Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sanyi cike da tausayin ibtisam din, sai take ji kaman a jikinta

Bayan Dr ya gama ya fara ce mata sorry dear, an gama.

Ibtisam kam tasha wuya idonta har yayi ja, dan azaba, an d'aure Mata hannun, wanda ana gamawa ta kwanta akan gadon wajan, babu komai cikin ranta sai tsanar NAJEEB wanda shine silan Jefata cikin wannan halin, ita ta rasa mai tamai ya tsaneta, tun Farko ta gaidashi yayi banza da ita, daka karshe ya zageta, toh miye laifinta danta kama kanta? Sannan miye na shiga sabganta har yace ta kawo mai ruwa bayan baya kulata, baya ganin darajanta, akan wani dalili zai aiketa? Lokaci d'aya ta sauke wani ajiyar zuciya tare da fad'in komai yayi min, danya ganni a gidansu ne, inda a gidanmu ne yaushe zai ganni, Bari Granny ta dawo gobe dole Zan koma Kano I..... Zarah da mum ne suka Katse Mata tunani da fad'in sannu ibtisam.

Ta kasa koda magana sai d'aga musu Kai da tayi.

Dr yace ibtisam dan yaji su mum sun kirata da Sunan, yace yanzu ya daina zafi, tunda Anyi miki alluran cire zafi, za'a baki magani, saiki kiyaye kar kiyi abunda hannun zai kuma gocewa Kinji?

Kaita d'aga mishi alaman toh

Mum ta kalli Dr tace zamu iya tafiya? Koya?..

Dr yace eh zaku iya tafiya, but tayi a hankali, zuwa jibi ku dawo sai muga hannun, kallon fuskan ibtisam yayi tare dayin murmushi yace ibtisam sai ayi tacin nama da yawa, a rage tsalle tsalle.

Ibtisam haushi Dr ya bata, waima a rage tsalle tsalle tunda ya maidata karamar yarinya ai dole yace haka.

Tashi sukayi suka fita inda zarah ta bud'ema ibtisam Mota ta shiga, sannan ta rufe, ita ta shiga gaba, mum baya, Bayan sun shiga driver yaja motar suka wuce

Koda suka isa Gida, Sun tarar da Granny da Mata har guda hud'u, ibtisam da hannu ke ciwo sakan baki tayi tana mamaki, domin kana ganin yaran Kaga y'an kauye futuk, d'aya harda yaro sai dai ibtisam tana tunanin Maman d'aya ce a cikin y'an matan, sai d'aya harda irin kalangun nan na Fulani, sauran biyun su basu da aibu sai dai sunyi yara da yawa, wanda zata ce basu wuce shekara Goma sha d'aya d'aya ba K.... Granny ce ta katse mata tunani tare da fad'in maiya sameki a hannu kuma?

Ibtisam jin haka yasa ta saki kuka, ta nufi Granny tana fad'in Granny faduwa nayi, mu tafi gida gobe

Granny tace garin yaya kika fad'i? Sannu Kinji Kai maiya samu hannun toh? Badai karaya bane?

Ibtisam cikin kuka tace gocewan k'ashi ne Granny

Su mum ko kallon matan da Granny ta Kawo ya hanata magana, tunani take badai suta kawo ma NAJEEB, ba ko waccen su tasha atamfa anyi d'inkin riga da zani, an cabe fuska da kwalli da janbaki, dinkunan yayi musu yawa, ita mai Yaron ma hannun rigan sai Zame mata yakeyi danya Mata yawa Sosai, ga falon gaba d'aya ya d'auki karni duk Kalan kamshin da yakeyi amma zuwan wannan ba'kin na granny yasa kamshin falon ya canza

Granny tace sannu takwarata maza jeki huta Kinji

Ibtisam tace toh Granny amma gobe zamu tafi koh?

Mum tace kina nan, har sai kin warke, sai sannan ibtisam tama tuna Ashe dasu mum take, sai taji kunya tare da fad'in kiyi hakuri mum wasa nake mata, ai nasan jibi zani ganin Dr

Mum tayi murmushi tare da fad'in hakane, kije ki huta Kinji, sannan ta kalli Granny tace sannu da dawowa mama, kunsha hanya.

