Mum nima yanzu baki ji yanda nake jin dad'i ba, nasan miye rayuwa nasan yanda zan tafiyar da rayuwa domin samun tsira wanda da duk ban sani ba yanzu kam Alhmdlh

Mum tace najeeb Allah yayi maka albarka

Tashi yayi tare da kamo hannun Mum Ya ri'ke tare da fad'in mum plz ina son duk wani abu dana miki na rashin tarbiya ki yafe min, Dan Allah domin na gane da ba'a akan dai dai nake ba

Mum ta rungumo shi tare da fad'in na yafe maka duniya da lahira, Wlh najeeb komai kayi min ban taba ri'keka ba cos ni uwa ce sannan nasan duk wannan abunda kakeyi ina maka uzuri duba da irin kasar daka taso a cikinta

Wani irin hawaye ne ya zubo a fuskanshi wanda yayi sauri ya goge, lallai uwa uwace, shida kanshi yana jin kunyar abubuwan daya musu baya amma gashi yanzu tace bata rik'eshi ba, Allah sarki rayuwa duk Wanda bai mutunta iyayenshi ba yayi Asara, kun dai ga irin abubuwan da najeeb yayi amma Mum tace bata ri'ke shi ba, waye Zaima wannan inba Uwar data haifeka ba

Jin kiran sallah magrib yasa najeeb nufa masallaci

Su dad sun k'arasa Kano wajan karfe 9 da wani abu, kai tsaye asibitin suka nufa wanda koda Dr ya fito baiyi musu wani bayani akan abunda yake damunta ba, yadai ce jikin da sauk'i sannan suna kan gwaje gwaje akan abunda ke damunta, sannan har yanzu bata farka ba

Hankalin kowa ya tashi da wannan ciwon na Granny, ibtisam gaba d'aya sai kuka take, inda Zarah take ta rarrashinta, wajan k'arfe Goma Ummi tace ya kamata su tafi gida ita zata kwana da Granny....


Nan ibtisam tace ina, ita zata kwana da ita, saida ummi tayi dagaske Kafin ibtisam ta yarda harta suka wuce suda Zarah da abba inda Dad ya tafi hotel shima Bayan ya sai musu su madara ruwan roba da duk wani abu da zasu bukata sannan yaba Ummi kud'i yace ko za'a bukata

Koda su ibtisam suka je gida sai kuka take tana fad'in Wlh Ina jin tsoran wani abu ya samu granny ina matukar Sonta da yawa, Wlh baki ji yanda nake jiba na shiga uku Granny na

Zarah tace haba ibtisam babu abunda zai sameta addu'a za muyi mata, ki daina fad'in haka insha Allah komai zai wuce sannan granny zata warke Kinji

Ibtisam shuru tayi tana sauraran zarah

Zarah tace ki tashi kije kiyi wanka, kinga duk Fuskanki ya tashi idonki ya kumbura kaman wacce tayi shekaru gidan yari

Ibtisam tace hmm zarah Wlh hankalina a tashe yake ban son wani abu ya samu granny Wlh ko kad'an

Nan zarah tace babu abunda zai sameta maza tashi kije kiyi wanka Kinji

Ibtisam tashi tayi ta fad'a toilet tayi wanka, koda ta fito zarah bata d'akin can saiga zarah tazo da tea a hannunta da kazan da abba ya siya musu

Ta ajiye ma ibtisam tace gashi Nima Bari inje in had'a nawa tea din

Tashi tayi ta nufi kitchen inda itama ta had'o tea d'inta ta dawo ta Fara sha ibtisam kam kasa sha tayi

Zarah tace wai miye haka ibtisam kisha mana, ibtisam tace Wlh zarah bana son sha

Zarah tace Indai baki shaba Nima Wlh bazan shaba.....

Ibtisam tace ke nifa bana jin yunwa gwara kici

Zarah tsaki tayi tare da fad'in kinga saida safe
.ganin dagaske take yasa ibtisam fad'in zo kici Nima zanci

Jin haka yasa Zarah ta zauna tare da d'aukan cup din tea din ta farasha tare da kazan

Bayan sun kammala, itama Zarah wanka tayi tazo ta kwanta

Washe gari tunda sukai sallah asuba suka shiga kitchen inda suka d'aura abinci domin sukai asibti, Bayan sun kammala sukai breakfast suka nufi asibitin Wanda suka tarar har yanzu Granny bata farka ba ga oxygen ansa Mata.

Ibtisam hawaye ta farayi domin tausayi, taji Granny ta bata, tare da furta ciwon lokaci d'aya jiba jiya Uwar haka lafiyanta kalau amma kalla yanzu ko numfashi saida aka sa mata oxygen, kai ikon Allah, fita tayi waje tana kuka domin tausayin halin da Granny d'inta ke ciki

Zarah ce ta biyota inda ta zauna kusa da ita Tana fad'in ibtisam hakuri zakiyi kibar wannan kukan, inba haka ba kanki ne zaiyi ta miki ciwo....

Zuwan Dad ne yasa Zarah fad'in Ina kwana dad? Da fatan an tashi lafiya

Dad yace lafiya yamai jiki??

Tace da sauki

Itama ibtisam gaida Dad tayi inda yace har yanzu kina wannan kukan mamana

Ibtisam hannu tasa tare da share hawayen idonta

Murmushi Dad yayi sannan yace yauwa gwara kibar wannan kukan

Dad ya kalli Zarah yace Mum d'inki bata k'araso ba??

Zarah tace eh

Dad yace a'ah tace min fah tun d'azu sun shigo Kano bari in kirata d'auko wayarshi yayi yana k'okarin kira Zarah tace ga sunan

Nan Dad ya nufesu inda sukai gaba shida mum bayan ibtisam ta gaidata, d'ago kanta tayi sukai ido biyu da najeeb wani irin faduwan gaba taji wanda bata taba jiba sai yau, najeeb kam kallo d'aya yayi mata ya kauda kai tare da kallon Zarah yace yamai jiki hope da sau'ki??

Zarah tace toh har yanzu bata farka ba dai.....

Mum ce tazo tana fad'in ibtisam kuna ina kuzo Granny na kiranku NAJEEB kaima tawo

Da gudu ibtisam ta nufi d'akin inda taga Granny tana kallon sama hawaye na zuba a idonta, jin muryan ibtisam yasa Granny kallonta ibtisam nufan Granny tayi tana kuka tare da kamo hannunta

Granny cikin murya tana hardewa tace ina na je bu

Mum tace najeeb jeka mana

Najeeb kusa da gadon yaje inda Granny ta Kamo hannunshi Tana mishi murmushi, shima murmushin ya sakar mata, had'a hannunshi tayi dana ibtisam ta Fara magana najeeb Ina son ku kasance kaida ibtisam a haka har karshen rayuw..... Kallon mum tayi tace fad'a mishi abunda nake fad'a nan Mum ta Fara fad'a mishi abunda Granny take fad'a..... Granny tace naso inga yaranku amma Allah bai nufa ba.....

Ibtisam cikin kuka tace Granny ki daina fad'in haka dan Allah na ro'keki

Granny tace ibtisam ni nasan bazan tashi ba, wannan ciwon bazai barni ba, dan Allah najeeb ku koma ku zauna kaida ibtisam hakan zaisa koda na mutu in mutu cikin salama, wlh Ina takaicin rashin jituwan ku,, ina so kumin alkawari zaku zauna a tare har abada......

Da sauri najeeb yace I promise Granny kin gani tare da K'ara matse hannun ibtisam duk mum na fassara Mata

Granny wani irin murmushi tayi lokaci d'aya ta saki hannunsu Tana salati wanda dai dai lokacin oxygen din da aka saka mata yake k'okarin d'aukewa.......



Plz I don't tin gobe zanyi posting coz gobe gaba d'aya Ina busy sai yasa na muku yau but inna samu time may be inyi koda babu yawa









Read and leave it, dnt share to anyone*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI*

*WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN*

3138831065 Firstbank Maryam Alhassan

*SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY*

*KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI K'ARYA 2 IDAN AKA AMINCE MASA YAYI HA'INCI 3 IN YAYI ALKAWARI YA SABA, KIN DAI JI, KINCE KIN MIN ALKAWARI, IDAN KIKA SABA KIN ZAMA MUNAFUKA, KUMA WUTAR MUNAFUKI DABAN TAKE, IDAN KIKA FITAR KINMA KANKI*








Lokaci d'aya oxygen din ya tsaya cak........