Granny tace yauwa, hanya bakya, jikina duk yayi tsami, na gaji Sosai, ina wannan Yaron yake ne yazo ga mata nan ya zaba wacce tayi mishi

Zarah bata san sanda ta fashe da dariya ba, tare da fad'in Bari in dubashi, part d'inshi ta nufa amma bata ganshi ba, dan haka ta dawo ta shaida ma Granny da cewa baya nan, mum kam mamaki ne ya isheta, yanzu wa Innan ne NAJEEB zai aura? Lallai kam

Granny ta kalli mum tare da fad'in a basu masauki su huta, Kafin ya dawo.

Mum ta kalli zarah tare da fad'in kaisu gefen ba'ki, sannan kisa a basu abinci, Zarah tace toh tare da kallonsu tace muje, tashi sukayi suka bita inda takai su gefen ba'ki, sannan ta dawo Taba d'aya daka cikin masu aikin gidan umarni takai musu abinci suci.

Granny mi'ke k'afa tayi akan kujera, Tana zayyano ma mum bayani kaman haka, nasan cikinsu bazai rasa wacce zai zaba ba, ni Inda so samu nema ya auri Mai yaron, mijinta ya rasu ya barta da yaro dan shekara d'aya, gata marainiya, Abun dai gwanin tausayi, kin ganta duk ta tside saboda wuya, in miskili ya aureta Nasan zai ri'ke yaron tunda yana da hali, in kuma duka yake so shikenan saiya aure su, kallon zarah tayi da take ta dariya danta kasa boye dariyan ta.

Tace ku yanzu ba abun kunya bane, gid'a gid'a daku kuna gida babu aure, haba ai wannan abun yayi yawa wlh, yanzu dai Bari a d'aura ma miskili aure, ita takwara ta samu miji, ina fatan Kema kina da saurayi, in baki dashi sai in nemo miki

Zarah dariya ta saki har tanayin k'asa dan dariya, tace Granny Wlh na yafe zan zaba da kaina, dan inna baki zabi sa'an kakana zaki kawo min

Granny ta tamke fuska tare da fad'in, naga dai duk zaban da zakiyi bazai Kai wanda zan miki ba, jiba kyawawan matan dana zabo ma miskili, ku yanzu babu abunda kuka iya sai zaban maza masu shiga irin ta wa incan mutanan, bakwa zabo masu saka manyan kaya, Kema Fulani nake son ki aura yanda zaki dinga jin yaranki, ita ibtisam tana ji, tunda uwarta Fulani ce, Keko uwarki baji take ba Hhhhh Kai granny wannan maganan da takeyi duk a gaban mum takeyi

Zarah tace nikam ban son in iya wannan yaran, Kinga Bari inje in duba ibtisam inga ya take ciki, Granny itama tashi tayi tana fad'in muje Nima inga takwaran tawa, kai wannan Abu baiyi kyauba, Shigowan NAJEEB yasa Granny tsawaya.

Kallonta NAJEEB yayi tare da fad'in sannu Granny cikin gurbatarciyar hausan shi, dabai kware ba.

Granny tsaki taja tana fad'in shikenan abunda aka iya, sannu daka shi babu wani, ja'iri, ai yanzu na Kawo karshen Abun Wlh.

Najeeb kam ko kallonta bai kar'ayi yi, dan bajinta yake ba, sai dai yana d'an jin wasu kalma kad'an cikin magananta, wanda hakan ya nuna mishi cewa dashi take, dan haka k'okarin barin falon yayi tace Najeebu.... Tsayawa yayi ya tsana Tana kiranshi da wannan Sunan wai najibu, kaman wani d'an kauye, tsaki yaja tare da fad'in what Granny?

Tace kama uwarka tsaki gata a tsaye, mara kunya, kallon zarah tayi tace miye yake nufi da zat Hhhhh wai what shine zat, na daiji yace grandi, zat grandi Mai hakan ke nufi? Ko zagina yayi? Yanzu Inci uwashi

Zarah tace a'a cewa yayi miye Granny

Granny tace oho yanzu naji Batu, matsawa Granny tayi kusa dashi, wanda ya ri'ke kugu da hannunsa biyu alaman yana son ta fad'i abunda zata fad'a ya wuce, dan baya son takura irin Nata ko kad'an

Granny tace miye ka wani kama kugu? Ko dukana za kayi d'an banza, Toh Bari kaji tana mishi magana tana nuna mishi abunda take fad'a da hannu, tace aure za kayi wlh, ta rungume hannunta tare da nunashi tace Kai sannan ta k'ara rungume hannunta tace aure zakayi, na Kawo maka Mata guda hud'u ta nuna Mai da yatsa alaman, kallonta ya tsayayi sannan yace I think this old woman need to see a doctor, am sure she has mental problem.

Mum tace kana dakai kuwa, cikin harshen turanci

Granny kuka tasa Wai suna zaginta, tare da kamo zarah tana fad'in zoki fad'amin Mai sukace? Fad'amin inji.

Zarah tace Granny ba zaginka sukayi, ba, cewa yayi bai gane mai kike nufi ba, zai wuce, shine mum tace bashi da hankali taya kina mishi magana zaice zai wuce baki Gama ba.

Granny tace oho na gane, tare da cema Zarah jeki kiramin matan da nazo dasu.

Kallon Mum tayi tare da fad'in ki fad'ama wannan miskilin ya zauna, in sun fito ya zaba d'aya

Mum ta kalli NAJEEB tace ka zauna son, Granny zata maka magana.

Tsaki yayi tare da zama, yana fad'in wannan matar ta isheni Wlh.

Zarah ce ta fito da matan sun k'ara shafa ma fuskansu, kwalli da janbaki duk sunyi d'ige d'ige.

Najeeb dake zaune ta setin wajan, da sauri ya tashi yana fad'in wa innan wasu irin kazaman masu aiki kuka Kawo mum? Haba mum taya zaki kawo irin wannan yaran, plz ki sallamesu, Niko Abu suka taba bazan iyaci ba, kallon zarah yayi tare da fad'in plz tell them subar falon nan, sai wari sukeyi

Suko da bajin abunda yake fad'a sukeyi ba, duka sun saki baki suna kallonshi, domin fad'i suke Ashe bature ne, irin mamanshi, sai fari suke mishi da ido

Zarah tace bros wannan matan fah ba y'an aiki bane, Granny ta Kawo ne ka zabi d'aya ka aura.

Yace what? Wani irin kallo ya watsa ma Granny tare da fad'in you better tell them to leave, tun Kafin in illatasu tare da sakin tsaki yabar gidan ma gaba d'aya cikin bacin rai, Granny kam fadi take Ina zaka, ke Zarah kira mun dan banza.

Zarah tace Granny shifa yace ki fad'a musu su wuce tun Kafin ya illatasu

Granny tace au haka yace, zanyi maganinshi Wlh Bari audullahi yazo, wlh duka za'a d'aura mishi su zanyi maganin rashin kunya miskili mara mutunci. Kuyi manage plz na gaji sai gobe ko jibi kuma












~MARYAM OBAM~


*NAJEEB*


*BY*
*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam obam)*


*https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/*


*http://WWW.Maryamobamnovels.com*

*Wattpad@ Maryam-obam*

*Instagram@maryam_obam*



*DEDICATED TO.....*

*MY LOVELY MUM*




*PAGE 8*







Granny barin falon tayi,bayan tace ma y'an matan su koma, ta nufi d'akin zarah inda ta iske ibtisam kwance tana baccin wahala, cikin tausayin ibtisam tace sannu Allah sarki dole kiyi bacci, gocewan k'ashi akwai azaba, targad'e mutum yayi yasha azaba, balle ace k'ashi ya goce

Zarah ta shigo d'akin Tana fad'in Granny bacci take amma kina damunta da surutu.

Granny tace Hmmm, wlh tausayi taban, gocewan k'ashi akwai azaba, Allah sarki takwara, Allah ya baki lafiya, k'aran wayan ibtisam yasa Granny tace wayar Waye haka? Duba ki gani karya tasheta k'aran, zarah d'auka tayi taga kabir, tace Granny kabir ne.