Ibtisam gaba d'aya k'asa tayi ta fad'i bata san ta fad'i ba, gaba d'aya hawayen dake idonta lokaci d'aya ya tsaya cak....

Dr ne ya shigo inda ya fara dubata amma ina rai yayi halinsa, Innalillahi'wa inna ilaihirajiun abunda Dr ya iya fad'a kenan tare da fad'in Allah ya amshi rayuwarta

Zarah kuka ta saki ita dasu Mum suko su Dad da abba kukan zuci suke, najeeb kam gaba d'aya wani irin yanayi ya shiga Mai wuyan misaltuwa, lokaci d'aya hawaye ya fara zuba a idonshi lallai sunyi babban rashi a family d'insu

Ibtisam kam gaba d'aya ko kukan ta kasayi ma, zan iya cewa kaman tunaninta ya dauke Domin gaba d'aya ta daina jin komai, ita gadai ta nan ne kawai

Nan aka d'auki Granny bayan Mum ta d'aga ibtisam tare da ri'keta suka nufi Gida inda aka ma granny wanka domin kaita gidanta na gaskiya, kafin kace Mai mutane har sunji kabarin mutuwar lallai Granny tayi mutane sosai sai dai muce Allah yaji kanta lallai ciwon ajali kenan, wanda ya kama Granny lokaci d'aya ashe ciwon bana tashi bane Anata amsan gaisuwa.....

Ibtisam kam gaba d'aya ta kasa kuka, magana ba ta kasa furta komai, ganin haka yasa hankalin Mum ya tashi inda taita fad'in ibtisam kiyi kuka domin rashin kukanki akwai matsala.....

Ibtisam ido ta bita dashi tana kallonta kaman wata mara wayau yanda takeyi da idonta

Mum ganin haka yasa ta janyota jikinta tana fad'in ibtisam Granny ta rasu kiyi kuka, duk wannan abunda Mum take fad'i tana fad'a ne domin ibtisam tayi kuka amma ta'ki yi.

Koda Ummi tazo taga Mum na fama da ita akan tayi kuka amma ta kiyi kaman ma bata jin mum din, sai taji ibtisam din ta bata tausayi lallai dole tayi kuka domin kuwa ibtisam tayi mugun sabo da Granny, sunyi mugun shakuwa Sosai

Ummi itama babu yanda batayi ba amma ibtisam taki yin kuka, gaba d'aya su duka sun shiga cikin wani hali, zarah itama tayi tayi amma ta'ki kuka

Mum ta kalli ummi tace rashin kukanta Akwai matsala babba, inaga ko zan kaita hspt ne??

Zarah tace Bari dai a kira najeeb ya kaita tunda kuna amsan gaisuwa ku a nan

Zarah kiran najeeb tayi a waya ta fad'a mishi halin da ake ciki, kai tsaye yace Bari ya shigo cikin gidan

Shigowa yayi inda ya iske basa falo sai mutane wanda suka zo gaisuwa, ummi ce ta fito ganin najeeb yasa tace yauwa tana d'aki tare da nuna mai d'akin ya shiga

Koda NAJEEB ya shiga itama mum fita tayi Bayan tace ya kaita asibti, ganin haka yasa Zarah itama ta fita

Najeeb kallonta yayi gaba d'aya sai yaji ta bashi tausayi domin yasan sun shaku da Granny Sosai, gashi ta tafi ta barta bazata sake dawowa ba

Najeeb kusa da ita ya zauna tare da kallonta lokaci d'aya ya juya da ita tare da kallon fuskanta ya fara fad'in ibtisam kin tuna alkawarin da Granny tace mu d'aukar mata??  We don't love each other but we have to live together saboda munyi Mata promise, kin San bana sonki I.....

Kuka ta saki mai sauti tare da sauke idonta akanshi, wani irin abune ya tsaya mata a wuya Mai zafi

A hankali ta Fara kiran sunan Granny tare da fad'in shikenan na rasa ki, sai kuka Sosai wi wi wi......

Najeeb jin kukanta yake har cikin ranshi, Lokaci d'aya ya janyota jikinsa tare da rungumeta yana rarrashinta tare da fad'in ibtisam addu'a za muyi mata, ba kuka ba, wannan kukan baida amfani plz ki daina....