Granny tace Kabiru dan arziki d'auka kiban, dannawa Zarah tayi tare da mi'ka ma Granny, Granny tasa a kunne dai dai lokacin Kabir yana fad'in my ibti, da sauri Granny ta cire wayar a kunne tana son fad'in abunda yace mi ibt, lokaci d'aya kuma ta maida wayar a kunnenta tare da fad'in Kai Kabiru grandi ce.

Gaidata yayi tare da fad'in ya Abuja?

Granny tace habuja lafiya, kasan takwaran tawa ta samu gocewan k'ashi koh? Yanzu haka bacci takeyi

Yace Subhanallah, wlh ban sani ba, yaushe hakan ya faru? Dazu nazo na ganta fah?

Granny tace Kabiru a Ina ka ganta ita da take habuja, yace Granny Nima ai nazo Abuja din

Granny tace ah lallai soyayya, toh sai kazo ka dubata inta farka, yanzu dai tana bacci, yace insha Allah Zanzo inganta tare da kashe wayan, yana tunani, wani abokinshi dake kusa Mai suna Tahir yace kabir lafiya kuwa?

Yace Wlh ibti nace ta samu gocewan k'ashi, kuma dazu mun had'u, kai Wlh banji dad'i ba, ko kad'an ban son in ganta cikin damuwa, ina sonta da yawa

Tahir yayi murmushi tare da fad'in ina matsayin amininka, komai naka kana fad'amin amma shine baka fad'amin wannan ba, Allah ya bata lafiya

Kabir ya amsa da Ameen, tare da fad'in sorry Tahir naso sai Abu ya kankama Kafin in fad'a maka, domin kasan dagaske nake

Tahir yace Toh wannan wace yarinya ce haka da Abokina ya mutu a kanta? Gaskiya ko wacece tayi sa'a, toh amma irin halin da kake son mace dashi ita tana dashi?

Kabir yace Sosai kuwa, wannan shine dalilin da yasa na K'ara Sonta, sai dai abunda yake damuna, tana da burin tayi karatu, toh ni banda matsala, infact ma Ina son iyalina suyi karatu Mai zurfi, but matsalan shine ita ta'ki yarda muyi aure wai saita kammala karatu nan da shekara hud'u, ni kuma gashi an matsa min akan ya kamata in ajiye iyali, gashi wacce nake so tace sai nan da shekara hud'u, so ni Abun ma duk ya jagula min lissafi, gashi nace mata na amince data gama karatun, kuma gaskiya ban tunanin family d'ina zasu yarda Wlh.

Tahir dariya yayi sannan yace mutumi na an fad'a love, Niko in zaka dubiya tare zamu inje inga wannan yarinyar data tafi da Abokina, Toh amma Indai har Tana Sonka zata yarda kuyi auran, ai wannan ba hujja bace mace tace saita kammala karatu Kafin tayi aure, hakan bai kamata ba, aure ai baya hana karatu, sannan tace ka jirata shekara hud'u ai yayi yawa, sai kayi ta zama haka? Ni gashi inada yaro d'aya gana cikin na biyu amma kai har yanzu kuma Nima iyalin nawa na karatu, ya kamata ka mata bayani Sosai in Tana Sonka zata yarda.

Kabir yace sai dai in wakiltaka, dariya Tahir ya saki tare da fad'in ikon Allah, wato Kai bazaka iyaba, inko hakane zaka rasata Wlh, ko ince zata shigo Ata biyu, dan Nasan Wlh baza'a Bari ka K'ara shekara biyu babu iyali ba, balle har shekara hud'u haba is too much mutumina, kabir yace kai Abokina nifa bani da ra'ayin ajiye mace fiye da d'aya, ibti ta isheni kawai, nidai na wakilta ka, kayi Mata bayani kawai yanda zata fahimta.

Tahir dariya yayi sannan yace babu damuwa, yaushe zaka dubiya, sai muje danta sanni, inta warke daka baya mayi mata maganan, koya kace?..