Cikin kuka tace ya zanyi??  Just muna fira nida ita ta fad'i ban taba kawo mata mutuwa ba, amma ta tafi, ban taba zaton zata mutu yanzu ba, amma gashi ta tafi ta barni, zuciya ta babu abunda take sai ciwo tare da rad'adi Innalillahi'wa inna ilaihirajiun

Ibtisam gaba d'aya ita tama manta ko wa take tare dashi, domin bata cikin yanayin da zata iya tunawa ko ganewa

Shi kam NAJEEB sai shafa mata baya yake alaman tayi shuru.....

Mum ce ta shigo d'akin domin taji shuru basu fito ba, ganin tana manne jikin najeeb tana kuka hakan yasa Mum jin dad'i tunda tana kukan

Itama Mum zama tayi a kusa data gefen ibtisam din, ganin haka yasa Najeeb tashi tare da fad'in tunda tayi kukan bari in fita waje

Tashi najeeb yayi ya fita tare da tausayawa ibtisam din

Mum ta kira sunanta da fad'in ibtisam

D'ago Kai tayi ta kalli mum wanda gaba d'aya idon ibtisam din ya canza yayi ja

Mum tace ki daina wannan kukan addu'a ya kamata ki mata domin shine babban gatan da zaki nuna mata a rayuwa, idan mutum ya mutu babu abunda yake bukata face addu'a

Ibtisam kaman an danna stop, gaba d'aya ta tsaya da kukan lokaci d'aya, inda ta kwantar da kanta akan gadon d'akin, gaba d'aya abubuwan daya faru ita da Granny taita tunawa, lokaci d'aya kuma ta Fara Mata addu'a tare da neman Allah ya gafarta mata zunubanta, lallai ibtisam taji wannan mutuwar Sosai.

Ibtisam gaba d'aya ta rame saita k'ara yin haske, fuskanta yayi fayau, Mum a gidan take kwana dad da najeeb kuma a hotel

Yau akayi sadakan uku

Ibtisam dai har yanzu ga tanan ne dai, gaba d'aya bata jin dad'in komai, rayuwa kenan, shikenan yanzu babu Granny a wannan duniyar

Sallama Dad ne da Abba da najeeb yasa ibtisam d'aga Kai tare da gaidasu ta tashi tabar falon

Najeeb da ido ya bita harta bace Mai

Shima kanshi najeeb din yayi mugun jin mutuwar Granny, wanda ya tabbata da yanzu tana nan yazo data Fara fad'a Mai magana, Allah sarki rayuwa kenan

Dad yace Yau zasu koma Abuja, dan haka saisu tashi su wuce

Abba ya kalli Dad yace zaku tafi da ibtisam, tunda mijinta yazo banga amfanin zamanta a nan ba....

Mum tace hakane duba da irin yanayin data shiga, Indai tana nan zatai ta tunani, musamman yanda ta saba da Granny kwana tare sukeyi yau ta bud'e ido ta ganta ita d'aya Abun akwai ban tausayi

Dad yace hakane tare da fad'in Ina ibtisam din ku kirata

Mum tashi tayi inda ta nufi d'akinsu ta gansu ita da zarah duka sunyi jigum babu Mai magana

Mum tace ibtisam zo ana kira

Ibtisam tashi tayi tare dasa hijab tabi Mum inda sukai falo

Bayan ta zauna, Abba yace ibtisam inaso ki shirya zaku wuce abuja yau, za Kibi mijinki ku tafi, ina son kiyi hakuri ki zamo Mai biyayya, sannan karki manta abunda mama ta fad'a kafin ta rasu....

Kuka ta farayi domin ta tuna da abunda granny tace, tana son su kasance ita da najeeb har abada.......

Abba ne ya Katseta da yake fad'in ibtisam Nima Ina neman alfarma dan Allah....