Kabir yace hakan yayi, sai mu shiga zuwa anjima Bayan sallah isha'i. Tahir yace Toh Allah ya kaimu

Koda NAJEEB ya fita, wani store yaje yasai giyanshi, tare da tafiya dashi, yaje ya kama d'aki a hotel, domin ya sha abunsa, tunda yake bai taba shan giya a Nigeria ba sai yau, saboda duk abunshi yana taka tsan tsan, dan baya so ya batama iyayenshi rai, koya zubar musu da Kima, uhm Najeeb kenan, baka tunanin Allah, Allah yasa mu dace,.

Koda ya shiga bud'e kwalban yayi ya fara sha, domin granny tayi matukar bata mishi rai, wai kaman shi, Najeeb za'a ce ya zaba cikin wannan kazaman matan, ido ya lumshe yaci gaba da Kwan kwadar alcohol d'inshi, lokaci d'aya ya fara surutu ni NAJEEB ni that old woman zata ma haka, ta rasa wanda zata kawo min sai wa innan dako takalmi na bazan iya basu su goge min ba, zanyi maganin wannan tsohuwar Wlh, tunda nace mata ina son aure ai dole ta Kawo min wa innan tarkacen, koda nace ina son auren ni banda ido ne K... Shuru yayi lokaci d'aya kuma ya saki tsaki tare da fad'in Wlh ta raina ni that old woman, ci gaba yayi dashan alcohol d'inshi har saida ya shanye duka kwalban sannan yayi jiba dashi gaba d'aya wani bacin ran da yakeji saiya nemeshi ya rasa, baya iya tuna komai, toh taya Zaima tuna tunda a buge yake, k'okarin tashi yayi lokaci d'aya ya fad'i akan gadon bacci ya D'aukeshi

Zarah kallon Granny tayi wacce take ta cema ibtisam sannu, tace Granny Wai yanzu wa Innan matan Najeeb zai aura? Ibtisam dake zaune hannu na Mata azaba domin alluran da aka mata na cire zafi ya gama aiki, ta d'anja tsaki mara sauti domin jin an kira sunan Najeeb din.

Granny tace kwarai kuwa, duka zansa a aura Mai su, tunda shi Dan banza ne, inko kikaga bai auresu duka ba toh a ciki ya zaba d'aya ne, ni Wlh mai Yaron nake so ya aura, yaron tausayi yake ban, duk ya fige, Kinga ya murmure Idan miskili ya auri uwarsa, zasu tafi inane ma yake aiki k'asar masu jajayen fatan nan?

Zarah ta kwashe da dariya tare da fad'in America.

Granny tace yauwa Ameka.

Ba zarah ba harda ibtisam da hannu ke Mata zugi sai da tayi dariya

Zarah tace Kai granny America ba Ameka ba, kawai kice Turai in baki iya fad'a ba

Tsaki Granny taja tare da fad'in kince Ameka, maina fad'a ba dai dai ba Ameka

Zarah dariya harda sauka k'asa tace Wlh Granny bazaki kasheni da dariya ba, kallon ibtisam tayi tare da fad'in za kiyi wanka ne In taimaka miki?

Kaita d'aga alaman eh, toilet zarah ta nufa ta Tara Mata Ruwan zafi a bath sannan ta fito ta tayata ta tashi, har toilet takai ibtisam sannan ta fito ta barta dan tayi wankan, tunda tace zata iya

Wayar ibtisam ce tayi k'ara, Zarah ta d'auka ta Fara tsokanan Kabir tare da fad'in sai kira kake tayi, toh yanzu ta tashi amma tana wani uzuri kad'an, dariya kabir yayi tare da fad'in ya hannun nata? Zarah tace da sauki, yace Alhmdlh ina kofar gida nazo in ganta.

Zarah tace ok bari inzo in shigo dakai, tare da kashe wayan, ta kalli Granny tace kabir ne yazo, Granny tace maza jeki shigo dashi.

Zarah fita tayi inda taba security umarni dasu bud'e gate, bayan an bud'e kabir ya shigo, nan suka gaisa harda Tahir, falon ba'ki takaisu Kabir ya bata ledojin kayan fruit din daya siyo da yawa, ansa tayi tare da fad'in bari in kirata, koda zarah ta shiga saida ta bada umarnin akai musu Abun tabawa sannan ta nufi d'akinta, inda taga ibtisam tana cire hijab alaman ta idar da sallah, tace Aida kin maida Kabir yana jira

Granny tace maza kije Kinji, zarah rakata, zarah ta amsa da toh, tare da taimaka ma ibtisam tasa hijab din, sannan suka fita falon ba'kin, inda an ajiyema su kabir abun taba baki, amma basu ci komai ba

Kabir yana ganin Sun shigo ya tashi tsaye cikin tausayin ibtisam d'inshi, ya fara fad'in sannu ibti, ya hannun?

Murmushi tayi tare da fad'in Alhmdlh, zarah cikin wasa tace tunda ka ganta sai a zauna

Dariya yayi tare da zama, yana fad'in baki da dama, wai yaushe abun ya faru? Zarah tace dazu Wlh, yace Kai Allah ya kyauta. Shiko Tahir tunda ibtisam ta shigo ita da zarah, idonshi ke kan ibtisam din, lallai Allah yayi halitta, dole Kabir ya nace, gata ita ba faran mace ba chocolate colour, kala Mai tsada kenan, amma kallo d'aya zaka mata kaga madaran kyau lallai inda b.... Kabir ya katse mishi tunani da fad'in Tahir ga Ibtisam fah

Murmushi Tahir yayi tare da fad'in, Malama ibtisam ya hannun? Allah ya k'ara lafiya yasa kaffara ne

A hankali tace Ameen nagode, cikin muryanta Wanda ya dashe dan tasha kuka

Kabir yace ibti wannan shine Tahir, aminina, ko ince dan uwana, danya wuce amini a wajena.

Ibtisam murmushi tayi tare da kallon Tahir Wanda idonshi na kanta tace sannu da zuwa.

Nan dai sukayi fira harda zarah, inda ibtisam duk ta gaji da irin kallon da Tahir yake mata, bini bini daka ta d'aga idonta sai su had'a ido, sai ta kauda kai, gashi tana ta setin shi, kaman Kabir yasan ta gaji da zaman ya tashi tare da fad'in za muyi magana Allah ya k'ara sauk'i, ya kalli zarah yace plz ki dinga kulan min da ita Sosai Kinji?

Zarah tace insha Allah, amma fah sai an Biyani, gaskiya

Dariya kabir yayi yace ki fad'i farashi Mai tsada in biyaki, domin my ibti komai nata Mai tsada ne, duka dariya suka sa, sannan sukai musu sallama suka wuce ba tare da sunci abunda aka kawo musu ba.

Zarah da ibtisam cikin gida suka shiga inda suka ga Dad da mum da Granny zaune akan dinning, Granny na fad'in na kawo mishi Mata har guda hud'u amma dan banzan yaron nan baka ga Rashin mutuncin da yayi min ba, toh yanzu na yanke koya auresu duka koya zabi d'aya, inko ya'ki zaba toh Wlh cikin satin nan za'a aura mishi dukansu, tunda su auransu ba irin na y'an bariki bane, babu tsada

Dad yace kiyi hakuri mama, zai zaba, ina Najeeb dinma?

Granny tace tunda yamin rashin mutunci ya fita, bai dawo ba har yanzu

Su zarah da ibtisam sannu da dawowa sukai ma Dad, inda ya kalli ibtisam yace ya hannun naki?

Tace da sauk'i Alhmdlh

Dad yace sannu mamana Allah ya k'ara sauki. Ta amsa da Ameen , mum tace kuzo kuci abinci, zama sukai akan dinning din inda zarah ta Fara zuba ma ibtisam.

Dad yana ta kiran wayan Najeeb bai d'aga ba, yace Wai ina ya shiga haka ne, sai kira nake ya'ki d'agawa

Granny tace taya zai d'aga, bayan ya gama zuba min rashin mutunci, wlh inaga aljanace ta aureshi, yaro kwata kwata baya son aure, inaga Wlh a d'aura Mai duka hud'un zaifi

Dad yace Indai sun Mai AI babu matsala saiya auresu duka.