Da sauri tace Abba karka nema alfarma a wajena ka bani umarni, zanbi ni y'arka ce komai kace inyi nimai biyayya ce a gareka

Idon najeeb na kanta ya rasa mai yasa take bashi tausayi Sosai, kodan saboda halin data shiga ne oho

Abba yace Allah yayi miki albarka, ina son ki zauna da mijinki lafiya, sannan ina son ki sani shifa aure bauta ne, sannan hakuri ne, duk abunda hakuri bai baka ba, toh rashin shi bazai baka ba, Kibi mijinki sauda k'afa, domin aljannanki tana k'asan kafarshi, sannan ki kasance mace Mai rufa ma mijinki a asiri, karki zama d'aya daga cikin mata masu fad'ama kawaye sirrin miji, komai mijinki yace kiyi, toh ki tabbata kinyi indai bai saba ma Shari'a ba, sannan karki manta najeeb dan uwanki ne, idan kika ga yayi abunda ba dai dai ba ina son ki daurashi a kan hanya, wannan Abun shine kawai nake nema a gareki ina fatan zan samu

Kuka take Sosai, bata samu ta iya bama Abba amsa ba sai kukan da takeyi Mai cin rai, yanzu shikenan kaddaranta ta soma daga yanzu, domin a wannan karan tasan dole ta zauna da najeeb, duba da yadda Granny ta nemi alfarma kuma wannan itace magananta na karshe kafin tabar duniya, inda tace tana son su kasance tare har abada, yanzu shikenan gaba d'aya rayuwarta zata koma irin rayuwar da sukai baya, za suyi rayuwa irin wacce sukai da, cikin kunci da rashin ganin girman kowa, amma babu komai zanyi k'okarin in cinye wannan jarabawan insha Allah,....

Ummi ce ta katse mata tunani tare da fad'in saiki tashi kije ki had'a kayanki.

Ibtisam tashi tayi jiki a sanyaye inda ta nufi d'akinta wanda Zarah ke zaune nan ta Fara hada kaya itama Zarah tayata ta farayi, idon ibtisam yakai wajan kayan granny da sauri ta nufi wajan kayan tare da rungumo kayan Tana kuka Sosai, tana fad'in wayyo granny shikenan yanzu kin tafi kin barni, ina nan ina kewarki Mai yasa kika tafi?? Yanzu kinsa gaba d'aya bana jin dad'in komai na rayuwa kuka take Sosai tare da shessheka

Dakyar Zarah ta rarrasheta tayi shuru inda Mum ta shigo ta kira Zarah domin tazo su tafi, motar su Dad mum da Zarah suka shiga

Ibtisam kam ita da najeeb Mota daya, duka suna baya, driver ya tada motar suka Kama hanya, ibtisam naji an tada motar ta kuma sakin sabon kuka, najeeb na jinta baice mata komai ba sai wayarshi daya d'auko yasa ear piece a kunne

Ibtisam kuka take Sosai har kanta ya fara ciwo, bata san lokacin da bacci ya d'auketa ba, ta dai farka ta ganta a kwance kanta a cinyar najeeb, wanda yasa ta tashi da sauri tare da kallonshi suka had'a ido, tayi saurin kawar da kanta gefe

Murmushi yayi domin ganin yanda take Abu kaman dole an matsa mata.

Tafiya suke har suka k'arasa garin Abuja babu wanda ya k'ara koda kallon Dan uwansa balle yayi mishi magana, koda suka k'arasa masu aikin Gidan suka kwashe musu kaya, inda ibtisam kai tsaye tayi d'akin Zarah domin har yanzu kanta na Mata ciwo tana bukatar ta kwanta ta huta, tana shiga toilet tayi ta dauro alwala tazo tayi sallah tana idarwa ta hau gado sai bacci

Zarah ganin tana bacci yasa tayi dariya tare da fad'in ai dole gaba d'aya tunda akai rasuwa bata samun wani baccin kirki

Najeeb shima part d'inshi ya nufa, inda yayi toilet tare dayin wanka, da yake shi yayi sallah domin saida yasa driver ya tsaya yayi sallah, shima kwanciya yayi domin yana bukatar ya huta

Yau kwanan ibtisam Biyu a Abuja bata K'ara bari sun hadu da najeeb ba, domin kullum tana d'aki, yau Tana zaune tayi wanka tasa Wata ba'kar jallabiya tare da yafa gyalen jallabiyan yayi mata kyau duk da ita ba ma'abociya son kwalliya bace.....

Zarah ta fito daga toilet tace sai Ina haka??

Ibtisam tace ai tare zamu fita, domin zamu skul din su Ahmad ne Ina son ganinshi na tabbata bai San Granny ta rasu ba

Zarah tace hakane kam, bari insa kaya muje Toh, Suma naji ance sun kusa Fara exam, ya kusa dawowa gida

Zarah itama jallabiya ta saka amma ita nata brown, ya mata Kyau, tace ma ibtisam muje

Fita sukayi inda Zarah tace bari in fad'ama Mum samu fita, part din Mum tayi inda ibtisam ke tsaye a falon tana jiranta.....

Najeeb ne ya shigo falon kallonta yayi har zai wuce ya fasa tare da dawowa yazo gabanta ya tsaya.....

Ibtisam fat fat fat gabanta ke fad'i ga zuciyarta dake bugawa da karfi

Idon shi na kanta yana kallonta, da sauri tayi k'asa da kanta

Yace sai Ina??

Kasa magana tayi domin gaba d'aya yanzu ta rasa mai yasa take jin nauyinsa gashi yana mata wani kwarjini Sosai

Yace am asking

A hankali tace zamu skul din su Ahmad

Yace da izinin wa??

Da sauri ta d'ago ta kalleshi ganin ita yake kallo shima yasa tayi k'asa dakai da sauri

Najeeb yace ban yarda a fita ba, saida izini na, tunda zaki fita without my permission ban amince ba, and kin San hukuncin macen data fita ba tare da izinin mijinta ba??

Ibtisam shuru tayi tana jinshi, amma cikin ranta Abun haushi yake bata akan wani dalili zaice saita wani tambayeshi Bayan shi ba d'aukanta yake a matsayin mata ba....

Yace koh kina son tsinuwan mala'iku ne a kanki??

Da sauri ta girgiza kai alaman a'a

Ganin haka yasa yace so as from today duk inda zaki you have to ask me, inna yarda sai aje in ban yarda ba a zauna a gida

Ibtisam bata ce komai ba,..... Zarah ce tazo tana fad'in bros Mum ta fita ne??

Yace eh ta fita d'azu what happen??

Tace no dama zan fad'a mata zamu fita ne

Najeeb yace zaki fita da matata ba tare data tambayeni ba?? Wato ke kike son janta yawo right???

Zarah ta zaro ido tare da fad'in Wlh bros nifa Banyi niyan fita ba, ita tace in shirya in rakata, ni Wlh fitan nan dan dole zanyi ni dama zaka kaita.....

Ibtisam wani harara ta sakar ma Zarah ta gefen ido

Najeeb kallon ibtisam yayi tare da fad'in Kinji abunda tace nima inada abunyi saiku koma ciki, domin ban yarda da wannan fitan ba

Yana fad'in haka yayi part d'inshi

Ibtisam wani haushi ne ya cika ta, ji tayi kaman ta fasa ihu dan takaici, yanzu kenan duk inda zata saiya bata izini

Zarah dariya tayi tare da fad'in Kinji abunda mijinki yace saiki koma

Tsaki taja tare da hararan Zarah tayi ciki da sauri

Zarah dariya tayi tana fad'in, wannan Abun naku yana ban dariya

Najeeb koda ya shiga part d'inshi kwanciya yayi tare da lumshe ido bacci yake son yi amma ya kasa gaba d'aya sai juyi yakeyi, maganan Granny ne yake tamai yawo a kunne, ina son ku kasance a haka har abada, da sauri ya k'ara lumshe ido yana mata addu'a

Tashi yayi lokaci d'aya ya fita inda ya shiga mota tare da tada ta ya fita yabar gidan

Ibtisam na kwance gaba d'aya ranta babu dad'i domin tana son ganin k'anin Nata amma ya hanata fita

Tana nan zaune saiga Ahmad ya shigo yana fad'in sis sis

Ibtisam da sauri ta tashi Tana fad'in Ahmad, dama yau zaka dawo? Rungume juna sukayi ita dashi suna murna

Yace a'a bros NAJEEB ya daukoni yace Kece kike son ganina

Ibtisam bata san lokacin data saki murmushi ba

Zama sukayi inda zarah ta shigo d'akin Tana fad'in Toh

Please Login or Register in order to submit comment