Granny tace Aiko basuyi Mai ba, saiya auresu tunda shi ya kasa kawo wacce yake so, yanzu ni na zabo mishi, a ciki harda wani Wanda mijinta ya rasu ya barta da d'a d'aya, ni Wlh tausayi take bani, Niko bai zabeta ba inaso inna isa kasa ya aureta saboda Yaron Nata, ta k'arasa maganan cikin tausayi

Dad yace Mai yaro kuma? Toh fah sai kuma yayi shuru yana nanata maganan cikin ranshi, lokaci d'aya ya cire tunanin tare da fad'in Bari Najeeb din yazo saiya zaba, inya d'auketa Mai yaron Kinga shikenan, in kuma bai had'a da itaba sai mu bashi ita mu

Ibtisam kam cikin ranta dad'i takeji, dan d'azu taga matan da Granny ta Kawo, kuma tasan sune, wani irin murmushi takeyi na mugunta, taso sanda aka nuna ma Najeeb matan ace tana nan taga yanda zaiyi, amma ba komai zanyi ta zuga Granny Wlh, a aura Mai y'an kauye mugu kawai, saiya kashe kanshi karshen miskilanci da mugunta...




*gskya zan daina typing kullum saboda rashin sharhi, nifa bana bukatar godiya a'a sharhi nakeso inga kuna min, ta yanda zan gane kuna fahimtan sa'ko na ko a'ah, wlh saboda rashin sharhi gaba d'aya bana jin dad'in typing din, daka na Fara sai inji na gaji, amma in kuna sharhi Zan gane kuna fahimta*


*Pls masu samun sticker a whatsapp in Nayi posting ku daina, wlh da kisa min sticker gwara ki karanta baki cemin komai ba yafi min dad'i, indai kin San zaki dinga samun sticker ki ri'ke sticker d'inki bana so*

*facebook kuma ina bukatan sharhi ba thanks ba, wasu ko thanks dinma basa iya karasawa sai dai susa maka T, haba for god sake taya writers za suji dad'in muku posting kullum kaman yanda kuke bu'kata, gskya in bakwa sharhi zan daina posting kullum sai naga dama zanyi, tunda comment din da baifi 30 second ba inya dad'e minti d'aya ya gagara taya nida nake zama wajan awa biyu uku Ina typing sannan inji dad'in muku posting kullum, kunga hakan bazai yihu ba, duk da Nasan akwai masuyi Sosai so Ina magana akan masu samun thanks ko T, plz ku gyara*











~MARYAM OBAM~


*NAJEEB*


*BY*
*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam obam)*


*https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/*


*http://WWW.Maryamobamnovels.com*

*Wattpad@ Maryam-obam*

*Instagram@maryam_obam*



*DEDICATED TO.....*

*MY LOVELY MUM*




*PAGE 9*







Mum kam ita duk wannan abunda sukeyi, ita bata ganin zata yarda, " Ayi ma d'anta haka, "dan ita gaskiya bazata yarda a d'aura ma d'anta wa Innan matan ba, haba ai wannan ba adalci bane ko kad'an, "taya yaron daya taso a waje, yayi karatu a can, ace za'a aura Mai wa Innan matan, gaskiya da sake, inshi Dad yayi shuru gaskiya ita bazata yarda a cuci d'anta ba, 'In ma auren akeso yayi sai a Bari ya zaba da kanshi bawai a Kawo mishi wa Innan y'an kauyen ba, ai sai a matsa Mai ya kawo mata a aura Mai indai haka akeji.

Dad tashi yayi "yana fad'in saida safe Bari inje in huta.

Granny tace "Allah ya tashemu lafiya.

Ya amsa da Ameen sannan ya wuce "itama Mum ta tashi tabi bayanshi

Ibtisam da zarah da Granny suka rage "Granny ta kalli ibtisam "tace wai yaushe shima kabirun zai turo ne? "naji shuru ya kamata dai ya turo "musan halinda muke ciki.

Ibtisam tace "haba Granny aikya Bari in warke koh,

Please Login or Register in order to submit comment